Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

. edited by
29/08/2022, 10:42 am - Khadijah Salisu fari


MACIJINE SHI


Na mammy kabeer
(Anty mammy)


Elegant online writers📚📚

Free book

Page 1


Bismillahir rahmanir rahim,Ina godiya ga Allah daya bani damar fara wannan littafi ,bayan kammala littafin soyayyata.Allah kasa yadda na fara lafiya naga bayansa lafiya ameen.


Gargadi banyarda wani ko wata ya juyamin wannnan littafi ta kowace sigar ba.





_______________Wata kyakkyawar yarinya na hango sanye da kaya irin na Fulani ,wato rigar saki dakuma zaninta,duka duka rigar da kadan ta wuce cibiyar ta,saidai kuma ta daura zanin ya rufe mata cikinta ta yadda ba wanda zai ga jikinta awaje.

Farace irin mai sirkin yallow -yellow din nan,tana da doguwar fuska mai kyan tsari dauke da dogon siririn hanci har baka,bakinta dan karami kamar gidan tsutsa,tana da irin manyan idanunnan masu kamar tana jin barci,ga gashin ido zara -zara.
Girarta kuwa ,kamar wacce aka dora Mata ita dan saiti,gaban goshinta wasu yan kananan gashine kwance lub lub kamar na jarirai.
Masha Allah yarinyar ta ko ina ta hadu ,dan doguwace marar jiki saidai fa Allah ya hore mata hips Kai kace wata babbar macece Sannan akwai alamun girma akirjinta , ma'ana dai akwai dukiyar Fulani dasuka fara tasawa akirjin nata.

Duka duka wannan yarinyar bata wuce shekara 15/16 ba ,amma kallo daya zaka yi mata kasan Allah yayi halitta agurin.

Sandace irin ta Fulani ahannunta tana dagawa sama ,da alama tana son hada kan wasu tarin sha'nun dake kiwone wani kayataccen jeji ,dan kuwa ciyawace agurin Kore sharr da ita ,sha'nun suna ta cin abarsu .

Tafiya ta farayi gurin shanun dake dan nesa da ita ,dan ita tana daga jikin wata bishiya ne tana kallon yadda suke kiwo abinsu.

Kanta ta daga ta kalli yadda garin ke hada wani irin hadari baki kirin dashi ,kuma da alama koda yaushe ruwa na iya saukowa.
"Kuzo mu tai gida abokaina kada ruwan nan ya sauko ya taba mu banin son nai mura aradu"
Cikin Yaren fulatanci take musu magana ,tana daga sandarta .aikuwa kamar wanda suke jin me take fadi suka fara yin hanyar gida .
Murmushi tayi tana mai binsu tana kara daga sandarta .


Tafiya suke cikin jajen ita kadai daga ita sai wadannan garken shanun ,sam ba alamun tsoro tattare da ita,yar wakar tama take tana daga sandar sama.

Kusan tafiyar minti biyar sukayi ,sannan na fara hango bukkokinsu dake can gaba kadan .
AHankali naga duk wani annurin dake kan fuskar yarinyar ya dauke ,nan da nan damuwa ta maye gurbin nishadi da take ,sosai naga jikinta yayi sanyi har suka karasa wata bukka dake farkon rigar da alama nan ne gidansu.

Garken shanun ta fara zuwa ta daure su tsaf sannan ta nufi cikin gidan,bakinta dauke da sallama.
Lokacin har anfara yayyafi .

Ba kowa a tsakar gidan nasu ,hakan yasa ta sauke ajiyar zuciya tare da nufar wata bukka cikin sauri.
Saidai kafin ta karasa kofar bukkar aka daka mata wata uwar tsakar da saida sandar hannunta ta fadi kasa.

Afirgice ta juyi jikinta na rawa sosai kamar dan mazari.da sauri ta karaso gurin matar data daka mata tsawar,
"Gani gwagwgo"ta fada cikin rawar murya. Kallon matar nayi sai na tarar da
matar farace saidai kuma kazanta da rashin kulawa yasa tayi wani irin baki baki fari fari,sannan tana da jiki sosai sam fuskar ta ba alamun rahama a cikinta.
Tana tsaye a kofar bukkar ta tana hararar yarinyar dake durkushe gabanta.
Cikin masifa da bala'i matar ta fara magana da hausarta marar kyau.

"Da kake kokarin shigewa dakin,ubankane zai debi ruwan?
Ko kin ajiye bawanki ne a gidan?matar ta fada cikin zaro ido.
Kan yarinyar akasa jikinta na rawa ta fara magana
"Allah hukkumu hakuri gwagwgo naga ruwa na don sauka ne shiyasa ban deboba"ta fada cikin rawar murya da tsoro.

Wani wawan mari matar ta kai mata cikin rashin imani da tausayi cewar yanzu ta dawo daga kiwo kuma ko abinci bata ci amma take kokarin sake turata rafi.

"Shegen yaro mai bakin hali wllh yanzu koke kidobo min ruwan nan dan ubanki karuwa kawai"matar ta fada tana mai hankade yarinyar .

Faduwa tayi sosai hannunta ya bugu da wani dutse dake ajiye tsakar gidan da alama na zama ne.

Kara ta saka cikin azaba tana mai dafe hannunta dake mata wata irin azabtar zafi.
"Wayyo handi É—in boni lalashewa gwagwgo hannu na ta É“alle" ya rinyar ta faÉ—a cikin azaba.

"Shege wllh dama zai karye danafi kowa jin dadi yarinya kamar aljana,ace kinfi kowa kyau arugarnan? Na tsaneka fatto saina bata wannan shegen fuskan baki.maza ki tashi kona shakeki agurin ki mutu kowa ya huta" cewar matar cikin bala'i da tsantsar nuna tsana ga dattin.

Cikin hanzarin ta mike ta zari wani boket din roba ta fice tana kuka sosai.

Tafiya mai nisa tayi kafin tazo rafin, har zuwa lokacin kuka take hannunta sai zogi yake mata, ruwan ta debo cike da sauri dan kuwa ruwan da ake ya fara karfi.

Saidai me ?tana juyawa tayi arba da wani murtukeken maciji katon gaske ya fasa kai yana huci.

Wani irin mugun tsorone ya kamata nan da nan jikinta ya kama rawa har batasan lokacin da boket É—in ya fadi kasa ya fashe ba.


Tashin hankali kenan wanda ba'a sa masa rana ,iyakar rushewa da tashin hankali yarinyar nan ta shiga.
Hannu ta ɗora aka tana mai kara ƙarfin kukanta.

"Wayyo ni fattu bukar na mutu na lalashe ya zanyi da rayuwata nashi zai karni wayyo baffana wayyo Allah ,taimaka min"
Ta faÉ—a tana kallon boket É—in dake tarwatsa,dama kuma rana ta gama cin ubansa.
Shi kuwa macijin nan ganin yadda ta tsaya tana kallon sa kuma tana kallon fasashshen boket É—in ta ,sai taga kamar neman makami take ,dan haka afusace yayi kanta


Ihu ta kwalla mai karfin gaske tare da zubewa agurin sumammiya dan ganin yadda macijin nan yayi kanta baki bude.

Masu karatu ya kukaji?
Meye ra'ayinku akan wannan Nobel É—in?
Ina bukatar comment dinku idan buk din nan yayi muku dadi muci gaba.

Takuce har kullum anty mammy

Msr babi💘💘
29/08/2022, 10:43 am - Khadijah Salisu Fari: 🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄

MACIJINE SHI🪱🪱🪱


Na mammy kabeer
(Anty mammy)



Elegant online writers📚📚


Free book

Page 2



_______________Ihu ta kwalla mai ƙarfin gaske ,tare da zubewa agurin sumammiya,dan ganin yadda macijin nan yayo kanta baki buɗe .

Hakan ba ƙaramin tsorata ta yayi ba .
Dai dai lokacin ne kuma wani katon macijin ya nufo wannan macijin da gudun gaske ,yana zuwa ya sarkeshi suka fara kaiwa juna sara .hakan shi ya hana wannan katon macijin ya sami damar karasawa inda fattun ke kwance asume.

Sosai macizan nan ke kaiwa junansu sara suna murdewa cikin jikin juna.ko wanne na ƙoƙarin illata dan uwansa.

Ahankali fattu ta fara bude idanunta da sukayi mata mugun nauyi tana kuma lumshesu,hannunta ta daga da nufin dafe kan nata,saidai wani azababben zafi da radadin ga wani irin zugi dataji hannun yana mata ,shine ya sanyata sanya kara tare da fashewa da kuka."washhhh hannuna wayyo kaina"ta fada cikin kukan tana mai dafe kan da dayan hannun marar ciwon.
Sai kuma ta zabura cikin azama ta zauna tana mai zare idanu da rarraba su,sakamakon tunowa da katon macijin da yayo kanta dazu.saidai kuma can ta hangi macizan biyu suna ta artabu,gaba daya sun jima kansu ciwo jini yana ta zuba akikkunansu,amma sunki daina fadan.

Tsoro ,fargaba ,tashin hankali da rudewa suka saka fattu kurma wani uban ihu tare da yunkurawa ta felle da mugun gudu tana ihu cikin rudewa dan ganin macizan sun zama biyu wato har fada suke akan waye zai cinyeta.

Duk da irin ruwan da ake zugawa mai ƙarfi ga iska ,haka tayi ta cin uban gudu ko gabanta bata gani.ikon Allah ne kawai ya kawota gidansu lafiya.
Kai tsaye ta danna cikin gidan da gudu ta shige dan dakin dayake amatsayin nata,cikin rawar jiki ta janyo wasu karare dogaye guda hudu ta kara a kofar,dan sune
Matsayin murfin kofar tata.

Dakin ba komai sai wata yar yaloluwar taburma ,wacce kallo daya zaka mata kasan cewa taga duniya,dan gaba daya ta ciccinye kuma tayi lakwam da ita.sai wani zani dake gefe daure ,da alama kayanta ne acikin.
Tana tsaye atsakar dakin ,har lokacin jikin ta rawa yake ,ga ruwa sai zuba yake ajikinta yararara!!!
Kallo daya zaka mata kasancewa afirgice take sai kif-kifta ido take tana kallon kofa,gani take kamar macizan nan zasu biyota.tayi kusan minti biyar acikin wannan halin ,kafin ta fara cire kayan jiki ta dake yararin ruwa."masha Allah nace,sakamakon ganin wani uban dogon bakin gashi mai santsi akanta,lokacin da take zame dan kwalin dake kanta .an raba kan biyu an daure ko wanne bangare sai kuma aka nannade ko wanne abarinsa kamar gammo.hakan da akayi shine ya hana mu ganin gashin nata tun farko.

Daurarren zanin nan ta kwance ta dauko wani zanin irin wanda ta cire da rigarsa ,saidai kayan fa sun sha jiki sosai ,sun kode sun jeme sunyi wani fari,sai wata hula baka irin ta sanyin nan ta dauko ta ajiye kusa da kayan ,sannan ta mike tsaye ta cire rigarta ta ajiye ta gefen ta barmar ahankali ta warware tsangalallen zanin shima ta ajiye gefe,ya zama daga ita sai wani kodadden pant Wanda kana gani kasan shima yaga rayuwa.kallonta nayi tun daga sama har kasa kawai nace Masha Allah.dan sura kam Allah ya halicce ta agurin fattu jikintahar wani sheki yake kamar yar masu kudi wacce ke rayuwa cikin jin dadi.

Haka ta dauki kayan ta saka ajikinta tanayi tana kuka abin kwanon ban tausayi.
Bayan ta kammala sanya kayan ne kuma saita dauki wanda ta cire ta matse sannan ta makalasu ajikin karan dake jingine akofar dakinta.

Zama tayi akan yar tabarmarta ta dukunkune jikinta tana kuka.abubuwa dayawa ke dakinta ahalin yanzu,na farko tsantsar tsoron macizan data gani dan bata taba ganin irin wadannan macizan ba,dan dayan kam jikinsa mai matukar shekine da kyau,sai kuma hannunta dake mata azabar ciwo uwa uba kuma yunwa,rabonta da abinci tun safe data sha nono har kawo yanzu da magrib ta sanyin kai ba abinda taci.
Sosai take tausayi rayuwarta, tabbas rashin uwa babbar gibine arayuwa,yanzu da innarta na kusa da ita data rungumeta ta fada mata damuwarta,amma rashin dace ta daya shine sam batasan koda fuskar innarta ba ,bata sani Bama kotana raye koya mutu Allah shine masani.
Tana cikin wannan halin taji an ture kararan data rufe dakinta dashi.
Azabure ta mike tsaye tana shirin sanya ihu.

"Ke fattu nutsu mana nine fa ,nine baffanki"wani dattijo ne fari mai dan tsayi yake maganar,yana sanye da riga da wando na wani yadi mai arha sai takalmin sau ciki na roba,da hula irin mai malafar nan.ya shigo cikin dakin da wani kwano hannunsa.

Ajiyar zuciya ta sauke sakamakon ganin baffan nata ,da sauri ta karasa kusa dashi tace "baffan usee wollahi na tsorata ne"ta fada idonta akan kwanon dake hannunsa.

Murmushi yayi yace "hoo fattu akwai tsoro,sannu maza karbi wannan tuwon ka shinye nasan kanajin yunwa,kayi sauri kar hansai ta gani"yana fadin haka ya mika mata kwanon yayi saurin fita,dan kar matar tasa ta fito ta ganshi ya shiga uku.

Cikin sauri _sauri fattu ke cin tuwon nan kamar zata kware, tas kuwa ta cinye ta side kwanan, da sanda tafice tsakar gidan ta wanke kwanon ta ajiye akicin sannan ta sha ruwa tayi alwala ta koma daki.
Sallar la'asar tayi da magrib dan tuni an kira.
Har zuwa lokacin ruwa ake saidai bai kai ƙarfin na farko ba.tana zaune cikin zullumin matakin da gwogwgo zata dauka akanta ,na fasa mata boket har akayi ishsha tayi salla sannan ta kwanta tana mai karanta addu'a ,nan da nan barci yayi gaba da ita,har baffanta ya shigo ya duba ta yaga tayi barci addu'a yayi mata cikin tausaya wa halin kuncin da take ciki kafin yayi saurin fita.

Gwagwgo kuwa tana daki ita da yaranta suna ta hira suna cin gyada ,ba ruwansu da wane halin fattu ke ciki,shin ta dawo gidanma ko yaya taci abinci ko bata ciba?sam ba wanda ya damu ,kuma ba wanda yayi Sallah a cikinsu.

Can cikin dare fattu na barcinta damuwa da tsoro dan kuwa mafarkin macijin nan take ,saidai kuma ba na farkon bane yazo mata yanzu wannan mai kyakyakywan jikin ne,saidai gaba daya jikinsa jini yake zubarwa,ga wani irin hayaki da tururi dake fita ajikinsa, sai burkima yake yana wani irin kuka da wata murya mai amon sauti,kuma yana nufota da ƙoƙarin hawa jikinta .

Wani razanannen ihu ta kwalla tare da mikewa zaune afirgice ,tana mai waige waige,ba abinda take iya gani saboda duhun dakin ,hakan yasa tayi saurin komawa ta kwanta tare da karanta addu'a kala_kala,hannu ta mika dan janyo zaninta ta rufe jikinta dashi ,saidai kuma hannun nata taji ya sauka akan wani abu mai dan karen sanyi da santsi.
Cikin tsoro take shafa abun dan jin ko menene,tabbas MACIJINE dan kuwa ta tabo har kansa ....


Masu karatu badai macijin ne ya biyo fattu da gaske ba?

Wane hali fattu zata shiga ?

Muje zuwa yaki ce dai anty mammy

Mrs babi💘💘💘

Share and comment fisabilillah.

More comment
More typing.
29/08/2022, 10:43 am - Khadijah Salisu Fari: 🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄


MACIJINE SHI🪱🪱🪱


Na mammy kabeer
(Anty mammy)



Elegant online writers📚📚


Free book

Page 3/4






________________Cikin tsoro take shafa dogon abun dan jin ko menene,tabbas MACIJINE dan kuwa har kansa ta taɓo.

Aikuwa da hanzari ta janye hannunta cikin kidima ta fara ja baya tare da fasa wani irin gigitaccen ƙara,
"Ahhhhhhhh wayyo Allah baffa maciji!maciji !!maciji!!!"gaba É—aya ta kidime abinda take iya faÉ—i kenan jikinta na rawa kamar É—an mazari.
Allah Sarki baffa dama ba wani barci yake yi ba ,dan yana kula da ɗakin fattu ,kasancewar ɗakin yana gaf da ƙofane,dan haka jin ihunta da yayi ,yasa shi tashi agigice ya nufi ɗakin nata.
Haskawa yayi da tocila can ya hangota jikin bangon ɗakin ta duƙunƙu ne tana ta ihu,da alama batama cikin hayyacinta.
Da sauri ya nufeta yana kiran sunanta"fadimatu !ke fadimatu menene ?ya isa haka gani akusa dake baffanki ne kinji daina ihun "baffa ya faɗa cikin ƙasa ƙasa da murya dan karya ƙara tsorata ta.

Ita kuwa gaba É—aya ta rikice kawai kira take "baffa maciji zai sareni baffa wayyo Allah na"
Ganin halin da take ciki ne yasa baffa ya fara tofa mata addu'a ,cikin minti biyu kuwa tayi shiru sai rawa da jikinta ke famanyi,ahankali ta daga kanta ta sauƙe kyawawan idanunta akan baffan nata,kawai saita saki kuka tana mai cewa"baffa MACIJINE yake son sarina aradu da idonsa na ganshi anan"ta faɗa tana nuna masa gurin dataga macijin.

Kallon gurin baffa yayi ,shifa ba abinda ya gani agurin ,kawai yana tunanin ko mugun mafarki tayi,dan haka cikin ƙokarin kwantar mata da hankali yace "shike nan fattu ya tafi maza koma ki kwonta kiyi addu'a ba abinda zai sameka kinji"ya faɗa cikin yanayin Hausar su ta Fulani.

Cikin kuka take girgiza masa kai "aradu baffa dawowa zaiyi tun daga rafi suke son cinyeni baffa ,bazan iya kwonshiya Ni kaɗai ba"ta ƙarasa tana mai matsowa kusa da baffan.

Shiru yayi yana tunanin mai ya kamata yayi,dan gaskiya yaga ta tsorata da yawa,dan haka cikin ƙarfin hali yace "tashi muje gurin hansai saiki kwonta shan ko"ya faɗa cikin tausaya wa.

Ai kafin ma ya rufe bakinsa ta kai ƙofa,dan ita kam babban burinta ta bar ɗakin nan,tama manta da gurin wa baffan yace taje.

Ahankali baffa cikin É—an tsoro yake tura murfin É—akin na hansai harya buÉ—e shi duka.suna kwance abinsu kan gado ita da yaranta su uku,na miji É—aya sai mata biyu Dukansu basu kai fattu shekaruba, da alama na mijin zaiyi shekara sha uku,matan kuma basu fi sha daya ba.
Kuma dan rashin tsari irin na goggo hansai da ita da yaranta duka suke kan gadon ,har na mijin.

Ahankali baffa ya karasa yana dan bubbuga fillon da hansai ke kwance ,sai uban munshari take zabgawa,banda wari ba abinda dakin keyi.

"Hansai!hansai!!"baffa ya faÉ—a cikin Muryar tsoro,dan yasan idan ta farka saitayi masa bala'in ya tashe ta tana barci.

Juyi tayi tare da goge yawun barcin dake zuba abakinta taci gaba da barcinta.ahankali ya fara kiran sunanta da É—an karfi "Hansai ! Hansai!!" Har sau biyu.

Buɗe ido tayi ahankali ta sauke su akan baffa dake tsaye ,buɗe idon tayi sosai cikin bala'in ta tace "to jarabarce ta motsa haka da cikin dare zakazo ka dameni?to wllh garama ka koma inda ka fito dan ba abinda zaka samu agurina ,wannan jaraba dame tayi kama ,ko sati biyu bakayi da saukemin jarabarka ba shine yanzu ka ƙara jajiɓo jiki kazo ka sake ko ?to wllh banda lokacinka kaficemin daga ɗaki"ta faɗa cikin masifa tana juya masa baya.

Girgiza kai yayi cikin jin kunyar fattu ,dan yasan taji abinda gwogwgo take faÉ—i ,kuma ai ita ba yarinya bace bare ace bata san me hakan ke nufi ba,tunda tana karatun addini.
Cikin sanyin murya yace "ashsha Hansai ba wannan ta kawoni ba ,dama ina neman alfarmar fattu ta kwana anan ne daku,dan bazata iya kwana ita kadai ba ,atsorace take "ya faÉ—a cikin shakkun zata amince ko yaya.

"Kan ubannan yau kuma da wannan sabon munafurcin kuka zo ?fattu ta kwana aÉ—akina ,lallai in baka mutu ba zakaga ikon Allah,da can da ubanwa take kwana? sai yau zakace ta kwana aÉ—akina?yarinyar mayya wato cikin dare ta lashemu ko?kai baka da asara,to ku ficemin aÉ—aki ,Allah yasa abinda yake tsoratatan ya cinyeta ta mutu kowa ya huta "tana gama faÉ—in haka ta juya taci gaba da barcinta.

Sosai maganganunta suka É“atawa baffa rai ,saidai bashi da damar magana ,kai kawai ya girgiza yace "muje fattu"
Kuka sosai fattu keyi na tausayin su ita da baffanta ga wannan matsalar dake ƙoƙarin Kunno mata kai ,basu da gata sai Allah kawai.

Suna fita baffa yace "shiga É—akina ki kwanta fattu,Ni bari na je É—akin naki kinji"ya faÉ—a cikin sanyin murya.

Girgiza kai tayi tace "baffa Zan koma É—akin nawa In kwanta kaima kaje É—akinka ,idan gwagwgo tasan na kwana aÉ—akinka yanka Ni zata yi,dan ta hanani shiga É—akin"ta faÉ—a tana mai share hawayenta tare da nufar É—akin nata ,gabanta naci gaba da bugawa.

"Kiyi hakuri fattu komai yana da iyaka kinji,Allah zai miki sauyi Na alkairi"baffa ya faÉ—a yana mai mika mata tocila ya ce ki haska ki kwanta kinji ,kiyi addu'a"
Karba tayi tare da É—aga masa kai ta koma cikin É—akin.

Daga bakin ƙofa ta tsaya tare da haska ɗakin ko ina ,ba abinda tagani aɗakin ,hakan yasa tayi zamanta bakin ƙofar ɗakin da tocilan ɗin ta ko yaya taji motsi saita zabura ta haska .

Sam awannan daren bata sami damar runtsawa ba ,ga sanyi da garin ya É—auka sakamakon ruwan da aka zabga jiya.

Sai gabannin asuba sannan barci É“arawo ya saceta.
Wani irin azababben sanyi daya ratsa ƙasusuwan tane sakamakon ruwan sanyin da gwagwgo ta kwara mata ,shine ya sanyata zabura ta miƙe da sauri tana haki,kafin ta gama dawowa cikin hayyacinta kuma taji duka yana sauƙa ajikinta ta ko ina ,ihu ta fara tana neman taimako amma ba wanda yazo dan taimakon nata,dan baffa yana masallaci kasancewar shine limamin rugar,

"Wayyo Allah na gwogwgo kiyi haƙuri wllh bazan ƙara ba ,tsautsayine yasa na fashe miki bokati, dan Allah kiyi haƙuri gwogwgo"abinda fattu ke daɗi kenan cikin azaba dan ko ina na jikinta ciwo yake mata barin ma hannunta daya kumbura sosai ,alamun tayi targaɗe a hannun kenan.
"Wllh yau saina kasheni Shegiyar yarinya muguwa, kafin baƙin cikinki ya kasheni ,na Tsaneki fattu bana ƙaunar ganinki arayuwata, kinsan nawa nasai bokatin nawa?kika je kika fashemin shi? Murtala huɗu da nairagoma fa na siya,wllh saina daki kuɗina kuma kije duk inda zaki samo min kuɗin bokatina ki samomin dan bazan ɗauki asarar ba"gwogwgo ta faɗa tana haki,kuma bata daina jibgar fattu ba ,kamar ta sami jaka.
"Wayyo gwogwgo dan Allah kimin rai hannuna zai karye, wllh bada gangan na fashe miki bokati ba,macizaine suka biyo ni zasu cinyeni shine na gudu amma bada gangan nayi ba wllh"ta faɗa cikin azaba dan tuni ƙarfinta ya kare ko iya ɗaga hannunta bata yi.

"Allah ya tsine muku keda mashizan shegen yaro karuwa ,ina ruwana da macizai ?dama sun cinyeki kowa ya huta mai baƙin hali marar farin jini har yanzu kin kasa auruwa ,dama shegun macizan sun.......kasa ƙarasa magannarta tayi sakamakon wani ƙaton abu dataji ya faɗo kanta jifff !!!kamar buhun hatsi.

"Wayyo Ni Hansai menene wannan ɗin yake zagayemin jiki?ta faɗa cikin firgici da tashin hankali tana mai jefar da iccen hannunta.aikuwa carab idanunta suka sauka akan ƙaton macijin daya nannaɗeta ko motsi bata iya yi,kuma ya fasa kai a saitin fuskarta sai huci yake yana Filato da harshe.

"Wayyo Allah na Ni hansai yau me zan gani ?na shiga ukuna malam kazo fattu ta min ture maciji zai kasheni ka taimakeni, handi ɗin bonu lalashewa ni yar nan wayyo malam"ta faɗa cin tsantsar tsoro da razani da ƙyar take magana dan ba ƙaramin shaƙar mata jiki macijin yayi ba har wuyanta.

Tsoro,fargaba da tashin hankali sune suka daɗa kashewa Fattu jiki ,dan faɗuwa tayi ƙasa warwas ko motsin kirki bata iya yi,shikenan Tata ta ƙare yana gamawa da gwogwgo tasan kanta zaiyo ,Allah Sarki innarta ,yanzu shikenan zata mutu bataga innarta ba,batasan ya fuskarta take ba ?bare tasan dangin innarta?,amma Gara ta mutumma ta huta da wannan baƙar azabar da take sha agurin gwogwgo.

Shikuwa macijin nan ƙara matse gwogwgo yake sosai ,gaba ɗaya ta fice daga hayyacinta,dan ko magana ma ta kasa ,idanunta sunyi jajur sai nishi take numfashinta na ƙoƙarin ɗauke wa.
Saida macijin nan yaga gwogwgo bata motsi alamun ta suma,kafin ya sake ta ta hanyar janye jikinsa daga gareta.

Da gudu kuma yayi kan fattu wacce ke kwance cikin tashin hankali ganin yadda macijin nan ya kashe gwogwgo.runtse ido tayi da mugun ƙarfi tana salati da sallama da duniya,ko motsin kirki batayi ,dan da kyar take iya jan numfashi ma.

Shikuwa macijin nan yana zuwa gareta ya tsaya saitin fuskarta ya fasa kai yana huci,sai kuma ya fara zagayeta cikin sauri da sassarfa, kafin
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment