Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ku shiga bandaki ku kamata karta gudu"
Mamaki ne yakama Rasheed, wanan wana irin abune Mom dinsa keyi haka, yasan Batul da karya badai sata ba, idan ma sata tayi how com ta sace one earring, wata zuciyar tacemai it can be possible mayb siyawar xatayi tayi kudin data ta jima tana mafarki zama mai kudi. saurin kawar da tunanin yayi yana girgiza kai.
"Mom dan Allah kiyi hakuri, nasan bakison zaman princess agidan nan, insha Allah yanxu zatabar miki gida".
Mugun kallon ta jefasa dashi.
" idan na barta taci bulus kenan, bai xai yuyuba dole hukuma su yanke mata hukuncin daya dace da ita koda ma ace yanke hannuwan ta xa suyi"
Dafe kai yayi cike da tashin hankali, yace "xan yanke mata hukunci da kaima, dan Allah Mom ki sallami yan sandan nan" kamar xaiyi kuka ya karashe maganar.
Tausayi yabata saidai kuma bazata iya hakuri so called princess ta zauna mata a gida ba, kallon police tayi ta sallamesu hade da ce masu zata bukace if needed. Fita sukayi ta mara masu baya hade da hararar Mardiyya dake tsaye tsuru tsuru.

Zuciya daya ta fito tana kakkabe ruwan gashin ganta, jikinta daure da towel, ganinsa datayi bakin kofar yasata azama komawa ciki, da sauri yasa hannu ya riko gashin kanta hade da finciko ta waje, ware idanu tayi tanai kokorin kwace kanta, Mardiyya dake tsaye ta shigemai gaba, "sweetie plz calm down, trust me nasan ba ita ta dauka ba"
Ido jajir ya kalleta, turera gefe yayi yana fadin "stay out of this."
Jan Batul yayi suka fice daga dakin ayayinda take mai magiyan ya saketa.
Ran Mardiyya ya sosu, ina xai kaita ahakan daba kaya jikinta, binsa tayi abaya, kafin takai ga karasa wa dakinsa tuni ya shige da Batul ya banko kofar da karfin gaske.
Gabanta na dukan uku uku ta makale jikin kofar hade da dasa kunne tana sauraran abunda zai wakana.

Wurgi yayi da ita kan gado har kanta yana buguwa, zaburewa tayi ta mike zaune, atunanin ta ko fade zai mata yasata kara susucewa
"Dan Allah kayi hakuri" ta fadi cikin murya kuka.
Iya kuluwa yakai, koma miye Mom dinsa tayi mata itace sila,
Fuska ba annuri yazaro belt dake cikin closet. Zama yayi bisa kujera dake dakin yan fuskan tar ta.
"Zonan" yace da ita.
Mikewa tayi tsaya cikin rawar jiki ta nufesa.
Kawar dakai gefe yayi yace "On our kneels"
Astorace tayi axaman ijiye gwiwowin ta kasa tana kara basa hakuri.
Daga belt din sama yayi hade da mikar da ita sannan ya kalleta.
"Miyasa kika sacewa Mom Gold earring dinta"
Tsuru tayi dan bata fahimci inda xancen sa ya dosa ba. "wana Gold" ta fadi cikin shesheka.
Tashin yayi yakai mata bugu daya, tuni ta bankare hade da kwalla uban ihu. Rutse Idanu Mardiyya tayi, bazata jure abunda kunnanta ke saurara ba, bugun dataji yay mata tamkar ajikinta taji sa, barin gurin tayi cike da tsananin tashin hankali ta sauka zuwa dakin Mom.

Zare mata idanu yayi yace "ki gayamin gaskia, nasan ke kika sace ?
Kuka sosai take tana fadin bata dau komai ba, rufe idanu yayi ya dinga dukan ta iya son ransa sannan ya kuma tambayanta "ke kika dauko, Yes or no ?
Hawaye kadai take iya zubdawa, tuni karfin ihun ta yakare, ta lura idan ba cewa tayi itace ta dauka ba bazai kale taba
"Yes nina dauka" ta fadi cikin hopless murya.
Cikin rashin damuwa da yanayin yace "Good, abunda nakeson ji kenan"
Saida ya kara bugunta sau uku sannan yayi cille da belt ya shiga toilet.

Ko kwakwara motsi ta kasa, zubar kwalla kadai take tana kallon farin fatar jikinta daya sha tabon laftar daya yi mata, "duk adalili mene" ta tambayin kanta, bakin halinta na rashin wadatar zuci, biyyayyar iyaye, kwadayi da neman duniya ya janyo mata, Sata da bata taba yiba yau an k'alamata tasha duka abanxa, sai yau ta kara gasgata xance bature dayace All that glitters is not Gold, shedan yakaita ya barota, kaso abu ya zama shairin ka, kuka sosai take tasan ukubar ta bai kare ba idan Baba da Hajjo suka san abunda ta aikatawa kanta. Amma mijinta Mamuda fah mai zatace dashi, abun kunya nema ace da auranta tazo gidan wani namiji da zama, duk a zuci take fadin hakan.

Tsaye yayi gaban mirror dake toilet din, idonsa jajir yanai zubda hawaye mai cike da bacin rai, ji yake tamkar ya cire hannusa yayar tsabar yadda yake jin haushin bugun da yay mata akan laifin da bata aikataba.
Hannusa yakai ya bugi madubin da karfin gaske ya tarwatse, jini sosai yafara malalowa daga hannusa, dafe hannu yayi jikin bango yana kuka cike da wani yanayin marar fasara, tunanin kadai yake ya zaiyi tabar gidan, dabarace ta fado masa ya dauki karamin hand towel dake gurin ya lullube hanusa dake tsiyaya da jini ya fice daga bandakin, nan tsugunne ya ganta inda ya barta baice kala ba ya fice daga dakin.

Banko kofar dakin Mardiyya tayi ta k'usa kai ciki, Mom na zaune tana karatun Newpapers taganta tsaye fuska ba annuri.
"Mom kije tsoron Allah, bakya tunanin ki mutu da alhakin princess akanki, am 100 percent sure ke kikayi plotting komai"
Mikewa Mom tayi tsaye ta nufo, "ni kike gayawa magana kamar wata saarki"
Mari Mom ta kwashe ta dashi kafin takai ga bata amsa.
Kuka ta fashe dashi hade da dafe kuncin ta.
"Zaki ci ubanki ne" Mom ta fadi hade da daukan waya ta kira Hajiya Safara, magana sukayi sannan ta mikawa Mardiyya wayan.
"Hello, Umma" ta fadi cikin shesheka.
Ashariya Hajiya Safara tahau lailayo mata cikin masifa tace "Mardiyya ki shiga taitayinki, am trying to secure your future kina can kina hauka, idan nazo gidan nan zaki ci ubanki ne, yar banxa yarinya marar wayo.
"Umma nifa bance komai ba, nidai injustice ne banaso, makirci da kuke plotting da Mom bazai amfane ni da komai ba saidai ya kashe min aure" duk cikin kuka take fadin hakan, bata jira cewar Umma ba ta mikawa Mom wayar, amsa tayi cikin zafin nama ta dasa a kunne suka cigaba da magana sannan ta katse.

Mugun kallo tama mardiyya tace "Rasheed da nane, koda kin gayamai nice nayi plotting komai, bazai yadda dake ba cox he loves me alot more than yadda kike tunanin, tun muna mu biyu ki lallaba bakin ki kiyi shuru, yarinyar nan da kike siding she is a big treat to our lives, am warning you stay away from her"

Karaf a kunna Rasheed dayake kokarin shigowa dakin, fasa shiga yayi, yabi hanyar fita waje da azama cike da mamaki kalaman Mom, ina tasan Batul da har take ikirarin treat, kawar da xancen yayi dan ba wannan ne ya damesa ba, Batul kadai yakeso tabar gidan tun kafin Mom ta illata ta.
Ma'ajiyar motoci ya nufa yashiga mota yaja, bakin gate ya karaso yace da security subarta ta fice idan ta fito sanna yaja yabar gidan, tuki yake yana kara jajjadawa kansa last chance kadai ya rage ma Batul, idan har tayi loosing he has no choice other than to leave her.

Kuka sosai Mardiyya takeyi, fitowa tayi daga dakin ta haura sama zuwa dakin. Zama tayi hade da tagumi tana tunanin wana abu mamanta da maman mijinke ke aikatawa, koma miye tasan babu alheri cikinsa.

Dakyar ta iya mikewa, dafe bango tayi ta karasa dakin ta, zani da hijabi kadai ta dauka ta sanya jikinta, barin gidan kawai zatayi koda ace ta fence ne, ahankali tasamu ta sauka taci saa ba kowa palon tayi saurin rugawa waje, tun kafin takai ga isa bakin gate din taga an wangale mata, atunanin ta wata motace zata shigo, ba tare da bata lokaci ba tayi sauri ruguwa ta fice daga gidan.
[10:01PM, 5/26/2017] Xarah Bukar: 💖 *INA ZAN GANSHI*💖
Rubutawa
Xarah Bukar

®NWA

xarahbukar.wordpress.com

63 - 68

Cab ta gani pake gurin da azama ta fada tanai fadin mai unguwar da zai kaita, bai tsaya ciniki da ita ba, yaja motar, da isar su, fitowa tayi, cikin sheshek'a ta tambayesa nawa kudi, "oga ya biya" ya fada had'e dajan motar yayi gaba.
Mamaki da faduwar gaba ne suka diran mata.
"kodai Rmd yaga fitar tane" ta fadi a zuciyar ta.
Kallon kofar gidan tayi tana tunanin makomarta, wani sabon kuka ne ya kufce mata dakyar ta iya samu courage din tura kofar langalangar ta k'usa kai ciki gidan hade da sallama.
Zaune yake a tsakar gida bisa tabarma, kunnen sa nad'e da radio yana sauraro, jikinsa sanye da koriyar yadi da bakar hula bisa kansa, sauraran radio yake cikin nishadi da annashuwa.
Ciki ciki ya amsa, ba tare daya dago kansa dake kollan k'asa ba.
Arakub'e ta karaso gabansa hade da tsugunna wa, dukar dakai kasa tayi, kasa kallon sa tayi tsabar kunya shi dataji ya diran mata, ko adama ba wani k'are mai kallo take ba tsanin yadda take k'insa, yanxu data fara sonshi kunyar abunda tayi ya hanata ta dagowa.
K'ara sautin kukan tayi tace
"Sannu da zuwa"
Dago dakai yayi ya dube ta sannan yace
"Nina dace da miki sannu da zuwa, ya duniyar fatan dai kin samo abunda kikeso ko dayake amsa takardar ki ya dawo dake"
Kai ta girgiza hade da riko hannunsa.
"Mamuda dan Allah kayi hakuri ka yafemin"
Dan k'ara ya saki kadan tsabar azaban yadda ta matse mai tafin hannunsa.
Saurin sakin hannu tayi sakamakon jinin da taga yana diga, cike da kid'ima ta ciro hijab dinta tahau kulle gurin dake yanke. Bruises din jikinta ya kalla yana kara jin haushi kansa, hannu yakai gurin yana fadin "Batula miya same ki haka ?
Tsigarr jikinta ne ya tashi, ga wani uban radadi da gurin kemata.
"faduwa nayi" ta fadi cikin matsananci kuka, mikewa tayi da axama ta fada cikin dakinta, kuka sosai take tana tunanin yadda xata fadimai gaskia, saidai tsoro take karya rabu da ita.
Jinjina kai yayi yasan zaa rina, shi kuma yadau alwashin idan bata fadi mai gaskia halin data shiga ba bazai cigaba da kasancewa tare da ita ba.
Mikewa yayi hade da cire hijab din dake kulle hannusa ya fice daga gidan zuwa pharmacy dan samun cikekken treatment.

Sallamar Almajiri ce ta katse mata kukan da take, hijab dake ghanarta ta ciro ta sanya sannan ta fito, mika mata ledar kayan miya da danyar shikafa yayi yana cewa maigidan ya aiko sa, amsa tayi sannan ta roki almajirin ya dibo mata ruwa a burtsatse, ba musu ya dauki bokitai dake gurin ya fice waje.
Tun shigowarta bata lura da dakin Inna dake datse da k'wad'o ba sai yanxu da hankalinta yakai gurin, jiki mace ta nufi Bakin murhu aza wuta.

Har bayan sallah isha bai dawo ba, dan abinci data ajiye mai cikin samira tuni tayi sanyi, kara aza wuta tayi ta dumama sannan ta zauna bakin kofar dakinta jiran dawo warsa cikin tagumi.


Mikewa Mardiyya tayi dakyar ta karasa gaban drawer, janyowa tayi ta ciro magunguna kusan kala hudu sannan ta balle ko wanne tasha ta kora da ruwa dake rike hannuta a glass cup. Jiri sosai takeji, ta jima bata jita jikin yanayin ba, tsabar kuka da tayi ke barazanar janyo mata zazzabi, Shuru har dare bata ji motsin Saba atunaninta ko yana office, dakin Batul tuni ta duba bata cikin, kayanta data gani yasa tayi tsammanin ko ta shiga toilet gasa jiki dan tuni ta leka dakinsa babu kowa.
Dakin Batul ta nufa, wayam ba labarinta, toilet ta leka babu ita balle alamun danshin ruwa, cike da tashin hankali ta nufi dakinsa nan ma ba alamun bil'adama ciki, tura kofar toilet tayi ta shuga, saidai jinin da broken mirror data gani yasata girgiza, azaman tsaftace gurin tayi cike da mamaki abunda ya faru, fatan ta daya kar ya zamana Rasheed ya jima princess ciwo agarin bugunta.
Fitowa tayi ta leka office baya ciki, daki ta koma tadau wayarta tahau kiran sa no response.
Saukowa kasa tayi ta nufi dakin Mom dake kwance kan gado tana kallon tashar Aljazeera a Tv, ganin Mardiyya ta fado dakin yasata daure fuska.
"Mom banga princess ba kuma Rasheed baya gida" akideme take maganar.
Tsaki Mom taja, tuni taga ficewa Batul da gudu ta window dakinta.
"Ta koma gidan Ubanta" ta fadi.
Ware idanu Mardiyya tayi tace "mom badai kin kore taba, kinsan dai Rasheed bazai ji dadi ba"
K'wafa Mom tayi
Tace "Mardiyya ki shiga taitayin ki, kinsa dai auran nan naki nice nayi insisting, Rasheed ba sonki yake ba".
Anzo gun, b'ata rai Mardiyya tayi, yau ita Mom kema gori, batace uffan ba ta juyawa zata bar dakin.
"Rasheed ba karamin yaro bane, he has the right to sleep duk inda yakeso dan bai dawo ba dat doesnt me ki hana kanki bacci" Mom ta fadi cikin kota kula da yanayin ta.
Karasa ficewa Mardiyya tayi cike da kunin rai, dakinta ta nufa ta kwanta cike da tunanin yadda rayuwarta zata kasance gaba.

Karfe sha daya Rasheed ya dawo gidan da Batul take, leka dakin yayi yaganta makure can karshen bango tana bacci, tabarmar dake jingine yadau ya warwareta hade da shimfuda ta, kwanciya yayi kai yana tunanin bazai iya kwana agidan ba, asalima ya dawo yaga lafiyar tane.

Motsin dataji yasata farkawa, mikewa tayi ta fito rike da samirar abincin, gidan duhu ko haske babu banda haske farin wata daya gauraye gurin, karasa tayi inda yake kwance, ta durkusa aladabce, cikin sanyin Murya tace "ga abinci"
"Na koshi" yafada ataikace.
"Dan Allah kaci"
Banxa yayi da ita bai tanka ma, idan yayi magana mai tsawo tana iya dago muryar sa.
Ajiye abincin tayi gefe, ta kwanta kan tabarmar dan nesa dashi suna fuskantar juna. shuru sukayi na dan sakwanni kowa da abunda yake sakawa aranshi.
Ajiyar zuciya ya sauke yace
"Batula ina kikaje ranar da kika bar gidan nan ?
Gabanta ne ya fadi, tace
"Ranar dana fita wani mutum ne ya kadeni da mota yakaini gidan sa da matarsa mai kirki, shine nayi masu karyar ni yar sarki ce na manta komai, barina sukayi na zauna a gidan shine kuma yau na dawo, Nasan nayi kuskure dan Allah ka yafemin" cikin muryar kuka ta karase maganar.
"Cigaba" ya fadi.
Shuru Batula tayi tana tunanin gayamai abubuwan daya faru tsakaninta da RMD, tsoro takeji sosai, mudin yasani tasan rubuwa xaiyi da ita, bazata fadimai ba amma tayi alkawarin gayamai nan gaba idan ya fara sonta.
Cikin shesheka tace "Shikenan abunda ya faru"
"Kin tabbata abunda ya faru kenan, babu ragi babu kari ?
Kuka sosai ta kufce dashi tace "eh na tabbata".
Numfasawa yayi yace "gobe zamu je inda xan yanke maki hukunci"
"Dan Allah kaiyi hakuri ka yanke min ko wana hukunci amma karka rabu dani, i cnt leave without you" sosai take kuka.
Hannu yakai bisa fukarta yace "ki kwantar da hankalin ki"
Tsayar da kukan tayi, tana feelling hannusa dake bisa fuskarta.
"Good nyt" ya fadi hade da cire hannusa.
Lumshe ido tayi tana mai jin dadin kasan cewa tare dashi.

****
Washe gari data farka tuni ya rigata tashi ya fice masallaci sallah asubah, Murmushi tayi data jima bata yiba, kama ruwa tayi sannan tayi alwala ta shige dakin gabatar da Sallah.
Karfe bakwai shuru bai dawo ba, tashi tayi ta kyalyale gidan fes sannan ta dubama shinkafar ta sanya asamira ta ajiye jiran dawowarsa.
Sai kusan sha daya saura ya dawo, tana daga dakin ta jiyo dirar mota agaban gidan, gabanta ne yafadi atunanita RMD ya biyota, hijab ta dauka ta sanya, fitowan ta tsakar gidan yayi da daidai shigowar sa, bata kallesa ba tasan shine sakamakon kyakyawan kafarsa data kalla,
Risina wa tayi tace "ina kwana
Bai amsa ba ya riko hannuta zuwa waje, ganin dankareriYAR jeep parke agurin yasata firgita, saurin tirjewa tayi tana fadin
"Mamuda ina zaka kaini"
Bude bayan motan yayi ya turata ciki ya rufe sannan yashiga gaban mazaunin banxa ya zauna.
Gabanta ne ya fadin Ganin wani daban ke tuka motar, tsoronta daya kar ya zamana gidan RmD zasu nufa.
"Gidan zamuje ?" Daddy malam ya fadi yana kokarin tayar da motan..
"Eh, hurry up inason zuwa office" Rasheed ya fadi cikin muryar sa na ainihi.
Ware idanu Batul tayi jin Mamuda na batun office, bama wannan ba Muryar sa sounds familiar, tsananta bugun gabanta yayi har suka karasa madaidaicin gidan Rmd na ainihi wanda babu mai zama ciki sai shi idan ya tashi b'adda kama.

Parking Daddy malam yayi a farfajiyan Gidan, sauka Rasheed yayi ya bude side dinta, ta fito yayi gaba ta mara mai baya cike da tashin hankali da tunani kala kala.

Parlour ya bude ya shiga, ta shigo ta rakube gefe, zama yayi bisa kujera yanai kallon yadda tayi tsuru tsuru.
"Zonan ki zauna" yace mata yanai mata nuni da kujerar dake fuskantar sa.
Karasa tayi ta zauna fuska duke.
Yace "Dago ki kalle ni"
Ahankali ta tago tana kallan sa,
"kin gane ni ?
Daga kai tayi alamar eh sannan tace "mamuda ne mai keke Napep"
Murmushi yayi dan kuwa ta basa dariya.
Mustache din fuskarsa ya cire ya kuma tambayanta kota ganesa, kura mai idanu tayi yaso yayi kama da Rmd amma tasan bashi bane.
"Baki gane niba bako princess ?"
Jin kalamansa tayi tamkar saukar aradu, mikewa tayi cike da tashin hankali tana kallon sa.
Daure fuska yayi yace "to show how stupid you are kin kasa tantance mutum daya with two different identity"
Kai ta girgiza, it cant ba possible, tayama xaace mutum daya ne, sai yau takarewa Mamuda kallo bammanci su da Rmd mi haske ne da muryarsa daya canxa.

Daddy Malam ne ya shigon Parlour, kallonsa yayi hade da mikewa tsaye yace
"Make sure bata gudu ba, she is really good at it" shigewa daki yayi ya nufi toilet.
Kuka Batul ta fashe dashi zuciyar ta na azalzalanta da bashi bane, plan ne kawai ake son rena mata wayo, amma Mamudan ta ba Rmd bane.

Bayan 30 min ya fito sanye da Grey suit, kyakyawar fatarsa sai kyalle take, yayi kyau matika, binsa tayi da idanu har ya zauna.
Cikin kuka tace "i dont believe you, nasan Mamuda is somewhere around, dan Allah ka fito dashi
Cikin ko in kula da yamayinta yace
"I dont own you any explanation, na baki chance jiya still baki gayamin gaskia ba, it seems you will never stop been a liar, ajininki yake"
Kallonsa take tana gasgata lailai shine, amma miyasa xaiyi playing dinta haka, tasan both mamuda da Rmd tana sonsu miyasa shi ya boye mata kanshi, lailai ramin karya kurarre ne, all this while da mutum guda take zauna tana sharo mai karya akan wanda batama sani ba, duk azuciyan ta take fadin haka.
Takadda ya ciro daga aljihunsa yana fadin "burinki Mamadu ya sake ki, gashi yau ya cika maki" mika mata takarda yayi taki amsa saima sautin kuka data kara, cilla mata yayi bisa fuska tasa hannu ta bude. Saki daya taga yayi mata, wani irin ihu ta kurma tanai rokonsa,
Mugun kallo yakai mata yace "tashi ki fita na sallameki", rokonsa sosai tayi akan ya janye sakin, tsawa ya daga mata ba shiri ta mike tsaya cike da kidema, hanyar kofar tayi taji yana fadin "kina iya kwana a gidan for today, gobe saiki tattara ki koma gidanku saboda suma iyayenki goben zasu dawo daga kauye, saiki saurarun jiran hukuncin su"

Bata iya tanka saba ta cusa kai tayi waje, tashin hankali mai tsananin ke tattare da ita, idan har Baba yayi hakuri ya barta tasan Hajjo ba zata barta da rai ba, kuka sosai take wani irin mugun son Rmd da Mamuda ke fuzgarta lokaci guda, ita kanta ta kasa tantance wata fiso acikin su.

Kallonsa Daddy Malam yayi cike da tausayin Batul yace "she loves you alot, kayi hakuri ka maida ta, "
Mikewa Rasheed yayi cikin rashin damuwa yace "am late for work" bai jira cewar Daddy ba ya tsuri mukulin mota dake ajiye ya fice daga parlour.
[10:01PM, 5/26/2017] Xarah Bukar: 💖 *INA ZAN GANSHI*💖
Rubutawa
Xarah Bukar

®NWA

xarahbukar.wordpress.com

69 - 70


Tsananin ranar daya k'walla garin bai hana ta ganin duhu da jin sanyi ba,
Tafe take tana lailayi sakamakon jirin dake neman d'ibar ta tsabar yunwa da radad'in da zuciyan ta yake, kuka take ba k'agauta, horn din motar dataji bayanta yasa ta daskarewa tsaye batare data waigo ba.
Tuk'owa gaban ta yayi hade da wining glass kasa, hada idanu sukayi yanai kallon yadda idanuwanta sukaisauya launi zuwa ja, kawar da kai yayi ya ciro d'ari biyar daga wallet dinsa, cikin rashin damuwa da yanayinta ya cilla mata kudin afuska yabai wa motar wuta yayi gaba.
Yak'en da yafi kuka ciwo tayi hade da sa hannu tadau kudin da tuni ya fad'i k'asa, jinjina kai tayi, tana xancen zuci, ko mi yay mata bataga laifin sa ba ita ta jama kanta, asalima sonshi ba raguwa yayi a xuciyan taba idan ma ya dawo gareta hannu bibbiyu xata amshe sa, saidai ayadda taga fuskar sa she doesn't tink xai k'ara waiwayanta, kuka sosai take tana consoling kanta, tasan Mamuda nada kirki da kyakyawan zuciya baxai share taba, he will definitely come for her.
Hope sosai tayi ta bawa kanta, taxi ta samu ya dawo da ita gidan sanna ta biyasa da dari biyar din.
Marwa tagani tsaye gaban gidan, yana zuba yan tarkace a gidan baya, da azama ta shige gidan sanin cewan tarkacan Inna ne.
Tsaye taga Inna bakin kofa tana kokarin datsewa da k'wado, dan ihu mai tattare da tashin hankali tayi tana fadin
"Inna karki tafi ki barni"
Sai sannan Inna ta ankara da ita, sosai Batul ta bata tausayin sakamakon fita hayayyacinta da taga tayi.
"Batula kin dawo ashe" Inna ta fadi hade da zare mukillin k'wadon.
Karasawa gabanta Batul tayi ta tsugunna, cikin kuka tace "inna dan Allah ki zauna dani, bansan ina xan nufa ba, Mamuda ya sakeni ko kuma ince RMd ya sakeni dan nasan kinsan komai"
Dagota Inna tayi tanai kallonta.
"Batula laifin kini ai, kwanaki ba yadda ban rokeki karki tafi ba kikayi kunnan uwar shegu kika kara gaba, inda ace kin tsaya da Rasheed bai sake kiba, aranar yaso bayyana maki kansan amma ke kika tafi nuna mai kanki"
Sosai take kukan tace, "nasan na tafka babban kuskure, amma Inna ai bai kamata ya sakeni ba kodan son dana kemai"
Goge mata hawayan Inna tayi.
"Kidaina kuka, Allah yasa sakin yafi alheri, yanxu
Ki dau kayanki ki koma gidan ku"
Kai ta girgiza, "Inna tsoro nakeji bazan iya komawa gida ba, ki temaka ki zauna dani kafin wasu kwanaki saina koma gida inyaso muje tare ki tayani bawa Baba da Hajjo hakuri"
Ajiyar zuciya Inna ta sauke tace "kinga ni baa garin nan nake ba, Jikana ne abokin rasheed shiya kawoni nazauna dake na dan wasu lokuta, yanxu kuwa gida xan koma Zaria na cigaba da sana'ata shiyasa kika ga na dawo daukan sauran tarkace na"
Kyankyame Inna tayi tana rokonta, "dan Allah kije dani Zaria, ko talla ce xan miki, Inna ki temaka.." Karashe maganar tayi cikin matsananci kuka.
Ba karamin tausayinta Inna taji ba, tace mata ta dauko kayanta su tafi, cikin rawar jiki Batul ta fada daki ta warb'o ghanar ta fito sukayi waje, Marwan suka shiga yajasu zuwa tashar kawo suka shiga motar Zaria.



*Kauyen Marke*

Jigawa state.

Zaune Hajjo take a tsakar gidan su mai zagaye da kara masu kauri, Rike take da rariya tana tankadar garin masara. Shigowa baba yayi yanai wa su Hassan nuni da inda zasu ajiye buhun albasar dake lafce bisa bayansu, ajiyewa sukai hade da sauke numfashi.
Zama Baba yayi bisa tabarma dake shimfud'e, Hajjo tamai sannu hade da mikewa bakin randa dibo mai ruwa.
"Noma akwai dadi, kaman karmu koma Kaduna" Hussaini ya fadi yana zama kan tabarmar.
Hassan dake tsaye yace "nikam na matsu mu koma naga Batula"
Guntun tsaki Hussaini yayi.
"Batula ta manta mu, tunda tayi

Please Login or Register in order to submit comment