Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

kuma suka sake dawo kata fes saman kai kamar yadda suka dinga yi mata kai komo a qwaqwalwa.

Yadda suka kafe juna da idanu haka bibi ta kafe maina din da ido. Gabanta nason faduwa zuciyarta na ayyana mata abubuwa da dama. Meye dalilin irin wannan kallo da yakeyi mata haka?. Zuciyarta yanzun bata da tabbas akan maina,duk wani motsi nasa a yanzun abun ta sanya masa ido ne.

Idonsa ya dauke daga kan sultana din yana qarasowa cikin falon. Ba abinda ke dawo masa a rai irin qarfin halinta da kuma taurin zuciyarta,ta yadda har ta iya kaishi ga kwana a policestation,wannan wanne irin hadari ne da ita?,a wadannan shekarun nata da duka duka idan aka kacaccalasu gida uku baifi ta tsira da shekaru qwara hudu ba?,me zai faru a nan gaba muddin dai tana da irin wannan zarrar?.

"Barka da safiya bibi" ya furta yana zama daura da ita,abinda ya sanya sultana sake kame jikinta guri guda kenan,ta kuma lanqwasa qafafunta tana maqalewa jikin bibi,har yanzu idanunta qur a kansa,tana jin kamar ma kowanne motsi idan yayi zai iya zama cutarwane a gareta. Bata sake kuma shiga matuqar tsoro ba saida bibi ta zaunar da ita a daxu bayan sallar asubahi tayi mata irin fadan da bata taba yi mata makamancinsa ba,ta kuma gaya mata meye ma'anat fyade da har zata yiwa dan uwanta mummunan qazafi da shi,illarsa da yadda yake taba rayuwar diya mace. A lokacin ta sakejin jikinta yayi mugun mutuwa,ta kuma sake jin mugun tsanar maina da tsoronsa. Banda haka duk da sanin illarsa shi da yayi din amma yaci alwashin sai yayi mata?,dama ashe shi din DAN ISKA ne bata sani ba?. Tayi furucin fyade ne saboda gani data taba yi wata jaruma tayi cikin shirin film,kuma ta samu kubuta daga hannun jarumin.

"Lafiya qalau" bibi ta amsa masa da salon amsa gaisuwar da ba irinta suka saba ba

"Tashi ki bamu guri" maina ya fadi yana maida dubansa ga sultana dake masa kallon Allah ya tsine uwar me qarya,kallon da yayi kama da kallon ban sanka ba, yau na fara ganinka

"Ki nemi hijabi ki saka" bibi ta fada tana bin sultana da kallo wadda ke sanye da wando da 'yar Short sleeve shirt wadda ta bayyana santala santalan damtsenta. Maganar ta sanya hijabin sai maina ya gaza fahimtar me ma'anarta?,da bai gane ba sai ya share batun ya dubi bibi din bayan sultanan ta iske daki

"Haquri nazo na baki akan furucina na jiya,kiyi haquri,ba kuma ina nufin hakan har raina ba,kuma ba zan sake lafazi makamancin wannan ba" idanu bibi ta gwalalo tana dubansa

"Wa?,ai tsohonka kadai nake jira ya dawo yayi mana shamaki,ni zaka yaudara aliyyu?,kaman bansan halinka ba?,kafiya taurin kai da naci akan dukkan abinda kace zakayi?,ni zaka yaudara da kalaman ban haquri?, tabdi.....bazan taba yarda ba" bibi ta fada tana kada yatsanta dan manuni.

Shuru kawai yayi yana kallonta har ta kammala,sai yadan lumshe idonsa ya bude yana dubanta,can qasan maqoshinsa yana qoqarin hadiye bacin ranshi,donshi a son ranshi banda bin umarnin ama ma bazaizo wani bata haquri ba saidai aje a haka

"Ki yarda dani,da gaske nake baki wannan haqurin bibi" ya maimaita yana kafeta da ido. Dubansa tayi cikin idanu na wasu sakanni,kamar zatayi magana sai kuma ta fasa,ta juye da rufeshi da masifar da yayi imani sultanan ya kamata ta yiwa ita amma tazo shi ta balbaleshi da ita.

Har tayi ta gama bai sake ce mata kanzil ba,sai data sauke sannan yace

"A bani breakfast"

"Yau bamuyi da kai ba"

"Nasan hanyar kitchen" ya fada yana miqewa hadi da gyara zaman rigar jikinsa ya soma takawa

"Kaga,nifa yanxu ina da diya mace da nake raino nan sashen,ba kowanne lokaci ya kamata ma ka dinga shigomin ba,ko zaka shigo ma ka dinga neman izini saboda mu kintsa" cak ya dakata da tafiyar,ya waiwayo yana duban bibi din yana jin maganar nayi masa banbarakwai.

Wata irin dariya mara sauti ce ta subuce masa,sai kawai ya cije lips dinsa yana kada kai. Wai dukka akan sultana take gaya masa haka?,sultana ce wai har za'a kira budurwa?,sultanar da tasan hanyar club tasan hanyar hotel wai yanxu ita akewa kaffa kaffa?,bama haka ba.....shi tasa lalacewar ma ta rasa ina zata qare sai akan wannan qaramar halittar?,ya baro manyan mata da komai yaji a hostel,suna kiransu ma free of charge,matan abzinawa,shuwa da fulani masu shegen kyau da baijin duk kyau irin na sultana zata bude musu idanu tunda nata bai riski 'yammatanci ba,su basu tsone masa idanu ba sai sultana?.

Har zai biyewa bibi din sai yaga ma bashi da lokaci,ya sanya kai kawai ya wuce kitchen din abinsa.

Har ya cinye asabar da lahadinsa baima sake haduwa da sultanan ba. Litinin da sassafe ama ta sakashi a gaba akan ya koma. To shi dinma dama ranar yayi niyyar komawar,don haka ya tattara ya nasa ya nasa ya koma din.

Kamar jira sultana din takeyi dama ya tafi sai ta warware ta koma halayyarta. Sau tari idan ama na veranda dinta tana hangenta ta farfajiyar gidan tana wani iya shegen saidai kawai taja tsaki

"Allah ya shirya". Tana hangen abubuwa da yawa da yarinyar ke dashi wanda sauran sa'aninta a gidan basu dashi. Amma mugun gata da saken da ake bata a gidan ya hana komai ma tasiri.

Bata sake shiga taitayinta ba sai ranar da ya sake zuwa hutun kwanaki uku. Shi zam baima wani lura da yadda take mugun gudunsa da d'ari d'ari da shi ba sai a wannan zuwan da yayi,d'ai d'arin da shi baima fahimci akan meye takeyi ba.

A hankali bibi ta fahimci komai,rashin sakewar sultana din a duk sanda akace yau maina ya sauka a gidan,abunda ya dinga taba ranta kenan,ta dinga jin babu dadi. Hakanan zuciya ta dinga yi mata saqe saqe kala daban daban cikin ranta. Kwata kwata itama bibi din sai ta dinga rasa nutsuwarta idan yana nan din,a hankali itama sultanan saita daina kwana dakinta duk sanda maina yake gari,idan kaga ta koma dakinta to baya nan ne ya koma makaranta.


*********K'arfe hudu na yammacin ranar,ranar da gidan ya kasance akwai qarancin jama'a,saboda kusan duka yaran gidan sun wuce islamiyya idan ka dauke sultana dake kitchen din bibi a dai dai lokacin. Oat takeson sha amma kuma tanja bata kusa,ita kuma baya ga tanja din bata yarda kowa ma yayi mata komai a gidan sai bibi. Bibi a lokacin bacci take,ita kuma ta matsu da tasha din,abinda ya sanya ta shiga kitchen din kenan ta dinga hada kwabarta.

A qalla babban gwangwanin oat da qatuwar gwangwanin madara ta kusa juyewa cikin bowl,ta kammala tayi tsaye riqe da qugunta tana tunanin yadda zata tafasa ruwan zafi. Tana dari dari saboda tana tsoron wuta,tana kuma iya tuna yadda ruwan zafi ke mugun tururi duk sanda tanja ta saukeshi daga saman gas.

Bacci yayi me nauyi a yau din,saboda muguwar gajiyar dake jikinsa sakamakon training da sukayi duka wancan satin babu hutu,wannan dalilin ya sanya yana samun interval na kwanaki a wannan satin yayo gida,yasan a nan dinne kawai zai huta sosai,kanshi yayi fresh yadda ya kamata,babu me takura masa,koma bayan hostel da ba lallai su sultan su barshi ya huta ba su da gayyar abokansu.

Dispenser dinshi babu ruwa ciki,don haka ya zura jallabiyyarsa me sulbi 'yar marocco ya sauko ya fito daga dakin.

Tun azahar yasan ama bata nan,don tana da taro na musamman a qungiyarta data bude don taimakawa mata iyayen marayu da zauwara,wannan dalilin ya sanyashi wucewa kai tsaye sassan bibi.

A falo yayi sallama,tunda yaji shuru yasan bacci ne ya sace bibi din,sai kawai ya wuce kai tsaye ya kutsa zuwa kitchen yana mamakin yadda yau sam babu wulgawar masu aiki ko daya a sassan.

Da sallama ya shiga kitchen din,sallamar data sanya zuciyar sultana wani mugun bugawa,wani tsoro ya mamayeta wanda ya sanyata waiwayawa da sauri tana dubansa.

Duba biyu yayi mata ya dauke kashi yana qarasa shigowa, shigowar da ta qarawa sultana razani,ta duba hagu da dama,ba kowa a kitchen din sai su biyu rak,hasali ba motsin kowa ma a sassan sai nata da nashi,tayi wura wura kawai saita sanya gudu tana ficewa daga kitchen din. Da kallon mamaki ya bita

"Anya yarinyar bata samu motsuwar kai ba?,gudun na meye takeyi kamar wadda aka biyo?,ko wani zallar rainin wayonne?" Ya raya a ransa,sai kawai ya juya yaci gaba da takawa,takun da baiyi guda uku cikakke ba ya jiyo bibi tana doka salati,kafin kuma muryarta ta maye gurbi

"Ke!,meye hakan?,waye ya biyoki?,lafiyarki qalau?" Duka bibi ta jefa mata tambayar,tambayar da ta gaza amsa mata sai riqe bibi din kawai da tayi. Har cikin zuciyarta ita kanta tana jin yadda take gudu qwarai da gaske,bugun zuciyar da take motsawa da wani irin qarfi da batasan meye sila ba

"Matsamin ni na shiga naga wanne qaddararren abune" bibi ta fadi tana ture sultana din daga jikinta ta kuma kutsa kitchen din babu tsoro ko dis a ranta.

Cak ta tsaya saboda ganin maina da tayi a kitchen din,ita batasan ma ya shigo garin ba,dama shine ya biyo sultana din?.to me yake shirin aikata mata?, Sai ta runtse ido tana furta

"A'uzubillahi" a sarari saboda wani mummunan tunani da ya d'arsu a ranta

"Dama kaine ka biyomin yarinya?,me tayi maka?,me kuma zakayi mata?" Bibin ta fada zuciyarta tana dan bugawa.

A nutse ya waiwayo ya dubeta,cikin sakanni qalilan ya samu amsar tambayoyin da ya jima yana yiwa kansa game da kaffa kaffan bibi a kansa da yadda yarinyar ke wani guje guje. Murmushi ya subuce masa, murmushin da ya sake dada yawan fargabar bibi

"Me kuwa zanyi mata?,ko tace miki fyade nayi mata?"

"Qaniyarka aliyu" bibi ta furta tana watsa masa daquwa duk kuwa da yadda zuciyarta ke tsananta bugawa. Bai sake ce mata komai ba kamar yadda itama ta kasa ci gaba dace masa komai,saboda qafafunta sunyi nauyi kamar yadda jikinta ya sanyaya,sai kawai ta juya tana fita a dakin.

Qaramin tsaki maina din yaja,shi lamarin nasu ma sam yanzun dariya yake bashi,inda sun kwantar da hankalinsu ma sam ya fidda sha'anin sultana a ransa,duk da abun yana matuqar yi masa wani irin ciwo qasan zuciya,to amma ya ajewa ransa akwai lokacin da zai fatali da komai da kowa ya kuma gyarata koda kowa bayaso.

Tunda ta koma daki tunani iri daban daban yake bijiro mata,har ta shiga bandaki ta daura alwala ta fito duk tuntuni tayi sallar la'asar dinta sultana na maqure saman gado. Kallo daya tayi mata ta dauke kai,ai kuma shikenan,duk wani sakewa da walwala tata tayi qaura,tasan bata da wani sauran sukuni kuma.

Gefen gadonta ta zauna tana fidda numfashi. Ta soma gajiya da mugayen saqe saqen da zuciyarta keyi mata akan maina din,ta gaji da kokwanto,ta kuma gaji da bacci da ido daya,tasan kuma tunda zuciyarta ta dasa zargi akan maina ba zata taba bari ba,ba kuma zata taba bari ta huta ba.

"Gwara na kawo qarshen komai" bibi ta fada tana janyo wayarta.
[4/18, 10:43 PM] C.E.O HUGUMA CLOSET: *_GUDUN ƘADDARA_*

*H U G U M A*

PAGE 26


Bugu biyu rak ya daga wayar,daga can bangarensa cikin matuqar girmamawa yayi mata sallama

"Wa'alaikummus salam warahmatullah,ka yini lafiya ya aiki?"

"Lafiya qalau bibi,alhmdlh,kuna lafiya?"

"Lafiya muhammat,kamar yaushe zaka dawo?"

"Gobe ma nake sanya rai bibi......wani abune ya faru?" Kai ta girgiza

"A'ah babu komai,faduwa ai tazo dai dai da zama,Allah ya dawo dakai lafiya"

"Ameen ya Allah,amma ina fatan lafiya?"

"Lafiya qalau sai alkhairi"

"To Allah ya tabbatar"

"Ameen ya Allah" basuyi doguwar magana ba jin cewa yana cikin jama'a tayi masa sallama ya ajjiye wayar.

Qatuwar ajiyar zuciya ta sake saukewa tana ajjiye wayar,sai a yanxun takejin kamar nauyin dake zuciyarta ya fara raguwa,ta hade hannayenta biyun duka ta lanqwasa waje daya tana furta

"Allahumma salli wa sallim ala sayyidina muhammad" sai ta maida dubanta ga sultana. Ga mamakinta har bacci barawo yayi awon gaba da ita,sai ta samu kanta tana me zuba mata idanu,ba abinda take tunawa sai nafessa,shin KO TARIHI ZAI MAIMAITA KANSA?,shin hukuncinta shine dai dai ko akwai gyara?,akwai ta inda ta kuskure?.

Duk ta inda ta laluba a zuciyarta da neman amsar tambayar sai taji ta gayawa kanta da kanta dai dai tayi, addu'a ta dinga yi cikin ranta tana sake tsananta neman zabin Allah,sai ta dinga jin tabbatuwar jin cewa dai dai tayi din.


*_THE BEGINNING_*


Hira sukayi a qalla ta kusan mintuna arba'in,irin hirar dake tsakanin uwa da danta. Su biyu ne rak a falon,dai dai sanda agogo ke tafiya a hankali har zuwa sanda ya nuna qarfe tara saura na dare

"Bibi" Sir muhammat mayak'i ya furta yana gyara zamansa

"Na'am" ta amsa masa tana dubansa

"Jiya kin kirani,kuma kiran da kikamin din nasan akwai babban dalili"

"Qwarai kuwa" bibi ta fada tana gyara zamanta

"Wato akwai wani al'amari da ya faru ranar da tafiya ta kamaka safiyar juma'a,washegarin ranar da akaga maina" gyara zamanta tayi ta warware masa komai sannan tayi shuru tana dubansa. Kai kawai muhammat mayak'i yake jinjinawa

"Shi aliyyun a gabanku ya furta wannan mummunar kalmar?,ashe aliyyu bashi da hankali har yau ban sani ba?"

"Na gaya maka ya shigo ya bada haquri,to amma ni gaskiya zuciyata har yau har kwanan gobe bata nutsu ba.....muhammat duk sanda naji motsin maina a sassana sai hankalina ya tashi,duk sanda naji maina yazo gidan nan bani da sauran nutsuwa har sai ya koma. Dani da kai da dukka sauran wanda ya rage cikin gidan nan mun sani,Aliyyu bai taba furta cewa zai aikata abu be aikatashi ba,ina tsananin tsoron sharrin zuciya,ina gudun halin 'ya'yan yau,ina kaucewa faruwar mummunan abu cikin zuri'ata,ina da tsoro muhammat ina da fargaba,kuma babu abinda zai kawo mini qarshen wannan fargabar sai abu daya....."

"Idan da raina kuma ina da iko bibi,bazan taba barin mahaifiyata cikin fargaba ba,meye abinda zai faranta miki?"

"A daura auren MAINA da SULTANA,koda har yanzu akwai qudurinsa cikin zuciyarsa,koda zai aikata din zaizo da sauqi saboda ta kasance halalinsa ce ita din".

Jinjina kai kawai aba yakeyi cikin nazari,saidai tako ina maganar bibi ta gamsar dashi,shi kansa bazaiso ace diyan cikinsa ya yiwa 'yar mammodu mummunar barna ga rayuwarta har haka ba.

"Juma'ar nan me zuwa nan da kwanaki hudu zan daura aurensu bibi in sha Allah,hakan yayi miki?"

"Allah ya albarkaci rayuwarka muhammat, ubangiji yadda kake farantamin yaci gaba da faranta maka kai da sauran 'yan uwanka"

"Ameen ya Allah"

"Amma kuma hamdiyya fa?,ina gudun kada tarihi ya maimaita kansa" qanqanin tsaki yaja

"Kada ki sanyata a sahun qalubale bibi,wancan dinma RABO NE YA RANTSE shi ya kawo komai".

Duk da ba shakka ko shayin hamdiyya ama yakeyi ba,amma haka ya dinga juya yadda zai gabatar mata da zancan,a haka har lokacin kwamciya bacci yayi,ta kawo masa tea din da duk dare saita dafa masa yasha yake kwanciya,tunda jajayen sawaye kawo yau ba tana nan da wannan dabi'a tata bata canza ba

"Allah yayi miki albarka,amma zauna zamuyi magana" ya fadi yana karbar tea din daga hannunta sannan ya kurba kadan yana ajjiyewa saman bedside drawer.

Zaman tayi idanunta bisa kansa tanason jin abinda ya sanya ya dakatar da ita a irin wannan lokacin da yace mata a matuqar gajiye yake,hutawa kawai yakeso yayi sosai

"Kin qagauta kiji meye ko?" Ya tambayeta cikin zolaya,sai ta saki murmushi tana kauda kai gefe. Tana da zafi a wasu al'amuran,ba a komai takan sanya baki ba,tana kuma da kawaici saidai a wasu abubuwan kuma bata da haquri sam ko daukan ganganci ko ba dai dai ba

"Inaso idan Allah ya kaimu juma'ar nan na daurawa danki aure" ya fada cikin halin ko in kula,kuma hankalinsa kwance kamar ba wani batu bane me muhimmanci.

A mamakance ta juyo tana dubansa,kanta yana daurewa tam

"Dana kuma?,wanne dan nawa?"

"Kina da wani shaqiqin d'anne sama da Aliyyu maina?" Ya tambayeta idanunsa cikin nata

"Maina kuma!?" Ta jefa masa tambayar ranta yana motsuwa cikin zallar shakka da mamaki

"Eh mana,amma fa kada kice zaki wani daga hankalinki,ba wani aure bane da za'a yiwa shagali ba,sultana ce kawai zan daura masa aure da ita shikenan suci gaba da rayuwarsu,sauran lamarin kuma mun barwa Allah ikonshi".

Batasan takai tsaye ba sai da taji qafafunta suna taka qasa,tamkar wadda aka daurewa jijiyon jikinta gaba daya haka taji. Aba ya daga kai ya bita da kallon yadda ta miqe din a razane

"Ko a yanzunma bai isa aure ba kaman yadda kika yi akan nafessa mahaifiyar ta?" Motsa bakinta tayi,akwai maganganu masu yawa a ciki amma sai ya sake datsar hanzarinta

"Kayi GUDUN K'ADDARA iya iyawarka,amma ka sani matuqar tana rubuce cikin littafin KADDARARKA to sai ta iskoka.......shawara daya zan baki,koda wasa kada kice zaki kwatanta abinda kika kwatanta a baya,domin qarshen wannan karon kece ba zaiyiwa kyau ba......an zana a cikin zanen qaddarar sultana maina ne yafi dacewa a daura mata aure dashi a yanzun,bansan gaba ba,bansan kuma me gaban zata haifar ba" ys qarashe jawabin yana jan blanket zuwa qafafunsa.

Kamar wadda aka dasa haka taci gaba da tsaiwa a wajen,ta gaza furta komai saboda wani bahagon yanayi data kasa tantance launinsa dake kai kawo a zuciyarta SO KO K'I?,MURNA KO BAQINCIKI?,oho itama bata sani ba......abu daya dai ta riga ta sanyawa ranta,ta yaya zata so abinda tasan wani irin ZARGE ne me wuyar kwantuwa?,sultana fa?,kaf yaran gidan a rasa waye za'a bashi sai sultana?, sultanar da tun ba'a diga samuwarta a mahaifiyar mahaifiyarta ba ta nesanta tsakanin maina da mahaifiyartata?,ta hana UWA yanzu kuma 'YA zata maye wannan gurbin na UWAR?,ta yaya hakan zata faru?.

Wadannan dama tarin wasu tambayoyin su ta dinga yiwa kanta ita qwallin qwal cikin dakinta. Batasan da waye zata tattauna wannan maganar me uban nauyi da tarin sarqaqiya ba,abun tana jinsa kamar a cikin mafarki ne kawai bawai a gaske ba,SULTANA?,MAINA?,to waye ya qulla?,......amsar dai daya ce,ta tabbatar bibi ce,da basu cimma nasara ba wancan karon shine a yanxun suka shammaceta?. Gwara nafessa sau malala gashin tinkiya NAFESSA tafi sultana nagarta nesa ba kusa ba,sultana din ALBASA CE wadda sam batayi halin ruwa ba,nafessa bata da wani aibu gabanta da bayan halayenta kaf,banda wani dalili guda biyu rak,bataga abun gufu ga nafessa ba,amma kuma sultana fa?,aibubbuka da abubuwan gudu gasunam birjik basu da iyaka

"Karki matsantawa kanki da yawa,ina kikaga hadi tsakanin maina da sultana?,ko hankali ya bada haka?,barsu suyi iyakar iyawarsu,idan suka sheqa suka samu babu qwaya zasu warware da kansu" hajiya dezatou tace da ita.

Daren gaba daya bata samu wani isashen bacci ba. Da safe da maina ya shigo suna breakfast kallonsa kawai takeyi tasan baisan abinda ke shirin faruwa cikin gidan ba,amma taji aba din yace idan ya kammala ya sameshi a baya ta gurin swimming na gidan,ta tabbatar zancan zaiyi masa.


*_TOFA MASU KARATU,AKWAI TARIN TURKA TURKA CIKIN LABARINNAN_*

"_akwai BAZATA masu yawan gaske_*

*_inason na jaku zuwa wata kyakkyawar gaba da zata zame mana tamkar tsani ko shimfida na labarin da zamu samu bigire me kyau bayan sallah da zamu dora_*

*_SHIN MAINA ZAI YARDA?_*

"_SULTANA FA?_*

*_IDAN HAR HAKAN YA YIWU ME ZAI BIYO BAYA?_*

*_AKWAI WATA MURDADDIYAR QADDARA CIKIN LABARIN,WADDA KE ZAMOWA TAMKAR WATA GUGUWA DAKE WAJIGA ZUKATANSU DA ZUKATAN MUTANE DA DAMA_*

*_AKWAI TARIN KUKA/NADAMA/SADAUKARWA/BA ZATA DA QARFIN DA QADDARA KE DA ITA CIKIN RAYUWAR KOWANNE BAWA_*

_INA SAKA RAN GOBE NA BAKU SHAFUKAN DA ZASU ZAME MANA MURFI NA LABARIN IN SHA ALLAH,MURFIN DA ZAI RUFEMU HAR ZUWA BAYAN WATAN AZUMI_


HUGUMA CE 👑👑
[4/18, 10:43 PM] C.E.O HUGUMA CLOSET: *_GUDUN ƘADDARA_*

*H U G U M A*

Page 28



***Wani irin jiki ne da ita wanda baya qaunar zafi ko kadan,wannan ya sanya take da vest da wandunansu masu yawa da takan sanyasu koda kuwa bawai zafi akeyi a garin ba. A hakanma bibi din ta kwashe wasu ta bayar saboda ta fara girma baici ace tana ci gaba da sanyasu ba.

Su hudu ne a falon,bibi din,deeja mai aikin bibi,tanja sai sultana din da tanja ta kama kan nata take gyarawa. Ana gyaran kan tana qorafi don ita sam bata son a taba mata suma. Yatsuntsa guda goman duka lalle ne aka saka mata. Idan akwai abinda takeso cikin ado kaf to jan lalle ne,shi dinma kuma bawai tana iya zama bane ayi mata qafa da hannu ba,saidai ayi mata iya yatsun qafa ko iya yatsun hannun.

Sallamarsa cikin falon goye da qatuwar jakar 'yan makaranta ta tsaida numfashi na daqiqu daga jikin sultana,sannan tayi wani tsallen albarka tana miqewa,da sauri tanja ta riqota amma tuni ta zille,lallen kuma dake hannunta ya sabule yayi nasa guri,bata kuma tsaya ba ako ina sai daki.

Dukkansu suka bita da kallo har ta qule cikin dakin. Wani abu ya hadiye yana qarasowa cikin falon. Karon farko da ranshi ya baci akan abinda takeyi din idan ta ganshi,ya karanci abun nata harda iskanci da iya shege,banda hakan daga sallama kamar wadda taga mala'ikan daukan rai.

Bayan sun gaisa su tanja miqewa sukayi suka basu guri kamar ko yaushe. A yau din bibi ta sakar masa sosai kamar yadda suke a baya,har abun yadan bashi mamaki

"Sai yau aka tuna damu?" Ta fada tana 'yar dariya

"Sai yau akaga damar sakarmin fuska?" Ya fadi yana dage mata girarsa guda daya

Please Login or Register in order to submit comment