Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

dayi son ransa har saida yaga jikinta duk ya mutu sannan ya saka bakinsa akan nipple d'inta yana tsotsa d'ayan sai cika hannu yakeyi yanata mammatsawa, dad'i ne yabi jini da sassan jikinta ta k'ara sakin jikinta tareda k'ara bank'aro masa boob's d'inta tana nishin dad'i, ganin yadda take amsar sak'onsa yasa ya k'ara k'aimi wurin zuk'ar boob's d'inta kamar jariri.

Ya dad'e yana rikita mata lissafi sannan daga baya ya fara aiki akanta babu ko sassautawa, wani irin rikitaccen zafi da rad'ad'i ne ya ziyarci k'wak'walwarta da sassan jikinta nan da nan ta saki k'ara da kuwwa amma ina Ridwan baya jinta domin ya riga yayi nisan kiwo bayajin kira, awa biyu cur yayi akanta sannan ya dawo cikin natsuwarsa hankalinsa yana dawowa ya sungumeta yayi cikin bathroom da ita.

Acan ya had'a mata ruwa masu d'umi domin ta gasa jikinta cikin ruwan ya sanyata ta zauna tana kukan takaici yana lallashinta da yaudararrun kalamansa, haka ya chanza mata wasu ruwan ta sake zama cikinsu tana hawaye sannan daga k'arshe ta gasa jikinta saida ya gasu sannan suka fito daga cikin toilet d'in, wurin wardrobe ya kaita ya ciro mata doguwar riga mai adon flowers yellow bayan ya taimaka mata ta shafa lotions sannan ta sanya rigar, chanza wani sabon zanen gado yayi sannan yaja hannunta suka fito daga cikin d'akin suka nufi parking lot, shi ya taimaka mata ta shiga cikin motarsa sannan ya juya ya koma mazaunin driver ya zauna tareda danna horn maigadi ya wangale musu get suka fice daga cikin gidan da sauri ya nufi unguwarsu Raihana..........
[12/5, 9:30 PM] Mugiratmusa66: 🛸🛸🛸🛸🛸🛸
🛸🛸🛸🛸🛸🛸
*JINKIRIN ALKHAIRI*
🛸🛸🛸🛸🛸🛸
🛸🛸🛸🛸🛸🛸

*INTELLIGENT WRITER'S ASSOCIATION*®✍🏻
[Onward together].


*WRITTEN BY MUGIRAT MUSA*


*PAGE 8*


Suna isa bakin k'ofar gidansu Raihana ya parker motarsa ya kalleta cikin lallashi yace"kiyi hak'uri kinji babyna kada ki bari Inna ta gane yanayin tafiyarki ya chanza ,ki daina kuka da sannu zaki samu lafiya sonki ne ya rufe mini idanu na aikata miki haka".Raihana ta sanya tafin hannunta ta share hawayenta tsab tace"ni bawai abinda kayimin bane yake sakani kuka a'a ina gudun ne ka k'ini kace ka fasa aurena bayan ka sanni d'iya mace".Kallonta yayi cikin k'auna yace"ki daina saka damuwa aranki baby indai nine ki daina shakku akaina bazan tab'a cin amanarki ba! Idan na cutar da rayuwarki nida ubangiji shi zai miki sakayya tun anan duniya kafin muje lahira".Raihana tayi ajiyar zuciya tareda sakar masa murmushi tace"har kasa hankalina ya kwanta yanzu".
Ridwan ya lumshe idanunsa yace"bakida damuwa muddin muna tare da juna ki fita kije bayan boot ki d'auki kayanki so nake in tafi gida"."OK ba matsala nagode sosai ubangiji Allah yabar zumunci da k'auna"."Amin baby".
Raihana ta fito daga cikin motar direct bayan boot ta nufa ta ciro ledar sannan ta rufe boot d'in,d'aga masa hannu tayi alamar bye bye 👋 shi kuma yaja motarsa ya fice daga bakin k'ofar gidan yayi gaba, saida taga b'acewarsa sannan ta juya ta nufi cikin gidansu tana tafiya tana cize baki alamar k'asanta yana mata ciwo haka ta daure tana game k'afafunta domin kada Inna Zulai ta fahimci abinda yake faruwa.

Tana isa tsakiyar gidan ta hango Inna Zulai ta shik'ar shinkafa jin tafiyar mutum yasa ta waigo da sauri idanunta suka fad'a cikin na Raihana, ganin leda ahannunta yasa ta aje kwanon da take amfani dashi k'asa ta iso wurin Raihana farin ciki k'unshe afuskarta tace"Raihana sannu da zuwa har kin dawo?".

Raihana ta zauna saman tabarma dak'yar tana cize bakinta tace"yauwa Inna ina Rayyanatu take ne?".

Inna Zulai ta yamutsa fuskarta ta iso wurin Raihana ta zauna tace"shegiyar tana cikin d'aki tun safe batada lafiya sai kwara amai takeyi zad k'azanta kila ma ciki ne da ita ta kwaso awaje".

Gaban Raihana ya bada rasss hankalinta yayi k'ololowar tashi zuciyarta ta tsinke! Amma saita tattaro dauriya da hak'uri ta sanya azuciyarta tace"haba Inna ina Rayyanatu take zuwa bale ta kwaso ciki itada ko saurayin kirki batada ina ganin rashin lafiya kawai ne yake damunta?".

"hmmmmm bakisan halin yarinyar nan ba shiyasa kike fad'in wannan maganar, amma ki zuba idanu kiyi kallo wata rana kina zaune za'ace miki ciki ne da ita! Aiko mahaifiyarta Basira kafin Mustapha ya aureta saida aka cire mata cikin shege sannan akayi aurensu!"..

"da gaske kike fad'a Inna ko kin fad'a ne domin kiji dad'in bakinki!?".

Inna Zulai ta karkarce kai tace"kina tsammanin zanyi miki k'arya ne ko kuwa kin fini son k'anwata ne?Saboda haka ki daina yimin wasu irin tambayoyi haka".

"afuwan Innata ubangiji ya huci zuciyarki bari kiga kayayyakin da Ridwan ya siyomin".Cewar Raihana tareda bud'e ledar tana fitarda kayayyakin d'aya bayan d'aya tana ajiyewa a k'asa.
Inna Zulai sai d'aukar kayan takeyi tana murmushin jin dad'i saboda ita mace ce mai tsananin kwad'ayi da son abin duniya, jijjiga kanta kawai takeyi tace"kayan sunyi k'yawo gaskiya kinyi dace da masoyi amma ya kamata kice ya turo magabatansa asa muku ranar aure ko ya kika gani?".

Raihana tayi yak'e tace"karki damu Inna zan gaya masa amma mu bari ya ida k'arasa gidansa sannan in bijiro masa da maganar aure".

"wannan shawarartaki tayi gaskiya to mu bashi lokaci har ya kammala gidansa lokacin hankalinsa yafi kwanciya ayi komai atsanake".

Raihana ta langwab'e kanta tace"wannan gaskiya ne".
Firarsu suka cigaba dayi kamar k'awayen juna yayinda Rayyanatu take kwance cikin d'aki batada lafiya sosai, tana jin yadda Inna Zulai ke k'agawa mahaifiyarta sharri da k'azafin tayi cikin shege hawaye masu zafi sai shatata sukeyi afuskarta zad tausayi wani irin tururin d'aci da bak'in ciki ne ke yawo cikin k'wak'walwarta da sassan jikinta.
__________________

Tun lokacin da Ridwan ya fara saninta d'iya mace yaji dad'inta to tun daga lokacin data warke ya mayarda ita abar hutawarsa, tun bata saba ba har ya zamana ta saba tana jin dad'in harakar har takai wata rana da kanta take iskosa cikin gidansa suna aikata masha'arsu son ransu.

_Allah ubangiji ya karemu da afkawa cikin tarkon nadama da dana sani ya kuma tsare mana imaninmu._

Haka rayuwarsu ke gudana cikin shek'e ayarsu da biyawa junansu buk'ata,yayinda iyayenta basuda labarin abinda take aikatawa tana samo kud'i tana kawowa mahaifiyarta, dayake Inna Zulai k'wak'walwar kifi gareta bata tunanin a ina d'iyarta ke samo kud'i ko tayi tunanin wata rana ta tuhumeta waye yake bata mak'udan kud'i haka?Bata tunanin mi Raihana keyi tana samo kud'i haka tana kawo mata, babu ruwanta itadai muradi dai akawo mata kud'i tana cin kayayyakin dad'i, shidai Baba Iliyasu harakokin gabansa yakeyi duk abinda Raihana takeyi itada uwarta ya kawo idanu ya sanya musu tunda ya fahimci bason nasiha sukeyi ba ,Rayyanatu kawai yake bawa kulawa tareda nuna mata tsantsar soyayyar gaskiya saboda shi tausayi take bashi matuk'a fiyeda misali.

Wata rana Baba Iliyasu yaga wata bazawara anan cikin unguwarsu mai suna Lauratu yaji ya kamu da matsananciyar soyayyarta kuma yana buk'atar mai bashi kulawa domin Inna Zulai kwata kwata bata damu da damuwarsa ba, banda ta samu kud'i d'iyarta ta auri hamshak'in mai arzik'i babu abinda ta sawa gaba, baiyi k'auron baki ba wurin bayyanar da ita yana sonta da aure ba itama dayake tasan Iliyasu mutumen kirki ne, bata tsaya b'ata lokaci ba ta gabatar dashi wurin iyayenta amatsayin wanda takeso iyayenta su amsheshi hannu bibbiyu tareda bashi umurnin ya turo magabatansa asa ranar aure.
Yana komawa gida ya turo magabatansa asaka rana sati uku masu zuwa nan da nan aka yanke musu sadakin Lauratu dubu talatin suka biya, sannan sukayi ciye ciye da lashe lashe suka rankayo suka dawo gida tareda sanar dashi duk abinda ake ciki, Baba Iliyasu yayi matuk'ar farin ciki da kalamansu tareda yi musu godiya suka wuce gida, ya k'udurta bazai gayawa Inna Zulai labarin aurensa ba saidai taji daga sama yasan ta haka ne zatafi jin haushi da rad'ad'in aurensa .

Itadai Inna Zulai babu abinda ta fahimta duk da taga Baba Iliyasu yanata shirye-shiryen gyaran d'akin dake gefe cikin gidan wanda suke ajiye tukane da kwanoni, taga yasa angyare d'akin tsab tareda yi masa plaster amma dayake bata sa ran zaiyi mata kishiya ba shiyasa batayi tunanin zai k'ara aure ba, hidimomin gabanta ta cigaba dayi itada Raihana suna cin abinda ransu keso tareda saka irin suturar da suke ra'ayi domin Ridwan ba k'aramin kud'i yake sakarwa Raihana ba ganin yana morar jikinta yadda yakeso akowane lokaci akodayaushe.

*BAYAN SATI BIYU DA UKU*
Ana saura kwana hud'u rak ad'aura auren Baba Iliyasu da Lauratu har yanzu Inna Zulai batada labarin auren ko amak'wabta,tun safe Baba Iliyasu bai zauna yana can kasuwa yana yiwa kansa sayayyar kayan sawa shida su Rayyanatu, shadda kala biyar ya siyo kansa yadi kala uku sannan ya siyowa Inna Zulai atamfa kala uku lace biyu Rayyanatu itada Raihana ya siyo musu atamfa bibbiyu da lace d'ad'd'aya, direct wurin telensa ya nufa ya bashi d'inkin kayayyakinsa duka nasu Inna Zulai ya nufo hanyar zuwa gida dasu.
Dayake Raihana ta fita tunda safe tana can gidan saurayinta Ridwan yana aikata abinda ya gadama da ita, Rayyanatu kawai ce cikin d'aki zaune tana tilawar karatun qur'ani mai girma tana tunanin mahaifiyarta data rasu ashekarun baya hawaye masu zafi sai sintiri sukeyi afuskarta wani irin zogi zuciyarta keyi zaune take sanye da hijabi black colour.

Inna Zulai fita tayi daga cikin gidan ta shiga cikin gidan k'awarta Inna Abu wadda ita kad'aice Inna Zulai ke shiri da ita kaf unguwarsu saboda kowa yasanta da rashin mutunci da mugun bak'in hali,tana shiga ta hango Inna Abu zaune sai zabgar lomar tuwo takeyi tana lasar baki kamar *MAYYA CE* 😅.

Inna Zulai ta k'araso wurinta tareda cire takalminta ta zauna wurinta tace"Abu barka da zama gida ya yau? ".
Saida takai lomar tuwo abakinta tace"yauwa Zulai uwargidan Iliyasu ".Ta fad'a azolaye.

Inna Zulai ta bintsire baki tace"fad'i ki k'ara fad'a nice guda ba k'ari".

Inna Abu ta bushe da dariyar mugunta harda rik'e cikinta akan dariyar k'eta can ta tsagaita dariyar tace"kinji ki da wani shirmen magana bakida labarin abinda yake faruwa acikin gidan mijinki kinzo kinata cika bakin banza".
"ba wani cika baki sai gaskiya bayan ni kin tab'a jin Iliyasu ya k'ara aure ne sannan mi yake faruwa cikin gidan mijina wanda bansan dashi ba? ".

"lallai Zulai bansan bakida wayo ba sai yanzu to bari in gaya miki abinda bakisan dashi ba ki bud'e kunnuwanki ki saurara da k'yau malam Iliyasu mijinki kwana hudu ne kawai ya rage masa ya angwance shida amaryarsa Lauratu! ".

Duuummm Inna Zulai taji gabanta ya fad'i zuciyarta ta girgiza kanta ya k'ulle ta kalli Inna Abu cikin kad'uwar maganarta tace"anyah da gaske kike fad'a Iliyasu Sam bazai tab'a iya yimin kishiya ba!? "."Zauna nan Zulai k'arya nake miki amma ranar assabar itace ranar da Iliyasu zai d'aura aure kina ji kina gani babu abinda zaki iyayi saboda bakin alk'alami ya riga ya bushe! ".Inna Zulai ta jijjiga kanta alamar maganar ta soki k'ahon zuciyarta tace"idan na binciko k'arya kikeyimin ki sani zamu samu babbar matsala".Inna Abu ta banka mata uwar harara tace"je ki tambayi munafukin mijinki kiji abakinsa idan ba aure zai k'ara ba".

Inna Zulai ta mik'e zumbur kamar wadda aka tsikara tace"idan ko gaskiya ne abinda kika fad'a za'ayi balbalin bala'i bisa kwakciyar masifa agidan nan wallahi! Daga amarya har wad'anda suka kawota duk saina k'onesu da ransu".Tana k'arasa maganarta taja k'afafunta fuuuuuu kamar zata tashi sama akan kumburi da bak'in cikin auren da baba Iliyasu zai k'ara, ganin Inna Zulai ta wuce yasa Inna Abu ta sake fashewa da muguwar dariya tace"shashasha kawai idan banda kina mahaukaciya wake bugun gaba azamanin nan yace mijinsa bazai masa kishiya ba sai irin masu k'arancin tunani iirin naki".Tana rufe bakinta ta cigaba da ayyukanta na gida tana nasa abubuwa da dama cikin zuciyarta...........
[12/6, 3:20 PM] Mugiratmusa66: 🛸🛸🛸🛸🛸🛸
🛸🛸🛸🛸🛸🛸
*JINKIRIN ALKHAIRI*
🛸🛸🛸🛸🛸🛸
🛸🛸🛸🛸🛸🛸

*INTELLIGENT WRITER'S ASSOCIATION*®✍🏻
[Onward together].


*WRITTEN BY MUGIRAT MUSA*


*PAGE 9*



Inna Zulai da tana tafiya idanunta har rufewa sukeyi akan tsabar masifa da zogin dake cin zuciyarta dak'yar ta samu ta iso tsakiyar filin gidan, zaune saman tabarma ta hango Baba Iliyasu turamen zannuwa jibge agabansa tana isa wurinsa zuciyarta cunkushe da tsantsar tashin hankali da takaicin rayuwa tayi tsaye jugum babu alamun fara'a afuskarta, ganin haka ne yasa Baba Iliyasu ya bud'i baki yace mata cikin lalama"bismillah Zulai zauna mana kinyi tsaye kiga abin arzik'in da muka samu".

Inna Zulai ta d'aga murya tace"abin arzik'in da muka samu ko ka samu bak'in munafuki azzalumi! Kana zaton duk k'ulle -k'ulle da makircin da kakeyi ne baya dawowa kunnena?".

Baba Iliyasu yayi jugum cikin matuk'ar mamakin zancenta huci yayi mai tattare da bak'in ciki yace"subahanillah!Zulai duk mi ya kawo haka da zaki jefeni da wad'annan mummunan kalmomi! ?".
Inna Zulai ta banka masa harara tace"ai kasan irin munafurcin da kake k'ullawa yanzu kayi tunani da kanka Iliyasu eheehhh kuma daga yanzu ka k'ulla abota da masifa da tashin hankali acikin gidan nan! Babu kai babu kwanciyar hankali har abada ".
Baba Iliyasu ya b'ata fuska yace"kinga banason shirme ki fito fili ki gayamin munafurci da k'ulle -k'ullen da nakeyi miki Zulai banason rainin wayo da sakarcin banza".
"karkaso sakarcin banza ai duk abinda nayi maka kaine silar faruwan haka, saboda haka bakada wata kima da daraja a idanuna".
Baba Iliyasu ya sassauta murya tareda b'oye b'acin ransa yace"kisan irin kalaman da zasu fito daga cikin bakinki Zulai domin kinsan ni mijinki ne abu kad'an zaki fad'a wanda zai iya jefaki cikin wutar jahannama, saboda haka ki kiyaye ki daure ki gayamin abinda nayi miki in baki hak'uri".

"tun yanzu kazo ka jefani cikin wutar jahannama idan kaine da ita, tabbas Iliyasu ka nunamin halinku na maza ka tabbatarmin da cewa ku maza bakuda tabbas! Yanzu ka rasa abinda zaka sakamin dashi sai kishiya lallai ka nuna kai butulu ne".
Murmushin dake k'ayatar da fuskarsa yayi yace"yanzu duk akan zan k'ara aure ne kike tayarda hankalinki haka? Haba Zulaihata ki kwantar da hankalinki har abada bazan tab'a cin amanarki ba zanyi k'ok'ari in daidaita adalci atsakaninku".

Inna Zulai ta firfito da idanunta awaje tace"ashe da gaske ne aure zaka k'ara nan da kwana hud'u!?".

Baba Iliyasu ya jijjiga kansa alamar haka ne sannan ya dubeta cikin matuk'ar tausayawa yace"tabbas k'arin aurena gaskiya ne Zulaiha amma banyi haka bane domin in b'ata miki rai ba nayi haka ne saboda in raya sunnar ma'aiki annabinmu Muhammad (S. A. W) ".

Hawayen takaici suka wanke fuskar Inna Zulai wani irin zogi da k'una zuciyarta keyi wani irin abu ya tokare mata a k'irji, ji takeyi gwamma mutuwarta da wannan bak'in labari daya risketa nadama da bak'in ciki ne ya shige cikin zuciyarta zama guda tace"hmmm babu abinda zaka gayamin wanda zaisa zuciyata tayi sanyi Iliyasu ka riga ka nunamin banda wani matsayi azuciyarka tunda har ka nemi aure baka gayamin ba saida naji awurin shanun tallah, haka kake ik'irari da tutiyan zakayi adalci atsakaninmu tun yanzu kafin ta shigo ka fara nunamin tsantsar rashin adalci dama yawancin maza haka kuke da kunyi sabon aure kun mayarda matarku ta farko banza bola shara! Amma inason ka sani tunda har zaka k'ara aure duk abinda ya faru cikin gidanka kaine domin baka d'auko hanyar dazai sa azauna lafiya ba".

Baba Iliyasu ya bud'i baki yace"kiyimin afuwa Zulaiha nasan ban k'yauta miki daban sanardake zan k'ara aure ba kinsan d'an Adam mai aikata kuskure ne arayuwa, saboda haka kiyi hak'uri ki bani dama mu fahimci junanmu".

"babu wata fahimtar da zamu yiwa juna saboda ka riga ka dab'amin wuk'a azuciya".

Ganin yayi yana lallashinta tana botsarewa shiyasa yayi ajiyar zuciya yace"to tunda bak'ya jin lallashina ga turame uku da lace biyu ki d'inka ki sanya aranar biki".

"ka ajiye kayanka banaso saboda ba kaga nayi maka kamada mara sutura ba! ".

Baba Iliyasu ya d'auki sauran kayansu Raihana zai shige cikin d'akinsa ya adana ya waigo ya kalleta yace"ga kayanki abakin k'ofarki nidai na fitar da hak'k'inki ubangiji ya sani idan kin gadama ki k'ona babu abinda ya shafeni! ".Yana kammala maganarsa yayi shigewarsa cikin d'akinsa.

Hawayen takaici da zafin kishi ne suka gangaro afuskar Inna Zulai tana sharewa k'asan zuciyarta sai k'una da ciwo yakeyi mata, cikin matuk'ar b'acin rai ta kwashi turamen daya bata ta jefasu tsakiyar gadonta ta cigaba dayin rikitaccen kuka mai tattare da bak'in ciki da tsananin tashin hankali, ta jima zaune tana kuka saiga Raihana ta shigo cikin d'akin ba ko sallama ganin mahaifiyarta tana zubar da kwalla yasa hankalinta ya d'unguma zuciyarta ta tsinke! Ta isa wurin Innarta da sauri fuskarta k'unshe da damuwa tace"lafiya Inna mi ya sameki kike kuka?".

Inna Zulai ta d'ago idanunta wad'anda suka kumbura akan yawan kuka sunyi jajir dasu wani irin abu mai matuk'ar d'aci ta had'iye a mak'oshinta tace"Babanki ne zai k'ara aure nan da kwana hud'u kinga turamen daya siyomin gasunan aje saman gado".Ta nuna mata inda turamen suke ajiye.

Mayarda kallonta tayi ga turamen sannan ta juyo ta kalli mahaifiyarta atsanake cikin matuk'ar b'acin rai tace"ki daina kuka Innata wannan aure da Baba zaiyi bazai rageki da komai ba, idan muka lura matarsa batada mutunci inhar auren ya tabbata nayi miki alk'awarin zamu bi duk hanyar data dace mu fitar da ita daga cikin gidan nan ko ta halin k'ak'a".

"kina nufin inbarsa yayi aurensa kenan kina nufin zaki bani had'in kai idan har ta shigo cikin gidan nan da mugun nufi?".

Raihana ta jijjiga kanta alamar eh mana sannan tace"kefa mahaifiyata ce aduniya banda wanda yafi ki zan iya sadaukar da nawa farin ciki akan naki, saboda haka ki cire komai azuciyarki Inna ki cigaba da sha'anin gabanki".

"zan daure in gani ko zan iya cire komai azuciyata amma kishiya tanada matuk'ar ciwo da zafi azuciya Raihana, ni kaina bansan inada bak'in kishi ba sai yau ".

Raihana ta dafa kafad'arta tareda rik'e hannunta d'aya ta nisa tace"haka ne lamarin duniyar sai hak'uri da kawaici Inna duk abinda yake faruwa ki sani *RAYUWA CE* wata rana sai labari".

Inna Zulai tace"maganarki gaskiya ne ubangiji yayi mana jagora".

"Amin amin Innata".
____________________

*BAYAN KWANA HUD'U*

Aranar Assabar aka d'aura auren Iliyasu Hussaini da amaryarsa Lauratu Dauda akan sadaki dubu talatin lak'adan dubban mutane suka shaida d'aurin aurensu, mutane sun taru birjik ko'ina abakin k'ofar gidansu Lauratu anyi taro lafiya an watse cikin k'oshin lafiya mutane kowa ya kama gabansa.
Ab'angaren Inna Zulai zo kuga bak'in ciki da takaici ne shimfid'e afuskarta yayinda wani irin tururin d'aci da zogi ne ke yawo cikin k'wak'walwarta da magudanar jikinta, dak'yar take danne abinda yake cikin zuciyarta tana maraba da mutane Inna Abu babbar k'awarta ita ke dannar k'irji tana bata maganganu masu sanyi da sanyaya zuciya, haka dai suka cigaba da hidima da tarbon mutane har suka fara watsewa suna zuwa gidansu Lauratu amarya ganinta.

Da dare misalin k'arfe 8:30 aka kawo amarya Lauratu gidan mijinta Iliyasu mace biyar ne suka rakota gidan mijinta, sun d'an zazzauna suna kallon gado da kujerun d'akin sannan suka fito suka nufi d'akin Inna Zulai suka gaisheta adak'ile ta amsa musu fuska k'unshe da walwala, cikin zuciyarta haushi da takaicinsu duk ya mamaye mata zuciya haka dai ta daure suka gaggaisa sannan sukayi mata saida safe tayi musu rakiya har waje, saida taga sun fice sannan ta juyo ta dawo d'akinta cikin matuk'ar b'acin rai da bak'in cikin wannan aure.

Inna Zulai kasa runtsawa tayi cikin dare sai juye juye takeyi hawayen takaici sunata shatata afuskarta, Raihana barcinta kawai takeyi hankalinta kwance babu abinda yake damunta dak'yar Inna Zulai ta samu barci ya saceta koshi sai kusan k'arfe 3:00am na dare, ab'angaren Baba Iliyasu ya gwangwaji amarcinsa shida matarsa Lauratu aranar ya tabbatar yayi sabon aure, domin ya tsinci kansa cikin wata duniyar mai wuyar fassaruwa nan da nan yaji k'auna da tsantsar soyayyar Lauratu ya k'ara yawaita azuciyarsa, rungume da juna suka kwana suna masu jin dad'i da farin cikin kasancewarsu ma'aurata.

Washe gari da safe kusan tare suka tashi sukayi wanka sannan Lauratu ta shiga cikin kitchen domin ta had'a musu karin kumallo, yayinda Baba Iliyasu yake zaune saman gadonta yana murmushin farin ciki da tsananin nishad'i acikin ransa.

Lauratu tana kitchen zaune har ruwan zafin sun tafasa ta juye aplask k'ok'arin kashe wutar murhun takeyi saiga Inna Zulai ta shigo kadaran majaran cikin kitchen d'in, ganinta yasa Lauratu ta noce kanta k'asa tace"Ina kwana".

Inna Zulai ta banka mata harara tace"da ban kwana ba k'ya ganni tsohuwar karuwa munafuka!".

Jikin Lauratu yayi matuk'ar sanyi saboda ita arayuwarta ta tsani tashin hankali da fitina cikin sanyin murya tace"ubangiji Allah ya baki hak'uri".

"da hak'uri ta mutu sadakar nawa kika bani!? ".

Lauratu tayi shiru jikinta ya mutu bata sake cewa uffan ba ta mik'e tsaye zata wuce ta gefenta kenan Inna Zulai ta sanya hannu ta jawo bayan rigarta cikin son fitina tace"ina zaki bak'ar bazawara k'are dangi!?".

Lauratu ganin walak'anci da rainin wayon Inna Zulai ya wuce gona da iri dole yasa ta b'anb'are hannunta ajikinta tace"ki daina shak'emin wuya malama".
Inna Zulai taja tsoki mtssss tace"na shak'e miki wuya mi zakiyi ?Ke nifa na haifi kamarki saboda haka babu wata buro ubar da zakiyimin in k'yaleki !".
"naji bani wuri in wuce angona yana can d'aki yana jirana".

"babu inda zakije muna nan atare".

Lauratu ganin tayi tayi ta bari ta wuce tak'i barinta yasa ta d'aga murya da k'arfi cikin kissa tace"maigida!Maigida!!Macijiiiiiii..... ".Jin kuwwar amaryarsa yasa Baba Iliyasu ya shek'o da gudu daga shi sai guntun wando dayake har ya cire tufafinsa saboda yasha iska.

Yana isowa wurinsu yaga sunyi tsaye cirko cirko yaja ya tsaya turus yana k'are musu kallon tareda sakarwa Lauratu murmushi yace yana waige waige"amarya lafiya naga kunyi tsaye ina macijin yake ne!? ".Lauratu ta zumb'ura baki tareda langwab'e kanta tace"Anti ce nayi nayi da ita ta bani hanya in fice daga cikin kitchen tun d'azu tak'i shine ni kuma na buga kuwwa domin kazo kayi mata magana ta bani hanya in wuce".
Baba Iliyasu ya mayarda kallonsa wurin Inna Zulai cikin matuk'ar b'acin rai yace"Zulaiha haka ne abinda ta fad'a gaskiya ne ko k'arya ne? ".Inna Zulai ta kauda kanta gefe cikin son fitina da tsantsar tashin hankali tace"eh mana abinda ta fad'a babu k'arya acikinsa gaskiya ne Iliyasu".Ta fad'i sunansa gatsau babu ko girmamawa da sanin darajar miji duk dayake ba yau ne karo na farko ba da take ambaton sunansa............
[12/6, 3:20 PM] Mugiratmusa66: 🛸🛸🛸🛸🛸🛸
🛸🛸🛸🛸🛸🛸
*JINKIRIN ALKHAIRI*
🛸🛸🛸🛸🛸🛸
🛸🛸🛸🛸🛸🛸

*INTELLIGENT WRITER'S ASSOCIATION*®✍🏻
[Onward together].


*WRITTEN BY MUGIRAT MUSA*


*PAGE 10*



Baba Iliyasu yayi nannauyar ajiyar zuciya ya sake kallon k'wayar idanun Inna Zulai yace cikin lalama da lallashi"to uwargida ayi hak'uri aba amarya hanya ta wuce zuwa d'akinta kinga tun d'azu nake jiranta tazo ta bani karin kumallo yunwa nakeji".Inna Zulai ta yamutsa fuskarta cikin nuna isa da tsantsar gadara tace"babu inda zataje muna anan tsaye da ita"."Bangane manufarki ba Zulaiha so kike yunwa ta illatani ne? Dan girman Allah ki jaye ta wuce nifa banason tashin hankali da rashin gaskiya arayuwata! ".Inna Zulai ta murgud'a baki kamar k'aramar yarinya tace"ni kuma idan ba'ayi tashin hankali ba fa ba dad'i nakeji ba gaskiya".
Ganin yana bata magana da lallashinta tana botsarewa shiyasa Baba Iliyasu yasa hannu ya jayeta da k'arfi agefe, cikin tsananin hasala da suk'uwa yace"Zulaiha bazan dauk'i rainin wayo da walak'anci acikin gidana ba saboda haka ki chanza salon tafiyar da rayuwarki idan ba haka wata rana zan baki matuk'ar mamaki!".Yana k'arasa maganarsa yaja hannun Lauratu suka fice daga cikin kitchen d'in suka nufi d'akin Lauratu.

Ganin walak'ancin da yayi mata ne yasa tayi tsaye k'yam idanunta suka cicciko da kwallar zallar takaici, wani irin tururin d'aci da bak'in ciki ne ya gauraye sassan jikinta da magudanar jininta ajiyar numfashin bak'in ciki tayi, sannan tasa hannunta ta share hawayenta tsab ta fice daga cikin kitchen d'in ta nufi d'akinta, duk diramar da akeyi sai akunnen Rayyanatu tana cikin d'akinta tana jiyo duk abinda yake faruwa wani irin sanyi takeji azuciyarta ganin Inna Zulai ta samu daidai da ita wurin kissa da makirci, Raihana kuwa bata cikin gidan tunda tayi sallar asuba tayi wanka ta fita yawon gantalinta wurin saurayinta Ridwan yana morar ni'imar jikinta.
____________________

Zaune suke manne da juna bayan sun kammala aikata masha'arsu itada Ridwan, tana rungume ajikinsa sai shafarta yakeyi yana shinshinar k'amshin turarenta sai can ta bud'i baki tace"heartbeat ya kamata ace tunda ka
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment