Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

CIN AMANA KO FANSA
Zahra muhammad Mahmud
Made by:- Shuraih Usman
Ku shiga nan kuyi like na shafinmu http://fb.com/hausaebooks

[4/26, 10:10] Zahra Surbajo: 📓📓📓📓📓📓📓📓

*CIN AMANA*

*KO*

*FANSA*

📓📓📓📓📓📓📓📓

*(TRUE LIFE STORY )*





Zahra Muhammad Mahmud





® *PURE MOMENT OF LIFE WRITERS*

*PML*



*Godiya ga Allah mad'aukakin Sarki, tsira da Aminci sutabbata ga annabinmu Muhammad sallallahu ala'ihi wasallam.*



*Wannan labari ba k'agagge bane yafaru dagaske,duk abinda ke ciki anyine da gaske, suna kawai na wa'inda abun yashafa Nasauya,da d'an abinda ba'a rasaba.baya ga haka babu abinda Nasauya*



Ya Allah, yadda nafara rubuta littafinnan lfy,Allah kasa nagamashi lfy.





*page 1*





Y'anmatane su biyu, y'an kimanin shekara goma sha shida da haihuwa,suka rugo da gudu zuwa Cikin d'akin kakarsu suna ta kiranta, uniform ne ajikinsu, alamar daga makaranta suke,



"Grany!!! Grany!!! where are you? we miss you so much,mekika tanadarmana yau."

A zaune suka ganta tana Kallonsu, k'arasawa jikinta sukayi, suka rungumeta, kowacce tamata kiss a gefen kumatunta.



"Kai ni banason iskancinnan naku, ace gird'a gird'a daku Amman har yanzu baku girmaba,wato abinnaku gaba yakeyi,yau kuma harda sumbatata ko?".



Dariya sukayi suka K'ara rungumeta,Khairat ce tace,



"Haba Grany, danma kinsamu munzo gidanki yau shine harda yimana wulak'anci,ni dama wlh banso zuwa ba,Fatima ce da shegen naci tace muzo gidanki,gashi daga zuwanmu kinfara halinnaki."sakin Grany tayi takoma gefe tazauna,



Fatima tace, "Wayyo Sis kiyiwa Grany uzuri, bakiga se kallonmu takeyiba, alamun taji dad'in ganinmu, hala taji haushin bamuyi sallama bane, ko Grany?",tawaiga Tana kallon kakar tasu.



Grany dariya tayi sannan taruk'osu dukansu tace ,



"Haba kha'iriyya ta fushi kikeyi danine?, nicefa babbar k'awarki ranar bikinki,"dariyace takwacemusu dukansu,khairat tace,





"Wai,dagwargwajiya kenan Grany ansha gwargwaro ranar aurena,"cigaba sukayi da dariyar.



Ranar wuni sukayi agidan Grany,seda la'asar suka mata sallama suka wuce gida.





Khairat da Fatima sa'annin junane, dan anhaifi Fatima da Sati biyu aka haifi Khairat.



Iyayensu mata ya da k'anwane,haka zalika, Iyayensu maza suma wa da k'anine.





Alhaji Nasir Abubakar shine mahaifin Fatima,suna kiranshi da Abba,mahaifiyarta Mesuna Hajiya Salamatu suna kiranta da Umma.yaran Alhaji Nasir hud'u biyu maza biyu mata,Yaya Jameel shine babba, se Yaya Umar mebimasa,se Fatima, da autarsu Yasmeen.



Alhaji Mukhtar Abubakar shine mahaifin Khairat,suna kiranshi da Daddy, Wanda wa yake agurin Alhaji Nasir,uwa d'aya uba d'aya,

Matarshi d'aya Hajiya Binta,wacce take yaya ga mahaifiyar Fatima, yaransu guda shida,hud'u mata biyu maza,Aunty Fareeda Itace babba ,se Yaya Kamal mebimata,se Aunty Khadija,se Kha'irat, se Fa'eeza,da autansu Yusuf.



Gidan Alhaji Nasir dana Alhaji Mukhtar ahad'e suke sede katanga data rabasu,

Suna zaune da iyalansu agarin Kaduna awata anguwa Mesuna Tudunwada dede layin k'osai kan katagum road,



kansu ahad'e yake haka na iyalansu komai nasu tarene ko kasuwancin suma a tare sukeyi inda suke Saida kayan sawa kama daga na maza zuwa na mata, da yara, komai suna saidarwa a kasuwar checheniya dake Kaduna.



Zumunci ne me k'arfi a tsakaninsu inda ahalin yanzu babban d'an Alhaji Nasir yana auran Y'ar gidan Alhaji Mukhtar Khadija, harda yaransu guda biyu suna zaune a kinkinau dake Kaduna,ita kuma Farida wani ma'aikacin nepa take aure harda yaranta guda uku.



Rayuwar wannan family rayuwace mecike daso da k'aunar juna.



Grany,wacce sunanta na aynihi Hajiya Asiya amman jikokinta nace mata Grany,yayinda y'ay'anta da sirikanta kecemata Hajiya, Itace tahaifi Iyayensu maza,kuma a kakanninsu ita kad'aice tarage musu sauran duk sunmutu



Kha'irat da Fatima kansu ahad'e yake ko bacci tare sukeyinsa babu abinda ke rabasu suna matuk'ar k'aunar junansu ko kad'an ba'ajin kansu,ajinsu d'aya Boko da Islamiyya, suna da k'ok'ari sosai dan sotari twins ake cemusu,dan duk jarabawa sede suyi bracket, kowa cikinsu beson b'acin ran d'an uwansa.





Maman Yusuf

[4/26, 10:10] Zahra Surbajo: 📓📓📓📓📓📓📓📓📓

*CIN AMANA*

*KO*

*FANSA*

📓📓📓📓📓📓📓📓📓





Zahra Muhammad mahmud





*LOSING SOMEONE WHO DOESN'T RESPECT OR APPRECIATE YOU IS ACTUALLY A GAIN, NOT A LOSS.*





*pure moment of life writers*

*p.m.l*





*page 2*





Rayuwar Fatima da Khairat rayuwace mecike da son juna.



Khairat irin matannanne masu azababen kyau don ko daga nesa ka hangota kasan me kyauce,farace me hanci ga yalwar gashi tamkar indiya, komai da akeso ajikin mace Allah yabata,wannan baiwa da Allah yay matane yasa ta d'auki dogon buri akanta tanaji da wannan kyau da Allah yay mata shiyasa ko saurayi take burin me kud'i,in talaka yazo gurinta seyasha wulak'ancin dako a hanya yaganta baze sake marmarin kulataba,

har k'awayensu na makaranta sunsani shiyasa yanzu kirarin dasuke mata shine matar Manya,jin dad'i take insuka kirata da sunan.



Fatima nada kyau dede misali Amman bata Kama k'afar khairat ba,sede dirin halitta na y'a mace itama Allah yabata,batada da wulak'anci ga kowane ne yanuna yana sonta burinta de Allah yabata miji nagari.



Akan wannan halin na Khairat sunsha yin fad'a da Fatima sabida hakan,inkaji fad'ansu to akan wannan halin na Khairat ne Sam Fatima batason halin.





Yau ba makaranta dan haka su Fatima suka tsefe kansu sukaje Kitso,ahanyarsu ta dawowane wani me liffan yatsaresu,saurayine matashi ba laifi akwai natsuwa da kamala atattare dashi sallama yamusu,



"yan mata barkankude," yafad'i yana kallon Khairat da alamun ita yabiyo.



Khairat bata amsaba sema wata uwar harara data watsa mishi.Fatima ce ta amsa,



"barka kadai malam".



murmushi yayi sannan yace,





"Don Allah kuyi hak'uri da tsaidaku da nayi wlh son yar uwarkine yakamani tunda na hangota duk danaga ita ranta kamar beyi na'am daniba Don Allah kubani number d'inku da Address dannazo har gida nasameta,"yafad'i yana kallon Khairat.



"Dank'ari mune zamu baka address d'inmu harda number waya,to wlh bakaji da kyauba gwara tun wuri kanemi dede kai danmu ba sa'anninka bane dahar zaka wani ce kana sona Allah yakyauta wlh farashin gold beyi karyewar da za'ayiwa jaki mangala dashi ba,"tafad'i rai abace taja hannun Fatima da niyar suwuce subarshi, kwace hannunta Fatima tayi ta tsaya,itako Khairat gaba tayi abunta,cikin sigar tausayawa Fatima tace mishi,



"Don Allah malam kayi hak'uri wlh banji dad'in abinda tayi maka ba, kuma in zan baka shawara ka hak'ura da ita wlh tunda tanuna bata sonka banajin akwai abinda zesa tasoka kayi hak'uri kanemi wata don katsira da mutuncinka kaji,don Allah kuma kayafemata pls,"tafad'i cikin sigar rarrashi.





Murmushi yayi Yace, "bakomai baiwar Allah nagode dake kika saurareni, Amman kinsan sharrin so wlh jinake bazan iya hak'ura da ita ba kitaimaka kibani address d'inku da sunanku pls banak'i shawarar ki bane zuciyata ce bazata iya hak'uraba ki taimakamin pls",yafad'i kamar zeyi kuka.



Ba musu Fatima tabashi abinda ya buk'ata dan ta tausaya mishi daga k'arshe tamishi fatan alkha'iri, dazasu rabu yafad'a mata sunanshi Ahmad.



A hanya tasamu Khairat se cika take tana batsewa kotakanta bata biba sabida inda sabo tasaba da halinta, ahaka suka ci gaba da tafiya bamecewa kowa uffan.



Suna shiga gida d'akinsu suka wuce dan ajiye hijabansu ananne Khairat tacewa Fatima,



"Wai don girman Allah sis se yaushene zaki gane darajata tafi k'arfin irin wa'innan samarin? kina zubarmin da ajina wlh ni matar manyan mutanece,yakamata kigane har yanzu ban samu kalar mijin daya dace daniba, amman ke da Kare da doki kowama address d'inmu kike basu suzo su tak'uramin dan Wlh wannan ma nasan kinbashi address d'in watak'ila ma harda rakiyar phone number mitsss,"tayi tsaki ranta ab'ace.



murmushin takaici Fatima tayi ta dubeta tace,



"Sis kenan wani lokacin inkikayi wani abun senaga kamar ba'a family d'aya mukeba,dan de tarbiyya dede gwargwado iyayenmu suna bamu kuma sunsamu a makarantun da ake koyar damu sanin darajar d'an Adam.Haba Sis kituna fa Allah dakanshi yace yakarrama bani adam kewacece dazaki dunga wulak'anta mutane?,kituna Allahn daya baki kyaun dakike wulakanta mutane sabida shi shine yayi kuma wainda kike wulak'antawar bayan yahanemu dayin hakan, tabbas nabashi address sede inyazo shima ki koreshi kamar yadda kika saba,ni narasa mekike nema aduniyar da watarana ko labarinki baza'aji acikintaba, haba Sis yakamata ki farka daga wannan banzan mafarkin dakikeyi."



"Mafarki fa kikace Sis to wlh kece kike mafarki ni reality show nake yi, koma mezakice naji amman wlh babu yadda za'ayi nakai kaina gidan talauci sede kita fad'in abinda kika dama,kuma wlh shima wannan dakanshi ze kama kansa dan bade niba sede wata wlh."kiran da Umman Fatima tai musune yasa suka bar maganar suka tafi gurin kiran.





Maman Yusuf

[4/26, 10:10] Zahra Surbajo: 📓📓📓📓📓📓📓📓📓

*CIN AMANA*

*KO*

*FANSA*

📓📓📓📓📓📓📓📓📓





Zahra Muhammad mahmud





*Pure moment of life writers*

*pml*





*Page 3*





Yau Ahmad yashirya yazo gurin Khairat hira, dakyar tayarda tafito koda tagashine me kirannata wani uban tsaki taja gami dayimasa kallon uku saura kwata,Shiko se Murmushi yake adole ze saci zuciyar ta tun kamin yay magana tarigashi,





"Amman duk yadda akayi agidanku cikin tumaki kake kwana Shiyasa zama dasu yasa kad'auki halinsu,kai jakin inane nace ma bana sonka bana k'aunarka Amman sabida taurin kunne irin na balama yasa kabiyoni gidanmu wlh baka da zuciya sam ni matar manyan mutanece ba irinka ba ubanme kaci ubanme Kabani dan haka kaje kanemi dede kai d'an wahala kawai",ta fad'a tana tsartar da miyau.



Zuciyar Ahmad kamar zata fashe sabida bak'in ciki,tunda yake wani mahaluki betaba cimishi mutunci irin hakaba se yau,hannu yad'aga ze kifa mata Mari sekuma yafasa.



Wata shewa tayi sannan tace,"hattarade d'an samari ni ba irin wa'innan matan bace da ake duka wlh ka kuskura katab'ani sekayi danasani wawa kawai,



Dakyar ya iya cemata,



"Ni acikin tumaki nake Kwana amman wlh bantab'a tsammanin tumaki suna haifar y'ay'an mutum ba se akanki,baki da hankali bakisan darajar mutane ba Kije duniya ce zaki had'u da dede ke komai daran dad'ewa,yana gama fad'amata haka yaja liffan d'inshi yabarta atsaye baki bud'e. Dagudu tashige cikin gida tana kuka kai tsaye d'akinsu tanufa inda ta sami Fatima na kwance tana chatting a wayarta,fad'awa kanta tayi tana kuka, afirgice Fatima ta ruk'ota sabida batasan damuwar Khairat ko kad'an in akwai abinda kesata damuwa toshine ganin hawayen Khairat,arud'e take tambayarta,



"Sis keda waye don Allah Ki sanar dani abinda aka miki zaki sani cikin damuwa pls",cikin kuka Khairat tace,

"Sis nida shegen Ahmad d'innanne yau ancimin mutuncin da tunda nake bawanda yatab'a yimin",tasake rushewa da kuka.



"me yayi miki just tell me",

Cikin kuka takwashe duk abinda yafaru ta fad'amata bata b'oye komai ba,duk da Fatima taji zafin kiran Iyayensu tinkiyoyi dayayi amman Seta daure tace,



"Wow that's good,gaskiya gayennan yaburgeni wlh inason mutumin dayasan darajar iyayensa, ke kin kira iyayensa tinkiyoyi why not baze kira naki da sunanba ?bayan kece kike aykata abinda kowa yagani ze d'auka tinkiyoyinne iyayenmu,ni wlh banji haushinshiba ke nake jin haushi sabida kece kika ja yazagesu,"





"Sis kinada hankali kuwa?, su Abba fa yazaga amman shine bakiji haushinshiba Lalle ma Sis wlh kinbani mamaki,"



Dariya Fatima tayi tace,tana k'ok'arin fita daga d'akin cikin dariya,



"Wayyo ga abin duka amman ba Kara Allah yataroki Sis",tak'arasa ficewa daga d'akin.





Ranar wuni Khairat tayi kuka dan takaicin zagin iyayenta da akayi,wanzami bayason jarfa dama.





Yau ana bikin wata k'awarsu acan cikin unguwar rimi GRA,dan haka Khairat shiri take kamar zata sauya fata dan kwalliya ita ala dole zata samu saurayi me kud'i tunda bikin manyane,Fatima dariya kawai takeyi tana mata fatan shiriya.



Sun isa gidan bikin k'arfe hud'u na yamma nanfa kawayensu aka shiga koda kyan da Khairat tayi habawa tuni tafara shan k'amshi ita ga me kyau Musammam insuka kirata da sunan datake matuk'ar k'aunar wato matar Manya kanta har girma yake k'arawa.



5:30pm suka tafi dinner zokuga Khairat yadda take tafiya kamar Bazata taka k'asaba ita adole zata jawo hankalin mutane kanta Fatima ko gaba tayi ta kyaleta.



Dayake k'awar tasu wani Reps ta aura to gurin dinner y'an majalisu ne sosai suka zo,anyi duk abinda akeyi agurin dinner inda aka bukaci Khairat da Fatima suyi jawabin godiya ga manyan bak'i ,kunsani base nafad'iba,khairat gwalli da iyayi bawanda batayiba me hoto se d'aukarta yakeyi ,har tagama Fatima ta amsa tunda Fatima tafara mgn hankalin wani d'an majalisa me wakiltar Kaduna south,yadawo kanta sosai ta burgeshi shigowarshi kenan yatarar tana mgn,beji Lokacin da Khairat tai nataba.



Koda aka tashi agurin dinner da sauri yasa wani excode d'inshi yakaiwa Fatima wayarshi yace tasa mishi number d'inta amman be fad'i kowaye yaturoshiba kawai yace wani bawan Allah, Fatima ba wulak'anci amsa tayi tasa number tayi flashing anata wayar,Khairat wacce haushin rashin kasuwar datayi yacikata Masifa tadunga yiwa Fatima akan me zata bada number d'inta ga wani banza,Fatima bata kulataba Illa janta da tayi su tafi gida,dagudu me hoton dayayi hotunan bikin yak'araso gurinsu gaishesu yayi sannan yafad'i abinda yakawo shi Wai Khairat yake so😜.ay Khairat rushewa Tay da kuka tashiga tsine mishi tunda yace yana sonta,Fatima ko inbanda dariya ba abinda takeyi dakyar tajata Suka tafi gida.





Maman Yusuf

[4/26, 10:10] Zahra Surbajo: 📓📓📓📓📓📓📓📓📓

*CIN AMANA*

*KO*

*FANSA*

📓📓📓📓📓📓📓📓📓







Zahra Muhammad Mahmud





*pure moment of life writers*

*pml*





*page 4-5*







Koda suka isa gida Khairat gaban mirror taje ta tsaya tana k'arewa kanta kallo,can kuma tasake fashewa da kuka ta fad'a kan gadonsu,Fatima wacce dariya tagama kamata da k'yar ta daure tace.



"Sis lafiyarki k'alau kuwa?, wai kukan me kikeyine haka?".



Cikin kuka Khairat tafara magana.



"Haba ki dubenifa wai ace duk had'uwar nan tawa manyan mutanennan bawanda yakalleni bare yace yana sona,nibama wannan ne yake sani kukaba more than 3hours nad'auka ina Kwalliyar nan Amman wai ace me hotone kawai na burge ay dole nay kuka,"taci gaba da kukanta harda majina.



Fatima ko inbanda dariya ba abinda takeyi sabida gaba d'aya takasa magana abun yabata dariya sosai. Fita Khairat tayi a d'akin sabida dariyar da Fatima take mata.



Tunda wannan D'an majalisa ya amshi number Fatima se yau ya gwada kiranta kimanin sati guda kenan da had'uwarsu,lokacin daya kira suna zaune ita da Y'ar darunta wato Khairat suna labarin wani littafi da ake rubutawa na online writers nawata marubuciya Zahra Muhammad mahmud me suna *Allah gatan bawa*.ajiyar zuciya Khairat tayi tace.



"Ya Ubangiji nima kasa nayi irin wannan dacen da jarumar littafinnan ilham tayi,nima nasamu miji kamar Anwar Tunda nima kyakkyawace",ta fad'i harda d'aga hannu sama,dariya Fatima tayi tace.



"Allah yataro minke Sister".



k'arar wayar Fatima ce takatse musu hirar,number tagani da kamar karta d'aga cande kuma ta d'auka,tace,



"Salamu alaikum".



"Wa'alaiki salam ya ma'abociyar natsuwa da hankali,".



Tsigar jikinta seda ta tashi sabida jin daddad'ar muryar me maganar, katseta yayi da cewa.



"Am sorry princess tunda na amshi numberki ban kiraki ba se yau please ayimin afuwa, al-amurane suka sha kaina tuba nake sarauniyar mata".



Murmushi ne ya sub'ucewa Fatima kamar yana kallonta,sabida ba k'arya muryarshi kad'ai dataji tasa taji takamu da son mamallakin wannan murya.cikin salo najan hankali tace.



"Ammaka afuwa duk da bansan dawa nake maganaba pls can you tell me more about your self?".



muryarta se yau yake k'ara jin dad'in muryar da k'yar yace.



"Am Hydar Jibrin Lamid'o, wanda yaturo kibashi number ranar bikin friend d'inki Jameela sati guda daya wuce, so inbazaki damuba inason address d'inki dannazo mugaisa kinji pls badan na isa ba sedan Allah."



Fatima tunani tashiga yi agame da sunannashi dan ita tabbas tasan d'an majalisarsu me wakiltarsu a Abuja sunanshi kenan,toko suna ne yazo d'aya?, ko shine dakanshi?,kai mezeyi dani?bashi bane.haka tadunga tunani ita kad'ai shine dayaji shurun tayi yawa yakatseta.



"haba princess wlh ba cutar dake zanyiba kidaure kibani address d'in kinji zuwa anjima da yamma zan shigo mugaisa,"ba musu Fatima tai mishi address d'in gidansu,yay mata godiya yace se yazo anjiman sukayi sallama. Tana ajiye wayar Khairat wacce tun d'azu kallonta kawai takeyi tace.



"Sister wlh tunda nake bantaba ganin budurwa me arha irinkiba, haba don Allah shikenan kowa yataya ba jan aji kike siyarwa Wlh kina badamu,nide gani nake yadda akasan address din gidanmu ta dalilinki ko gidan gomna se haka ace ayi mutum sam bajan aji wlh kigyara halinki ni nafara gajiya da hakan,"tafad'i har da tsakinta.



murmushi Fatima tayi tace.



"Sister kenan shi wannan Jan ajin dakike magana ba irinshi addininmu yakoyar damuba, sabida duk wacce takeyin irinshi ba sunanshi Jan ajiba wulak'anta halittar Allah sunanshi wanda kinsani nasani ba abune me kyau ba dan haka ni inde hakan danakeyi shine rashin aji to nayarda har atashi duniya bazanyi ajiba arayuwata".



"to Allah ko yakyauta miki wlh,yanzu kuma wanne d'an wahalar ne yakiraki?"inji Khairat.



"Wanda ya turo nabashi number na ranar dinner d'in Jameela Habib,yacema zezo anjima mu gaisa."





Dariya Khairat ta kwashe da ita tace.



"lalle Sis wato ke baki d'au ishara akainaba kina ganin duk kyannan nawa me hoto kawai na burge agurin,ayko tunda haka ko tafaru akaina Allah Sis may be megadin gurinne ya turo kibashi number,"tasake fashewa da dariya.



Fatima itama dariyar takeyi tace,"to in megadine seme?, shiba mutum bane?,koko shi ba Allah ne yayi shiba?,kinga rabani da wannan shirmen naki koma waye ni ina maraba dashi,tunda wannan Karon gurina megadin zezo ay da sauk'i bagunki naturoshi ba bare ki tsine mishi son ranki."



Wata shewa Khairat tayi tace, "ina wlh Sis ayni nafi k'arfin irinsu sede ke, ni ay matar manyace ko kin mantane?".



"Natuna matar Donald Trump,"

Fatima tabata amsa tana dariyar tsokana ita ta d'auka Khairat zataji haushi ga mamakinta seji tayi Khairat tarungumeta tana fad'in.



"Wlh Sis kinyimin fata me kyau,ni abin yace yana sona wlh auransa zanyi baruwana da kafircinshi yayi addininshi nayi nawa,nazama First Lady a America wai ranar ina zansa kaina dan dad'i".



Tureta Fatima tayi cike da mamaki tace.



"Sis ke har son kud'in naki yakai ki auri kafiri matuk'ar yanada kud'i kuma sunanki ze fita as celebrity a duniya wato zaki iya auransa kenan?Allah yashiryaki lamarinki yafara bani tsoro wlh,"tafad'i cike da damuwa.



Khairat ko ko a jikinta mik'ewa tayi tad'auki gyalenta tace ni natafi gidan su Zainab Umar zan amso note book d'inta na chemistry na kwafa sabida banida complete note sena dawo Ummu shuhada",tafad'i tana dariya tafice a d'akin tabar Fatima baki bud'e.





5:30pm Hydar yazo gidansu Fatima,acikin wata arniyar motarshi Range Rover new model fara tasha tinted glass bak'i sosai bame ganin naciki,numbar motar sunane ansa Hydar 1,gashi yayi shiga ta alfarma wacce duk macen data ganshi seta koka ba laifi Hydar kyakkyawane ajin farko dan yafi Fatima kyau nesa ba kusaba.



Kiranta yayi a waya ya shaida mata gashi ya iso.





Hijabi tasa bayan tad'an k'ara gyara fuskarta tafesa turare tafito zuwa k'ofar gidan, lokacin Khairat bata dawo daga anso littafinba.



Fatima koda tafita wata arniyar mota tagani a k'ofar gidansu wanda batai tsammanin acikinta me nemanta yazo ba, waige waige takeyi tarasa ina wanda yazo gurinnata yatsaya,shiko daga cikin motar K'are mata kallo yakeyi yana k'ara godiya ga Allah daya had'ashi da nutsatsiyar yarinya irinta,ganin tana nemanshine yasa yakirata a waya yace gashinan acikin motar dake gabanta,dasauri yaga ta kallo motar sannan tace.



"to kafito mana,"yace.



"Princess inda hali mushiga daga cikin gidanku in akwai inda zamu zauna peacefully banason intsaya awaje kowa yazo yaganni kinji pls,"amsa tabashi dacewa.



"sekace mara gaskiya".



dariya yayi wacce tasa Fatima k'ara fad'awa kogin sonshi yace.



"watak'ila hakanne banida gaskiyar ay ba laifi bane dan na nemi mafaka daga gareki," murmushi tayi sannan tajuya cikin gidan,gurin maman Khairat tanufa tace mata tayi bakone tade fad'amata yadda sukayi dashi yanzu tanason abata key d'in sit room d'in Abban su,jamata kunne maman tayi sosai akan tade tsare mutuncinta sannan ta bata key d'in.



zuwa tayi tabud'e sannan tafita takirashi awaya tace yafito to yak'araso sushiga daga ciki, ga mamakinta me makon taga yafito setaga ya tuk'o motar har zuwa k'ofar gidan sosai sannan yay parking yafito.



Hasbunallahu wani'imal wakil itace kalmar dake fita a bakin Fatima sanda tai arba dashi,ba iya kyan shine ya ruda ta ba a'a sanin wayeshi a jihar kaduna shine ya rud'ata, shiko se murmushi yake sakar mata me kashe zuciya har yak'araso gurinta bata saniba,Ta tafi tunani hura mata fuska yayi sannan tadawo daga duniyar data tafi,kashe mata ido d'aya yayi yad'aga gira yace.



"yadai princess wannan kallo ay sekisa nafad'i ayimin dariya", kunyace takamata da k'yar tace mishi su shiga daga ciki.



koda suka shiga gaisheshi tayi sannan takawomishi drinks kad'an yasha sannan yace.



"Princess the way you act for the first time dakika ganni nasan kinsan koni waye so no need natsaya ina cemiki nine wane, kawai abu d'aya zan iya sanar dake shine tunda naganki Allah ya jarabceni da sonki so me tsanani,don haka nake rok'on alfarmarki kisoni koda rabin son danake miki ne pls,"yafad'i cikin sigar tausayi.



Fatima bata hana kanta abinda takeso inde be sab'ama addini da al-adar ta ba don haka bata jamishi raiba ta amshi soyayyarsa kuma dama Hydar ba irin mazan da ake cewa kaje senayi shawara bane.



yaji dad'in amsar soyayyarshi datayi batare data wulak'antashiba, abinda y'anmata suka d'auka wai Jan ajine,hirarsu ta soyayya suka shigayi duk da Fatima kunya ta isheta takasa sakin jikinta dashi shine ke mata hirar.





Khairat ta dawo daga amsar littafin lokacin datayi arba da motar Hydar a k'ofar gidansu seda tayi tuntub'e ta fad'i sabida kallon datakewa motar,Allah yasota bakowa agurin da sauri ta Mik'e tashiga cikin gidan tana waigen motar.

tana tunanin gurinwa me motar yazo a gidansu,zata wuce cikin gidane taga takalmin Fatima a k'ofar sit room d'in Abban
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment