Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

nufi hanyar waje. Tarar da su Sadiq sukayi a yashe cikin jini. Sosai su ke kuka, sun rasa yadda zasu sa rayuwarsu.

Cinci barsu sukayi suka nufi part din Su nadira dasu, inda kowacce ta Fara kula da mijin ta. Kwantar da su Dad akayi, yayin da Aunty amarya ta Bawa Dad magani, yasha,

bayan hour 3, jikin kowannen su ya lafa, yayinda su sadiq sun farka, kuma doct khadija tayi musu treatment, kowa aikinsu ya tashi, amma banda Kabir da haryanzu baiko Motsa bah.

Hankalin su Khalid ne ya kara tashi, Dad yace Meyasa Haryanzu Kabir bai tashi bah, Dan Allah ku ceci rayuwansa, banason wani abu yasami d'ana, doct khadija tace, nayi iya bakin kokarina wajan ganin ya farka, amma babu alamun zai farka, ina tunanin fa ya fada a doguwar suma.

Gaban kowannen su ne ya tashi, grandma tace khadija doguwar suma fah kika ce, yanzu menene mafuta.

Dafe kanta Aunty amarya tayi, tana mai nazarin mafuta a garesu. Da sauri Aunty amarya da Dag'o, sa'anan tace, akwai mafuta, juyowa gabadayansu sukayi, suka hada baki wajan fadin, menene mafuta?

Aunty amarya ta basu amsa da fadin, "Amriya", kwarai kuwa Amriya itace mafuta, zata iya, da taimakon ta, da taimakon Allah, zata iya cetan shi.

Doct khadija tace da kyar Amriya ta yarda, tazo, saboda ta fadamin cewar bazata kara tako kafarta cikin wannan gidan bah, kuma yanzu bah karamin tsana tayi wa Kabir bah, da kyar mu iya shawo kanta tayi. Tazo, Khalid yace insha Allah zamu yi iya bakin kokarin mu, wajan ganin ta zo. balla kofa sukaji anyi.


""""""""""""''''''''''''''''''''''""""""""""""""""""
Rasss gaban Amriya ya fadi ! , zuciyar ta, yafara Dukan uku uku, dafa ta doct Amina tayi tace, y'ata Amriya meyafaru?

Amriya tace, Ammi", jikina yana bani cewar, ahalin dana baro suna cikin halin tsaka mai wuya, tundazu gabana yake ta faduwa, yusuf yace toh kije ki gani mana, ko kuma muje,

Sai a lokacin Amriya ta tuna da irin cin mutuncin da suka mata. Amsa ta bawa yusuf da fadin, bazanje bah, na fasa, na ruga dana daukar wa kaina alkawarin bazan sake sanya kafafuwa na a wannan ahalin bah, dan aka, su nemar wa kansu mafuta, batareda taimakona bah.




COMMENT & SHARE PLS.
ALKALAMIN
AISHA M.B






Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/JYYV16dbYaX1dykLX7EE91


https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v
*JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*??
(J.W.A)
_Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ?asaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sau?i_.??

ALJANAR RUWA CE ??♀??
PAGE 4??7????4??8??
WRITTEN & DIRECTED??
BY AISHA M.B (BABY ISHA) ???

----------------------------------------

cikin rashin fahimtar maganar Amriya Doct Amina tace, taimako Kuma! Wane taimako kike musu? Ganin aka yasa Amriya Saurin chanza magana da fadin, Aa Ammi kawai dai nafada ne cewar bazan Kara taimakon su bah, amma wasa nake babu wani abu.

Rike hannunwan ta Ammi tayi tace Amriya kenen, yanzu kenen baki yarda dani bah, kinai tsoro ne? na ruga dana fada miki cewa ki dauke mu tamkar ahalin ki, ki daukeni tamkar mahaifiyar ki, ki fadamin gaskiya,

Dan jimmm Amriya tayi, sa'anan tace ina tsoron bayyana muku wacece ni ne saboda, dalilin akan ne yasa wancan ahalin suka koreni, Kuma ina tsoron kada kuskure daya faru ya Kara maimai ta kansa.

Kallon ta bban yusuf yayi, yana mai fadin, Aa y'ata babu abunda zai faru, ki shafa wa zuciyar ki ruwan sanyi, bazamu taba butul talki bah kinji,

Gyaran murya Amriya tayi sa'anan tace, a gaskiya nidin bah mutum bace kamar yadda kukayi tsanmmani, nidin ALJANAR RUWA CE, Amma Dan Allah kuyi hakuri ban fada muku asalin wacece ni bah kafun na Fara zama daku a matsayin bakuwa, ni yanzu mah zan tafi,

Kallon Ammi Amriya tayi tace, gaskiya Duk wacce ta sameki a matsayin uwa, toh tabbas bah karamar yar sa'a bace, rayuwata bah karamin kyau zaiyi bah,
Ni yanzu zan tashi na tafi zanje na cigaba da lallaba rayuwata.

Jin kalaman ta, yasa Jikin kowanne sune yayi sanyi, shafar fuskar ta Ammi tayi tace, Aa Amriya kada kidamu muna tare dake Duk rintsi Duk wuya, baza mu taba rabuwa dake bah, Sanin cewar ke bah mutum bace akan bazai sanya mu gujeki bah, koh kadan baki yi kalan wa enda suke cutarwa bah, Kuma nidin zan kulada ke tamkar yadda mahaifiya zata kuka da yarta .

Ki sani mu dake gabadaya ahalin ne yanzu, kada ki kara bambamta kanki damu kinji, nima na rasa y'ata mafi soyuwa a gareni kamar dai yadda kema kika rasa mahaifiyar ki, dan aka yanzu kinzama y'ata

tabbas kedin yar sa'a ce, na tabbata da mahaifiyar ki tana nan zata yi farin cikin ganin wannan d'iya tata wacce take tattare da sa'a da Kuma alkhairy, na tabbata a koda yaushe zata kasance tana Alfa'ari dake.

Murmushi Amriya tayi sa'anan tace nagode sosai Ammi, hakika kedin mahaifiya ce ta kwarai, bazan taba mantawa da irin alkhairy da kika aikata a gareni bah, rungume ta Ammi tayi Tana Mai fadin Allah yayi miki albarka y'ata.

Tura baki gaba Yusuf yayi Tareda cewar, wato yanzu Ammi kinsamu Auta, ni kuma za'a manta dani koh, murmushi Ammi tayi tace Yusuf kenen sarkin k'ishi toh kaima tawo na sama albarka,

Tashi yayi ya nufi inda su Amriya ke Zaune, yana isa ya zauna a kusada Ammi yace, toh nima asaka min albarka,

Tom shikenen yusuf Allah yayi maka albarka, Allah ya baka Mace ta gari wacce zata haifa min jikoki,

Yusuf yace, Aba Ammi jikoki kuma tun yanzu, Abba yace, toh yusuf idan bakayi aure ka haifan mana jikoki bah, me kake so kayi, wai yaushe zaka futo da mata nee,

Yusuf yace kada kadamu Abba nan bada dadewa bah insha Allah, Amriya tace Kardai ka dauko mana mumuna irin wannan budurwar taka dana gani.

Kallon sa sukayi baki daya, Ammi tace Dama kanada wacce kakeso baka taba Sanar mana bah, Sosa k'eya yusuf yayi Tareda fadin, Hmmm Ammi fah karya Amirya takeyi, babu wata budurwar danake da.

Amriya tace Bawani karyar da nayi, ai ranar nan na ganta, yusuf yace a ina kika ganta din? a awajan nan.. ganin Amriya na shirin tona masa asiri yasa yayi Saurin daukan pillow zai buge ta dashi,

Amriya na ganin aka tayi Saurin mikewa tareda nufa hanyar daki da gudu, Ammi tace Kardai ka cutar min da d'iya, dan bazan kyale ka bah, Yusuf yace Kinaji fah Ammi wlh karya take min

Abba yace mum yarda karya take amma kada ka Bari wannan watan ya Kare baka kawo mana suruka bah kaji na fada maka,

Yusuf yace aba Abba wata daya fah, ina laifin shekara, yanzu ni ina zanje na samo budurwa na nawa maka cikin wata nan,

Abba yace Oho duk inda Kaga yayi maka ka samo , mudai burin mu ka kawo ta mugan ta, inba aka bah da kaina zan aurar dakai.

Shagwaba fuska yusuf yayi, yana mai fadin Ammi kinajin mijinki koh wai ni zai aurar, kenen auran dole za'a min. Ammi tace kwarai kuwa auren dole za muyi maka, danna ga idan bah auren dolen muka makaba, toh bazaka futo mana da suruka bah.

Yusuf yace Tom shikenen zan futo da mata, amma gaskiya sai an karamin lokaci, danni bah yaro bane bah, Ammi tace kaji dashi dai,


-----------------------------
Cikin tsorata gabadaya suka juya don ganin wanene, juyawar su keda wuya suka ga Mom a tsaye ta dora wuka akan wuyan Fatima wato matar Dad,

dayan hannunta kuma rike take da files, Gyaran murya tayi sa'anan tace kuna ji kuna gani zan kashe ta a gaban ku batareda kun ceci rayuwarta bah,

Dafe zuciyarshi Dad yayi wanda yakeji tamkar zata fashe sabida kunci da takaici,

Cillawa Dad document din hannunta mom tayi, tana mai fadin wannan itace kadarorin ka gabadaya, ka saka hannu, kasaka cewar wannan kadarar Ba taka bace ta Karima ce, in Kuma bah aka bah, kana gani zan kashe ta har lahira.

Kallon Fatima Dad yayi wacce ta rintse idanuwan ta hawaye na zubowa kan kuncin ta, sannan yace dama Fatima kina a raye ban Sani bah, meyasa baki fadamin cewar kina raye bah Tsawon wadanan shekarun, kinsan wane Hali na Shiga tsawon wadanan shekarun da bakya tareda dani.

Kallon shi Fatima tayi tace, Bah lafi na bane, danasan aka zata kasance daban saka rayuwar ku da d'ana a cikin hatsari bah.

Aunty amarya tace bake kika saka rayuwar mu a hatsari bah, wannan shedaniyar matar ce,

Cikeda baccin rai Mom tace kwarai kuwa, nice nan, Wato har kun manta abunda kuka aikata mu shekarun baya da suka gabata kenen, kun manta yadda kuka Shiga tsakanina da yar uwata kuka saka mu cikin kunci da bakin ciki,

Dad yace wai waye yasa kaki kunci,shin nasan ki ne a da? Fadamana me muka aikata miki,

Mom tace bani zaka tambaya bah mahaifin kah dake Kabari zaka tambaya, danshi yasan komai da komai da yafaru, abunda ya aikata shi yake shafar y'ay'an sa kuma gashi harda jikokin da yatara,
Wato kun taru kuna cin Dukiya kuma kudin haram, kun taru kuna siyan tufafi abinci, yin abunda kuka gadama da kudin da ba naku bah ,

Kuma a akan kuke tunanin zan barku ku sha, akan bazata faruba, maza maza kasa hannu akan takardan nan in bah aka bah na yanka wuyan ta yanzu nan.

Cikin fusata Dad yace bazan saka bah, Kuma baki isa kiji mata koda kwarzane ne,

Murmushi mom tayi ta cilla mahaifiyar kabir gun Dad, babu bata lokaci Dad yayi Saurin riketa,

Mom ta kallesu tace, na baka nan da 24hours, da zaka sa hannu akan files dinnan, in bah aka ba, toh na rantse da ubangijin da nake bautawa, gabadaya saina kona ku da ranku, karasa maganar ta keda wuya ta fuce daga cikin dak'in.

Rungume Mahaifyar Kabir Dad yayi, yana mai fadin, ki gafarce ni Fatima, kiyi min aikin gafara, danasan kina raye kuma kina cikin gidanan, dana saka police sun kama Karima. Kiyi hakuri,

murmushi Mahaifyar Kabir tayi tace, babu abunda ka aikata min, yanzu burina shine na sanya d'ana a cikin idona, ina d'ana yake,

Nuna mata inda Kabeer ke kwance Dad yayi, Kallon wajan tayi, yayin da ta sauke idanuwanta akan kabeer, Wanda ke kwance har yanzu ba ya motsi.

Tashi tayi da sauri tareda nufan inda yake, kuramasa idanu tayi hawaye na sauka kan kuncin ta, tace Allah sarki d'ana, wancan azzalumar matar ta rabani dakai, bata Bari naji dimin ka bah, ta dauke min Kai, yanzu bah lallai ka soni kamar yadda ka sota a baya bah.

Tabbas yanada wuya ka iya yarda cewar ni asalin mahaifiyar ka ce, domin kuwa zaka kuma dauka ko wani raina mah hankali za'a kuma yi, tunda na haifo ka wannan duniyar baka taba ganina bah, bare ka kirani mama, ka taimaka ka kirani mahaifiyar ka koda sau daya ne kafun numfashi na na karshe, tana kaiwa nan ta fashe da kuka mai ratsa zuciya,

Jikin gabadayan su ne yayi sanyi, yayin da su kaji tausayin ta ya matukar kamasu. Hawayen dake shirin zubowa Dad yayi Saurin sharewa, tareda fadin, kada kidamu Fatima" yanzu ai kin dawo rayuwar shi, tabbas nasan bazai guje ki bah, Kuma na tabbata zai rike ki hannu bibbiyu,

Fatima tace da wuya ya yarda ni Mahaifyar sace, kasan yadda zuciya ta ke kuna da radadi, kasan yadda naji yayin da ina ji, ina gani, aka raba ni da dana daya tilo, shin meyasa bata dau raina bah ta barni a raye tana gallaza mun azaba, babu irin azabtarwar da bata yi min bah, tabbas laifi na ne, dana dora mata yarda ta, daban dora mata yarda ta ba, da bata aikata akan agareni bah.

Cikin rashin fahimta Dad yace, kamar ya? Shin dama kin San tane tuntuni? Shiru Fatima tayi ba tareda ta bawa Dad amsa bah.

Daga sama sukaji Doct khadija tace, Kuyi hakuri, ku gafarta min, duk abunda ke faruwa da ahalin nan gabadaya laifi na ne,
Tabbas a yau zan bayyana muku gabadaya abunda ya faru, da har kukaji nice da laifi,
Dakatar da ita Dad yayi da fadin, Bamua son jin komai daga gareki, kawai kiyi shiru khadija, hawayen ta Doct khadija ta share, tareda fadin Yahya a matsayina na kanwar ka, ka taimaka kabani Dama daya kacal, zan bayyana Duk kulla kullan da Karima ta aikata. Kaima kasan bazan taba maka karya bah.

Ka yarda dani, Dad yace khadija a matsayin ki na kanwata ai bai kamata ki aikata aka a garemu bah, meyasa kika ci amanan wannan ahalin, meyasa kikayi mana karya, ga mama nan kema kinsan yadda mama take matukar kaunan ki duda cewar bah ita ta haife ki bah, amma tafi rubuta ki akan mu.

Lokacin da Abban mu ya kawo ki gidan mu a matsayin marainiya, aka muka dauke ki tamkar yar ahalin mu har kika girma, soyayya, kulawa, da qauna, babu wanda bamu nuna miki bah, bamu taba bamban ta kan mu da ke bah, amma akan bai hanaki guduwa da wani namijin a wajan bikin ku wanda za'a muku keda Maryam bah, sannan kika je kika aure shi. kinsan halin da muka Shiga da muka ji labarin kin gudu da wani saurayin,

Kinsan kunya da bakin cikin abunda kika aikata ya sanya mahaifin mu har silan akan yasa ya rasa rayuwar shi, meyasa tun farko baki fada mana ga wanda kike so bah, ai dashi zamu baki, basai kin kunyata mu a idanuwan jama'a. Amma bakomai komai yayi farko zaiyi karshe.

Hawaye ne yafara gangaro wa daga idanuwan Doct khadija, cikin sheshekar kuka tace Dan Allah kubani dama daya zan fada muku duk abunda ya faru , tabbas kun yimin gurguwar fahimta ne, ku tsaga ku saurare ni.

Grandma tace toh shikenen y'ata munajin ki, Muhammad Kabari ta fada mana abunda ya faru,

Dad yace Tom shikenen muna jin ki, Kallon su Khalid da su nadira Dad yayi yace, ku bamu waje zamuyi magana.

Dakatar da Dad doct khadija tayi da fadin Aa zuyi zaman su, suma aiba yara bane, ka barsu Suji abunda ya faru.
Amma dan Allah kafun na fara inaso kowa ya bada hankalin shi wajena.

Zama sukayi baki daya, yayin da kowa ya nutsu, tattaro nutsuwan ta Doct khadija tayi,
ta fara magana kamar aka.

Asali nida Karima babban kawaye ne tun muna bording school, zaro ido gabayansu sukayi, what! Dad yafada.

Kwarai kuwa nida Karima babban kawaye ne, Kuma itadin sunan ta hassana ne, sudin yan biyu ne, but not identical twins, abunda yasa bakusan Karima bah shine bata taba yarda tazo gidan mu bah, saidai Ni dakuma Amina, koda tazo bata taba yarda ta shigo bah.

sunan yar uwarta Amina , mun taso Cikeda kaunan junan mu, ko ina tare muke zuwa gidane kawai ke rabani dasu, saboda qaunan junan da mukeyi har alkawari muka daukan wa junan mu cewar Duk y'ay'an da muka Haifa saimun hada su aure, domin akan takara mana zumunci

Nida Amina yar uwarta mun kasance masu kokari a class, yayin da ita bata da kokarin ko kadan, akan yasa muke yawan samu matsala da ita, take nuna k'ishin ta a bayyane, koda gasa ake ta makaranta toh nida Amina ne kawai ake kira gasa.

Amina itace hussainan ta. Amina ta kasance Mace mai hakuri da Kuma kawaici, Tana da farin jini sosai a makaranta, Duk inda Ta shiga mutane na yabon ta.
Ashe akan na bakan tawa Karima, kwatsam wata rana Aka aiko mana da sakon gayyata na makarantu wanda za'a fafata tsakanin dalibai.

Kamar yadda muka saba, a lokacin ne itama Karima tace tanason Shiga gasar da akeyi, Tana son ta nunawa duniya cewar itadin bah doluwa bace bah, abunda yar uwarta keyi zata iya yin finsa mah.

Malaman makaranta kuwa basu ja da akan bah, amma suka mata gargadin cewar indai ta bawa makaranta kunya toh za'a sallameta daga makarantar, cikin rashin tsoron abunda zaizo ya biyo baya Karima ta amince da Sharadin da malamai suka fada mata.

bayan nan, gabadaya makaranta muka hallarci wajan taron daliban da akeyi, yayin da akace Duk wacce taci za'a bata babban kyauta dakuma scholarship na makaranta.

Ni da Kuma Amina mun fafata Kuma munyi nasara, yayin da Karima kuwa ta bamu kunya a bainan jama'a, ganin hanata mata dariya yasa bakin ciki da kuncin ya dameta ta futa daga cikin hall din da gudu tana kuka.

Yayin da mu Kuma aka bamu kyautu tuka da Kuma scholarship, iya kyauta muka karba bamu karbi scholarship bah, akan bah karamin bawa mutanen wajan mamaki yayi bah, inda dalibai suke fatan su sami scholarship, amma mu mun samu munce bamua so, dalilin akan kuwa shine Karima,

Domin kada Karima taji Ba dadi akan yasa muka ki karba, bayan koma wan mu hostel, Karima ta daina mana magana, koh mun mata magana bata kula mu, saidai taita kula wasu kawayen banza marasa tarbiya, akan bah karamin damun yar uwata keyi bah,

Hana tsaka da aka, wani matashi Mai suna Habib Dan sarkin bauchi ya fada a soyayyar Amina, sosai masoyan nan suke shan soyayya, Wanda baki bazai iya masalta irin son da suke wa junan su bah,

Lokacin da muka rubuta WEAC din mu, muka futo da sakamako Mai kyau Dama mu a bangaren science muke nida Amina Ita Kuma Karima ART class, amma duda akan bata futo da sakamako Mai kyau bah.

Akan bah karamin bata ran mahaifin su yayi bah domin kuwa mahaifinsu yana da kudi, dukiya, da Kuma wadatar arziki. Amma ace yarsa bata da kokari koh kadan, cikin baccin rai kuwa, budar bakin mahaifin su keda wuya ya kirata da Mai kwakwalwar kifi, jin akan datayi yasa tun daga ranar ta dora tsanan duniya ta dora mana. Amma akan baisa ta bayyana mana bah.

Hana aka Habib yaje wajan Amina hira, daidai lokacin itama ta ganshi taji duk duniya babu Wanda takeso kamar shi,

Ni kuma a lokacin ne mahaifin ku yace yayi min miji nida Maryam, daga nan sai na dora karatu na a inda na tsaya ban musa bah Kuma na amince da maganarshi, saboda a lokaci Banida wani a raina,

Lokaci zuwa lokaci Habib ke zuwa gidansu Karima har wani sa'in yake futa damu shopping, Hana aka har labari yaje kunnen iyayen su, har sukace masa ya turo magabatan sa, jin akan bah karamin sanya shi farin ciki yayi bah,

yayin da aka ce itama Karima ta futo da miji. Jin akan da Karima tayi yasa ta bayyana wa kowa abunda ke cikin ranta, jin akan kuwa bah karamin bata ran mahaifiyar su mai suna Jamila yayi bah, da Kuma y'ay'an su Suleiman bah.

Amina tace tayi hakuri domin kuwa bazata iya sadaukar da soyayyar ta bah, ita kuwa Karima ta nuna mana cewar, komai ya wuce babu komai a zuciyar ta, ashe itadin munafuka ce.

Bayan wasu kwanaki Habib ya turo magabatan sa , yayinda aka tsaida auren Amina da Kuma Habib.

Ni kuma a lokacin an kusa bikin mu nida Maryam. A lokacin kuwa, Karima ta bijiro da kule kulen samarin, harta kawo min wani saurayi mai suna Harun, wai yana sona, ta karfi da yaji, Karima tasa na fada a soyayyar Harun,

Yayinda muke soyayya Cikeda burgewa, Harun, ya kasance masu matsakaicin karfine, amma akan bai hana ni k'in sonshi bah,

Ranar aure na kuwa, ta zuga ni wai mu gudu da Harun, ni kuwa nace mata gaskiya bazan iya butulci bah, kunyi mun abubuwa da dama, amma in rasa da abunda zan saka muku sai wannan.

Aka dai taita zuga ni, nace indai saboda soyayya zaisa na gudu toh saidai na hakura, data ga nak'i sauraron ta, ta shakamin abu a hanci na, cikin kankanin lokaci bacci yayi hawan gaba dani. Aka suka cincibe ni suka kaini daji batareda nasan inda kaina yake bah,

Bayan farfado wata, take fadamin cewar saita dau fansar abunda muka aikata mata nida Amina, lokacin ne Harun ke fadamin cewar bah sona yakeyi bah ita ta biyashi danya cimin zarafi Kuma nasa ahalin da suka yarda dani, su tsaneni, Suji kaff duniya babu ma yaudariya maciya amana sama dani,

Kuka kamm nasha shi Harna godewa Allah, Hana tsaka da aka, Harun ya bayyana mun soyayyar sa agareni, tareda cewar shin zan auresa, Babu bata lokaci na yarda muka daura aure nidashi, yayin da ya gina mana gida na masu rufin asiri,

Ashe a lokacin Karima ta dai photo na da Kuma Harun ran auren mu, ta tura muku, akan yasa kuka nuna baccin ranku akaina, rana bazata tashi ta fadi ba Tareda nayi kuka bah,

Hana aka naji labarin itama Amina an daura mata aure da Habib, murna sosai nayi shi, domin kuwa har naso zuwa inda gidan ta yake amma kuma bansan gidan ta bah. Ba yadda na iya, aka na hakura na fauwala wa Allah komai, domin shine Mai jikan bayinsa.

Babu bata lokaci, Harun ya neman mu makarantar Jami'a, na fara zuwa Harna karanci medicine, yayin da itama Amina abunda ta karanta kenen.

Hana aka mukaji labarin cewar Abba ya mutu bisa hatsarin mota daya gamu dashi, kuka mai cike da danasani nayi, saboda a ganina nice sanadiyar mutuwarsa .

Bayan lokaci ne Kuma naji labarin kayi aure ka auri Fatima. saboda kunya abunda na aikata bah Lallai ku yarda dani bah yasa nak'i zuwa auren.

Hana aka kwatsam watarana na fara amai mukaji asibity, hanan likitoci suke sanar mana da cewar ina dauke da cikin wata biyu.

Sosai mukayi murnan wannan cikin yayin da Haruna ya dora son duniya akaina har cikin yakai wata Tara.
Ganin muna rayuwa cikin farin ciki da qaunan juna, yasa Karima ta kuma dawowa cikin rayuwar mu, a wannan karan bah ita daya bane, su dayawa ne domin kuwa tayi joining yan kungiyan asiri .

Lokacin ta umarci mijina Harun da ya dunga mata aiki, shikuwa yace bazai taba aikata akan bah. Kuma yace da ita sai ya tona asirin ta a idon jama'a, ya dau Wayanshi Tareda kira police.

Karima na ganin akan ta harbe shi da buduga, ya fadi a wajan mutacce, daidai lokacin kuwa na kuda ya kamani.

Babu bata lokaci police zuka zo, suka kamata, aka kaita police station.

Ni Kuma a lokacin na Haifi dana, kuka nashashi Harna gode Allah, yayinda aka suturta harun aka kaishi gidansa na gaskiya.

Bayan shekaru biyu na gama makaranta na nayi NYSC na a garin Kano, yayinda akayi posting dina'a hospital, na Fara aiki

bayan wasu lokaci naji labarin ta futo daga cell, akan bah karamin tayar min da hankali yayi bah, domin kuwa bansani bah ko wannan futowar tata ya kasance wani gagarumar matsalan, cikin sa'a kuwa ta daina bibiyar rayuwa ta.

Hana aka na shirya Domin naje na nemi gafarar ku, zuwa na keda wuya naganta acikin gidan nan wai a matsayin matar aure, ganin aka bah karamin tayar min da hankali yayi bah, domin kuwa nasan da cewar bah alkhairy ne ya kawo ta wannan gidan bah.

Akan yasa na juya na tafi gida na cigaba da lallaba rayuwata da Kuma na dana. Ina nan duty na a hospital naji kira ya shigo bah bata lokaci, na d'aga Kiran tareda karawa a kunne na,

Muryar dana ji ne yayi matukar girgiza ni, muryar dana ji kuwa bata kowa bace illa na Amina, sosai Nayi murna Mara misaltuwa a ranar, mu ka taba hira, Kuma tace min zata dawo asibity da nake aiki.

Nadira tace kina nufin Doct Amina itace yar uwar Mom, Doct khadija ta bata amsa da fadin kwarai kuwa itace yar uwata, amma kuma har yau har gobe babu wani a tsakanin su dayasan cewa sudin yan uwa bane, domin kuwa, duk saida na bi hanyan danasan cewar Karima baza ta ga Amina bah, domin karta ganta.

Kamar yadda nake fada, bayan kwanaki aka kawo matar yahya, asibity zata haihu, yayinda iyaka Karima take na kuda, a taredai naga kun kawo su asibityn, ganin akan dana yi yasa nasa face mask ta yadda baza ku gane ni bace,

Na karbi haihuwar Fatima da Kuma na Karima, cikin rashin sa'a Kuwa, dan da Karima ya haifa ya ruga mu gidan gaskiya,

Shine sai Karima tamin barazana da d'ana, tace idan ban sauya yaron bah, na bata na Fatima saita kashe d'ana, jin akan yasa

Please Login or Register in order to submit comment