Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

hausa novel blog
‹ Home
View web version
Thursday, 22 December 2016
aisha ummi at 01:08
ALHERI DANKO NE 1-50
mmi A'isha: ALHERI DANKO NE!
1⃣
Na UMMI A'ISHA
JAN KUNNE- duk wanda ya canza min wannan labarin ko ya canja sunan taurarin ciki, ko yayi min editing ALLAH YA ISA BAN YAFE BA.
Tafe yake yana cire safar hannun dake hannunsa yana cillar da ita akan tile din dake malale aharabar runfar asibitin, leburorin wurinne suke biyeda shi suna tsince duk abinda ya yar awurin shikuwa sai faman yatsina fuska yake yi sai kace yaune ranar farko wadda yafara karbar haihuwa kokuma yafara operation,ahankali yake tafiya sai kace marar jini ajiki yana sanye da light blue colour din t shirt mai dogon hannu da black din jeans idonsa sanye cikin farin gilashi amma da alama gilashin nasa na gayune bana kara karfin ido bane, duk inda ya ratsa babu abinda kakeji sai weldon sir! Shi kuwa gogan baya magana sai daga hannu domin magana tana mutukar bashi wahala saboda yangarsa da jan ajinsa gashi da iyayi kamar mace amma hakan yana mutukar kara masa kyau kuma da alama iyayi nature dinshine, ayanda na hango fuskarsa zan iya kiyasta shekarunsa bazasu haura 27 ba aduniya,fari ne dogo siriri lange lange kana ganinsa zaka gane baya aikin wahala kuma hutu ya zauna ajikinsa, cikeda yanga ya karasa office dinsa wanda yake jere a rukunin ofisoshin manya likitoci ( consultants) wani office yabude yashiga wanda asaman kofar aka manna wani dan katako aka rubuta DR TAFIDA ajiki da manyan harrufa, ahankali yashiga cikin office din wanda yayi tsananin tsaruwa kamar ofishin shugaban kasa, kan wata doguwar kujera baka yaje yakwanta yamike yatasa kansa da hannun kujerar yafara cire (neck tied) din wuyan rigarsa yacire gilashin fuskar sa yalumshe manyan idanuwansa wanda suke zagaye da bakaken gashi masu mutukar baki sai da yadan huta sannan ya mike a hankali tamkar mace ya isa kan teburinsa yadanna wata kararrawa aguje wasu fadawa guda uku sanye cikin jajayen kaya suka shigo, suna shigowa suka fara zabga kirari, Allah ya taimaki mai girma tafida, dan sarki jikan sarki kuma sarkin gobe da yardar Allah, Allah yakara maka nisan kwana!
[6:56PM, 11/11/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE!
2⃣
Na UMMI A'ISHA
Hannu yadaga musu take sukayi shiru saboda sun gane nufinsa kuma dama can shi baya son yawan magana duk maganarshi atakaice yake yinta itama sai takama mutuka amma in bakamawa tayi ba sai dai yayi umarni da hannunsa, kallonsu yayi yanuna musu kan table dinsa tuni suka zabura suka fara harhada takardun dake kan table dinsa gamida dibar wasu files manya, laptop dinsa da brief case dinsa suna gama harhadawa sukayi waje yayinda shi kuma dr tafida ya sake mikewa a kujerar da yake kai sai da ya shafe sama da minti 20 ahaka sannan yatashi yahau kan kujerarsa ta aiki yajawo drawer dinsa yaciro tabar wiwi (ganye) yadauki ashana ya kyasta yafara busa hayaki, wani dan madaidaicin glass cup ya ajiye musamman akan table dinsa inda yake tara tokar tabar da yakesha kuma da alama yana sha akai akai domin har kofin yakusa cika da tokar tabar, zukar tabar wiwin yaci gaba dayi har ta kare sannan ya kishingida ajikin kujerarsa nanma yashafe fiyeda minti goma sannan yatashi ya dauki phones dinshi da gilashinsa yafita daga office din yana fita fadawansa suka zabura suka nufi motarsa dasauri suka bude masa gidan baya yashiga yazauna suka rufe kofar motar suka runtuma tasu yayinda daya daga cikinsu yashiga mazaunin direba ya zauna yatashi motar ya harba suka bar harabar cikin asibitin.
[7:33PM, 11/11/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE!
3⃣
Na UMMI A'ISHA
Fita sukayi daga harabar asibitin mutane sai kallon motocin nasu sukeyi gamida daga musu hannu amma dan mulkin yana daga kishingide acikin kujerar baya hannunsa rikeda jaridar daily trust yana karantawa da haka har suka isa kofar fada inda anan gidansu dr tafida yake, wani makeken gida nagani gaba dashi kuma filine babba tuni digarawan dake zaune abakin kofar gidan suka mimmike tsaye saboda ganin motar tafida,kan motocin suka kutsa cikin babban gidan wanda yasha zane iri iri da adon kala kala irin na sarakai nidai ummi Aisha tun daga nan nagane cewar gidan sarki nashigo domin gaba daya tsarin gidan namasu sarauta ne, cikeda iyayi da takama hadida kasaita dr tafida yafito daga cikin motar yatasamma cikin gidan wanda akalla sai da aka wuce zauruka sunfi 5 sannan yakarasa wani babban fili mai dauke da part part akalla zasu kai guda 5 kansa tsaye yawuce wani sashe mai mutukar kyau wanda yasha ado da kwalliya, budewa kofar falon yayi yashiga nan nahango wani dattijon mutum wanda akalla shekarunsa zasu kai 65 yana kishingide akan kilisan dake malale acikin falon wanda yawansu zai iya kaiwa guda biyar kala kala gashi jikin bangon dakin yasha zane na sarauta, gefensa tumtum ne wanda yajingina ajiki ga kayan marmari nan agefe dangin itatuwa kamar su inibi, tufa, ayaba, kankana, gwanda, zaitun, ruman, da sauran kayan itatuwa cike cikin wani dan madaidaicin kwando wanda aka tanada musamman dan adana kayan marmari, cikeda alamun gajiya yayi sallama ahankali yashiga wannan al'adarsa ce duk lokacin daya dawo daga office sai yaje ya gaida mahaifinsa da mahaifiyarsa,washe fuska dattijon yayi ya amsa sallamar da Wa'alaikas salam wa rahmatullahi wabrakatu, barka da zuwa ibrahim cikin jin dadi yakarasa inda mahaifin nasa yake yazube akasa yafara kwasar gaisuwa,barka da hutawa mai martaba dafatan mun sameku lfy, ya akaji da jama'a? Cikin jin dadi yace alhamdulillah ibrahim dafatan ka dawo lfy? Lfy lau yafada yana murmushi gamida mikewa yana fadin nabarka lfy ranka yadade, Allah yakara nisan kwana, Allah yaja zamani.
4⃣
Yana fitowa ya gangara izuwa wani sashen nagaba wanda tun daga nesa nafara hango bayi da kuyangu sai faman kaiwa da komowa suke, wasu suna aikace aikacen gida wasu kuma suna ta faman shige da fice tunda tafida yadoso su suka fara zubewa suna dibar gaisuwa barka da dawowa mai girma tafida, takawa lfy dan sarki jikan sarki, tafiya sannu sannu kwana nesa sarkin gobe, hannunsa kawai yake cira musu amma ko kala yakasa furtawa sai dai da alama sun san halin tafidan domin hakan bai hanasu cigaba da gaishe shi ba, ko kallo basu isheshi ba balle ya amsa gaisuwarsu wannan dalilin ne yasa mutane da dama suke kiransa da mai girman kai wasu kuma suce yanada iyayi da wulakanci to koma dai menene da alama iyayin nature dinsa ne
[8:36PM, 11/11/2015] Ummi A'isha: Tamkar wani mai ciwon kafa yaci gaba da tafiya har ya cimma sashen mahaifiyarsa hajiya Kilishi wadda yake tangamemen gaske yana shiga kasaitaccen falon nata wanda yasha adon kayan alatu yafara cin karo da bayinta wasu sunata aikin gyaran falon wasu sunata wawwatsa wani abu mai mutukar kamshi kamar turaren wuta suna ganinsa suka durkusa barka da shigowa mai girma tafida! Kai kawai ya gyada yawuce cikin dakin inno kamar yadda yake kiran mahaifiyar tashi, akan wata katuwar darduma ya hangota tana zaune ta jingina bayanta da babban filo kafafuwanta kuma ta dorasu kan tumtum wata baiwa sai aikin mammatsa mata kafafun take, da sallamarsa yashiga yana shiga wannan baiwar ta zabura barka da zuwa yallabai, bai bata amsaba tatashi tafice, agefen gadon mahaifiyar tashi ya zauna wani irin gadone nakarfe mai runfa fentinsa kalar ruwan hoda yasha lallausar katifa da shinfidu na alfarma ga kamshi mai dadi dayake tashi daga cikin dakin, barka da hutawa inno yafada yana wani lallausan murmushi, yawwa barka da zuwa tafida tafada tana murmushin itama, kallo daya zakayi mata kagane cewa mahaifiyarshi ce domin babu ta inda ya barta akama, kamarsu daya dashi kuma da alama tana jidashi sosai, macece mai fara'ar gaske kuma bata tsufa ba dan shekarunta bazasu wuce 45 amma bazaka taba gane hakan ba saboda jikinta bai nuna ba ko kusa, cikeda kulawa tace zakaci abinci ne yanzu? Kai ya girgiza tamkar wani karamin yaro yace a'a inno sai anjima yanzu bacci nakeji, to atashi lfy tafada tana murmushi,murmushi yakuma yi yakwanta akan gadon mahaifiyar tashi yaja filo yatasa kansa dandanan bacci yayi gaba dashi, tashi inno tayi takoma falo tazauna gudun kada azo adameshi yana bacci.
5⃣
Karfe 3:40 yatashi daga baccin da yakeyi yafito idonsa duk yayi kalar masu bacci afalo ya taradda inno tana salla dan haka bai tsayaba yawuceta yafita daga lungunta yanufi nashi yana shiga yafada toilet ya hada ruwan zafi yayi wanka yafito yasaka farar t. Shirt mai gajeren hannu yasa wando jeans baki yafesa turaren FOGG yafito yanufi masallaci lokacin dayaje har anshiga salla, yana idarwa ya fito ya wuce ma 'ajiyar dawakai yasamu an shirya masa dokinsa anyi masa shimfida an gyarashi domin fita kilisa bai bata lokaci ba yahau suma fadawansa wanda suka hada da sarkin fada, sarkin mota, da maja sirdi suka hahhau nasu suka fito daga gidan ahankali suke tafiya tacikin garin har suka fita suka shiga dokar daji, dama idan da sabo sun saba dan kusan kullum sai tafida yafita kilisa, kilisa tana daya daga cikin abubuwan da suke burgeshi a harkar sarauta, tafiya kawai suke suna shakar iskar dake ratsa dajin sannan suka billa tawata hanyar domin komawa gida alokacin mangariba takusa yi har ta kawo jiki, suna zuwa gida ana kiran salla, akasalance tafida yasauka daga kan kosasshen dokinsa yayi alwala yashiga masallaci ana idar da salla yafito adaidai lokacin wata hadaddiyar mota tashigo baka kirar croutoure mai tsananin kyau ajiki an rubuta TAFIDA 1 kallon motar yayi yai tsaki yawuce gaba, agabansa aka yi packing din motar aka fito wani saurayine wanda zai kaishi atsaye kuma ashekaruma bazai fishiba yafito daga cikin motar yana dariya Allah yaja zamanin tafida, batare da tafidan yayi masa magana ba yawuce yafara tafiya shikuma yabishi abaya har suka karasa sashen tafidan suka shiga, afalo suka zauna cikin muryar iyayi tafida yace wai kai faisal meyasa bakada mutunci ne? Motar tawa kadauka katafi yawon iskanci? Dariya yayi wanda aka kira da suna faisal yace haba abokina kaima iskancin nan kana dan tafabawa, fuska tafida ya yamutsa, ni bana wani iskanci kaine dan iska, ok naji ni dan iskane saboda ina neman mata kai kuma dan ganye? Filon kusa dashi tafida yadauka yajefeshi kai dan iska ne idan ni dan ganye ne ai dasauki tunda har yanzu ni saurayine cikakken saurayi kuma, dariya abokin nasa yayi dakyau virgin boy, amma dai abi ahankali banda ganganci,shiru tafida yayi bai kara magana ba domin shi baya doguwar magana idan kajishi yayi magana mai tsawo to da mahaifinsa ne ko mahaifiyarshi ko kuma abokinsa faisal.
[1/20, 11:29 AM] Ummi A'isha: [7:23PM, 11/12/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE !
6⃣
Na UMMI A'ISHA
Tashi tafida yayi ya shiga daki yahaye gado yakwanta minti kadan faisal yabiyoshi cikin dakin abokina ya zaka kwanta bayan ba mugama magana ba? Kai malam bana son surutu, eh nasani ai shiyasa nake son na sanar dakai cewa na dauki wadannan kudin naka nayi sadaka dasu, tsaki tafida yayi mtwww to ina fata ba iskanci kaje kayi da kudina ba? Murmushi faisal yasake yi wai kai finka laifi nayi? Kaima fa mai laifi ne, kana shan ganye over ni kuma ina neman mata jifa jifa ba koda yaushe ba, murmushi tafida yayi yatashi zaune, to ai ni matan ne ma tsoronsu nake, gaba daya ban san ta inda zanbi ba yanzu haka idan ka ajiye min mace wlh ban san yadda zanyi da itaba, wata irin dariya faisal yayi hahahaha! Ammafa kacika dan rainin wayo, ta ina kake karbar haihuwa? Kaida ka karanci mata kasan yadda suke, karfa ka manta kai likitan matane su kake gani kake dubawa akoda yaushe, dan malalacin murmushi tafida yasaki to sai aka fada maka kuma nasan hanyar? Karya kake kasani mana, dariya tafida yayi kai dan iska ne, wlh duk ranar da mai martaba yasan kana neman mata sai ya tube rawanin da ya daura maka,cikin dariya shima faisal din yace kamar yadda kaima mai martaba zai tube rawanin daya daura maka ba duk ranar da yagane kai mugun dan ganye ne, murmushi tafida yayi ra'ayina shine nasamu cikakkiyar budurwa kamar yadda nake cikakken saurayi, taba baki faisal yayi eh munji kai saurayine amma ai dan ganyene, dariya tafida yayi duk da haka dai nafika,ni yanzu ma ka kyaleni wlh yunwa nakeji sai da inno tace naci abinci dazu nace bacci zanyi amma bari nayi mata waya akawo mana, wayarshi ya dauka kirar yota phone yakira inno yace akawo masa abinci shida faisal ba awani jimaba sai ga kuyangi guda 2 sun shigo hannuwansu dauke da tirarrika na silba manya manya anan suka ajiye suka fita, suna fita faisal ya fara bubbude kwanukan abincin, abinci ne kala kala na gargajiya saukowa tafida yayi suna ci suna hira har suka gama, suna gamawa suka tafi masallaci sukayi salla suka shigo gida afalo faisal yazauna yafara waya da yanmatansa shi kuma tafida yawuce daki yafada kan gado yajanyo tabar wiwi yafara zuka.
7⃣
Washe gari dasafe dr tafida yashirya tsaf cikin shirinsa nafita office bakin wando yasa da bakar t.shirt mai dogon hannu yadora jar jacket asama yasa bakin takalmi cover shoe
[7:38PM, 11/12/2015] Ummi A'isha: Yafesa turaren fogg yafito lokacin faisal yanata bacci kasancewar shi a ministry for local government yake aiki baya fita dawuri shikuwa tafida 7:30 yasaba fita office, yana fitowa sarkin fada da sarkin mota sukazo suka zube suka fara zabga kirari barka da fitowa mazajen fama hadiri sa gabanka inda kakeso, murucin kan dutsi baka fitoba sai da ka shirya, atafe dakyau, atsaye dakyau amma azaune kafi dadin kallo dan ahmadu jikan sani gyara kintsi giwa kinfi karfin waiwaye, kura ko kin mutu kinfi karfin kare, wani kaya sai amale wane jaki, cikeda takama yace barkanku da safiya yawuce cikin gida yanufi dakin inno mahaifiyarshi alokacin har ta harhada masa kayan karyawarshi tsaf ta zuba acikin akushi mai kyau tana jiran shigowarsa, yana shiga yazube agabanta tana kushingide hannunta rikeda carbi tana ja sukuma bayinta har sun fara aikace aikacen da suka saba yi, barka da asuba inno yafada idonsa akasa, barka da tashi tafida, kafito lfy? Lfy lau inno, to Allah yabada sa'a, Allah ya tsareka, Allah yadawo dakai lfy, amin inno nabarki lfy, tashi yayi yafita yanufi sashen mai martaba lokacin shima yana zaune afalonsa yana karatun alqur'ani mai girma, cikin girmamawa tafida yadurkusa barka da asuba ranka yadade, cikin murmushi yace yawwa ibrahim har anfito? To Allah yatsare Allah yabada sa'a, amin mai martaba yafada yatashi yafita inda aka adana motarsa yanufa aka bude masa gidan baya yashiga yazauna cikeda nuna isa yake daddana wayar hannunsa fadawa sai kawo gaisuwa suke yi amma yakasa amsawa,asibitin Rasheed shekoni specialist hospital suka dosa inda tafida yake aiki.
[7:48PM, 11/12/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE!
8⃣
Na UMMI A'ISHA
Suna zuwa kamar kullum yafito yashiga office dinsa wanda yake jere ajerin gwanon ofisoshin kwararru na asibitin, yana zama wata nurse tashigo tana sanye da fararen kaya,morning sir! Morning ya amsa mata idonsa yana kan laptop dinshi yana daddannawa, sir akwai patient wanda jiya kayiwa operation tofa har yanzu bata farfado ba, cikeda damuwa ya tashi domin shi yana tausayin mata duk lokacin dayaga mace acikin halin rashin lafiya sai yaji kamar zaiyi kuka, maternity yanufa wannan nurse din tana biye dashi abaya ita dai wannan likitan yana burgeta domin yasan aikinsa matsalarsa kawai yanada girman kai ga nuna isa kamar shine sarkin ko dan sarauta ne? Yahadu sosai ga kudi da sarauta ga ilmi ga uwa uba kyau, yana shiga maternity yafara bin patient din daya bayan daya yana dubasu har yagama yakoma office dinsa alokacin yafara ganin marassa lfy wadanda suka zo ganin likita kuma gaba dayansu matane domin shi mata kawai yake dubawa baya duba maza sai wurin 11 yagama ganin marassa lfy yayi breakfast yatashi yashiga round.
[8:16PM, 11/12/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE!
9⃣
Na UMMI A'ISHA
Yana dawowa daga round yanemi wuri a office dinsa yazauna lokaci lokaci fadawansa suna lekowa domin ganin lafiyarsa, sai misalin karfe 5 yatashi lokacin yafito daga theatre cikin gari suka shiga akan hanyarsu ta tafiyane suka ratsa tawani dan kauye anan yaga wata makekiyar gona wadda akalla zata kai kilo mita 5 anyi shukar shinkafa aciki, shukar tayi kyau sosai sarkin mota ya yiwa magana cewa ya tsaya cikin sauri ya taka birki yaja ya tsaya yabude kofa yafito suma fadawan firfitowa sukayi suka tsattsaya, gonar ya zubawa ido ta kayatar dashi hakika wannan zatayi daidai da wurin da yake nema domin gina business suit dinshi hadida gidan shakatawarsa motar ya koma yashiga ya zauna, fadawansa suka shisshiga suka nufi gida tun da suka shiga yasan cewa mai martaba yau yana fada dan hakan fadan yashiga wacce ta kayatu sosai, mai martaba yana zaune akan wata karagar mulkinsa ta alfarma wadda tasha ado da zinare, gefe daga hannunsa nadama wazirine da galadima ga chiroma, kusa dashi kuma hakimin cikin garine, daga hannun hagu kuma wani dan dattijone zaune wanda shekarunsa zasu kai na mai martaba kusa dashi kuma san turakine wato faisal aminin tafida, cikin sallama tafida yazauna yayi gaisuwa yatashi yashige cikin gida yawuce dakin inno yau bai wani jimaba yafito yashiga dakinsa yayi wanka yafito cikin bakar riga da bakin wando, yanufi lambu wanda yake girke acikin gidan, wurin yasha shukoki na kayan marmari ga wata korama daga tsakiya tana gudana can gefe wasu kujerune hadaddu aka ajiye saboda hutawa kan kujerar yaje yazauna amma ko minti 5 bai yiba yatashi yafita yanufi dakinsa yashiga yakunna tv yakamo tashar kwallo yafara ganin wasan arsenal da man u, wasan yafara kayatar dashi faisal yashigo remote ya dauka yakashe tv din domin yasan yanzu zasuyi fada saboda faisal dan arsenal ne shi kuma tafida dan man u ne gashi ancisu har 2-0 yasan idan faisal yagani yau zai sha tsiya, kusa dashi faisal yazauna.
[8:32PM, 11/12/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE!
1⃣0⃣
Na UMMI A'ISHA
Kusa dashi faisal ya zauna yafara dariya ko kallonsa tafida bai yiba yadauke kansa shikuwa faisal sai dariya yakeyi, haushi tafida yafara ji yace ya isheka haka,dariya faisal yayitayi sai da yayi mai isar shi sannan yace kasan me nake yiwa dariya? Jiya jiyan nan kagama yimun bayanin kaifa bakasan hanyar da zakabi ba awurin mace idanma aka ajiye maka mace bakasan yadda zaka bida itaba to sai gashi yanzu za abaka mace nan da sati 2,kaga ashe kenan ka kusa kasamo hanyar ko? Wani kallo tafida ya watsa masa ni zanyi aure amma ba yanzu ba sai nan da 3years dariya faisal yakumayi kasan Allah? Kai angone kakusa ganin hanya, wai kai waya fada maka aure zanyi ne? Uhm abokina bazaka yarda da abinda nake fada maka ba sai kaji kira daga wurin mai martaba sannan zaka gasgata ni, tsaki tafida yayi insha Allahu kai zai yiwa aure amma baniba,ni daba dan iska ba wa zaiyi min aure yanzu? Kai da kasan mata kake nemansu ai kai yadace ayiwa aure, dariya faisal yayi kasan Allah? Wlh kakusa zama ango kai barima kaji dazu daka zo kasamemu da mai martaba wlh maganar aurenka akeyi kuma nan da sati biyu za ayi, cikeda mamaki tafida ya kalleshi wai dagaske kake yi? Wlh Allah dagaske nake tafida wlh aure mai martaba zaiyi maka dazu akanka mukayi meeting da yamman nan kuma wani abin burgewar ma zaka samu virgin girl kamar yadda kake virgin boy, zumbur tafida yamike ni za ayiwa aure yanzu? Wanne laifin nayiwa mai martaba da zai hukantani ta wannan hanyar? Wa zai aura min? Yaya kamanninta suke? Girgiza kai faisal yayi wlh ban saniba abokina, to nima dai ummi Aisha ban saniba sai muci gaba da bibiyar tafida, masu karatu muje zuwa kubiyo Aisha.
[1/20, 11:29 AM] Ummi A'isha: [8:53PM, 11/12/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE!
1⃣1⃣
Na UMMI A'ISHA
Kallon faisal tafida yayi ai kuwa wlh bazai taba yiyuwa ba nikadai ne da agidan? Akan me za ayi min wani aure yanzu kai ba gaka nan ba haba da Allah wlh bana so babu wanda zai rabani da gidan nan yanzu, kuma wlh duk yarinyar da tayi kuskure ta aureni sai ta raina kanta, dariya faisal yayi wadda takara kular da tafida kaga bani zaka fadawa ba kamata yayi kaje gurin mai martaba kayi masa wannan bayanin amma nidai ina tayaka murna sai dai shawarata agareka itace kasan mai martaba baya yin magana 2 daga yayi magana to yagamata so be careful kar kaje kajawa kanka, kaga mitumin nan nadazu daka samemu afada dashi? Shine mahaifin yarinyar wlh kayi dacen suruki cikeda bakin ciki tafida yace malam banfa tambayeka ba dan haka kayi min shiru banza kawai dariya faisal yaci gaba dayi ganin haka yasa tafida ficewa daga dakin yatasamma lungun inno wadda yake da dan tazara daga sashensa, yana shiga yatarar da bata cikin dakin sai kuyanginta suna gyara dakin kusan ko wanne lokaci dakin nata cikin gyaransa ake, shiyasa koda yaushe yake cikin tsafta tamkar dakin sabuwar amarya, suna ganinsa sukayi waje suka bar aikin da sukeyi, gadon inno ya dale yakwanta idan dasabo kowa agidan yasaba ganinsa akan gadon inno koda wanne lokaci yagadama zai zo yahaye yasha baccinsa akai kamar wani yaron goye.
[9:36PM, 11/12/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE!
1⃣2⃣
Na UMMI A'ISHA
Rufe idanuwansa yayi amma yasan ba bacci zai iya yi ba maganganun faisal ne kawai suke dawo masa jiya jiyan nan kagama fadamin idan an baka mace baka san yadda zakayi da itaba sai gashi nan da sati 2 zaka zama ango an baka mata, zunbur ya tashi zaune jin abin yake kamar a mafarki aurefa? Daidai lokacin inno tashigo taganshi zaune akan gadonta, tafida ashe kana nan? Nima daga wurin mai martaba nake yakira ni yabani wani sako wurinka ras! Gabansa yafadi wato maganar faisal ta
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment