Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

๏ปฟ[11/13/2017, 6:26 PM] ~๐Ÿ‡ฉ ' ๐Ÿ‡ฏ ๐Ÿ‡ฆ ๐Ÿ‡ท ๐Ÿ‡ญโœ: ๐Ÿ‘ฉ๐Ÿปโ€๐Ÿ’ปtyping..........




๐Ÿ’Ž *_KARAYAR ARZEEK'I!!._*๐Ÿ’Ž



*_NA_*
*_Bilyn Abdul_*


_Sadaukarwa_
*_miss Xoxo na_*
*_Zarah bukar_*
*_Ayusha muh'd_*


*_NIKA'DAI๐Ÿ‘Œ๐Ÿผ WRITER ASSO....๐Ÿ˜œ._*


_Bismillahirrahmanirrahim_

_ya ALLAH kabani ikon fad'ar abinda zai amfani al'ummarka, ka tsare harshena daga fad'an abinda zai cutar da al'ummarka, ameen_

_ina farin cikin sake had'uwa daku a sabon littafina mai suna *KARAYAR ARZEEK'I*, ina fata zaku bani had'in kai, ngd da k'aunarku gareni, nima ina k'aunarku lodi Lodi._๐Ÿ˜˜๐Ÿ˜„

*_duk Wanda ya canja wani Abu a buk d'innan ALLAH ya isa ban yafeba.๐Ÿ™„_*




*_pageโ†’1_*

..........6urum aka turo k'ofar tamkar za'a cireta.
Zaune yake a bakin gado yana harhad'a wasu takardu, hankad'o k'ofar basashi ko gezauba barema ya d'ago Dan yasan bai wuce matarsace lubna ba, da wanan d'anyen aikin.
Ta huro hanci had'eda rik'e k'ugunta da hannu biyu, wata uwar harara ta watsa masa, wadda baimasan tanayiba.
*_Umar fharuq!!._* takira sunansa cikeda masifa.
Bai amsataba baikuma d'agoba, harkar gabansa kawai yakeyi.
Lubna dake tsaye tana karkad'a jiki takuma k'ufla, Dan haka tacigaba da magana cikeda tsiwa.......
Gsky nikam nagaji, kasan yadda zakayi dani wlhy, shekaranjiya kacire yara daga makaranta bance maka komaiba, yaukuma shine zakazo da mutane suna zazzagaye gida?, shin mikake nufu?, ko shima gidan saidashi zakayine?, to wlhy idanma tunanin haka kakeyi ka canja, Dan bazan rayu banida tsuntsu baniga tarkoba.
Aidama nasan tunda aka aura maka waccan 'Yar k'auyen, saimun shiga bala'i, gashinan tun ba'aje ko inaba komai yak'are, mayya mai farar k'afa tashigo rayuwarmu, saura kuma kurwarmu ake bibiya alashe yanzun...
d'an tsaki yaja idonsa akan takardun dayake zubawa acikin wata 'Yar jaka, saida yagama tsaf sannan yad'ago fararen idanunsa yana kallonta, yanunata da d'an yatsa lubna kishiga hankalinki, kinsan banason shirme ko?, gidakam zan saidashi idankuma nakine saiki hana, inama yimiki albishir daki fara shiri Dan nanda kwana biyu zamu barmusu gidansu.............
Jar ubannan kai, wlhy Umar baka isaba, ainima inada hak'k'i da gidan, tunda 'ya'yana sunada gado.
Kansa ya girgiza yana rataya jakar akafad'a, ya ce, "mahaukaciya kawai, saiki bari saina mutu kafin yazama gadon nasu mtsoww.
Umar nikake kira mahaukaciya?!.
Bai tanka mataba yatako cikin nutsuwa yanufi hanyar fita......
Da Sauri tasha gabansa tana huci, wlhy babu Inda zakaje saika sanar dani wacece mahaukaciyar?.
Kallon sama da k'asa yay mata, batareda yayi maganaba yaja tsaki tareda ra6awa ta gefenta zai wuce.
Da Sauri takuma shan gabansa.
Afusace ya ce, " wlhy koki tashimin a hanya, kokuma na kashe fuskaeki da mari......
Toka marenin mana, nagadai Nima ALLAH yabani hannun dazan rama.
Ya ce, "ko?.
"eh, kozaka gwadane?."
Wani k'asaitaccen murmushi yasaki, yara6a tad'ayan gefenta yafice yana cije le6ensa.
Binsa tayi da kallo tana girgiza jikinta alamar tsumuwar bala'i, saikuma ta rushe da kuka.

Na ce, "tofa, anayinta."

Shikam koda yafito d'ayan 6angaren ya Shiga, babu kowa a falon, sai sassanyan k'amshi dana AC dake tashi, TV ma a kashe take, hanyar wani d'aki yanufa.
Tana zaune abakin gadonta dayasha gyara, ananma k'amshine mai dad'i dasaka zuciya nutsuwa ke tashi, ta rabga tagumi, daga ganinta Kasan tana duniyar tunani.
Gyaran murya yayi had'eda sallama.
Firgigit tad'ago tana kallonsa, sai kuma tazamo daga gadon Baki narawa ta ce, "yaya ina yini.
Atak'aice ya amsa da lfy, yacigaba da fad'in kifara shirya kayanki nanda kwana biyu zamubar gidannan...... Baijira cewartaba yafito abinsa.
Wasu siraran hawaye suka zubo daga kumatunta, Afili ta ce, "na Shiga uku ni Asma'u, shima gidan ka saida ya Fharuq?!, nikam naga ta kaina, karfa maganar aunty Lubna yazama gsky, ta rushe da kuka maiban tausayi........



_nakalli zarah, Zarah takalli Xoxo, mukayi tsuru tsuru tamkar munafukai, Xoxo ta ce, " tawan ta'ina zamu fara?, na ce, "umm tawan tambayi Zarah kotanada idea nikam banida fus._
_Zarah ta gyara tsayuwarta, hannunta rik'eda Biro da 'Yar takardar d'aukar rahoto, ta ce, " bily nimafa na toshe Dan naga gidan kowa a rikice yake bansan wazamu tunkara yabamu labariba?, Xoxo kozakije wajen lubna?._
_Kam bala'i babu inda zani daga rakkiya?, agabankufa mijinta yakirata mahaukaciya, sannan kucemin naje tasaukemin na jaki._
_Dariya muka gumtse nida Zarah danjin zancen Xoxo, Zarah ta ce, "bily fa?._
_Na ce, " um um kodai ke ki gwada, nisainayima wannan magana?._
_Shiru Zarah tayi, Dan itama batason komawa wajen lubna........_
_Zuwacan Xoxo taja numfashi idonta akan Zarah, ta ce, "Zarah nibamfa gane mi tawan take nufiba?, catayifa murakota d'aukar rahoto, amma sai wani shirin lik'a mana aiki takeyi?._
_Harar Xoxo nayi, amma tawan idan kuntayani na buga labarinnan naga ba fad'uwa kukayiba ko?._
_Hakane, amma gsky nikam bazan iya da wannan iya bala'in matar tasaba, kumafa ni sonsama nakeyi, Dan guy d'in yahad'ufa._
_Dariya muka shek'e da ita nida Zarah, Zarah ta ce, " haba 'Yar uwa kice kishi bazai barkiba kawai, ammafa Nima bily bawai zan tayaki bane, namiki rakkiyane kawai, saidai mukoma gidan zan tayaki da shawarar yanda zaki d'auki wannan rahoto._
_To shikenen ngd Zarah muje, kekuma tawan dazanmiki hanya ki aureshi ammafa yanzu nafasa._
_Kai tawan nidakefa ba'a jin kammu?._
_Aikodai yau za'aji...........๐Ÿคฅ๐Ÿ˜._


*_tab masu karatu akwai aiki Dan bansan yanda zaku sami cikakken labarinba, tunda masu d'aukar Rahoton duk matsoratane._*
*_Daga miss xoxon Zarah Bukar, harni bilyn Abdul duk fararen kurayene๒“ฐฝ๒—€ฎ_*


_amma ni bilyn Abdul zan kawo muku cikakken labarin, tunda su o e anji tsoro๐Ÿ˜._


Kikasance dani danjin yadda zata kaya๐Ÿ˜ป๐Ÿ˜˜.

Bilyn AbDul ce๐Ÿ‘Œ๐Ÿผ



*_luv you all_*
*_(((S))).....2017_*
[11/14/2017, 5:05 PM] ~๐Ÿ‡ฉ ' ๐Ÿ‡ฏ ๐Ÿ‡ฆ ๐Ÿ‡ท ๐Ÿ‡ญโœ: ๐Ÿ‘ฉ๐Ÿปโ€๐Ÿ’ปtyping..........




๐Ÿ’Ž *_KARAYAR ARZEEK'I!!._*๐Ÿ’Ž



*_NA_*
*_Bilyn Abdul_*


_Sadaukarwa_
*_miss Xoxo na_*
*_Zarah bukar_*
*_Ayusha muh'd_*


*_NIKA'DAI๐Ÿ‘Œ๐Ÿผ WRITER ASSO....๐Ÿ˜œ._*



*_pageโ†’2_*

...........Tundaga k'ofar gida nafaracin karo da wasu manyan motoci akorikura har uku, duk an loda musu kaya, ra6awa nayi tagefensu nashiga cikin gidan, lallai tashi ya tabbata nafad'a azuciyata ina bin ko'ina nagidan da kallo.
Asma'u naga tafito da akwatuna biyu ahannu tanaja, Umar dake jingine da motarsa yana latsa waya yad'ago yana kallonta, d'an ta6e bakinsa yayi yana kauda kai daga kallonta, aransa ya ce, "yarinya tamkar mara laka ajiki?, komai nata salaf-salaf......
Maganartace ta katse masa tunaninsa ta ce, " yaya gasu.
Baiyi maganaba ya ajiye wayarsa saman motar, but yabud'e mata tasaka akwatunan, yarufe sannan yad'auki wayarsa yabud'e motar yashiga.
Asma'u tana tsaye sai faman bin gidan da kallo takeyi, kwata-kwata zuciyarta babu dad'i takeji, tasan yaya umar ma yana dakewane kawai kasancewarsa mutum jarumi mai dakiya da kawaici, duk 6acinran da Umar zai shiga mawuyacine kagansa shinfid'e afuskarsa, mutumne daya iya 6oye sirrin zuciya........
Ganin bata shigoba yay mata horn.
Da sauri tabud'e motar amma bata shigaba, tad'an sunkuyo ta ce, "ya Fharuk Anty Lubna fa?.
K'aramin tsaki yaja, yace batana canba tund'azu, kinafa 6atamin lokaci.
Jiki a sanyaye tashiga motar yaja yafice daga gidan zuciyarsa namasa zafi, amma sai ambatar innalillahi wa'inna'ilaihirraji'un yakeyi.
Tuk'i yakeyi ahankali tamkar bayaso, dagashi har ita babu mai iya magana, lokaci-lokaci ita takan share hawaye, yana kallonta ta gefen ido.
Ak'ofar wani matsakaicin gida yay farking, koba'a fad'aba nanne gidan dazasu dawo, domin annan muka tadda motocin akoru kurarnan sunata aikin sauke kaya dashigar dasu cikin gidan.
Kad'an ya kalleta, kishiga ciki su Hasiya da Rafi'a da fatee duk sunanan sune zasu tayaki gyara kayanki, ni bara naje wani waje.
To ALLAH yatsare, saika dawo.
Ameen, yafad'a akan la66ansa.
Bud'e motar tayi tafita, harta d'an fara tafiya saikuma tajuyo, ya Fharuk kayanfa?.
Baitanka ba saida yatada motar, kije idan nadawo zan shigo dasu yanzu Sauri nakeyi, magana yakeyi amma ko Inda take baya kallo.
Itama kanta ta jinjina tajuya tashiga cikin gidan, abakin matsakaicin bak'in gate d'in sukai karo da matasan samarin dasuka gama Shiga da kayan nata.
Sannu tayi musu sannan tashige ciki.
Bin ko'ina takeyi da kallo, gidan k'aramine irin ginin talaka mai k'aramin k'arfi, ko'ina shage yake da siminti lumus, haka tak'arasa cikin gidan tana raba hanya.
Abakin fanfo taga Afrah da Amrah yaran Anty Lubna sunata wasa da ruwa, bata musu maganaba gudun kar cibi yazama k'ari Dan Anty lubna batason abinda zai ta6a 'ya'yanta ko kad'an.
K'ofar falon tatura tashiga, Rafi'a da fatee Hasiya sukazo da gudu suka rungumeta, itama rungumesu tayi sunamai murnar ganin juna.
Hasiya ta ce, "kai Anty Asma'u kinganki kuwa, wlhy kinyi bala'in k'yau, gidan ya Fharuk ya kar6eki.
Hararar hasiya tayi cikin sigar wasa, Hasiya kina nandai baki canja haliba wlhy.
Dariya sukayi suduka, Asma'u tabi falon da kallo, babbane sosai, sai kowace kusurwa da akwai k'ofa.
Ganin kallon da takema falon yasa Rafi'a fad'in wlhy Anty tsarin gidan yayi sosai, kinga nan family falone, wancan k'ofar shine naki, akwai falonki da bedroom sai bathroom, wancan kuma na Anty lubna ne, itama iri d'ayane da naki, wancan na tsakkiyar kuma na ya Umar ne.
Murmushi Asma'u tayi, tace ALLAH ya tabbatar da alkairi to.
Ameen suka fad'a suduka.
Kama hannunta fatee tayi, tana fad'in zomuje kigani harmun fara had'a miki bedroom d'inki.
d'akin daya kasance NATA suka nufa, tuk'uru suka Dage suna aiki, kafin k'arfe biyu sungama komai har babban falon sun saka kujerun dasuka kasance ada na 6angaren bak'i agidan dasu dasuka taso, d'akin Ya Umar suka shiga, shima tsaf suka gyara masashi ko'ina yad'auki haske.
Duk bidirinnan dasukeyi basuji motsin Lubna ba sai yanzu, duk sunzube a family falo suna maida numfashin Hajiya lubna tashigo itada Suhaima k'anwarta.
Suhaima tabi falon da kallo tana wani yatsine fuska, Anty lubna wai kina nufin anan ya Umar zai ajiyeki?, aiko 'yan aikin gidanmu sunfi k'arfin zama acikin wannan kangon?.
Baki lubna ta ta6e kibarsa kawai Suhaima Nima INA rakashine naga iya gudun ruwansa, amma wlhy bazan zauna awanan k'onannan gidanba saikace wata fak'ira, shima yasan bamu gaji tsiyaba wlhy.
A to yakamadai kid'auki mataki, wannan gidan saidai su o e wad'anda dama atsiya aka taso, shigarta wannan gidan ai ita k'arin cigabane.
Rafi'a tamik'e danufin maida murtani dantasan sarai da Asma'u suke.
Da Sauri Asma'u tarik'e hannunta tana girgiza mata kai alamar a'a kartacr komai.
Lubna ta gallama Rafi'a harara, to tabbatacciya da dakika tashi dukanmu zakiyi?.
Shiru Rafi'a Tamata Dan Asma'u tahanata magana.
Suhaima ta tuntsure da dariya Anty lubna kinga muje nifa kinganni bakowace bola bace abin kallo agareni.
Fatee ma tabud'e baki Zata maida murtani Asma'u ta harareta.
Daga k'arshema tashi tayi takad'a Kansu suka shige cikin falonta.
Daga Lubna har suhaima Bahaka sukasoba, sunso su Hasiya su kulasu ayi badad'i, dama Neman dalili sukeyi da dangin Umar d'in.

Suna Shiga Asma'u tarufesu da fad'a akan itafa batason tashin hankali, danhaka komi sukaimata karsuce zasu sake kulasu.
Shiru sukai mata kowa tana turo Baki, dansu hak'urin Asma'u haushi yake basu.

Sai magriba ya Umar yadawo gidan, suna zaune bayan sun idar da sallah yashigo.
Suduka rissinawa sukai suna gaisheshi, ya amsa babu yabo babu fallasa.
Ya ce, ''kutashi namaidaku gida.
To, suna fad'a kowa tana mik'ewa daneman mayafinta, kowa yashirya sukaima Asma'u sallama, hawaye tafara da rok'onsu Dan ALLAH su ringa zuwa mata akai-akai.
Hak'uri sukabata sukace zasuringa zuwa, dama makarantace take hanasu.
Ya Umar duk yana jinsu, ganin sunk'i tahowa yadoka musu tsawa, kai banason rainifa........
Bama su bari yak'arasaba suka fita dad'an gudunsu.
Asma'u tacusa kanta tsakanin cinyoyinta tana kuka saboda kewar 'yan uwan nata, koba komai yau taji dad'in ganinsu, sunyi hira taji farinciki aranta.
Bata kuma saka ya Umar a idontaba har wayewar gari, dama bazuwa kwana d'akinta yakeyiba, itakuma bata zuwa d'akinsa Dan duk hak'urinta tanada matuk'ar zuciya, dukda tasan basonta yakeyiba hasalima taimakonta yayi, amma ai baidace yarik'a mata hakaba kodan darajar zumincin dake tsakaninsu......
Share hawayenta tayi tamik'e zuwa kichin domin had'a breakfast.

Ruwan shayi kawai tadafa da Lipton da kayan k'amshi Dan bataga wani abuba a stor d'in gidan.
A tsakkiyar falon tazo ta ajiye kofuna da filas d'in shayin Dan ya Umar bayacin abinci akan dinning.
Tana cikin d'an gyara kayan yafito daga d'akinsa sanye cikin farar jallabiya.
Rissinawa tayi ta gaisheshi, saud'aya ya amsa yafice.
Mintuna kad'an yadawo d'aukeda bak'ar Leda ahannnusa, Asma'u na zaune a babban falon tana jiran dawowarsa danta tambayesa yanda za'ayi.
Ledar yamik'a mata, hannu biyu tasa takar6a tana masa sannu.
Kujera yasamu daga d'an nesa da ita yazauna, itakuma tabud'e ledar, biredine aciki sai madara irin 'Yar sacet d'innan guda uku, sai sukari da bota ta Leda.............







*_luv you oll_*
*_(((S))).......2017_*
[11/20/2017, 6:20 PM] ~๐Ÿ‡ฉ ' ๐Ÿ‡ฏ ๐Ÿ‡ฆ ๐Ÿ‡ท ๐Ÿ‡ญโœ: ๐Ÿ‘ฉ๐Ÿปโ€๐Ÿ’ปtyping..........




๐Ÿ’Ž *_KARAYAR ARZEEK'I!!._*๐Ÿ’Ž



*_NA_*
*_Bilyn Abdul_*


_Sadaukarwa_
*_miss Xoxo na_*
*_Zarah bukar_*
*_Ayusha muh'd_*


*_NIKA'DAI๐Ÿ‘Œ๐Ÿผ WRITER ASSO....๐Ÿ˜œ._*



*_pageโ†’3_*

....... Ganin yanda kayan shayin yake yasata rarrabama kowa akofi ta ajiye, gamawarta babu dad'ewa saiga su Amrah sun fito da gudu.
Jikin babasu suka fad'a suna fad'in daddy?.
Ya ce, "na'am twin's d'ina kuntashi lfy?.
Lfy lau, daddy yaushe zamu koma gidanmu?, nan gidan babu dad'i sai zafi babu AC.
Murmushi kawai yamusu, yakama hannunsu suka sakko k'asa inda Asma'u tahad'ama kowa shayi.
Dai-dai nan Lubna tafito, taci kwalliyarta cikin pink d'in shadda sai zabga k'amshi takeyi.
Afrah data kur6i shayi tayi saurin zuboshi ak'asa tareda cillama Asma'u bread d'in data bata bayan tashafeshi da bota, nidai bazan sha tea d'innanba momy babu dad'ifa, ni dankali da kwai nakeso.
Galala Asma'u tayi tana kallonta, ganin haka itama Amrah tayi cilli da nata gefe.
Ya Umar duk yana jinsu amma yay kunnen uwar shegu dasu sai danna shayinsa da bread yakeyi hankali kwance.
Lubna ta harareshi, tokaji sufa bazasu iya shan wannan tea d'inba maikamada ruwan wankin kai, koni wlhy bangoyi bayan sushaba tundasu ba dabbobi bane.
d'ago idanunsa dasukayi d'anja yayi yana kallonta, baice komaiba yamaida kamsa yacigaba dayin break d'insa.
Asma'u ma tea d'inta taja tahausha batareda tasake kallon inda Lubna da yaranta sukeba.
Aiko ganin haka yasa Lubna fara zubar da ruwan masifa da tijara, sai zabgama Ya Umar gori takeyi.
Wai aii babantane dama silar arzik'in nasa, wlhy tayi nadamar aurensa Dan aurensa bai amfaneta da komaiba sai fad'awa tarkon wahala, dan haka dolene yasaketa ita bazata zauna dashiba taringa shan ruwan wankin kai amatsayin shayi.........
Haka taita zabga ruwan masifa babu Wanda ya kulata barema ya tanka mata, Asma'u tana gamawa ta tattara komai takoma d'akinta.
Shima mik'ewa yayi yashige nasa d'akin.
Itama ganin babu sarki sai ALLAH taja hannun Afrah da Amrah suka bar gidan.

Bayan wasu 'yan mintina Umar Fharuk yafito tsaf sanye cikin k'ananun kaya sai zabga k'amshi yakeyi.

Araina nace bawan ALLAHnnan ya iya d'aukar wanka wlhy.

d'akin Lubna yashiga, amma saiyaga wayam, baice komaiba yafito yashiga na Asma'u.
Tana falo kwance a doguwar kujera, chart takeyi abinta sai faman murmushi take zubawa.
Sallama yay mata sannan yazauna kujerar dake fuskantarta.
Itama tashi tayi zaune ta ce, "sannu.
Bai amsaba amma idonsa na kanta, Ita saima duk kunya takamata, ganin haka yasashi d'auke kai daga gareta, ya ce, " zanje shagunana Dan inaso afara gyaransa muga kuma abinda ALLAH zaiyi, idan kud'in sunkai angama gyaran to ko haya saina bada, idan kuma basu kaiba saimuga kuma abinda yadace ayi.
Jin yayi shiru tagane cewa yagama maganarsa, cikin sanyinta ta ce, "ALLAH ya tabbatar da alkairi aciki, Yakuma mayar da alkairi fiye da abinda aka rasa.
Yaji dad'in addu'arta danhaka ya amsa da ameen yana mik'ewa.
Saina dawo, yay maganar yana fita.
Itama tace ALLAH yatsare takoma ta kwanta.


%%%%%%%%%%%%
Umar nafita daga nan gidansu yanufa, gidan babu laifi mai k'yaune Dan tuni Umar yagyarashi tsaf, komai na more rayuwa saida yazubama iyayensa shi, horn yayi maigadi yabud'e masa gate, saida suka gaisa sannan ya ida shiga ciki, yasamu guri yay fakin.
Da sallama yashigo falon, Rafi'a ce kawai ta amsa cikeda farinciki, amma mama da Mufida da Harris sun amsane babu yabo babu fallasa.
Waje yasamu yazauna ak'asa yana gaida mama.
Dak'yar ta amsa masa, bai damuba yajuya yana amsa gaisuwar Rafi'a, harara ya gallama Harris da mufida Ku baku iya gaisuwa bane?, wai yaushe kuka rainanine?.......
Kafin suyi magana mama ta cafe, a'a yabazasu rainakaba? Tunda kagaza yimusu maganin abinda yadamesu.
Ajiyar zuciya yasauke, idanunsa harsun canja kala, ya ce, ''kiyi hak'uri mama abubuwane sai ahankali, kinsan dai halin Dana tsinci kaina aciki, inda Dane kobasu tambayaba zan basu, amma wlhy yanzu banida sh......
Kai dakatamin!!!, mama takatsesa cikeda tsawa, harni zaka bud'e baki kacema bakadashi, koma kunyar yin k'arya bakaji?, shekaranjiyafa kasiyar da gidanka miliyoyin kud'i amma har bakinka yafurta bakadashi, duk dai Wanda yagaza godema ALLAH to zai godema azabarsa.
Wani yawun 6acinrai ya had'iye, muryarsa cikeda girmamawa agareta ya ce, "kiyi hak'uri mama, wlhy kud'in gidannan acikinsu aka cire aka sayi gidan damuka koma, sauranne kuma zanje nayi gyaran shaguna nana, bammayi zaton kud'in zasu kaini ko inaba.
Hummm tonaji baban tsari tashi kabani guri, kama gyara duniya dasu ba shagunaba, itadai rayuwa duk Wanda yakedashi yagaza taimakon d'an uwansa aiyayi asara....
Da sauri Umar yad'ago yana kallon mahaifiyar tasu, idonsa yayi jajur, Rafi'a ma kuka takeyi, tana mamakin hali irinnan mahaifiyar tasu, kwatakwata mutumce dabata godiyar ALLAH, atunaninta ya Umar yafi k'arfin cin fuskarta kodan k'ok'arinsa nason k'yautata mata, duk cikinsu babu mai hak'urinsa dakuma kula da iyayensu, amma tunda iftila'in nan yasamesa 'yan gidan suka fara canja masa........
Maganar ya Umar ce takatse mata tunaninta, rissainawa yayi ya ce, " sai anjima, ALLAH ya huci zuciyarki, yakalli su Harris ya ce, "zantura muku insha ALLAH.
baki suka washe suduka harda mama, ko kaifa d'an nan to ALLAH yayi albarka kaji, ameen yafad'a ala6ansa.
Suma su mufida sai zabga godiya sukeyi, shidai ficewarsa yayi.
Koda yashiga mota saiya fice daga gidna, tafiya yakeyi amma zuciyarsa namasa zafi, gefen titi yasamu yay fakin, yakifa kansa jikin sitiyari yana duk addu'ar datazo bakinsa, wlhy yana mamakin hali irinna mahaifiyarsu, alokacin da yakedashi tafi kowa sonsa da tattalinsa, kullum addu'a take masa dafatan alkairi dagamawa da duniya lfy, amma abin mamaki tunda komai yak'are masa saita fara canjawa, yanzu babu Wanda tatsana samadashi, batada magana saita ya Abubakar da Anty Sa'a da Harris da mufida, suma Kansu 'yan uwansa sun canja masa gaba d'aya, anty sa'a ce kawai da Rafi'a suke sonsa, yasa handky yana share hawayen dake kwarara a kumatunsa.
Yakai tsawon lokaci awajen sannan yabirka motar yanufi kasuwa.
Alhmdllh aiki yayi nisa Dan anata kwashe tokar gobarar data k'ona shagunan, ganin komai natafiya dai-dai saiya shiga mota yanufi majalissar abokansu.


%%%%%%%%%%%%
Zazzaune suke sunata kwasar hira da dariya, motar Umar tatsaya.
Motsowwww ga k'aban nan cewar Hafiz.
Waye k'aba?, Salman yatambaya idonsa akan hafiz?.
Umar mana, kokai bakada ganewane, cewar Tasi'u.
Al'kasim yata6e baki kaini wlhy fa banason yana ra6armu karya goga mana talauci.
Ashe kagane d'an uwa, yanzufa d'angidan dayake mana tak'ama dashifa ya saidashi.
Kai Dan ALLAH kabeer dagaske kakeyi?.
Wlhy kuwa Hafiz da gsk, nima jafar take bani labari jiya, kunsan shi kunya bazata bari yafad'a manaba.

DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment