Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

RIJIYA GABA DUBU
Littafi na daya 1
Na Abdulaziz sani m gini
Ebook publish by - http://hausaebooks.cf

Typing:- Ibrahim S combatant
Post:- Shuraih Usman
@Shuraih 99%
Part 1A
.
Saurayin gudu yake iya karfinsa acikin dajin domin ya
ceci rayuwarsa,
.
yana gudu yana waigen bayansa cikin
tsananin tsoro,amma baya ganin komai kuma baya
jin sautin komai face na masifaffun karnukan dake
biye dashi.
.
Su dai wadan nan karnuka sun kai guda saba in da
doriya kuma sun kasance jibga jibga tamkar ba
karnuka bane kai kace kurayene sabo da girmansu da
kwarjininsu gami da ban tsoro,musamman aka
kiwata wadan nan karnukan kuma aka basu horo na
musamman domin suyi gadin babban kurkuku na
birnin Kisra.
.
A tarihin birnin na kisra tunda aka gina kurkukun
tsawon shekaru arba in ba ataba samun fursuna da
ya taba guduwa daga cikin sa ba sabo da karfin
tsaron da ke cikinsa sai wannan saurayi wanda ake
kira IMHAL IBN IMZANU,
.
sabo da tsananin karfin
gudun Imhal ne ya baiwa karnukan tazara ta kimanin
taku sittin amma sabo da nacin karnukan da mugun
horon da suka samu sai gashi sun fara hango shi,nan
fa suka kara kaimi,nan fa Imhal ya kara kaimin
gudunsa alokacin da ya waigo ya hango su yaci gaba
da falfala azababben gudu ta cikin kwazazzabai da
sarkakiya,
sabo da karfin gudun ma har tashi sama
yake yana tsallake duwatsu da karyayyun bishiyoyin
da suka fadi kasa
.
Shi dai Imhal gudun kawai yake yi acikin dajin amma
baisan inda yake dosa ba,sabo da baisan ma a inda
yake ba bare ma yasan hanyar da ya kamata yabi, a
duk sanda ya tuno da bakar wahalar da ya sha kafin
ya sami nasarar guduwa daga kurkukun sai ya kara
kaimin gudun nasa yana mai ayyanawa a ransa da dai
a kamasa a raye a mai dashi cikin kurkukun gwara a
sami gawarsa sabo da azabar da take cikin kurkukun
ta wuce tunanin mai tunani.
.
Asalin Imhal bin Imzanu mutumin birnin misira ne
kuma shi ba dan kowa bane kuma bai aikata laifin

komai ba,mahaifinsa wani makiyayi ne mai kiwon
dabbobi a daji,don haka rayuwar Imhal gaba daya a
cikin daji take,sai dai a karshen kowane sati ranar
Lahadi sukan shiga cikin gari suyi dan siye-siyen su
sannan su koma daji inda suka gina bukkarsu.
.
Imhal ya taso da Jarumtaka juriya da iya
farauta,sanan komai yawan dabbobi idan ya tafi kiwo
dasu yana iya sarrafa su
.
Lokacin da Imhal ya fara girma ya cika shekaru goma
sha shida ne ya tambayi mahaifinsa tsoho Imzanu
yace ya kai Abbana me yasa baka taba bani labarin
mahaifiyata ba?ban santa ba kuma bansan yanda
akayi ta mutu ba kullum sai kace dani kawai mutuwa
tayi,kayi sani cewa yanzu ni ba yaro bane karami na
mallaki hankalin kaina yakamata ka sanar dani
gaskiyar al amari,
koda tsoho Imzanu yaji wannan
batu sai hankalinsa ya dugunzuma ainun yayi shiru
yana mai sunkui da kansa kasa,kawai sai idanunsa
suka ciko da kwalla hawaye ya fara zubowa kas,
a sannan ne ya dago kai ya dubi Imhal yace yakai dana
kasani yau ka tambayeni wani sirri wanda dama nayi
alkawarin bazan sanar dakai ba sai bayan ka mallaki
hankalinka,don kada hankalinka ya dugunzuma
kwakwalwarka ta kasa daukar al amarin, koda imzanu
yazo nan a zancensa sai ya sake yin shiru kamar bazai
iya cewa komai ba,da kyar ya sake dago kai ya dubi
Imhal muryarsa na rawa yace ka gafarceni yakai dana
bisa abinda zaka ji daga bakina yanzu domin zakayi
matukar mamaki kuma zai iya girgiza ka,maganar
gaskiya ita ce ni ba mahaifinka bane na jini,koda jin
wannan batu sai zuciyar Imhal ta buga da karfi,nan
take idanunsa suka kada sukayi jawur,bai san sanda
hawaye ya zubo masa ba yace yanzu idan ba kaine
mahifina ba to wanene? Bansan kowa ba a rayuwata
sai dai kai kadai,
kaine kasan cina da shana tundaga
kuruciyata har izuwa yanzu,me yasa uban nawa ya
gujeni ya barni a wajanka cikin daji inda babu jin
dadi da tsaro?
.
lallai kuwa ashe babu soyayya tsakani
na da uban nawa tunda bai damu da rayuwata ba.
Koda Imhal yazo nan a zancensa sai tsoho imzanu ya
zubar
da hawaye sannan yace
Ni kaina bansan waye
mahaifinka ba,ka saurara dakyau kaji labarin da zan
baka yanzu,
wata kila idan kaji labarin zuciyarka tayi

sanyi ka rungumi kaddara a bisa halin da ka tsinci
kanka a ciki
....... ..¤¤¤¤¤¤¤
Wata rana da safe na fito kiwo acikin dajin nan ina
kada dabbobi na sai kawai na hango wasu mutane
bisa keken doki sanye da bakaken tufafi kuma sun
rufe fuskokinsu su biyu sun nufi bakin wani katon
rami mai zurfi da fadin gaske,cikin hanzari na kada
dabbobina izuwa cikin duhuwar bishiyoyi nima na
sami wuri na buya,
dama wadannan mutane basu
ganni ba,ina nan labe cikin duhuwa sai naga
wadannan mutane sun fiddo gawar wata mace daga
cikin keken dokin sun cillata cikin wannan
ramin,
kawai sai suka shiga cikin keken dokinsu da
sauri suka fice daga cikin dajin gaba daya,sai da na
tabbatar da cewa sunyi nisa da tafiya kuma babu
alamar cewa zasu dawo sannan na ruga izuwa bakin
wannan ramin na leka cikinsa kawai sai naga ashe
wata kyakkyawar mace ce aka yanka ta har a sannan
jini na bulbulowa daga cikin makogwaronta kuma
tana dauke da tsohon juna biyu,nan take naji na
kamu da tsananin tausayinta,
.
don haka sai na yanke
shawarar na shiga cikin ramin na dauko gawar
wannan mata domin na suturta ta sosai na haka
kabari mai kyau na binne ta,idan ma na barta acikin
ramin zata rube ne warinta ya dameni tunda ramin
yana kusa da inda bukkata take,nan fa na fara tunanin
dabarar da zanyi na iya shiga cikin wannan rami har
na iya dauko gawar,sai da nayi tunani na tsawon 'yan
dakiku sannan dabara ta fado mini,kawai sai na ruga
da gudu izuwa cikin bukkata,na dauko igiya mai tsawo
sannan na dawo bakin ramin,na daura igiyar a jikin
wata bishiya na wurgata cikin ramin sannan na kama
igiyar ina binta ina shiga ramin,sannu a hankali na isa
kasan ramin,koda naje kan gawar na duba ta sai naga
ashe da ranta bata mutu ba domin numfashinta na
fita kadan-kadan,cikin gaggawa na sunkuci wannan
mace na goya ta a bayana na daureta tamau,na sake
kama igiyar nayi iya kokarina na fito daga cikin ramin
goye da matar a baya na,hankalina a
dugunzume,sauri nake kawai na jarraba ceto
rayuwarta,ina fita daga cikin ramin na ruga da ita
izuwa cikin bukkata,na shimfide ta a kasa sannan nayi
sauri na dauko allura da zarin dinke fata na dinke
raunin wuyanta sannan na shafa magani akan
raunin,A sannan ne na kara hancina a dai dai hancin
matar don naji ko tana yin numfashi,amma sai naji
shiru alamar babu rai a jikinta,nan fa bakin ciki ya

lullube ni naji kamar na fashe da kuka sabo da
takaici,gashi nasaa wahalar dauko ta daga cikin
wannan ramin mai zurfi har ma tafin hannuwana sun
dade saboda kama igiya,cikin sanyin jiki na mike na
sunkuya da nufin daukar gawar na fita da ita waje
inda zan binne ta,kawai sai naji tayi tari,numfashinta
ya dawo,nan take murna ta kamani na ruga na dauko
wani ruwan magani na dura mata a baki dakyar tasha
mukurwa uku,jin kadan sai idanunta suka bude
dakyar,koda tayi arba dani sai naga ta firgita ta
yunkura zata tashi amma sai na danne kafadunta na
hana ta tashi,matar ta budi baki da nufin tayi magana
sai ta kasa,kawai sai naga tana dariya,wani lokacin
kuma sai ta hade fuska ta kama kuka tana fisgefisge,nan fa na gane lallai wannan mata ta samu tabin
hankali,al'amarin da yayi matukar bakanta raina
kenan domin naso ace ta iya yin magana acikin
hankalinta,domin na tambayeta ko ita wacece da
kuma wadannan mutane da suka kawo ta dajin acikin
keken doki a matsayin gawa,abinda zuciyata ta aiyana
min shine in ma basu bane to sun san wanda ya
kasheta,kuma akwai wani boyayyen al'amari akan
kisan nata,daga wannan rana naci gaba da jinyar
wannan mata har tsawon kwana ashirin da daya,A
tsawon wadannan kwanaki kullum a kwance take
kuma koda tayi yunkurin mikewa zaune sai ta kasa
sabo da raunin da yake makogwaronta,haka kuma
bata taba yin magana ba sai fisge-fisge da dariya
irinta mahaukata,abinci kuwa sai dai na dura mata
abaki tana ci tana kuka sabo da ciwo,da yake naga
tana dauke da juna biyu sai na dinga yawan bata
madarar shanu gami da abincin da yake gina jiki
domin abinda ke cikinta ya samu cikakkiyar lafiya,a
kwana a tashi har wannan mata ta shafe wata uku cur
a wajena,a sannan ne raunin makogwaronta ya
warke sumul har ya zamana cewa tana iya magana
sosai,amma a koda yaushe babu magana ta hankali
da nutsuwa a tare da ita sai maganganu irin na
mahaukata,nayi iya kokarina akan ta gayamin ko ita
wacece,daga inda take da kuma yadda akayi ta shiga
wannan hali sai tayi ta kyalkyala mini dariya,ganin
hakane yasa tausayinta ya karu a zuciyata,sau bakwai
ina nemo masana ilimin maganin mahaukata,wato
likitocin mahaukata suna zuwa su dubata kuma su
bata magani,amma duk a banza lafiya taki
samuwa,sau tari matar takan sulale ta nausa cikin
daji bansani ba,sai nasha wahalar nemota,bisa
wannan dalilin ne ma duk sanda zan fita kiwo ko
farauta sai na tafi tare da ita,wato na daina barinta a
gida.
Lokacin da cikinta ya tsufa sai tafiya da ita kiwo ko
farauta ya gagara,don haka nima sai na hakura da

zuwa ko ina,na tanadi abincina da na dabbobi na mai
yawa wanda zai kai tsawon kwana arba in,Ai kuwa
adaren kwana na talatin da bakwai nakuda ta kama
wannan mata acikin tsakiyar dare.Al'amarin da yai
matukar dugunzuma hankalina kenan tunda babu
halin in ruga cikin gari in nemo ungozoma,Da yake na
taba shiga irin wannan hali da nake tare da matata
wacce ta rasu a wajen haihuwa abinda ta haifa ma
yazo a mace,sai na shiga taimakon wannan mata,nine
na yankewa jaririn cibiya,na wanke shi sannan na
kimtsa mahaifiyar tasa,matar taci gaba da rainon
jaririnta tana shayar dashi ni kuma ina cigaba da fita
farauta da kiwona ina barinsu a gida,har tsawon
shekara daya da wata bakwai muna tare sannan
yaron ya fara tafiya da kafafunsa.
Kwatsam wata rana naje kiwo na dawo sai na nemi
wannan mata sama da kasa na rasa,kuma ga dannan
ta bar shi acikin bukka a zaune shi kadai yana ta tsala
kuka,cikin dimaucewa na dauki yaron na gaya shi a
bayana sannan na bazama neman wannan mata
wacce ko sunanta ban saniba bare na dinga kwalla
mata kira,Abu kamar wasa sai da na shekara daya da
wata tara ina nemanta amma ko alamunta ban gani
ba acikin wannan daji.A tsawon wannan lokacin ni
nake kula da wannan yaro da ta haifa dare da rana,ya
zama cewa na shaku dashi ainun shima haka
.Kwatsam wata rana da yammaci ina wasa da yaron a
kofar bukkata kawai sai na hango wannan mata daga
can nesa ta durfafo bukkata,cikin alamun tsananin
mamaki na mike tsaye na zuba mata idanu,matar ta
rame matuka,kuma duk rigar jikinta ta
yayyage,sannan tayi baki sabo da wahala da
kazanta,koda ta iso daf dani ta dubeni sai ta fashe da
kuka ta durkusa kasa bisa gwiwoyinta tana mai
neman gafarata tamkar mai cikakken hankali,nan take
naji na kamu da tsananin tausayinta don haka sai na
kama kafadunta na tasheta tsaye kuma na rungumeta
a kirjina a karon farko tun haduwa ta da ita,ita kuma
sai ta kankame ni ta da da fashewa da kuka,kawai sai
na janye jikina daga nata na dubeta nace me yasa
kika gudu kika barmu?shin kin manta ne cewa kin bar
danki a hannu na?koda jin haka sai matar ta dubi dan
nata ta girgiza kai tace ai ni kananin yaro na bar maka
bai kai wanan girma ba,da jin haka sai nayi dariya
nace to ai kullum mutum dada girma yake har yanzu
baki gaya min inda kika tafi ba kika barmu,Matar ta
bushe da dariya sannan ta hade fuska tace shan iska
na tafi na sake dawowa.Cikin tsananin damuwa nace
yau shekara hudu kenan muna tare baki taba gaya
min sunanki ba kuma baki gaya min sunan garinku ba
bare nasan asalinki da danginki shin bakya tausayin
wannan yaron da kika haifa ne?Koda jin wannan

tambaya sai matar ta sake bushewa da dariya tace
bansan kaina ba kuma bansan kowa ba sai kai,tana
gama fadin haka ta juya ta shige cikin bukka taje ta
kwanta ta kama bacci,tun daga wannan rana muka ci
gaba da zama tare,amma ko kadan wannan da nata
bai dameta ba,kuma bata yi masa komai sai dai ni
nayi masa,wani lokaci sai naga kamar hankalinta ya
dawo tana magana a nutse,amma da zarar na fara
tambayarta asalinta da garinsu sai ta birkice ta koma
hauka.
Wata biyu da kwana uku mukayi tare ranar kwana na
ukun ne matar ta wayi gari da tsananin rashin lafiya
wadda bansan sanadinta ba,cikin rudewa na shiga
hada mata magunguna iri-iri ina bata tana sha amma
duk a banza tamkar kara mata ciwon akeyi,kawai sai
naga idanunta sun fara lumshewa kuma numfashinta
na sarkewa,Al amarin da ya dugunzuma hankalina
kenan na fara zubar da hawaye,na shiga yi mata
tambayoyi akan ta sanar dani asalinta,matar na
kokarin bude baki tayi magana amma sai ta kasa,nan
take jikinta ya sandare,idanunta suka kafe ta daina
motsi.koda naga haka sai na rungumeta na fara
kuka,ganin ina kuka ne dannata wannan yaro dan
shekara kusan hudu ya rugo izuwa kaina shima ya
fashe da kuka.Hakika wanan rana nayi kuka mai yawa
sabo da shakuwar da nayi da matar nan sai da nayi
kwana ashirin da daya bana iya cin abinci
sosai,amma koda yaushe hankalina yana kan wannan
yaron ina kula da lafiyarsa sosai.
Koda tsoho Imzanu yazo nan a zancensa sai Imhal ya
tari numfashinsa suka dubi juna a lokacin da
kowannensu yake zubar da hawaye yace yakai
Abbana na gane cewa wannan yaro da mahaukaciya
ta haifa ba wani bane face ni dinnan,tabbas yanzu na
tabbatar da cewa ni marayane wanda bashi da uwa
bashi da uba kuma wanda baisan asalinsa ba,koda
Imhal yazo nan zancensa sai tsoho Imzanu ya
rungumesa suka fashe da kuka tare,can sai Imhal ya
janye jikinsa suka fuskanci juna ya dubi Imzanu yace
Bazan taba yarda bani d uba ba amma ni kai na sani
a matsayin ubana,ina son nayi maka wata tambaya
guda daya menene dalilin da yasa kake kirana da
suna IMHAL?
.
WASA FARIN GIRKI
.RIJIYA GABA DUBU
Littafi na daya 1
Na Abdulaziz sani m gini
Typing:- Ibrahim S combatant
Post:- Shuraih Usman
@Shuraih 99%
Part 1B.

Koda jin wannan tambaya sai hawaye ya zubowa
tsoho Imzanu yace Abinda yasa nasa maka suna
Imhal shine a iya zama na da mahaifiyarka har ta
mutu ban taba jin ta ambaci sunan wani mahaluki ba
face IMHAL,A kullum duk sanda za taci abinci sai naji
tana kiran sunansa tana cewa yazo suci abincin
tare,abinda na fahimta shine,koma wanene wannan
Imhal din lallai ya kasance babban masoyi a
gareta,zai iya kasancewa mijinta ne ko dan uwanta ne
ko mahaifinta,Abu na biyu da nake zargi shine,duk
yadda akayi mahaifiyarka ta fito daga babban gida
domin a ranar da na tsince ta acikin wannan katon
ramin mai zurfi sutturar dake jikinta mai matukar
tsada ce,babu mai sanya irinta face sarakai da
manyan attajirai,babban bakin cikina shine babu
wata shaida a tare da mahaifiyarka wadda zata iya
sawa a gano asalinta,koda tsoho Imzanu yazo nan a
zancensa sai suka sake rungume juna,daga can sai
Imhal ya dubi tsoho Imzanu yace,Lallai zan rike
sunana a zuciyata da bakina,lallai wata rana wannan
suna zai taimakeni na gano asalina.
Tun daga wannan rana Imhal da tsoho Imzanu suka
cigaba da rayuwarsu acikin daji kamar yadda suka
saba,amma sai ya zamana cewa kullum sai Imhal ya
shiga cikin garin Kisra kuma duk inda yaje si ya
tambayi mai suna Imhal,idan aka tambayeshi wane
Imhal yake nema sai ya kasa bayani domin baisan
wata inkiya ba ta Imhal din da yake nema,hakane
yasa suka dinga yiwa Imhal dariya suna cewa dashi
Bagidaje mutumin daji,saboda ganin yanayin
shigarsa ta makiyaya.
Wata rana Imhal yazo giftawa ta kofar gidan sarkin
kisra akayi sa a kuwa a lokacin sarki ya fito daga cikin
gidan sarautar zai fita rangadi kwatsam sai yayi arba
da sarki,Abinka da wanda baisan yadda ka idar
sarauta take ba sai kawai ya kurawa sarki
idanu,maimakon ya zube kasa gabansa ya kwashi
gaisuwa,ai kuwa sai dakarun sarki suka afkawa Imhal
da duka har suka kai shi kasa,cikin fushi ya yunkura
ya watsar dasu duka duk da cewar sunkai su
ashirin,nan take shima ya rufesu da duka,duk wanda
yayi wa naushi daya sai ya baje a kasa
sumamme,koda ganin haka sai ragowar dakarun
sarki suka zare takubbansu sukayi caa akan Imhal
zasu sassara shi,amma sai sarki ya daka musu tsawa
suka saurara,nan take sarkin kisra ya sauko daga kan
dokinsa yazo daf da Imhal yadda har suna iya jin
numfashin juna,sannan ya dubeshi cikin murmushi
yace,A duniya babu abinda yake birgeni sama da
jarumtaka,tabbas na yarda kai jarumi ne amma ina
son na gwada jarumtaka ta akan taka,nasan baka san
koni waye ba to nine Sarkin garin nan,koda jin haka

sai Imhal ya zube kasa bisa gwiwoyinsa yana mai
sunkui da kansa kasa yace ka gafarceni ya
shugabana,kasan cewa ni rayuwata gaba daya cikin
daji nayi ta,sau daya a sati muke shigowa cikin
garinnan,yau ne ranar farko da na fara ganinka a
rayuwata,ya shugabana kayi min afuwa domin bazan
iya fada da kai ba,Koda jin wannan batun sai sarki ya
bushe da dariya ,lokaci guda kuma ya hade rai ya
dubi Imhal cikin nutsuwa yace,ya kai wannan saurayi
ma abocin jarumtaka kayi sani cewa nahiyar nan
gaba daya babu wani jarumi ko mayaki mai karfi da
iya yaki kamata,yau shekara talatin kenan ina
gwagwarmaya da gumurzu kuma sau arba in da uku
ina lashe GASAR JARUMTAKA a kasashe arba in da
uku dake cikin wannan nahiya tamu ko sau daya ba a
taba samun jarumin da ya lakuci jikina ba bare ya
kaini kasa,naga jarumtakar jarumai da yawa a
rayuwata,amma ban taba ganin jarumi mai zafin
nama da karfin naushi kamarka ba,ina da tabbacin
cewa idan muka fafata sai na sami nasara akan ka
duk da cewar na yaba da karfinka,ka sani cewa kana
da zabi guda biyu kodai ka yakeni ko kuma yanzun
nan nasa tagobi na sare maka kai,koda jin wannan
batu sai hankalin Imhal ya dugunzuma ya mike tsaye
cikin sanyin jiki,abu na farko da ya fado masa a rai
shine,Ai bai kamata ya mutu yanzu ba har sai ya gano
asalinsa,koda gama aiyana hakan acikin zuciyarsa sai
ya mikawa wani badakare hannu yace bani
tagobinka,ba tare da gardama ba kuwa ya mikawa
Imhal tagobinsa ya karba,koda ganin haka sai murna
ta kama sarki,shima ya zare tagobinsa,a lokacinne
dakaru suka buda suka yi musu da ira aka sa su a
tsakiya,nan fa sarki da Imhal suka fara zagaya juna
suna kallo-kallo.
Lokaci guda kowannensu ya daga tagobinsa sama
suka ruga izuwa kan juna,suka ruguntsume da
azababben yaki ya zamana suna kaiwa juna sara da
suka cikin tsananin zafin nama,juriya da bajinta ta
ban al'ajabi,sai da suka shafe sa a guda suna wannan
bakin artabun amma dayansu bai samu nasarar koda
kwarzanar mutum daya ba,Al'amarin da ya fusata
sarki kenan kuma ya cika da tsananin mamakin yadda
akayi wannan mutumin dajin ya samu gagarumin
horon yaki haka,nan take sarki ya canza salon yaki,ya
dinga tsalle-tsalle da kwance-kwance,kawai sai yaga
Imhal ya iya duk irin abinda yake yi tamkar tare aka
koya musu yaki babu wani banbanci,koda ganin haka
sai sarki ya ja da baya taku biyar,shima Imhal sai yayi
hakan amma shi taku uku yayi,duk su biyun suka
kurawa juna idanu na tsawon yan dakiku kadan,kawai
sai sarki ya rugo da gudu izuwa kansa,shima sai ya
ruga gareshi,kafin su hadu sai kowannensu ya daka

wawan tsalle sama ya kai hari cikin mugun nufi,Acikin
tsananin zafin nama kowannensu ya kaucewa harin
takubbansu suka sari iska,amma kafin su duro kasa
sun gwarawa juna fuska,ai kuwa sai hancin
kowannensu ya fashe,a saman sai suka sake kaiwa
juna hari,sai sarki ya sami nasarar yankar Imhal a
saman cibiyarsa,Shi kuma ya sami nasarar yankar
sarki a gefen wuyansa,kowannensu jini yayi tsartuwa
daga jikinsa suka rikito kasa a matukar galabaice,A
guje Dakaru suka ruga aka baiwa Sarki rawani ya
daure wuyansa da jini,take likitan Sarki yayi masa
magani,Kawai sai Dakaru suka ruga izuwa kan Imhal
wanda yake kwance a kasa ya dafe raunin don tsaida
jini zasu halaka shi,Sarki ya daka musu tsawa suka
fasa,kawai sai sarki ya dubi likitansa yace Idan ka
gama dani kaje kayiwa wannan saurayin magani,Cikin
gaggawa kuwa likita ya gama yiwa sarki magani
sannan yaje yayiwa Imhal,Sa ar da Sarki da Imhal
sukayi raunikan basuyi zurfi ba a jikin su,Tunda
Likitan ya fara yiwa sarki magani sai zuciyar Sarki ta
fara tafarfasa kamar zata kone saboda tsananin bakin
ciki da takaici bisa ganin yadda a yau wannan bakon
saurayi ya karya alkadarinsa na jarumin dake rike da
KAMBUN JARUMTAKA na nahiyar gaba daya,Bayan
angama yiwa Imhal magani ya mike tsaye sai yazo
gaban Sarki ya risina yayi godiya,Sarki ya dube shi
cikin yake yace Tabbas ka cika jarumi abin kwatance
amma ka saurari ranar da zamu sake haduwa a filin
gasar JARUMTAKA wacce za ayi a birnin MISIRA nan
da cikar wata uku,ko kana so ko baka so sai ka shiga
wannan gasa kuma ina tabbatar maka da cewar sai
na sami nasara akan ka na kasheka murus har
Lahira,yin hakane kadai zai sa na huce bisa takaici da
bakin cikin da ka jefani a ciki,Koda ya gama fadin
hakan sai Sarkin Kisra ya dubi wani babban Badakare
nasa yayi masa rada a kunne sannan ya juya ya kama
dokinsa ya hau ya kada linzaminsa yayi gaba,sauran
dakarun gaba daya suka rufa masa baya.Shi kuwa
jarumi Imhal sai ya tsaya cak yabi sarkin kisra da
kallo cikin tsananin mamaki,Imhal ya tambayi kansa
cikin zuciyarsa yace WAI SHIN MENENE YAYI ZAFI
HAKA,HAR DA SARKI YACE ZAI KASHENI MURUS HAR
LAHIRA ALHALIN MA BASU TABA GANIN JUNA BA
SAI YAU?AKAN WANE DALILI ZAI TSANANTA GABA A
TSAKANINMU HAKA?koda Imhal ya kasa baiwa kansa
amsa sai ya juya ya falfala da gudu ya nufi hanyar da
zata kaishi daji.
Imhal ya ci gaba da gudu har sai da ya iso dajin da
bukkarsu take,yana cikin gudu ne ya hango tsoho
Imzanu ya goyo jakarsa ta tafiya yana dogara sanda
ya baro bukkar acan baya,cikin kaduwa da matukar
mamaki Imhal ya karasa wajen Imzanu da gudu ya

tareshi yana mai rike kafadunsa ya dube shi yace Ya
kai abbana lafiya kuwa?ina zaka je naga ka dauko
jakarka ka nufi hanyar cikin gari?Koda tsoho Imzanu
yaga Imhal a tsaye gabansa sai fuskarsa ta fadada da
murmushin farin ciki,har ya budi baki zai ce wani abu
sai idanunsa suka kai kan raunin dake kan kasan
cibiyar Imhal,cikin firgici Imzanu ya dube shi yace
yaya akayi ka samu wannan raunin?koda jin wannan
tambayar sai Imhal ya kwashe labarin duk abinda ya
faru tsakaninsa da sarki Kisra ya zayyana masa ba
tare da boye masa komai ba,koda jin wannan labarin
sai hankalin tsoho Imzanu ya dugunzuma ainun har
idanunsa ya ciko da kwallah ya dubi Imhal yace ya kai
dana ina so ka sani cewa kamar yadda ka kasance
maraya a garin nan haka nima nake,iyayena da
kakannina duk sun mutu,matata ta mutu tare da dan
da ta haifa kamar yadda na baka labari,A halin yanzu
bani da kowa face kai wane irin hali kake tsammanin
zan shiga idan na rasaka?ina mai tabbatar maka da
cewa idan har ka halacci gasar jarumtakar da za ayi
nan da cikar wata uku a birnin Misira sai ka rasa
rayuwarka domin tabbas sai sarkin garinnan ya kashe
ka,domin zai je yayi gagarumin shiri ne yayi amfani
da karfin sihirin tsafi wanda dole sai ya samu nasara
akan ka,A halin yanzu bamu da wani zabi wanda ya
wuce mu sulale mu bar Nahiyar nan gaba daya,indai
muka isa wata nahiyar daban shikenan mun tsira
daga sharrin sarkin kisra,duk inda muka tsinci kanmu
sai mu fara sabuwar rayuwa,duk da cewa ni tsufa ya
kamani ina da sauran buri guda daya a
duniya,wannan burin ba na komai bane face nason
ganin aurenka,koda tsoho Imzanu
DOWNLOAD
DOWNLOAD

4 Comments On RIJIYA GABA DUBU
avatar
mlm

9 months ago

Reply

Next please

avatar
khadija-1-4

7 months ago

Reply

??????

avatar
muhammad-musa

5 months ago

Reply

Good book

avatar
ismail-9-8

3 months ago

Reply

Please Login or Register in order to submit comment