Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

bata da niyya magana, kuma da alamun yar masu kudi ce, ita kuma batason harka dasu dan bata daukan raini, balle ayadda suke marasa hannu da shuni.
"Lafiya kika tsayamin akan" Goggo ta fada cikin kakkausar murya.
Tuni Batul tasha jinin jikinta, tace "Fatima ce, Budurwar Nafiu"
Ware idanu Goggo tayi tana kallonta, fatima da take expecting iri iren suce ba wannan ba, Sallamar Nafiu ce ta katse mata hanzari.
Karasa shigowa yayi, fuskar sa dauke da fara'ar yana fadin "Fatima kin iso ashe, na fita siyo kankana ne"
Gaidasa tayi aladabce, tabarma yayi saurin shimfuda mata yace da ita ta zaune, zama tayi cikin dardar ganin har yanxu Goggo bata saki fuska ba, saima dauke kai da tayi tana cigaba da dakan ta.
"Goggo ga Fatima fah ?
"Naganta" ta fadi atakaice
Baiji dadi da yadda ta ansa ba, tanason fatima yanxu data ganta kuma ta sauya yanayi.
Hira yahau jan Batul dashi, amsa shi kawai take, jikinta asanyaye, tunanin yadda zatai aure agidan take ganin yadda Goggo ta daure mata fuska.
kankanar Naja'atu ta wanko ta dire wa Batul, godiya tayi sosai, Naja ta mike zuwa aikinta suka cigaba da hirar su.




Gidan Inna Rasheed ya nufa, sun jima suna hira daga bisani ta shiga daki ta fiddo wata takarda
Zama tayi tana fadin "tun ranar data bani takardar na karanta abunda ke cikinta ya sanyani matukar mamaki da abunda take fadimin"
Dariya Rasheed yayi yace "ranar bata cikin hayyacinta, kallo daya tama abunda ke rubuce ta dauke kai, banyi tsammanin ta karanta ba"
Warware takarda Inna tayi tana karanto abunda ke rubuce kamar haka "Ni Mamuda na bawa Matata wata d'aya ta koma gidan ta zauna har tayi hankali" dariya sosai Inna tayi tana karantawa, tace "tsabar kidima yasa wata dayan data gani yasa tayi tsammanin Saki daya kayi mata"
Yace "ban sake taba, saidai ayadda tayi tunanin na mata sakin naji dadin hakan, sosai hakan ya temakamin cikin plans dina"
Nisawa Inna tayi "yanxu ya zaka fadi mata akwai auranta akanka kuma kai ba yayanta bane"
Ajiyar zuciya ya sauke yace "datx d problem, bazata ji dadi ba idan tasan ba Baba ne mahaifinta ba, shiyasa nake lallaba ta as my sister har Baba ya dawo ya sanar da ita da bakinsa"
"Ka kawo shawara mai kyau, saidai Mamanka fa, anya zata barta kuwa, kasan dai idan akwai abunda ta tsana bai wuce babanka da zuri'a saba"
Nisawa yayi yace "ayanxu dai bata san cewa nasan komai ba, dole na bitta ayadda ta dauke ni, dadin abun am one step ahead of her".
Jinjina kai Inna tayi tace "Mamanka tayi nisa Allah ya shirye ta"
"Amin" yafadi, mikamai takardar Inna tayi ta nufi gindin murhu tana iza huta.

Murmushi Rasheed yayi hade da shingidewa kan tabarmar dayake zaune, jinjina kai yayi yana mamaki halin Mom dinsa dana Batul two different womem from different world amma halin su daya, at first strategy din Batul yayi using har ya gyara mata zama ta shiryu, ga Mom dinsa data zauna tana fadi mai karya da gaskia, very cunning, haka take shiyasa shima yayi using style dinta ba tare data sani ba, baya Manta ranar data dawo daga Abuja, da dare ya sauko palon kasa sha coffee, yaji maganganu na fitowa daga dakinta, adan tsoroce ya karasa bakin kofar dakin da kusan rabinta bude yake, lekawa yayi yaganta tanai kai komo adakin tanai surutai kaman tab'ab'iya, kasa kunne yayi saidai bai dago inda xancenta ya dosa ba, kalamai kalilan yaji tana fadin "dole yarinyar tabar gidan nan tun kafin My boy yagano cousin dinsa ce" karaf yaji ta rufo kofar dakin da karfin gaske, barin gurin yayi batare daya dago inda xancen ta ya daso ba, washegari dayaga she was desperate ta kori Batul agidan ya sashi sensing akwai wata boyayye, begama gagasta xancenta ba saida yaga ta k'ala mata sata duk dan tabar gidan, baiyi niyyan duka Batul ba amma saboda Mom kawai ya dageta sanna ya bata chance din barin gidan.
Ranar daya bata takardar nan duk part of his plan ne dan ta koma Gidan Inna da zama just to protect her from Mom, unfortunately she was confused tayi tunanin ko sakinta yayi.
He wasn't stupid dazai barta ta kwana awannan gidan datx y turo Inna kwasan wasu takarce yasan definitely bazata zauna ba bin Inna zatayi.
Bayan ya koma gida ya fadi ma Mom Batul matarsa ce, yadda tayi overreacting yasa shi zuwa gurin Abban Mardiyya hade da rokonsa ya auri Mom dinsa akan ta rasa mashishini, dakyar ya amince mai, ranar daya zo kuwa yaji abunda ya dade yana son sanin daga bakinta.
Saidai inda tace Batul kanwarsace ya gigita shi, bai zame ko ina ba sai gurin Baba Lamido dayake ganinsa tare da Baba, gurinsa yaji labarin Batul ba yar cikinsa bace.
Tun ranar daya fadi ma Mom princess is missing ya lura akwai motar dake binsa duk inda ya nufa, shiyasa ya tsiro da aikin nemanta akullum tamkar baisan inda take ba, abunda bai saniba shine yadda Mom tagano Batul na Zaria saidai baiyi mamaki ba yasan hali mom, idan tasawa abu ido sai taga bayansa.

Abincin da Inna ta ajiyemai agaban sa ne ya dawo dashi daga tunanin daya lula,
"Inna harkin gama kenan".
Dariya tayi tace kusan awa daya fa baka hayyacinka.
Ware ido yayi, yace "nabar matata damai shayin"
Dariya Inna tayi, yahau cin abincin, sharp sharp yagama yay mata sallama hade da barin gidan.


Wajen gidan Batul da Naf'iu suka fito jiran dawowar sa, hira suke Nafiu na bata hakurin yanayin Goggo, "akwai ta da wadatar zuci, shiyasa akullum bata tunani kai kanta inda Allah bai kaita ba, laifina take ganin akan ban samo daidai dani ba"
Kwantar da Murya Batul tayi tace "karka damu Nafiu, ka kwantarwa Goggo Hankali, nida kai duk daya muke, saidai wata alfarma nakeso kamin"
Kallon nutsuwa yabita dashi
Tace "Nafiu aure nakeso muyi nan da kwana hudu".
Gabansane yafadi, yasan dawuya Goggo da Baffan sa su yadda yayi aure in four dayx.
Tacigaba "Nafiu ka temakeni ka aureni, karka damu da shirin komai, adai dauran auran kawai"
Sosai yaji ba dadi, saidai bazai iya kin auranta ba dan yana sonta sosai, balle ga dama yasamu bazai so ta kufce mai ba.
Nisawa yayi "insha Allah Fatima karki damu, na amince xan aureki"
Dadi taji sosai aranta dukda wata gab'a a zuciyar ta nai mata radadi, "nagode sosai Nafiu, Goggo kuma nasan zata soni"
Farin ciki shima yake, hira kadan suka taba Rasheed ya iso daukan ta, ganin yadda take washewa Nafiu baki yasa shi daure fuska, gaidashi Nafiu yayi bai amsaba yaja motar afusace.

Murnan dayafi bakin ciki ciwo take a motar, dadin ta daya Mom bazata kashe mata iyayenta ba, kallon Rasheed tayi daya daure fuska.
"Yaya prince ka tayani murna, yau ina cikin farin cikin"
Bai tanka ba banda gudu dayake.
Cikin rashin damuwa da yanayun sa tace "nan da kwana Hudu zamuyi aure da Nafiu, kuma kaine zaka dauramin auran" .
Wani wawa burki yaja da saida kanta ya buge da glass din window.
Huci kadai yake batare daya kalle taba ya kuma tada motar.
Kallonsa tayi kaman zatayi kuka, ba lailai ne ya yadda ya daura mata aure ba, saidai bata da wani zabi daya wuce ta daure ta rokesa.
Shuru tayi bata kara magana ba har suka iso gida, fitowa yayi ba tare daya jirata ba, da sauri ta fito hade da riko hannusa, "plz yaya ka dauramin aure, nayi magana da Nafiu xai turo gobe ayi maganar"
Bai tanka taba har suka shigo palon tanai mai magiya.
Mikewa Mardiyya tayi daga kujerar da take zaune tanai masu sannu da zuwa, bai iya tankawa ba banda tsayawa dayayi tsakiyar palon cikin tsananin baccin rai.
Hannun Mardiyya Batul ta riko tana fadin "Sister inlaw plz ki tayani rokonsa ya amince ya dauramin aure in four dayx"
Ware ido Mardiyya tayi cike da mamaki, saidai zuciyanta na fadin ta rokesa koba laifi zata huta da yadda Batul ke mannewa mijinta.
Kallon Rasheed tayi tace
"Sweetie if dax her wish, y not kayi mata granting, tunda tace aure takeso it better ka aurar ta b4 its too late"
Yaken da yafi kuka ciwo yayi, kusan minti biyar yadauka yana nazari sannan ya dubi Batul yace "na amince".
Ihun murna sosai tayi ta fada jikinsa,
Ran Mardiyya ya sosu, sosai take jin kishin Batul aranta dukda ma kanwar sace, b'ata rai tayi zata wuce daki taji ya riko Hannuta
"Am so happy My prince" Batul ta fadi hade da janye jikinta, idanuwan tane suka sauka kan hannusa dake rike dana Mardiyya, sosai taji ba dadi saurin dauke fara'arta tayi hade da juyawa ta shige daki.
Kallon Mardiyya yayi yana murmushi, "bazaki kawo wa Sweetie ruwa yasha ba"
Saurin sakin fuskarta tayi, cox she cnt afford to lose murmushin dayake mata, "right away my sweetie" ta fadi hade da janye hannuta, kitchen ta nufa da azama yanai bi dakin da Batul ta shiga da kallo.




Am sorry Rasheed, this time around Mom is one step ahead of you.
[10:01PM, 5/26/2017] Xarah Bukar: 💖 *INA ZAN GANSHI*💖
Rubutawa
Xarah Bukar

®NWA

xarahbukar.wordpress.com


75


kufcewa da kuka Batul tayi had'e da fad'awa kan gado, tunani barkatai ke yawo a kwakwalwar kanta, so take ta fad'imai akwai aure tsakanin su amma bazata iya ba, dole tayi sacrificing love dinta for her parent safety...
Kusan mintinu talatin ta kwashe tana zubda hawaye, turo kofar dakin ne yasata azaman mikewa tsaye tamkar marar gaskia, hannuta takai bisa fuskarta tanai kokarin goge hawayan hade da kirkiro murmushin dole, karasa nufota yayi, fuskarsa dauke da fara'ar yace "Amarya da kanta take kuka"
Girgiza kai tayi tana ja da baya sakamakon matsowan dayayi daf da ita suna shakar numfashin juna.
Hannunsa yakai bisa hab'arta hade da tallafo fuskarta sunai duban juna.
"Miyasa kike son yin aure in four dayx"
Kawar dakai tayi tana fadin "ina son Nafiu, bazan iya rayuwa ba tare dashi.." Kasa karasa kalamanta tayi sakamako murde mata baki da yayi yana fadin
"Gayamin gaskia"
"Dagaske nake" ta fadi kaman zatayi kuka, hannu takai tana matsa bakinta daya murd'e.
Kallon idanuwanta yayi tuni ya gano ba hakan bane band tsoro da fargaba dake kwance jikinsu, karanceta yayi tsaf ya gano akwai abunda take boyewa mai. Baice mata uffan ba ya juyawa ya fice daga dakin
Dakinsa ya nufa yanai kai komo, azuci yake fadin it doesnt make sense tace tana son yin aure in just 4dayxx, tabbas akwai wata boyeyye akasa amma ya kasa figuring out, kodai Mom ke threatening dinta ? Sauri kawar da tambayan yayi, yana fadin it cnt be. Sosai kanshi yayi zafi dabarar kirar Nafiu yayi da tuni numbarsa na wayan, bugu daya Nafiu ya dauka, atunaninsa Batul ce yasashi washe baki, jin muryar yayanta yasa shi nutsuwa hade da saurara kalaman da yake fadi akan yayi hakuri ya rabu da Batul matar aurece ita kanta batasan dakwai aure kanta ba.
Jiki sanyaye Nafiu yahau basa hakuri akan bai taba sanin matan aure ceba kuma yayi akawarin bazai kara kiranta ba dan tuni Gogonsa ta taka mai birki tsakanin su.
Sosai RmD yaji dadi da fahimtar sa, katse wayan yayi hade da hamdala, saidai yasan Batul bazata fasa nemo wani ya aure taba ayyadda yaga she is desperate taga tayi aure cikin kwanaki hudu, kaman wasa ya gwada trying Numbar Baba, yaji tayi ringing, farin ciki marar mitsaltuwa ce ta mamaye mai zuciya, sau kusan hudu yana ruri baa dagawa, ana biyar ne Baba dake aikace aikace agona ya adaga hade da sallama.
Gaisuwa sosai sukayi, nan take cikin girmama Rasheed yahau mai bayanin abunda ke faruwa in Brief.
Cikin nuna rashin damuwa Baba yace karya damu gobe zaibar abunda yake su dawo kaduna, maganar tafi karfin waya, sun jima suna tattaunawa daga bisani sukayi sallama.
Ajiyar zuciya ya sauke cike da mamakin rashin damuwa da Baba yayi, atunaninsa xai nuna farin ciki bayyanar dansa sai yaga sabanin hakan tamkar dama yasan shi amatsayin dansa.

***

Zaune suke su ukun a parlour, kowa wanne su da abunda yake tsakawa aranshi ba tare da sunce uffan ga junan suba.
Mikewa Batul tayi daga ce nesa da take zaune dashi ta karaso inda yake hade da daukar wayarsa sa, baice da ita uffan ba ta koma mazauninta hade da dialing no din Nafiu, akashe ta jita kusan sai goma tana trying.
Guntun tsaki taja hade da dubansa da gabadaya hankalinsa na kan Tv.
"Yayana nambar Nafiu bata shiga, kuma munyi dashi zasu xo yau"
Bai kalleta ba yace "nasani ai, suna hanya"
Ware idanu tayi cike da murna tace "kunyi magana dashi ne"
Kallo daya yayi mata yadauke kai, aranshi yana fadin "she's really an actress".
Shurub da yayi bai tanka ba yasa ta tunanin ko dagaske suna hanya.
Murmushi Mardiyya tayi daga inda take zaune tana latsar wayarta, kallon Batul tayi tace "Sister inlaw yakamata muje shopping, afara shirye shiryen bukin".
Yatsine Fuska Batul tayi
"Sister Mardyy banason wani shiri, iya kaci ashafa fatiha ya mik'a ni, aurena na farko aka akamin balle kuma ma na biyu" karashe xancen tayi cikin zolaya.
Dariya ne yakusa kufce mai amma ya daje yace "Diyya ta kowa good idea, ki tashi sai kuje tare yin shopping din"
Fir Batul taki yadda, saida taga yayi mata jan ido sannan ta amince suka fita shopping din bayan ya baiwa Mardiyya credit card su siya abunda suke so, shopping din kayayyaki masu tsada sukayi da temakon Mardiyya, saidai ita ko zobe bata siyawa kanta ba haka suka dawo gida.


****
Matashin saurayi da Mom ta tura unguwar su Baba sa idon dawowar sune tsaye a farfajiyan gidanta yanai jiran fitowan, cikin takun isa ta nufosa, yan dubu dubu rike a hannuta.
Gaidata yayi bata amsa ba tace "ya ake ciki ?
"Sun iso jiya da daddare" ya fadi hade da risinawa.
"Ka tabbata".
Yace eh.
Kudin hannunta ta mike mai ya amsa hade da godiya, ya juya ya fishi.
Ciza labba tayi tanai neman mafita, batayi expecting dawowar suba tun kafin Batul tayi aure, kwafa tayi tana tunanin abunyi, dole nate gidan naci masu mutunci kafin My boy su rigata zuwa, muddin ya iske Baba akwai amatsala.
Kwalla Altine kira tayi hade da fadin ta dauko mata mayafi da mukullin motar ta. Da azama altine ta dauko ta fito ta bata, saurin fadawa Mota Mom tayi taja tabar gidan..

Tun jiya da Batul taji shuru, babu alamun zuwan Nafiu da yan'uwa sa ya sanya ta tashin hankali, nambarsa da take trying abu daya yake fadi mata, switch off, iya kidima takai gabadaya ta rasa mafita kwana biyu kadai yarage a sharadun Mom, cikin sauri tagama shirinta cikin atampa zasu fita da Rmd, saidai batasan inda zasu ba fatan ta daya Allah yasa zaria zasu, cikin sauri ta fito palo, tuni yana waje cikin mota, sallama tama Mardiyya ta fito da azama ta shiga motar hade da sauke ajiyan zuciya.
"Miye haka" ya fadi yanai hararanta cikin sigar wasa.
Nisawa tayi tace "ba komai, muje plz, kar dare yayi"
Dariya yayi aranshi sai kace tasan inda zasu nufa.
Hanyar gidansu taga ya nufa, gabantane ya fadi, bata gama tsorata ba taga sun shigo unguwar..
Cike da kidema tace "ina zumuje, su Baba sun dawo ne ? Duk tare ta jeho mai maganar.
Cikin rashin damuwa da yanayin ta yace "tunda kinki fadimin dalilin sonyi aure ai dolen ki fadawa Baba..
Hannusa dake kan steering ta riko tana fadin "prince dan Allah karka kaini gurin Baba, kayi hakuri bayan nayi auran sai naje" karashe maganar tayi kaman zatayi kuka.
Murmushi yayi bai tanka taba, magiya da rokonsa tahau yi, bai kula taba har yayi parking gaban gida.
Bude bangaransa yayi ya fito hade da zagayawa gurinta ya bude motar.
"Fito'
Kin motsawa tayi banda bakin ta dake rokansa, janyota yayi ta fito ya rufe motar sannan yaja hannuta suka shiga cikin gidan.
Cikin kamala da farin ciki baba da Hajjo suka tarbesu, tattauwa sosai sukayi game da abunda ke faruwa, dakyar Batul ta fadi ma Baba yadda sukayi da Mom, sosai ran Baba ya baci, nan ya fayyace masu lailai ba siblings suke ba saida be fadi masu dalilin rabuwar sa da Mom ba dukda Rasheed yaso ace ya fadi, kukan dadi da bakin jiki Batul take, sosai tayi dana sanin rashin daa da take nunawa Iyayan musamma ma dataji baba ba mahaifinta bane, hakuri sosai da gafara ta rokesu.
Su hassan ma baa barsu abaya ba sunji ddin kasancewa da yayansu da yayarsu, yunin ranar agidan suka wuni, duk aikin gidan kin bari tayi Hajjo tayi da kanta ta kammale komai.
Zuwa yamma suka fara shirin komawa gida, karar dirar mota a gaban gidan yasa hankalinsu ya koma bakin kofar, garaf suka ji an rufe motar, karaso shigowa tayi cikin gidan cike da kyankyamin da kallon gidan a wulakance, ganin Family reunion dake faruwa tsakar gidan yasa ta jan dogon tsaki, kallon banxa tahau yiwa ko wannasu sannan tahau su zagi
Rikota Rasheed yayi yanai rokonta ta dena, fir taki denawa saima ashariya data dinga lailayo Baba da Hajji, basu iya tanka taba banda ido da suka xuba mata, inda sabo sun saba da halinta tun shekaran baya da suka shude.
Tuni jikin Batul yadau rawa tsabar tsoro, nunota Mom tayi da yatsa tana fadin "ke kuma matsiyaciyyy..."
Wanke ta da Mari Baba yayi kafin takai ga karashe kalamanta.
Cikin tsananin bacin rai Baba yace "rashin mutuncin ki ya tsaya akanmu karki kuskura ki koma kan ya'yana"
Dafe Kuncinta tayi cike da mamakin marin dayay mata, a iya zaman da tayi dashi da irin cin mutunci da take mai be taba mayar mata da martani ba saiyau, yau din ma akan Angolan yarsa.
"Muje na rakaki Mota" Rasheed ya fadi hade da janyo ta suka fito waje, kasa magana tayi banda hannuta dake dafe kan kuncin ta.
Shiga motar tayi yace "mom ki bawa Baba hakuri ku dawo normal, har yanxu fah akwai auran sa akanki"
Bata iya cewa uffan ba taja Motar afusace tabar gurin ciken da tsananin baccin rai da bata taba fuskanta arayuwar taba.
Dafe kai yayi aranshi yanai mata fatan shiriya, Gidan ya koma yabai wa Baba hakuri sannan sukayi sallama, dakyar dai Batul ta bisa, ba karamin tsorata tayi ba da yanayin Mom ba.

Tuki yake jifa jifa yakan kalli yadda take takure, yasan hakan baida nasaba da Mom dinsa.
Murmushi yayi yace.
"Princess weds mai shayi"
Dariya da batai niyya yiba ne ya kufce mata
Tace "Nafiu nada kirki, amma fah prince ka raina min wayo ba kadan ba, wai dama baka sake niba ?
Dariya yayi hade da bude side box din motar ya ciro takardar yabata.
Budewa tayi ta karanta, dariya tayi tace "i was so stupid & tense, ka shammace ni kuma saina rama" ta fadi hade da kaimai duka cikin salon wasa.
Damko hannuta yayi tahau basa hakuri, wasa sosai sukayi tayi amotar har suka iso gida, nan ma shagwaba tayi ta zuba mai ita bazata shiga gidan ba saida yace Gidan Mom zai mai data sannan tayi azaman fitowa hade dabin bayansa da gudu, palo suka shiga suna dariya atare.
Welcome Mardiyya tayi masu, fuskarta dauke da fara'ar tace
"Sweetie watx d good new, naga both of you are rejoicing"
Daki Batul ta gudu cike da kunya, hannu Mardiyya ya riko suka zauna kan kujera, murna kadai take tana jiran ya fadi farin cikinsa dan ta tayasa murna.
Murmusawa yayi hade da shafar fuskanta yace "you look gorgeous"
Thanks sweetie" ta fadi cikin kaguwa da yafadi mata.
Yace "the good news is nida princess ba siblings bane, dou na jima da sanin hakan".
Kallonsa take murmushi dake fuskar ta na raguwa.
Nan ya zayyane mata akwai aure tsakanin su, dama tun asali ba sakinta yayi ba.
Shuru tayi tana sauraran sa, tuni annurin fuskanta ya dauke, kiris ya rage ta fashe da kuka, daurewa tayi ta rungumesa tana fadin "am happy for you"
"Tnx Diyyah, tnx so much for your support, am always proud of you" yafadi hade matse ta jikinsan.
Kasa daurewa tayi hawayan dake makale ya zubo bisa kuncinta, gyaran Murya tayi hade da janye jikinta, bata bari yaga fuskar taba tace Sweetie bari na hada ma ruwa kayi freshen up" dakinsa ta nufa, ya shingide kan kujerar hade da lumshe idanu.
Kunya duk ta ishi batul, kasa fitowa cin Abincin dare tayi saida taga sun kammala ba kowa a palo sanan ta fita taci, kwance yake yana jiran shigowar princess dinsa unfortunately Mardiyya ta shigo sanye da nities hade da kwanciya kan gadon batare data kalle saba
"Diyyah princess tayi bacci ne" ya fadi murya kasakasa.
Banxa tayi dashi tamkar bata ji saba, haka dai suka kwantar hade da bawa juna baya, ko wanne su da abunda yake sakawa aransa.


***
Da safe kitchen suka hadu su biyu suna aikin breakfast, ko wanan su fuska ba yabo ba fallasa, babu mai yiwa juna magana tun bayan gaisuwa da sukayi.
Kammala komai sukayi suka jera a dinning sannan kowace tayi wanka tayi shirinta, dakinsa Mardiyya ta nufa ta iske har yayi shirinsa jikin suit.
"Sweetie breakfast is ready" ta fadi hade da kai hannu tanai gyaramai neck tie dinsa.
Cheeks dinta ya laguda hade da riko hannuta suka fito, dining suka nufa yaja mata kujera ta zauna, yace "someone is missing, ina zuwa"
Bai jira cewar taba ya nufi dakinta, kwalliya ya iske Batul tanai yi bakin mirror, da ganinsa tayi sauri labewa jikin labule.
Dariya yayi yace "yaushe princess tafara kunya prince dinta"
Kaman zatayi kuka tace "my prince dan Allah ka fita"
Karasowa yayi hade da janye labulan, tafin hannuta tasa ta rufe fuskarta
Sunkutar ta yayi kaman Baby, ihu take cikin salon shagwaba tanai rokonsa ya sauketa, bai kula taba suka fita, a Dining ya direta hade da ja mata kujera ta zauna.
Dauke kai mardiyya tayi kamar bata gansu ba tahau serving kowa a plate.
Fara ci sukayi, saidai rabin hankalinsu nakan juna, cike da nutsuwa Mardiyya kecin abincinta, kaiwa hannuta yayi daidai da kaiwa hannu Batul kan tumbler mai dauke da coconut juice, janye hannusu sukayi atare ba tare da kowannan su yadau ka ba.
Murmushi Rmd yayi hade dakai hannusa kan Tumbler din, dauka yayi ya zuba acikin glass cup dake gaban Batul sanan ya ajiye.
"Thanks my prince" ta fadi cikin salon dani kaina bansanta dashi ba.
Iya bacin rai da Kuluwa Mardiyya takai, wato shine bazai zuba mata ba, matsar da abincin tayi gefe hade da mikewa tsaye, barin gurun tayi ta koma dakinta, gado ta fada cikin matsananci kuka.

Cikin rashin damuwa da barin ta gurin suka cigaba da kallon love dinsu, kammalawa yayi yace "princess am off to work, kicewa Sister dinki na wuce" mikewa yayi cikin sauri dan tuni yayi latti.
Mikewa tayi kaman zatayi kuka tace "my prince xaka tafi ka barni"
"Oh princess, plz dont cry" hugging dinta yayi yanai lallashinta, tare suka fita saida taka ya shiga motar yaja sanan ta dawo tsaftace kan dining din.


Yunin ranar Mardiyya daki ta wuni tanai kuka, koda Batul ta isketa hakan, karya kadai tayi tace kanta na ciwo, ganin ba mafita yasata fita haraban gidan ta zauna kan sit din zama dan shakatawa da shan iska.

Daga cikin office ya kira charles, da azama yazo hade da risina
Yace
"Akwai wasu document na oil export a office din Mardiyya dauko min".
"Yes sir" charles ya fadi, harzai fita.
Yace "dont worry, bara naje dakaina, it been long dana leka marketing department".
Mikewa yayi ya fice daga office din, direct building din ya nufa, maaikata da dama sai gaidasa suke, shiga office dinta yayi, komai tsaf tsaf, zama yayi kan swivel chair

Please Login or Register in order to submit comment