Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

sa ba, blue eyes balls ɗinsa ya ɗaga ya kalli mahaifinsa nace cikin ƙasa da murya yace "but how can that happen?" Lumshe idanunsa Besty yay kamar yadda yaga ɗan nasa yay domin kusan habit ɗinsu ɗaya yace "is simple question ai,a ranar da naga kana ƙoƙarin mace min akan soyayyar ƴar ƙwailarka a ranar na sanya aka taramin mutane a acikin Masjid ɗin Masarauta,nasa Chiroma ya zama waliyyinka ni kuma na zama waliyyin Maimunatou my daughter in-law,a ranar kuma sarkin Adamawa yazu so shi ne da kansa ya bada sadakin Maimunatou,ni kaina kuɗin yaban tsoro 5.7m fa? Amma dake ya tara kuma an tara masa sai ban damu ba,kawai na tayashi addu'ar samun cikar muradin zuciyarsa" rungome Besty Deen yay yana faɗin "Wow Best thank you so much, wlh zuciyarta na gab da bugawa" dry Besty yay yace "akan ƙwailar taka?" Baki ya turo kamar ƙaramin yaro tare da kwaɓe fuska yace "Noo!! Ta girma fa look" ya faɗa yana zaro wayarsa ya shiga nuna wa Besty photonan Moon wanda yay mata a School bata sani ba,shi dai Besty ƙuri yaywa fuskar Moon abune da yawa a ransa,sai kawai ya share domin bai son tunanin yay tasiri a ransa, Nene dai sai Murmushin jin daɗi take sbd farin ciki data hango saman fuskar ɗan nata, miƙewa Deen yay ya ƙarasa wajanta yana zuwa ya rungome ta,kansa ta shafa zare jikinsa yay yace "lemme freshen up" murmushi su kai masa yana ƙoƙarin shiga flat ɗinsa da aka rubuta *OSOHINOYI FLAT* (Yarima flat) yaji an zabga salati ana tafe hannaye idanunsa da suke kamar na mage ya shiga juyawa, Yayinda ce tsaye tana sharce majina tana faɗin "Amma ko sallamme kudai wlh baku iya haihuwa ba,ga yadda ya mayar dani gangalliya bayan nice na bada shawarar ai masa auran sbd zuƙewar da naga ya nayi,a tohh zuƙewa mana yaro jaraba nata cinsa a rai amma babu wanda ya gano sai ni sbd baiwar da Ubangiji yay min,banda baiwa ta Ubangiji tayaya zan iya ganowa Danoo aure yake so fisabilillahi? To dai babu ruwana Wlh,duk wanda ya raina uwar wani tasa ya raina,domin uwa ba tafi Uwa ba" tsaye sukai suna kallonta Deen kam haɗe fuska yay bai taɓa jin kunyar iyayensa ba amma yau tasa yaji, juyawa yay ya nufi cikin tamfatsetsan flat ɗinsa, kuka ta saka masu tana ƙara sharce majina tace "kuna dai kallo ko?? Ɗan rungomar da yay maku yake baƙin cikin yay min,to wlh ta Allah ba ta ka ba wannan shegen jikin naka ma me za'ai dashi?kuma shawarar dana bayar kaje ban yafe ba" shi dai ko takan Yayinda bai biba ya shige flat ɗinsa yana taune leɓansa,Nene ce ta kalli Yayinda tace "Ayyaa! Momma ki san halin jikan naki muma baya raga mana bare ke da kike kaka wajansa" cikin kumfar baki Yayinda tace "Yau nake ganin ɓatan nono a ƙirjin budurwa,to ko a suwa? Me akai akayi ko?nace wacce shararce ko? Basai ya gimamani bai girmamaku banda lalacewa ta yaran zamani har Aliyou ne zai mance hallarcin da nayi masa,yay kashi na wanke ya tunbuɗi na wanke,haka zan ɗaga shi sama ina masa rawa ina _caka masinka ɗan Baba,nace caka masa kinka,_ amma yau Danooo ni yakewa baƙin cikin rumgoma dake ya haɗu da sallamammun iyaye suka zoba masa ido,toni ba gantalalliya bace wlh gidan zan bar maku" daga Besty har Nene kasa magana sukai domin sun fahimci yau rikicin tsofanne ya mutsa,dole Nene taja baki tai shiru tana kallon Yayinda ta nufi flat ɗinta tana share majina,Deen na shiga falt ɗinsa shower ya sakarwa kansa,yana jin zuciyarsa tayi masa wasai ciwon daya keji yanzu babu shi,kwanciya yay saman babban royal bed ɗin sa, babu komai jikinsa sai boxer haka yaja pillow ya rungome cikin ƙaramin lokaci bacci yay gaba dashi wanda rabinsa mafarkin Lollynsa ne. Washegari a makaranta ya kasance Monday tun asuba da Moon ta farka bata koma ba,sai ta zama very weak ta zama wata miskila ko magana sai Feenerh tayi da gaske take baya feedback,a haka suka shiga masjid bayan sun fito suka komai Hotel, ruwa ta ƙara sakarwa jikinta kana ta fito a nutse ta fara shirya sai da ta gama sanya uniform waro manyan idanunta waje tayi sbd hijab ɗin da Dad ɗinta yace ta dinga sauya ya zarce tunaninta domin har gwuiwarta ya sakko, dry Feenerh tayi tace "a'a kaga matar malam Mamman,wannan ai da ake bawa Amira domin zaki fi dacewa da ita" harara Moon ta watsa mata idanunta ya cicciko da ƙwalla harga Allah bata son saka hijab ɗin,kaf school ɗin ita kaɗai ce mai babban hijab wasu ma haka suke tafiya babu ko hijab ita kuma sai ta ɓuge da saka wannan kamar wata Malama?yanzu gashi ya riga ya tafi bare tace ya sauya mata wani,ita akan wanne dalilin ba zai ɗauke mata nata ya bata irin na mu'allima,tana cika tana batsewa ta ɗauki school bag ɗinta ta shige class tunda yanzu ba class ɗinsu ɗaya ba,tana zuwa cikin class ɗin data prioud ɗin farko Faizak ne ga mamakin ta kowa ta samesa a class ɗin, agogon hannunta ta duba taga 8 saura 10 minutes at, kanta ta sunkuyar ƙasa ta shiga wasa da yatsun hannunta tama rasa me zata ce masa,a jikinta taji kallonta yake tana ɗaga idanunta suka haɗa idanu,gira ya ɗaga mata ita kuma ta turo baki gaba kafin cikin siririyar muryarta tace "Morning sir" idanunsa na yawo a kanta yace "mrng late comer, sleeping baby" ba ƙara magana ba ta shige cikin class ɗin wajan kujerar ta ta zauna,kan ta a ƙasa domin dictation yake masu cikin sauri take Rubutun ta cikin good handwriting ɗinta, after 10 suka fita breakfast ita da Feenerh da Amira suka jera a tare suka nufi danning hall, abinda kowa yake so aka kawo masu Moon aka bata arish da tea da kuma dankali da ƙwai,tana jin shirar dasu Amira suke akan abinda su Yasmin su kaiwa wata new student yarinyar hatta faɗa tarkonsu, Murmushin jin daɗi Amira tayi tace "ai Moon ki gode Allah,duk sanda suka so yin abinsu a kanki sai Ubangiji ya kare ki daga sharrin su" Feenerh tace "haka fa,ai shiyasa addu'a tayi a rayuwa kuma Garkuwa ce ga dukkan Musulmi" jinjina kai Amira tayi tace "MANZON ALLAH yace idan muna jin tsoran zaluncin wani mai iko mu ce".
*بسم الله الرحمن الرحيم، الله‍�? رب السموات ورب العرش العظيم،كن لي جارا من (فلان) وآحزابه من خلانقك،ان يفرط على أحد منه‍�? أو يطغى،عز جارك،وجل تناوك،ولا إله إلا أنت.*
_(Ya ALLAH! Ubangijin sammai bakwai,da kuma Ubangijin Al'arshi mai girma,ka kasance mai tsari gare ni daga wane ɗan wane,da dukkan rundunarsa daga cikin halittunka kar wani daga cikinsu ya yi gaggawar azaba a gare ni,ko ya ƙetare haddi,kariyar ka ta buyawa,kuma yabonka ya girma,kuma babu abin bauta wa da gaskiya sai kai)_
Shiru sukai gaba ɗayansu ita Moon sai juya tea take ta gagara shan bare taci sauran abun,Amira tace "To! Kowa dukkan wanda ya zamar da addu'a abokiyar faɗan sa a baki tayaya kike ganin zai tuzarta? Ba kuji ance addu'a makarin mumini ba?" Feenerh tace "gsky kam,shiyasa zama da mai ilimi yake da daɗi wlh,ba kowa zai fahimci hakan ba sai wanda Allah! yasa ya gane" karɓar tea ɗin Moon tayi kana ta ajjiye gefe guda tace,kafin taja numfashi ta fesar cikin ƙasa da Murya Moon tace "haka kuma Manzon Allah! yace kayi addu'a yayin gamuwa da abokan gaba kamar haka;"

*بسم الله الرحمن الرحيم، الله‍�? انا نجعلك في نحوره‍م،ونعو�? بك من شروره‍�?*
_(Ya ALLAH! Mu muna sanya ka a gabansu,kuma muna neman tsarinka daga sharrace-sharracensu)_

"Ke hakan na nufin babu wata halitta data isa ta cutar dakai a yayinda kayi Wannan addu'ar,koda ta cutar dakai bawai wayonsu ya sanya hakan ta faru ba,haƙiƙa Ubangiji yay mana gata da yayomu a musulmai kuma masu riƙo da addininsu, Uwa ba kuma yadda da ƙaddara,koda su Yasmin sunyi min wani abu ni nasan cewa hakan wata sabuwar ƙaddara ce data bijiromin,kuma ance ƙaddara lokaci gareta wani lokacin sai dai ka bata labarin abinda ya shuɗe,dan kuma ka shiga cikin wata masifar hakan ba yana nufin wai ƙarshen rayuwarka ne yazo ba, a'a nan ma wani lessons Ubangiji yake nuna maka mai hankali ance shike gane ɗin gishin ƙwaɗo,to thank God! Ni Maimunatou idan har addu'a na zama gari ya to tabbas ta zama gari ya gareni domin babu abinda su Sumy suka isa suyi min" gaba ɗaya suka kalleta can kuma Amira tace "Amma wacce damuwar ke hanaki cik abincin?ina lura dake sam baki son cik abinci" murmushi kawai Moon tayi idanunta cike da hawaye tace "wata damuwa tana zama dole kayi ta,domin baka san lokacin da take faɗa maka ba,ji nake kamar zan yi rashi ina jin kamar Dad na bazai dawo gareni ba". Da mmki Feenerh tace "kmaryay?" Ka faɗa ta ɗaga masu ba tare kuma da tace masu wani abu ba,ganin time na tafiya yasa suka miƙe gaba ɗaya su kowa ya shige class ɗinsa,a last prioud ɗin su Ass-headgril ta kalli Moon tace "Teacher Faizak yana kira a office nasa" juyawa fararan idanunta Moon tayi kamar ba zata ce wani abu ba sai kuma tace "kuma at this time?" Girgiza kai tayi tace "no yace after class" ɗauke kai Moon tayi tare da gyara farin glass ɗinta,suna gama class ta nufi office ɗinsa ta rataya school bag ɗinta,a zaune ta samesa yana operating system ɗinsa shiru tayi masa shi kam duk abinda take yana kallonta ta cikin system ɗinsa,kamar daga sama taji muryarsa yana faɗin "you look like familiar Maimunatou!!" shiru tai masa tana kallon fuskarsa amma a zahiri tunaninta yana ga Dad ɗinta,can taji yace "Yeah! Kina kama da Mai martaba sosai,ban san me yasa ba,ko ni ɗaya nake ganin kamar ohhhu! Amma duk wanda yasan Mai martaba kuma ya ganki dole zai ga kamar" da ƙyar ta buɗe bakinta tace "Ohhh! ALLAH! sarki" miƙewa yay tare da nufar inda take a gabanta yaja ya tsaya, lumshe idanunsa yay yace "su waye samarin jiya??" Idanunta wanda yake ƙara jan hankalinsa ta juya masa kafin tace "samari kuma?"kai ya ɗaga mata yace "Uhm" shiru tai masa ganin hakan yasa yace "da farko kin tsaya da wani har ya riƙe ki,na biyu kuma wani ya ɗauke ya fita dake daga cikin makaranta" sarai ta gane mai yake nufi sai kawai tace "Ohhh! He's my father" taɓe bakinsa yay still looking in to her eyes yace "Tab, babu kama abin" da rashin fahimta ta kallesa tace "Kamarya?" Ka faɗa ya ɗaga mata yace "nothing" kafin yace "what about your family?" Kai tsaye tace "shi ne ko mai nawa ai, family, friends siblings anything" da sauri yace mata "Out" kamar jira take yana faɗin hakan ta fice,shi kuma saman sofa ya faɗa yana jin zuciyarsa nayi masa zafi,yabar baƙin ciki a can gida,tunda ya kalli Moon yaji soyayyyar ta kamashi amma ya fahimci abubuwa da yawa a tare da ita,me zai mata? Dole ne ya nemi mafita dole ya jawota jikinsa, Moon a coner su ta haɗu da Sumy da Yasmin sun sanya wata yarinya a tsakiya sai shafata suke, Sumy na ganin Moon ta saki yarinyar ta nufi inda Moon take tsaye, harɗe hannayenta tayi tana jiran zuwa Sumy,da farin ciki a fuskar Sumy ta ware mata hannayenta alamar ta isa gareta,wata uwar harara Moon ta watsawa Sumy dry Sumy tayi tace "Yasmin zoki riƙe min ita" da sauri Yasmin ta nufin wajan Moon kafin ta ƙarasa Moon ta saka wata gigitacciyyar ƙara da gudu ta nufi inda Yasmin take tana zuwa ta jata ta haɗa kanta da bango,wata gigitacciyyar ƙara Yasmin tayi sbd zafin daya ratsa ta,nan take kuma kanta ya fashe ganin hakan yasa Sumy tayi waje da gudu domin neman ɗauki,Moon na ihu Yasmin na ihu haka Moon ta danne Yasmin sai duka take.




Kuyi share ɗinsa please fisabilillahi
9/12/21, 5:42 PM - Buhainat😝: *MOON*
_✍�?47-48_


Mai makon tayi magana duk da tsawar da Deen ya sakar mata,sai kawai ta fashe da kuka iya kar ƙarfinta,baya yay a hankali ya kwanta tare da lumshe idanunsa ya shiga fesar da numfashi,shiru yay mata yana sauraren yadda take kuka bilhaƙƙi! sai da tayi mai isar ta dan kanta tayi shiru ta shiga sauke ajjiyar zuciya,kusan a tare suke fidda numfashi domin duk sanda zata sauke ajjiyar zuciya sai yaji shima a lokacin ya sauke tasa,shi yay shiru yana son yaji me zata ce masa,ita kuma tayi shiru sbd bata san mene za tace masa ba,jin shirun yay yawa yasa Deen yay clamly muryars very slow yace "What happened to you Lolly??"kuka ta ƙara sakar masa tana ta shiga mutsi da bakinta a ƙoƙarin ta na son faɗin wani abun,but she can't say anything to her Dad,gaba ɗaya taji ta gaji ta makaranta she need her Dad,runtsa idanunsa yay ya shiga fesar da numfashi da sauri da sauri,da sauri kuma ya zare wayar a cikin kunansa kamar mai neman wani abu haka ya shiga ƙarewa makeken photon Moon dake saman screen ɗin sa ido, cije lips ɗinsa yay kana ya kashe wayar gaba ɗaya ya jefar a saman makeken gadon, bai jira ya kalli lokacin ba ya Miƙe tare da ɗaukan key car ɗinsa ya nufi fita daga flat ɗinsa,wata baiwar sa mai suna Kaltu tayi saurin shan gabansa kanta a ƙasa tace "Ya shugabana ina dalilin wannan fitar taka??" Ko inda take bai kalla ba ya shige abinsa, Babu kowa a makeken parlour'n dake tsakiyar sides sai ƙarar A.c dake ta kaɗawa ita ɗaya,da sauri yake taka ƙafafuwansa a ƙasa kansa a ƙasa gashin kansa duk ya baje a lokacin idan ka gansa zaka ɗauka wani basamudan ne just like Yayinda's say, Yana ƙoƙarin fita yaji Muryar Eneye na faɗin "stop here" cak Deen ya tsaya a hankali kuma Besty ya ƙara so inda Deen ke tsaye yana zuwa yace "what are you trying to go?" Shiru Deen yay masa dan shi a yanzu bai jin akwai wanda zai iya hanasa zuwa inda yay niyya,yadda zuciyarsa ke a zalzalashi zuwa gareta ba ƙaramin illa zata masa idan akace za'a hanashi, kafaɗa Besty ya ɗaga yace "anyway idan kaga kamar place ɗin nan toka tabbatar ka zama King of Nufaz" jajayen idanunsa ya ɗaga zuwa ga fuskar Mahaifin na sa,yadda yake kallonsa yasa Besty miƙa masa hannu zai taɓa shi,da sauri yaja baya yana girgiza kansa, cikin ƙara ji yace "don't ever trying to touch me Abba" waro idanunsa sosai Besty yay sbd sunan Abba da yaji Deen ya ambata,hakan kuma shike nuni da zallar ɓacin ran da yake ciki, ƙara miƙa hannunsa yay zai taɓa shi da sauri Deen ya juya ya nufi flat ɗinsa kamar zai tashi sama,yadda yake fidda numfashi ma kaɗai ya isa mai hankali fahimtar ɓacin ran da Deen ke ciki,kai tsaye side ɗin game ɗinsa ya nufa,yana zuwa ya zare singlet ɗin jikinsa bai tsaya jiran komai ba ya shiga dukan jikin wani ƙaton ƙarfe da iya kar ƙarfin sa. Eki ce tare da Damus zaune suna tattaunawa akan dawowar Deen amma still babu wani impormation daya samu akan yaran da suke da target a kansu, Murmushi Eki tayi tace "wai kayi believe Deen yana aikin da kuka sashi?" Kallonta Damus yay ta ɗaga masa kanta tace "Yeah! Lemme tall you something,Deen ba aikin ku ne gabansa ba,tunda aka gaya masa anyi Missed yarinyar nan,kaga wani action da ya yi akai ne? To Moon she's with him" Damus da ya kejin abin kamar a mafarki yace "What the you mean by y Eki?" Gyara zama tayi sosai tace bari nai magana cikakken bayani sbd naga kanka babu Uban komai a ciki,daga shisha sai Win, Wannan yarinyar Moon tana wajan Deen,kasan tunda nayi rantsuwa a kansa cewa sai na mallakesa bazan taɓa kaffara ba, muna nan da kai at this week sai kaga Deen yazo,bazan taɓa rabuwa dashi sai na mallakesa,bazan taɓa rabuwa dashi ba sai na rabasa da wannan ƙwailar yarinyar"miƙewa Damus yay tsaye yace "sai yanzu na fahimci abubuwan da nake ta mmki a kansu,Mun saka private investigators,wanda zasu dinga kula da shigensa,to a shekaran jiya yake faɗa min Deen ya dawo gari,na yarda da maganar,kai tsaye na turawa Oga Taju maganar ta email address ɗinsa, nasan bazan taɓa samun magana dashi ko a waya ba ne,amma Oga Taju yace baya son shirme irin wannan,yar dar da yaywa Deen yasan har abada bazai taɓa iya cutar dashi ba,so daga nan ban ƙara magana ba,sbd nasan Oga Taju bazai fahimce ni ba,kaf cikin yaransa babu wanda yafi aminta dashi kamar Deen,tsabar soyayyyar da yake masa fa ya cire gefe guda na sunansa ya bawa Deen,kin san sunansa TAJUDDEEN shi ne ya bawa Deen ƙarshen sunansa, kafin ya yarda cewa Deen yau dararsa yake za'a daɗe,Amma idan har ya san gsky Deen da dukkan family ɗinsa zasu shiga uku tabbas"ya ƙare maganar yana zagaye tsakiyar parlour'n, taɓe baki Eki tayi tace "Wannan matsalarku ce,tawa na riga na shawo akan ta zuwansa kawai nake jira" tana faɗin hakan ta miƙe tsaye tare da nufar ɓangaren en matan gidan,Zau ne ta samesu kowa da abinda yake Salmerh na kusa da Nana wacce take kwance ta lumshe idanunta, Sai kuma Salymat dake zaune tana kallo sai tauna cimgum take,kallon Salymat tayi tace "Saly 2minutes please" tsaki Salymat tayi tace "nifa ba zaki katse min kallo ba,yadda nake masifar son JOHD & AKBAR ɗin nan" kallon cenemar Eki tayi taga yadda Queen Johda da Queen Rakayah,da Queen Salma suke ta fidda makamai suna kaiwa Abu Maleek sara ta ko ina,gefe guda kuma Mahmanga ce da zabgegiyar takobin ta sai sara take kaiwa,gaba ɗaya Masarautar ta birkice,sai ihu Mutane suke an kashe King Akbar,tsaki Eki tayi ta ɗauke kanta tace "Ai ke naga babu tsuntsu babu tarko,lalacewar taki takai kisa Wannan mutanan gaba kina kalla?mai makon kisa romantic film wanda zai kai maki har ka,amma kuma wasting time ɗinki a kan wannan, Allah dai ya kyauta" ta faɗi hakan tana neman wajan zama can kuma tai ƙasa da Murya tace "Wai ya Maganar wajan bokan?anya ba zamu koma ba kowa??" Tsaki Salymat tayi tace "Kina da matsala wlh,da ɗina dake brain ɗinki kamar ta kifi haka take,gaba ɗaya yaushe mukaje? Samnan sati nawa ya bamu yace idan aikin baici ba mu koma?to gaba ɗaya kawo zuwanmu da yanzu ko 4days ba ai ba" lumshe idanunta Eki tayi tace "wlh ba zaki gane ba,a matse nake nafi son ya kawo kansa da wuri wlh" harara Salymat ta fella mata tace "kaji wawiyya,banda hauka gaggawa ai aikin sheɗanne,kawai ki jira soon zaki gansa kamar yadda bokan yace" miƙewa Salmerh tayi tana faɗin "ALLAH ya kyauta" da sauri Eki tace "munafuka ai wlh ko son Deen kike sai dai ki mutu domin na daɗe da fahimtar inda kika dusa"Ita dai Salmerh bata kulasu ta shige part ɗinta, Wayar Nana ce ta fara ihu a hankali ta ɗaga daga can ɓangaren Ovasi yace "Wai Inna ga ta" jin hakan yasa Nana miƙewa da sauri idanunta na kawo ruwa, bakinta na rawa ta shiga faɗin "Innata" da sauri Inna tace "Eh nita walle,Yaya kike?yanzu uban gidanki ya kawo mana kuɗin ai kinki na wannan shekarar,kin san duk shekara sai ya kawo,kedai kiyi masa biyayya babu ruwana wlh sai yay maki baki ya biki tunda matsayin Uba yake wajanki,to ko Ubanki yay maki haka ne??ai baki samu wannan gatan ba" kasa cewa komai Nana tayi sai hawaye dake bin saman kuncinta,can Inna tace "Ke babu ruwana fa,ko a can kika samu miji kiyi aurenki kawai,to uban me zaki mana idan kin dawo?aikin ƙafa ta ne tuni anyi min nayi rass dani" Ovasi ne ya miƙa hannunsa zai amshi wayar Inna tayi saurin cewa "Nidai idan kika ɓatawa Uban gidanki rai wlh bada yawo na ba" Ita dai Salmerh bata kulasu ta shige part ɗinta, Wayar Nana ce ta fara ihu a hankali ta ɗaga daga can ɓangaren Ovasi yace "Wai Inna ga ta" jin hakan yasa Nana miƙewa da sauri idanunta na kawo ruwa, bakinta na rawa ta shiga faɗin "Innata" da sauri Inna tace "Eh nita walle,Yaya kike?yanzu uban gidanki ya kawo mana kuɗin ai kinki na wannan shekarar,kin san duk shekara sai ya kawo,kedai kiyi masa biyayya babu ruwana wlh sai yay maki baki ya biki tunda matsayin Uba yake wajanki,to ko Ubanki yay maki haka ne??ai baki samu wannan gatan ba" kasa cewa komai Nana tayi sai hawaye dake bin saman kuncinta,can Inna tace "Ke babu ruwana fa,ko a can kika samu miji kiyi aurenki kawai,to uban me zaki mana idan kin dawo?aikin ƙafa ta ne tuni anyi min nayi rass dani" Ovasi ne ya miƙa hannunsa zai amshi wayar Inna tayi saurin cewa "Nidai idan kika ɓatawa Uban gidanki rai wlh bada yawo na ba" tana faɗin haka Ovasi ya karɓi wayar tare da kashewa yace "Am going Inna" ita dai bata san me yace ba hakan yasa tace "Au har goyo teke Ita Khadii ɗin?"kallonta kawai yay ba tare da yay magana ba ya fice daga cikin ɗan ƙaramin gidan, Durƙoshe wa Nana tayi a wajan tare da rushewa da kuka,bata jin tsanar abinda yake domin komai tayi a yanzu dai-dai ne,haka kuma babu abinda su Damus zasu sata taƙi yi masu, amma me yasa take jin ƙunci da kuma baƙin cikin a cikin ranta? Tana nan zaune har kiran Ammar ya shigo cikin wayarta kasa ɗauka tayi sbd ciwon da kanta yake mata.A can Masarautar Nufaz kam fada cike take da mutane masu yawan gske,manyan mutane na cikin gari Kogi dake wayanta, Tiraki, Chiroma,Sarkin fada,Sarkin aska,Sarkin yaƙi,Waziri,Sarkin ƙofa,Galadima,Hikimai,Dagatai,Masu unguwanni, sa sauransu,sai kuma Bafadawa gefe guda kuma Ex king of Nufaz ne zaune cikin wata iriyar shiga dasu ta IBIRA,Saman wata rantsatsiyyar Kujera wacce aka ƙawata ta da adon ɗanyar azurfa sai walƙiya take tare da sheƙi, ALIYOU ENEYE AHUOYZA shi ne zaune saman kujerar ransa a haɗe,duk yadda ya haɗe ransa amma hakan bai sanya wani sihirtaccen kyau fita daga saman fuskarsa ba, sanye yake cikin wata dakakkiyar shadda Orange an sanya masa wata Alƙyabba milk sai ratsin Orange a jikin alƙyabbar,ga wani takalmi Kubta mai gashi-gashi wanda ya kasance half covert shoe a ƙafarsa,Gefe guda kuma Sarkin fada ne yake naɗa masa rawani mai bala'in kyau wanda ya kasance mai dai-dai ci,bayan an kammala aka miƙa masa Sandar girma,can kuma aka ɗauko wata zabgegiyar takobi a cikin gidanta, Lokaci da za'a bashi Takobin sai da kowa na fadar ya miƙe tsaye har da Eneye Ahuoyza,cikin girmamawa aka bashi Takobin kansa a ƙasa yasa hannu ya karɓa yana karɓa ya shigar zagaye kansa da ita,sai kuma ya durƙosa har ƙasa tare da miƙa Takobin gaban goshinsa sai kuma ya dawo da ita wajan bakinta ya sumbata,a hankali ya miƙe tsaye tare da komawa wajan kujerar ya zauna, ɗaya bayan ɗaya
Mutane suka dinga zuwa gabansa suna zubewa tare da kai masa gaisuwar ban girma, lumshe idanunsa yay sbd nauyin da yaji yana masa,ashe haka sarauta take? Haka take sawa Mutum yaji wata izza da girman kai na musamman,sai yaji bakinsa ya ƙara yi nasa nauyi fiye da ko yaushe, ɗan gyaran murya yay kaɗan tare Mutsa sandar hannunsa, Sarkin fada ne yace "Ma sha Allah kamar yadda kowa ya sani yanzu King Aliyou Eneye Ahuoyza shine sarki,kuma nan da wata uku cif za'ai bikin rantsar da shi kamar yadda akewa ko wanne sarki,muna gdy ga dukkan wanda yazo wannan taron sai kuma ALLAH ya nuna mana ranar da Za'ai bikin rantsar dashi tare bashi sandar girma na gold" daga nan zaman fada ya watse, Deen na ganin mutane sun ragu a fadar ya miƙe da sauri kamar zai tashi sama,da sauri shima Eneye ya miƙe yabi bayan Deen, kai tsaye flat ɗinsa ya shige ya shiga fatali da alƙyabbar jikinsa ya shaddar kawai ya bari,bai tsaya ɗaukan komai ba sai A.t.m ɗinsa da abubuwa masu amfani a garesa, kayansa yasa a trolly sannan ya fito Wata Jakadiya sai kirari take masa,a haka ya nufi babban parlour,a tsaye ya samu Nene da Eneye murmushi Besty yay yace "kana tunanin zan habaka hanaka zuwa wajan matar ka ne?tun ka amshi buƙatata zaka iya zuwa duk inda kakeso but make sure ka dawo before 3mouths"

Please Login or Register in order to submit comment