Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ba tare da ya waiwayo ba.

Dukka gwiwarta ya kashe mata da Maganarsa,tunda mommy dinta tace mata maina dinne yazo takuma kai masa ruwa da snacks hankalinta ya dauku. Ya jima yana burgeta,ta dade tana qissimashi cikin ranta a matsayin miji,saidai tana mugun shakkarsa,yana kuma yi mata matuqar kwarjini sosai,don koda taje gidansu daga gaisuwa babu abinda yake sake hadasu. To yau din tana ganin ta samu wata babbar dama da ko yaya zatayi wani motsi da zata isar masa da saqon zuciyarta,sai gashi shi din kuma ya katsi hanzarinta.

A sanyayen ta juya tana komawa cikin gidan,wanda da shigarta da kadawar wayarsa duka ba'a yi minti guda ba. Ama ce,sai ya daga yana saka wayar a kunnensa

"Aliyyu"

"Na'am" ya amsa mata

"Wanne irin shashanci ne wannan?,ya yarinya zata kawo maka ruwa ka maidota bakasha komai ba?,wannan ba maida alkhairi baya bane?"

"Afwan" ya fada a gajarce

"Gatanan dawowa,koda ruwan kasha ladan kyautata makan da tayi"

"In sha Allah" ya sake amsawa ama din sannan ta kashe wayar.

Iska ya furzar daga bakinsa yana kallon wani guri na daban. Ta cikin madubi yaga tahowarta,don haka kafin ta iso ya bude side din da yake,abinda ya yiwa meena din dadi sosai ta saki murmushi sanda ta iso tana miqa masa ruwan.

Hannu ya sanya ya dauki gora daya yana cewa

"Na gode" sai ya maida qafafunsa cikin motar yaja murfin ya rufe a hankali. Dan saroro tayi kafin kuma ta juya a hankali tana sake komawa cikin gidan,ranta duka a jagule babu dadi, wato kisan mummuqe yayi mata ruwa ne ya dauka kuma yayi godiya,ya yiwa amansa abinda takeso ba wani qorafi kuma da zata kai.

Sun dan jima suna waya da sultan kafin ama ya iskoshi. Tare suka fito da hajja dezatou din da meena dinma kanta. Tanayi tana satar kallon maina din har suka gama sallama,sai ta matso saitin window dinsa cikin siriryar murya take magana bayan ta miqa masa ledar turaruka

"Yaa maina.....ka gaida gida mun gode sosai da ziyara"

"Au yama gaida gida shi daya meena abun 'yar haka ne?" Ama ta fada tana kallonta cikin dariya. Dariyar tayi itama tana dan sunne kai

"Kiyi haquri ama,ki gaida gida kema mun gode"

"Banaso,sai dana roqa" ta fadi cikin dariyar tsokana maina yana tayar da mota.

Shuru ne ya fara biyo baya cikin motar kafin ama tayi magana

"Kaga meena ko?,yarinya nutsatsiya me hankali,kullum daga makaranta sai gida" ama din ta fadi

"Uhmmm" mainan ya amsa mata

"Ba ruwanta ba surutu ko hayaniya ko rawar kai,shekararnan zata gama karatunta,hajiya dezatou so takeyi ta bada aurenta ko kudinta a kawo idan yaso saita dora karatunta"

"Uhmmm" maina din ya sake fadi

"sanda zataci rabin karatun sai ayi auren,kafin takai ga haihuwa ma qila ta kammala karatunta"

"Hrmmmm" ya kuma fadi idanunsa suna kan titi. Wani kallon takaici ama ta bishi da shi

"Hala kam kurmantaka ta sameka maina?" Ta jefa masa tambayar cikin hasala. Kadan ya waiwayo ya dubeta sannan ya maida dubansa ga titi

"Me ya faru ama?"

"Ya ina baka labari kaman me ciwon baki?,daga hmmm sai hrmmm?" Dariya taso qwace masa amma ya daure,ya fuskanci inda ama din ta dosa tsaf,saidai kuma shi sam baiga macen data dace ya aureta ba kaf fadin niger da maqotanta,a yanzun dai bai gani ba,shi ko kusa ko alama meena batayi masa ba,baiga wani abu tattare da ita na musamman ba,shi da yakeson macen da ilimin addini suka ratsata ainun,ilimin boko dinma ya samu mazauni a wajenta,macen da shigarta ta banbanta da shigar matan qasar nijer ma gaba daya,shidai a yanzu cikin qasarsu baiga matar aurensa ba,kaf cikin matan da yake gani baiga wadda ta taba burgeshi koda kuwa sau daya ba

"Kiyi haquri ama,ai labari kike bani,bazaiyiwu kuma na katseki ba"

"Kaji dashi dai......ni meenatu banga ta dace da kowa ba saikai,ita nake maka sha'awa,saboda haka ka maida hankalinka,zaka saka rana ka koma ku sake ganin juna kai da ita"

"Allah yayi zabi mafi alkhairi" kawai yace da aman. Babu wani zafafawa,shi yasan halin ama,a yanzun rigima kawai takeji,shi yasa ya lallabata aka bar maganar a haka. Yanzun banda rigimar ama shi daketa kiciniyar ganin ya zama cikakken likita kuma soja wa yake ta wannan batun?,baijin yanzun zai kalli ma wata diya mace,har sai ya kammala cika mafarkinsa da tun yana yaro qanqani yakeyi.

Suna parking harabar gidan suka taka zuwa haraba ta biyu qasan rumfar da aka tanada saboda hutawa ya hanga cike da matasan yara,koda ya duba still dai sultana ce gang leader. Agogon hannunsa ya kalla ranshi yana baci,dai dai lokacin da ya dace ace tana islamiyya amma ta tara mutane ana buga game ana ihu.

Dole ya dauke kansa ya kuma taushi zuciyarsa yayi wucewarsa ciki,amma na ankare da shi,hakan kuma da yayin ya kwantar mata da hankali,ko banza tasan aliyyu din me biyayya ne.

Ta gabansu ta wuce,kusan hada baki sukayi suka gaidata. Wani abu guda daya dake bawa kowa mamaki cikin gidan. Yadda sultana din ke ganin girman ama ainun cikin gidan,tana cikin jerin sahun mutum ukun da ko meye sukayi mata bata iya maida musu martani.

Ita dinma kadaran kadaham ta amsa musu tana wucewa ciki.

******** To cikin kwanakin ukun da ama tace masa a cikinsun ya shirya ya koma makarantar. Abinda ya sake baiwa sultana dama tayi wata irin sakewa,komai nata gaba gadi take yinsa,koda bibi ta soma fada yanzu zata saki kuka,kukan da yake mugun raunata bibi din.

Hankalinta kwance ta baje kolinta,koda akayi hutu ma,dogon hutun da yakan dauki dalibai a qalla wata uku tafiya tayi yawan hutu abinta cikin dangi da 'yan uwa da suke abun arziqi tasu tazo daya. Abinda ya sake taka muhimmiyar rawa wajen koyon abubuwa da yawa a tattare da ita,saboda kusan duk gidan da taje din gida ne da yaran gidan basusan wani abu waishi takura matsi ko sanya takunkumi ba

(Kira a nan a gareku iyaye,bawai yara sunyi hutu ba a dauki kuma dabi'ar zuwa hutu gidajen 'yan uwa,a kula da inda yaro zayaje,a tabbatar inda zaije din saidai ya koyo wasu zababbun kyawawan halaye bawai ya sake bankada ko azama cikin nashi dabi'un da akeson rabashi da su ba).

Duk da maina din ya zare hannu da jiki da yawa daga cikin sha'aninnikanta amma hakan bai sanya a boye ya zare hannu daga kanta ba,a duk sanda yazo gida hutu yana biye da komai nata,abun da yake sake bata masa rai na rashin ci gaba akan dabi'unta saima koma baya da ake sake samu. Tuni a islamiyya dukka yaran gidan da suke aji daya sukayi gaba suka barta. Don su najma da lamira yanzun haka suna ajin sauka,watanni kadan zasuyi khatama. Ko a boko dinma don kawai tsarin makaranta ne na 'ya'yan masu dashi,abinda ya tseratar da ita kawai kenan,amma a matakin karatun dake cikin kanta duka duka bai wuce ace a sannan tana primary ba.

Abun yana daga masa hankali ta yadda kowa ya gaza hango abinda shidin yake hangowa,ko kuma yace me ruwa da tsaki da kuma damar sakata ko hanata suka gaza gano hakan. Ba abbansa kadai ba,hatta oncle bashar da oncle umar din suma duk sammakal. Wata irin soyayya ce gaba daya ta uwarta da kakanta wato dan uwansu suka aza mata,wani irin gata da ko quda basuso ya cutata mata.

Ama dinsa ce kadai yake hangen tana hangen abinda yake hange din,zuciyarsa ta jima tana gaya masa zata iya tallafa masa wajen taro sultana. Yana shakkar tararta da maganar,amma ranar da abun ya cishi tura dole ya isketa da batun.

Wani babban album ne a hannunta amma saita rufeshi tana kallonsa

"Maina,ka cireni daga wannan batun kwata kwata,ba hurumina bane,kai kafi kowa sanin haka,ni zan taba diyar nafessa?,a wanne matsayin kenan?,hatta da ubanka ka manta kallon da yakemin a kan sultana?" Kansa ya mirgina gefe,wannan maganar ta tsahon shekaru kudan sha uku zuwa sha hudu ta gaza mutuwa

"Karki duba wannan duka ama"

"A matsayina na wa?" Ta jefa masa tambayar

"Yarki ce ama jikarki ce kema"

"Kaine kaga haka,tashi ka bani guri maina,ni bana sanya kaina a abinda bai shafeni ba ko zai taba mutuncina"

"Sultana bata tana miki rashin kunya ba,bazata miki ba ama"

"Ka bani guri nace ko?kaidai da kaga zaka iya sai kayita yi...." Dauke kanta tayi tana qwalawa saddi kira

"Dauko remote ka canza min channel" ta fada tana sake bude album din nata,saidai can qasan zuciyarta itama wani abu yana tsunkulinta amma tana qoqarin kautar da kanta da tunaninta daga kai. Haka ya qaraci zamanshi a gabanta ya miqe jiki a sanyaye ya fice a falon.
[4/18, 10:43 PM] C.E.O HUGUMA CLOSET: *_GUDUN ƘADDARA_*

*H U G U M A*

PAGE 19


*_THE DESTINY |_*


Su hudu ne zaune cikin falon bibi da babu kowa sai tanja dake kai kawo ita da biyu cikin masu aikin bibi.

Su biyar ne a falon,hanan maama rachida bilkissou sai kuma sultana din. Dukkaninsu su biyar din kowacce idan ka kalleta akwai alamu na samun cikakken gata a tattare da ita,cikin duba na biyu kuma zakasan kowacce ta fita ne daga gidan da sukunin rayuwa ya samu muhallin zama. A tsakanin su biyar kowacce shekararta tsakanin sha biyu ne zuwa sha uku,saidai tarin iyayinsu da rawar kai zakayi tsammanin sun tasamma shekaru sha takwas takwas ne. Sosai halinsu yazo daya,shi yasa abota a tsakaninku keda matuqar qarfi da tasiri,duk wanda yasan daya a cikinsu yasan daya,kowaccensu tana ji da gata da kuma sakewa,duk da cewa a cikinsun babu kamar sultana,wadda bayan fifikon gata data samu,ta samu wani irin fifiko na kyawun sura tun gabanin ta kammala cika mace. Ta mugun iya dressing kamar yadda yaren faransanci ya zauna daram a harshenta,hakan kuma baya rasa nasaba da zaman da tayi a waje cikin turawan faransa na tsahon wasu shekaru harta kammala primary dinta.

"Ni so samu da magariba za'a fara birthday dinnan maganar gaskiya sai yafi dadi" sultana da ta qare karanta katin birthday din hanan ta fada tana maida dubanta ga fuskar rachida. Qaramar dariya rachida ta saki

"Allah ya shiryaki kedai,duk wani harkar rawa kina gaba gaba" ido sultanan ta lumshe

"Hmmm ke bakisan yadda rawa take da dadi bane,Allah ji nake kaman na fara takawa tun yanzu,ni hanan kin gama biyana,irin wannan birthday din nakeson yi qarshen shekarar nan" sultana ta fada tana tashi ta zauna sosai saman kujera,saboda tana hasaso yadda abun zai kasance

"Idan yaa maina ya bari ba" bilkissou ta fada tana zuqe madarar hannunta.

Harara sultana ta jefa mata

"Kina daga kwance kina shanyen madara kina min fatar tsiya,wanne ya maina din da yanzu baya zaman gidan nan ma,saidai munafukai irinsu goumar su gaya masa"

"Baqin buzu?,yana burgeni wallahi" hanan ta fada tana dan murmushi. Caa sukayo mata suna tsokanarta,yayin da sultana ke binsu da ido tana tabe baki. A rayuwarta haka kurum taji ta tsani koda zancan soyayya ma,duk da su din wannan ba fagensu bane dama,ba wani abu bane da sukeyin Maganarsa ba

"Meye abun burgewa a wajen wannan?,kaf halin yaa maina daidaiku ya baro" sultana ta fada tana tabe baki

"Wai ina su najma"

"Kin kuwa tunamin,basu nasu card din" idanu hanan ta zaro

"Ko kema fa lallabawa zakiyi kije baresu?"

"Kada ki damu,sun jima suna cewa a gayyacesu idan za'a yi,barema duka date din da aka saka dodon nasu baya nan,kinga nima hankalina kwance zamuje mu dawo abinmu ba wanda zaya matsa mana,wannan babban hotel da dad ya kama mana hall a ciki ai ya gama mana komai" ta fada tana dariya.

Sun jima suna hirarrakinsu suna sake tsara yadda zasuyi abinsu

"Sauran abinda m ba zamu iya ba auntie haula tace zata tsara yadda komai zai tafi mana yadda mukeso"

"Sai auntie" sultana ta fada tana dariya, tana jin dama itace cikin gidansu hanan,babu matsi babu kuma takura.

Sallama sukayi da Bibi ta rakosu makeken parking lot dinsu inda suka zaunar da driver dinsu yana jiransu. Sai da suka fice a gidan sannan ta juya ciki tana gyara card din hannunta.

Sassan uncle umar t soma shiga,ta samu mamma na sanya turaren wuta a falo. Gaidata tayi mamma ta amsa tana dubanta yadda ta shigo a wani mugun nutse

"Najma fa?"

"Suna daki ita dasu aminata" bata ko waiwayo ba ta zarce dakin da zumudinta,sai mamma ta bita da kallo har ta shige sannan ta dauke kanta tana ci gaba da zuba turaren wutan.

Cikin sa'a dukkansu ta samesu a dakin,aminata najma yasmin da lamira

"Kuzo kuga wani abun arziqi" ta fada tana rarraba musu card din. Karban nashi kowa yayi yana dubawa,najma ce ta fara daga kai

"Birthday din hanan?,haka akeji da ita aka kama mata wannan babban hall din?" Dariya sultana tayi

"Don hall kawai?,sai kinje ma kinga yadda aka tsara gurin"

"Zuwa kuma sultana?" Aminata ta fada tana zare ido. Da wurwuri sultana ta jefeta da harara

"Eh mana,hanan ce fa,kuma idan ya maina kuke tsoro ai baya nan,hasalima shekaran jiya duka duka ya tafi,shi kuma da sake dawowa sai wani satin nan da kwana goma ma,kunga hankali kwance zamuje mu dawo" shuru suka danyi suna kallon juna

"To ta yaya zamu fita su mamma basusan birthday muka tafi ba?"

"Karku damu da wannan kun manta ina da modu?" Dariya suka saki plan din nata yana musu dadi. A nan suka sake suna maida yadda abun zai wakana.

Tun daga ranar take shirya kaya da shigar da zatayi. Duk da dimbin suturunta da suka kusa kala dari biyu amma sai taga sam basuyi mata ba. Ta tashi hankali har sai da aba yasa aka dauketa taje ta siya abinda ranta yakeso da sunan wani taro zasuyi a makaranta. Ba wanda ya qaryatata tunda makarantarta daban data sauran.

*_THE DESTINY ||_*


*****Wadatacce kuma yalwataccen daki ne wanda a qalla yake dauke da manyan katifu masu azabar tudu da taushi guda uku. Turkey carfet ne malale a qasan dakin wanda ya dace da curtains dake maqale jikin manyan windows da qofar dakin.

Ba wani tarkace a dakin,domin kuwa komai yana tsare ne bisa muhallinsa cikin tsaf da kuma wayewa. Akwai babbar cupboard ta jikin bango wadda daga samanta akwatune masu kyau a qalla sunkai shida mallakin samarin dakin.

Daga gaban murfin cupboard guda daya maina ne a tsaye yake dauko wankakkun kayansa dake shimfide a ciki suna fidda qamshin sassanyan mayataccen turarensa yana jerawa cikin wata kyakkyawar madaidaiciyar luggage milk color da torches na Navy blue a jikinta. Daga yadda yake zaro kayan yana jerasu a ciki zakayi tsammanin yana yine saboda tsabar yanga da kuma salo irin nasa. A'ah,a yau din ba haka take ba,domin kuwa tun daren jiya ya tashi baya jin dadin jikinsa sam,wani irin kasala da mugun ciwon kai harda tsarabar guntun zazzabi su suka tayashi kwana. Zuwa wayewar garin yau kuma yaji babu abinda yake da buqata irin yaje gida,duk da cewa suna tsakiyar karatunsu da ya soma daukan zafi da gaske.

Wani matashinne kamar shi yayi knocking qofar sannan ya turo ya shigo dauke da jakar leda dake dauke da tambarin wani gidan abinci dake nan kusa da ecole din nasu. A bayansa wani matashinne da dukkansu shekarunsu zasu zo guda.

Kadan ya waiwaya yana amsa sallamar tasu sannan yaci gaba da qoqarin zuge zip din luggage din

"Ami(aboki)Me nake gani?,ya da hada kaya cikin bagage(luggage)?" Ya fada yana neman daya daga cikin sofa da suka qawata dakin da ita ya zauna akai idanunsu dukka su biyun suna kan maina din. Idanunsa yadan lumshe kadan yana jin kansa yana dan sarawa kadan duk da yadan samu sassauci

"Gid nikeson zuwa,amma gobe ma zan dawo ko lundi(monday)"

"Kace dai kawai raki zaka nuna da langwai,kanaso kaje ama tayi jinyarka" murmushin gefen baki kawai yayi,da mahadi da sultan din dukkansu gwanayen tsokana ne,ana cewa sai hali yazo daya ake abota,to amma su a kansu abun ba haka yake ba,akwai banbacin halaye da dabi'u masu yawa tsakaninsu. Kusan dukkan abokansu dake shigowa dakin mahadi da sultan ke kawosu,don ta maina kam shi daya ma zai iya qare zamanshi.

Yana jinsu sunayi masa tsiya ya wuce toilet dinsu dake manne cikin dakin,ya fiddo brushes dinsa da toothpaste da sauran kayan wankanshi ya dawo ya qarasa hada kayanshi. Order yayi na mota har cikin makarantar,ta iso bakin hostel dinsu sultan da mahadi sukayi masa rakiya har ya tashi.

Lamo yayi cikin motar,bai motsa ba har sai da kira ya shigo wayarsa. Da ya duba da kyau sai yaga meena ce,yaja siririn tsaki yana maida wayar silent ya jefata cikin jakar hannunshi da ya zuba qananun tarkacensa. Yadanbi jakar da kallo,shi da yace gobe ko jibi zaya dawo,besan me ya sanyashi debo kaya haka ba.

"Alhamdulillah" ya fada a nutse sanda ya sauka tsakiyar farfajiyar gidan yana duba yadda sassan gidan yayi shuru. Sake duba wrist watch din hannunsa yayi wanda ke dauke da sunan kowacce rana yanason ya gani ko yayi kuskuren tunanin yau din weekend ce saidai kuma koda ya kalla dai dai lissafinsa ya bashi. Bai tsawaita tunaninsa ya janye luggage dinsa kansa tsaye ya wuce sashensa,don duk cikin mutanen gidan yasan ba wanda yasan da zuwansa.

Ko yaya yaje makaranta ya dawo bai iya zama a daki haka,mafi yawan lokutta ma ama na sanyawa a gyara masa ne tun kafin ya iso din saboda saninsa da tayi da shegen tsantsami da tsaftar tsiya. Yau ba wanda yasan da zuwansa bare yayi masa wannan tanadin,don haka ya zage ya gyara dakin nashi yadda yakeso sannan ya shiga wanka.

Yaji qwarin jikinsa sosai,kamar ciwon dama yana jira ya baro makarantar ne. Wannan ya bashi damar shiryawa cikin trouser silk shirt me gajeran hannu. Ainihin cikar zati da surarsa suka fito muraran,kyakkyawan ba'abzinen matashi aliyyu haidar mayak'i.

Da salon nutsuwar nan tashi ya wuce zuwa sassan bibi. Duk yadda sukayi fada ko suka samu sabani,duk yadda sukaso share juna ita dashi amma hakan bai yiwuwa,shi yasa sam ba'a shiga fadan bibi da haidar maina,idanma ka shiga din kaine da jin kunya. Sai daya dan kalli sassan amansa kadan kafin ya shige,ya san muddin taji ya shigo gidan ba ita ya fara nema ba saita nuna masa fushinta koda da kalaman baki ne,sai ya qudirta a ransa bazai jima wajen bibi din ba,zai fito yaci abinci a wajen ama din nasa. Dab da zai shiga saqo ya shigo wayarsa,sai ya rage sassarfar da yakeyi yana dubawa.

Tailor dinsa ne yake gaya masa ya kammala dinkunansa duka,zaiyi tafiya zuwa diffa,idan baya gari ya aiko daga gida a karba masa,kada ya buqacesu shi kuma baya nan. Saqon ya rufe yana rayawa a ransa zai fita idan ya gama cin abinci ya karba,ko miqe qafarsa ya danyi qila ya sake jin qwarin jikinsa.

Baki bibi ta sake da ganinsa,abinda basuyi tsammani ba tunda duka duka wancan satin ya tafi,kuma a yanzun yakanyi sati uku ma baizo gidan ba

"Hala kewar matarka ta isheka kazo ganina ko?" Bibi ta fada tana dariya. Fuska yadan yamutsa kadan yana dubanta sannan ya nuna qirjinsa da yatsanta

"Ni maina?,Allah ya kiyaye,na barwa su saddi" wasa ne da ba kasafai suke yinsa ba ita dashi,amma duk sanda kaga ta jashi da wasan to tabbas tana cikin nishadi ne da jin dadin ganinsa.

Suna gama gaisawar bai jima ba ya miqe

"Bari na qarasa ciki"

"To,saika fito".

Kyakkyawan falon da ko yaushe yake cikin tsafta da kyau,komai nashi bata taba bari ya tsufa ko kyansa ya disashe. Ba kowa cikinsa sai masu aiki guda biyu dake yayyafin turare suna gohe marbles din dake shimfide a qasan falon. Wannan din kusan al'adarta ce,kowacce rana sai anyima qasan falon irin wannan gugar sau biyu zuwa uku,wannan ya sanya qamshi sosai ya kama wajen.

Sun shaida masa tana samanta,sai yace su barta,ya sanya suka shirya masa abinci ya soma ci,sannan ya fidda wayarsa ya fara kiranta.
[4/18, 10:43 PM] C.E.O HUGUMA CLOSET: *_GUDUN ƘADDARA_*

*H U G U M A*

PAGE 20


Ba jimawa ta sauko tana fadin

"Wanne irin shashanci ne haka maina?,zaka taho ba zaka sanar ba?" Dan qaramin murmushi ya saki,har yanxu ama tana kallonsa ne kamar wani saddi

"Banajin dadi ne ama,hakanan naji inason zuwa na ganku". Fuskarta tadan nuna damuwa,taja kujerar dake fuskarsa ta zauna idanunta a kansa cikin kulawa tana tambayarsa meke damunsa?.

"Zazzabi ne sai dan ciwon kai bame yawa ba"

"Subhanallah,Allah ya sawwaqe,to ya jikin yanzu?"

"Alhamdulillah,da sauqi sosai"

"Ma sha Allah" ta fadi dai dai sanda wayarta ta dauki tsuwwa. Fuskar wayar ta kalla sannan a hankali ta furta

"Mariya?" Sai ta daga kiran ta saka a kunnenta.

Sallama ta farayi sannan sauran maganganu suka biyo baya,tun tana maganar a hankali har alamun fushi suka dan fara bayyana saman fuskarta,kuma alamu sun nuna ranta ne ya far baci. Dukka maina yana ankare da ita yana diban abincin kadan kadan yana ci yana nazarinta

"Shikenan na gode,Allah ya qara zumunci" ta qarashe fada tana katse kiran.

Iska ta furzar daga bakinta tana hade yatsunta waje guda

"Lafiya ama?" Ya tambayeta yana ture kwanon abincin daga gabansa

"Wato shi zumuncin yanzu haka ya koma?,Allah ya sani ina bakin qoqarina gurin ganin na gina zumunci me qarfi tsakanina da 'yan uwana amma kowa sai ya watsamin qasa a ido saboda Allah ya jarabceni da son 'ya'ya mata kuma bai bani ba....."

"Wani abu ya sake faruwa kenan?" Ya kuma fadi ransa yana sosuwa saboda yadda fuskar ama din ta

Please Login or Register in order to submit comment