Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

aure bata kira kosau daya ba, gashi ita layinta baa samu, na tabbata arziki tayi ta yashe mu"
Kwafa baba yayi yace "banason gulma, ku tashi ku bani waje".
Tsum suka mike suka fice, takaici ne yakama Hussaini, ya dade da lura duk cikinsu Baba yafi son Batul, sau da dama tayi laifi baya hukuntata saiko Hajjo ta mata duka amma su abu kadan yahau masu fada, shiyasa sam Jinin su bai hadu da itaba dan kuwa bayason raini dukda ita din yayar shice.

Ruwan Hajjo ta mikamai ta zauna tanai kara mai sannu.
"Ka sanar da Mamuda batun fasa tafiyar ? Acewar Hajjo.
Wayar aljihunsa ya ciro yana fadin "zuwa gobe dai xan kirasa yanxu wayar ba caji".
Numfasawa Hajjo tayi tace, "na yaba da hankalin yaron sosai, saidai halin Batul nake tsoro, Allah yasa tana kyautatamai"
"Karki damu, Insha Allahu lafiya suke".
"Allah yasa" ta fadi,
Hira su cigaba dayi cikin kwanciyar hankali.

****
Kaduna.

Aiki sosai yayi a office, bayan yayi sallah isha ya nufi hanyar gida.
Cikin shirin atampa riga da skirt tayi, fitowa tayi daga dakinta da niyya sauka kasa taji tashin zuciya, da azama ta ruga toilet, wani mugun amai yaxo mata tahau kwararawa, dogon numfashi ta sauke bayan tagama ta wanke baki ta fito, bakin mirror ta nufa ta kara shafa powder sannan ta sauko kasa.
Mom ta iske zaune parlour tana shan fruit,
Kallon ta tayi sannan ta zauna tace
"Mom yaushe kika dawo " ta fadi in state of confusion tana kura mata idanu.
Guntun tsaki Mom taja bata tanka taba, zama Mardiyya tayi tana tunanin tambayar danai mata can kuma tace
"Mom har yanxu fa princess bata dawo ba
Takaici ne yakama ta, magana xatayi ya shigo palon hade da sallama, jacket suit dinsa rike a hannu.
Mardiyya ce ta amsa fuska dauke da fara'ara tanai mai sannu da zuwa, mikewa tayi zuwa kitchen dauko mai abun sha.
Zama yayi kan doguwar kujerar da mom ke zaune, gaidata ta yayi ta amsa ciki ciki.
"Ina fatan bakaje bibiyar matsiyaciyar yarinyan nan ba" ta fada tana kallonsa.
Amsar ruwan da mardiyya ta mike mai yayi ta koma ta zauna.
Kai ya girgiza yana kallon Mom yace "nasan bakya kaunar ta, pls Mom kibar kiranta da matsiyaciya, she was once your daughter inlaw but not any more"
Tashin hankali ne ya durar mata, cike da kidima tace "Bangane ba, inlaw as how.
Maida da dubansa yayi bisa Tv dake kunne yace "ex wife ditace"
Zabure wa Mom tay tsaye, cikin rawar jiki ta kwashe sa da gigitancen mari da saida Mardiyya ta kwalla ihu tsabar firgita.
"Abdulrasheed ni zaka rainawa hankali, da izimin ubanwa ka aureta.." Cikin huci mom tayi magana.
Ransa ya bacci matika, saidai bazai tsaya yi mata bayanin sanadin auran ba, dukda ba son Batul yake ba bazai fadi masu halinta da dalilin zuwanta gidan nan ba.
murya mai dauke da bacin rai yace "it doesnt matter tunda nariga na saketa" mikewa yayi yahaura sama ba tare daya tsaya jiran abunda zata ceba.

Rai bace Mom ta zauna tana huci, yaushen hakan ta faru bata da matsaniya, lailai kuwa Rasheed yayi betraying soyayyar da takemai, kallon Mardiyya tayi dako ajikinta saima remote dake hannuta tana canxa channel.
"Waike wace irin dabbace, kinaji ya maki kishiya bada saninki ba amma ko ajikin ki" Mom tafadi cikin tsananin baccin rai.
Ajiye remote din tayi ta dubeta sanan tace "Mom mi kikeso nayi, ihu da hauka dan kawai ya auri princess, d first time dana gansu tare nagane he truly loves her, shiyasa ban taba interfering da duk care da yake nuna mata ba"
Harara Mom takai mata tace "sai yau nagane bakya son d'ana kin aureshi ne dan kudin sa"
Murmushi Mardiyya tayi.
"Ko daya wlh, as far a good wife kuma maison mijinta dole nayi supporting abunda yakeso, koda ace zai dawo da princess i"ll support him.
Haushi da takaici ne suka cikata, miketa tayi hade da wurga mata pilo dake gurin tabar palon afusace.
Cikin rashin damuwa Mardiyya ta mike ta nufi kitchen, fridge ta bude ta dauko ice dake leda ta fito ta haura sama.
Ahankali ta tura kofar dakin ta shiga, zaune yake kan gado kansa dafe bisa hannusa, zama tayi kusa garesa hade da janye hannusa, dagowa yayi duban ta da idanuwan sa da suka sauya launi.
"Sweetie kayi hakuri" ta fadi tanai dumama mai gurin marin da ice, shuru kadai yayi ya kwanto da kansa bisa kafadarta haunta daya na shafar mai baya.

***
Washe gari daya tashi hankalinsa gabadaya yayi gurin Batul, ko breakfast bai ba ya wuce gidan, wayam yagani bata gidan kuma babu jakar kayanta.
Hankali tashe ya fito yana tunanin ko su Baba sun iso ne ta koma can gidan da sassafe, da axama ya fada motan ya nufi gidan Baba nan ba basu dawo ba.
Wayarsa ya fiddo yayi dailing no din Baba, buga daya ya dauko.
Aladabce ya gaidasa.
Baba ya amsa da fara'a
Shuru yayi yama rasa mai xaice, katse shuru Baba yayi da cewa "Mamuda kaji mu shuru ko, dawowar bata yuyuba sai nan da sati uku saboda aikin noma daya rikeni"
"Allah ya kaimu Baba" ya fadi cikin kokarin boye damuwarsa.
"Ya matar taka ? Baba ya tambaya.
"Kalau take" ya amsa agajarce.
Sun jima suna waya da Baba daga bisani sukayi sallama.
Iya kidima Rasheed yakai, tsoransa daya kar ace ta gudu wani gidan, number Daddy malam yahau trying, kusan sau biyu bizy, ana ukun ne yadauka.
Rasheed yace "wai dawa kake wayane kusan rabin awa"
Dariya yayi yace "inna ce fah, kasan jiya ta koma Zaria"
Guntun tsaki yaja.
"Miyasa Inna ta koma da kanta, naso ace nina maida ta Zaria dakai na".
"Kunfi kusa, saika kirata kamata ya hanya"
"Tukun nadai, nazo gidan banga Batul ba
Dariya daddy malam yayi yace , "why do you care, ta tafi gidan su kenan".
Bata rai Rasheed yayi yace "bata gidansu, so nake ka bincika min unguwan masu kudi ko Allah zaisa aganta sannan har kad poly ka je ka bincika min"
Dariya sosai Dady yake babbakawa, "toh kadai yace mai"
Rasheed ya katse wayan, can gidan da take ya koma ya zauna na kusan awanni biyar babu alamun ta.


Bayan kwana Uku

*Zaria*

Abinci dake gabanta ta matsar gefe tana sharar kwalla, rashin nemanta ba karamin ci mata zuciya yake ba, all her tot xai dawo gareta, amma shuru ko inuwarsa bata gani ba, kuka sosai ta fashe dashi, rashin zuwan sa kadai ya nuna mata both Rmd da Mamudan basu da good heart kuma ba santa suke ba, itace kadai take wahalar da kanta, share kwalla tayi ta mike tana alwashin yakace sonshi aranta, tunda har baixo ba he is dead to her, gwara kawai ta cireshi aranta dan samun nutsuwa.
Dakin Inna ta shiga ta sanyo Hijan ta fito gaban gidan inda Inna ke tuyar wainar, ga mutane da dama zagaye da ita suna jiran abasu.
"Inna kawo" ta fadi tana amshen ludayin hannuta,
Murmushi Inna ta sakar mata ganin yadda tayi maganar ba tare da kuka ba, tunda suka iso zaria bata da aiki saina kuka, asalima yauce rana ta farko data fito temakawa Inna, sabanin da saidai ta zauna gidin pampo tana kuka.
Sakar mata Inna tayi ta mike zuwa cikin gidan dauko miyar wainar, zuciya daya Batula ta dage da juya waina a tanda, tuni masu miko kudi suka fara tana zuba masu, wani matashi ne ya karaso gurin yana fadin "jikar mai waina sako min na dari" ba masu ta amsa mai hade da zuba mai.
Murmushi Inna tayi, tana daga gefe tana zuba miyar, mamaki sosai tayi da Batula bataji haushin sunan da yaron ya kirata dashi ba, sabanin ada saidai ta bisa da ashariyar an zubar mata da aji.

Babu inda Rasheed da Daddy Malam basu nufa ba babu labarinta, sosai hankalinsa ya tashi, duk wayar da sukayi da Inna bata taba cemai Batul na tare da ita ba, shima bai mata xancen ba yasan ba yadda xaai Batul taje gidilanta.
Sosai ya wahala ya gangara komawa gida.

Handbag dinta dake ajiye kan gado Mardiyya ta dauka, sanye take cikin doguwar abaya ta yane kanta da babban mayafi, gurin takalma ta nufa da niyya sanya heel sai kuma ta fasa sakamakon dan kumbura da kafafunta sukayi, flat tadau tasa, ta sauko ahankali tayi waje gurin motarta, shiga tayi taja ta fice daga gidan, motar Abbanta taga yayo kwanar unguwar, mamaki sosai tayi saida bazata iya komawa gidan ba sakamakon appointment da take dashi da Doctor a asibiti.

Jiki ba lak'a motarsa ta danno cikin gidan, parking yayi ya fito ya iske Motar Abba parke daga gefe, baiyi mamaki ba atunaninsa Mardiyya yazo gani.
Cusa kai yayi cikin palon, harxai haura sama ya jiyo muryar Mom da Abban Mardiyya daga can Guess Parlour.
Kaman xai wuce ya fasa, mamaki ne yakamasa, yasan Hajiya safara da Mom basu rabuwa da kuskus, yau kuma miya kawo mijinta gidan, karasawa yayi bakin kofar ya tsaya sauraran su.
"Alhaji nasha gayama ka rabu dani danba auranka xanyi ba, yama zaai ace na aurin mijin aminiyata bazai yuyuba" acewar Mom.
Nisawa yayi yace " amintakar ku ba hujja bace, gidanta daban naki daban"
Murmushin dabai kai xuci ba ta saki, ta lura dai yana son ballo mata ruwa.
"Bafa xan aure kaba" tafadi.
Magiya da rokonta yahau yi, Mom kuwa ta k'ule dashi, dan kuwa bai kai matsayin da zata aure saba, tafi karfin sa.
"Kai Alhaji ka bar batun auran nan, akwai igiyoyin aure akaina, kasa kuma baa aure kan aure".
Kallon rashin fahimta yayi mata yace "kina da aurene, yaushe kika sake aure, bayan mutuwan Baba Rasheed" atare ya jero mata tambayan.
Guntun tsaki taja cikin kagara da batun sa tace, "akwai Auran Baban rasheed a akaina
Ware idanu yayi
"Bangane ba, a aljanna ko a duniya, nasan mamaci baya dawo wa"
Afusace Mom ta mike tsaye
"Waikai baka da fahimta ne, nace ma auran Babban rasheed na rataye wiyana kuma yana nan da ransa bai mutu ba" cikin karaji ta karashe maganar.
"What" Abban Mardiyya da Rasheed suka fadi atare cikin zare idanu.
Karasa shigowa parlour Rasheed yayi yana kallon Mom da tuni tasha jinin jikinta.
[10:01PM, 5/26/2017] Xarah Bukar: 💖 *INA ZAN GANSHI*💖
Rubutawa
Xarah Bukar

®NWA

xarahbukar.wordpress.com

*Special greetings to IZG* *fans, thanks much for the* *love & Support, ILYSM*❤
*TeamDiyyah*❤


71


Daskarewa Rasheed yayi, tashin hankali da firgici shimfid'e bisa fuskar sa.
Shi kansa Alhaji Bello ware idanu yayi yana sauraran karin bayani, kallan wulakanci tamai sannan tace
"Alhaji ka fita idanu na, kaga adalilin nacin ka na furta abunda ba hakan bane, tunda kaki ganewa gwada nama b'aro b'aro, bana sonka dan Allah ka shafamin lapia".
Hular kansa yahau gyarawa yana fadin "Allah ya baki hakuri, kinga tafiya ta" ficewa yayi daga palon batare daya jira cewarta ba.
Ajiyar zuciya ta sauke ta maida dubanta ga Rasheed da itama kallonta yake
"My boy dont mind my words, haushi yaban yasa na furta hakan, babu wani aure akaina"
Cikin rashin gamsuwa da maganar yace "kince my Dad is alive"
Kwantar da Murya tayi tace "bakaji nace kawai fada nayi ba, believe me your Dad is dead".
Baice uffan ba ya fice parlour ba tare daya gamsu da abunda tace ba. Tunda har ta furtan hakan akwai kamshin gaskia ciki, idan ma koran Abba mardiyya take sonyi ai akwai oda strategies da zatayi using ba wannan ba.
Main palon ya k'arasa ya zauna yana tunanin wazai tuntuba da batun yadda mutuwar Babansa ta kasance, kawu Habibu ne ya fadomai arai, tabbas shi d'aya zai iya fayyace mai ko Babansa nada rai koya mutu, duk azuci yake xancan, dafe kai yayi, gabadaya duniyar tamai zafi, bai gama nutsuwa da b'atan Batul ba ga wata gagaruma Mom ta janyo mai.
Mikewa yayi da zama ya haura sama zuwa dakinsa. Freshen up ya shiga toilet yayi ya fito, ya shirya cikin kananun kaya, ya sauko kasa ya fice haraban gidan, motarsa yafada yaja zuwa home of hospitality (katsina).
Cikin sa'a ya iske kawu habibu gida bai fita ba, gaisawa sosai sukayi daganan ya zayyano mai xancen dayaji Mom ta fada.
Jinjina kai kawu Habibu yayi yace.
"Tabbas abunda ta fadi ta fade sane kawai dan wata manufarta, amma kam Baban ka ya dade da rasuwa, tunshi kuma bata sake aure ba"
D'aurewa kan Rasheed yayi da kalaman kawu, yakasa aminta da abunda suke fadi, shidai yasan akwai wata boyayyen al"amari dan jikinsa na fadi mai babansa na raye tunda Mom ta furta.
Nisawa yayi yace "kawu miye sanadin mutuwar sa, kunyi mai jana'iza ?
Girgiza kai yayi, yace
"Bana nan sanda ya rasu, ina Ghana karatu lokacin, bayan na dawo Maman ka kece min ya jima da rasuwa, nayi kuka rashin sa ba kadan ba, tsohonka akwai halin kirki da daddako"
"Allah yaji kanshi" Rasheed ya fadi asanyaye, saidai ayyada ya lura da xancen Kawu bai da matsaniya akan mutuwar Baba, same story da Mom tabasa shine wanda yasani, ba yadda ya iya dole ya nunawa kawu ya yadda da xancensa dan bazai iya mai masu ba.
Sun dade suna hira daga bisani yamai sallama ya kamo hanyar dawo wa Kaduna.


*Zaria*

8.26pm

Iya karfinta ta sanya tana wanke shinkafa wainar gobe, daga can gefe Inna ke zaune tana yankar alaiyaho.
"Ilimi akwai dadi, Inna nima dai xan shiga islamiyyar daran nan" Batul ta fada tana sauraran karatu dalibai dake tashin daga can islamiyar dake gaba dasu.
Inna tace "Islamiyar akwai karantarwa, babu wasa sam, yaro kadai xan tura ya karbo maki form ki ciki gobe ki fara zuwa'
Cikin jin dadi tace "nagode sosai Inna".
Yaro ya shigo hade da sallama, amsawa sukayi yace "Nafi'u mai shayi ke sallama da jikar mai waina, yana waje"
"Kai yaro koma kace bata fitowa" Inna ta fadi tanai zarowa yaro ido, tasan xaa rina sunga yar kyakyawa zasu fara damunta da k'wado sallama.
Dakatar da Yaro Batul tayi tace "kace mai gani nan"
Toh" yaro ya amsa ya fice.
Kallon Inna tayi tashe, "inna kiyi hakuri naje, kinsan shi dan adam komin yadda yake ba abun wulakantawa bane, wannan abu ya faru akaina, banaso tarihi ya kuma maimaita kansa.
Dariya Inna tayi, tace "gaskia ne, kije amma karki dade".
Hijabin ta dake lankaye kan igiyar shanya tadau tasa ta fice wajan gidan.
Tsaye ta iske shi, hannusa rike da bakar leda, jkinsa sanye da kodaddiyar tshirt da wando daga ganin wankan kure adaka yayi.
"Ina wuni" ta fadi hade da sunne kai kasa, tasan dama saiya biyota, dazu dataje teburansa siyan biredi sai wani kirki yake mata.
"Lapia kalau yammata" ya amsa.
"Sunana fatima" tace
Yace kiyi hakuri nakira ki da yammata, gaki da babban suna"
Murmushi tayi tace "ba komai, ya kasuwa ?
"Alhamdulilah" ya amsa mata.
Shuru ne ya biyo baya, sai can kuma yace "fatima tunda naganki naji sonki araina, dan Allah ki bani dama na nuna maki tawa salon soyyayar.
Murmushin dayafi kuka ciwo tayi, tuni ta cire so aranta, shi kuma gashi yaxo da kokan baransa, dago dakai tayi ta dubesa, Nafiu ba laifii dukda ba sonshi take ba tana iya aurensa, yana da kirki hankalinta zaifi kwanciya dashi.
Nisawa tayi tace "nagode sosai da Soyayyar ka, Allah yasa hakan yafi alheri".
Dadi sosai yaji ya mika mata ledar hannusa, kin amsa tayi, yace "ki karba, biredi ce na taho maki dashi"
"A'a wlh ka barshi, so kake na cinye ma jarinka"
Dariya yayi, ba yadda baiba ta karba taki amsa, hira kadan suka dan tab'a, tamai sallama ta koma gida, tuni Inna ta shige daki, zama tayi tsakar gidan tanai tunanin Baba da hajjon ta, kiransu take sonyi saidai wayar ma batasan a wace duniya ta yarba tsabar rawan jikin zuwa nema Rmd, ba mamaki ranar datai gudun nan Inna ta biyota wayar tafadi daga hannuta.


*****
Washe gari cikin mayuwaci Hali Rasheed ya kasance, duk ya susuce, bini bini ya koma gidan can ko zaiga Batul amma wayam, ta bangaran Mom kuwa bai kuma tunkararta da zancen ba.
Agajiye likis ya dawo gidan, dakinsa ya nufa ya iske Mardiyya na kokarin shimfuda bedsheet, saurin rikonsa tayi ganin yana kokarin faduwa.
"Sweetie are you alright" ta fadi tana kokarin zaunar dashi kam sofa,
"Am not" ya fadi cikin murya kaman xai kuka.
Zama sukayi atare tace "plz ka gayamin matsalar ka na taimake ka, i hate seeing you like this"
Ajiyar zuciya ya sauke yanai lumshe ido, murya kasa kasa yace "Diyya ki gayamin gaskia meke tsakanin Abbanki da Mom".
Gabanta ne ya fadi, jin tambayar bambarakwai, "babu komai" ta fadi.
Gyara zama yayi ya xayyane mata komai dayaji suna fadi.
Mamaki sosai ya kamata wai abbanta da Mom so disgusting ma, yaushe ma Ummanta zata yadda hakan ta faru.
"Amm sweetie kana ganin akwai kamshin gaskia babanka is alive"
Yace "Am sure he is alive, babu dai wanda xai gayamin gaskia"
Ajiyar zuciya ta sauke tace "i have an idea".
Kallonta yayi.
Gabanta na faduwa, tana tsoron fadi mai easy way dazai gano gaskia, saidai ayyanda yake bazata iya jure ganin sa cikin bakin ciki ba dole ta fadi dabarar dake ranta, amma tasan hakan na iya barazanar da auranta.
Tace "sweetie kaje ka samu Umma, ita kadai ce tasan duk wata sirrin Mom, am sure zata gayama gaskia, idan har tace ma your Dad is dead you have to believe her, itace kadai hope dinmu yanxu"
Murmshi yayi hade da riko hannuta yace "Diyyah you are smart saidai Hajiya Safara is smarter than you, kema kinsan ko sama da kasa zata hade she wont say a word"
"I know she wont say a word, shiyasa zan fadima weak point dinta"
Mikewa yayi kadan daga shigidan da yayi yana kallon ta.
tace "hajiya safara nada matukar kishi marar mitsaltuwa, abu daya zaka gayamata she will blow out all abunda kakeson sani"
Bakinta takai kunnan sa tamai rada danima banji ba.
Yace "are you sure it will work ?
Tace "trust me"
Mikewa yayi tsaye yana fadin "i'll be back" ficewa yayi da axama.
Numfasawa tayi, tana fadin "Allah yasa ban ballo wa kaina ruwa ba".


Bai zarce ko ina ba sai gidan Hajiya Safara dake unguwar Rimi, horn yayi mai gate ya bude, karasawa ciki yayi yay parking motar.
Tunda daga window palon Hajiya Safara ta kyallarosa, Biebee dee mai aikinta ta kwallawa kira, da azama Biebee ta karaso hade da risina, "sirikina ya iso, maza dauko kayan sha da motsa baki ki kawo".
"Toh Hajiya" Biebee ta fadi hade da juyawa zuwa kitchen, sosai take tsoron Hajiya shiyasa komai take kaffakaffa.

Knocking yayi ta karasa ta bude mai kofar, fuskar ta dauke da fara'a
"Auta momy yau kaine da kanka" ta fadi tanai washe baki.
Gaida ta yayi fuska ba yabo ba fallasa sannan suka karasa kujera hade da zama.
"Ya mardiyya, hope dai tana lapia"
Kalau take, urgent magana ya kawoni" ya fadi atakaice.
Cikin hankalta da nutsuwa ta kasa kunne saura ransa.
"Umma ki gayamin gaskiA nasan kinsan komai, dagaske Babana na raye ?..
Dariya sosai ta fashe dashi tace "waya gayama shirman nan, toh idan ma mafarki kake ka farka, ubanka na karkashin kasa.
Murmushi yayi ya kalleta yace "rumour naji agari, nima ban yadda ba".
"Karma ka yadda, karya ce babban". Acewar Umma.
Hira kadan suka taba cike da wasa da dariya daga bisani ya mike xai wuce, taka mai tayi zuwa bakin kofar ya juyo yana fadin "Umma Allah ya sanya alheri fah".
Kallon rashin fahimta tamai
Yacigaba "Abban yaje can gidanmu sun dade suna hira da Mom, ashe soyyaya suke, kwanannan ma zasuyi aure" cike da farin ciki ya karasa xancen, bai jira cewar taba yayi gurin motar sa.
Daskakera Hajiya Safara tayi kaman kankara tsabar kidima da tashin hankali, jikinta har wani rawa ya dauka, hango Mom kadai take amatsayin kishiya, dafe kai tayi tsananin yadda kanta ke tsarawa, ita Fatima zatama zamba cikin aminci, sai yanxu tagane kallon da mijinta ke mata idan taxo gidan, bazai yuyuba, fatima kinyi kadan baki isa ba, duk azuciya take maganar.
Cikin zafin nama ta karasa da sauri inda Rasheed ke tsaya yana kokarin bude motar.
"Yana nan da ransa bai mutu ba" ta fadi cikin huci.
Fasa bude motar yayi yana kallonta, hannuta ya riko yace "Umma yana ina, plz ki gayamin"
Cike da baccin rai take magana.
"yana garin Kaduna, saidai bansan a ina yake ba, kaine kasan inda yake"...
Kallon rashin fahimta yayi mata.
Tace "yarinyar da Mom ta tarar a gida she is your sister, babanta shine mahaifinka"...
Rasheed kam ya gama rudewa, wace yarinyar take nufi badai Altine mai aikin suba.
Tacigaba "ranar daka fadi mata fatima ex wife dinka ce she was very devastated, fatan ta daya Allah yasa auratayya bai shiga tsakanin kuba"..
Iya gigita Rasheed yakai yama kasa gane wace Fatima take nufi,
Haunnsa ta rike gam tana fadin "yarinyar nan princess kanwar kace ta jini"
Wani mugun kara ya kwalla wanda gabadaya gidan saida ya amsa, cikin rawar jiki ya saki hannuta ya fada motar yaja ta afusace.
Dogon tsaki Hajiya Safara taja aranta tace "no i messes with my husband" afusace ta juya tayi cikin parlour, garara raf sukayi da Biebee dake rike da jug da ruwa, wani wawan mari Hajiya safara ta kai mata sannan ta wuce daki. Jikin rawar jiki biebee ta durkusa tsince glass daya fashe.

Gudu yake shararawa harya karaso gidan, ko parking motar bai iyayi dakyau ba, ya fito cike da kidema ya shiga gidan, Mardiyya ya iske zaune Palo, ko kallanta baiba ya fada dakin Mom agigice, kwance take kan gado ganin yadda ya faddo cikin dakin yasata razana hade da mike tsaye.
Durkusowa yayi gabanta, cikin muryar kuka da tuni ya sarke sa yace "Mom y, miyasa kika min karya babana ya mutu, wosrt part of it princess kanwatace, kinsani baki gayamin"
Wani mugun mari ta kwashe shi dashi, tace "ni nake maka karya, a gidan ubanwa ka jiyo labarin nan".
Bai damu da mari ba, yace "hajiya safara ta gayamin, kuma nasan datx the truth".
Gabanta ne yafadi jin ya ambaci Safara, lailai kuwa itace babu wanda yasan da hakan sai ita, amma kinci amanata safara, mu zuba nidake, duk azuci take magana.
Karyarta ta kare dole ta fadi mai gaskia ayita ta kare, dagosa tayi kan gadon sannan ta zauna gefen sa suna fuskanta juna.
"My boy kayi hakuri, i did all that to protect you, your father was cruel, he never appreciate us"
Kuka ta fashe dashi, hannuta ya riko "mom cigaba sai miya faru ?
Tsayar da kukan tayi tace "rabuwa yayi damu adalilin matar daya auro, Mahaifiyar so called princess, My boy d first day dana ganta yasa nayi kokarin tabar gidan cox banason past dinmu yazo yana hunting dinmu, plz stay away from her"
Kuka sosai ya fashe dashi yan hango fuskar Baba wai shine mahaifinsa, saidai halinsa da Mom ta fadi he isnt buying it a bit, babban tashin hankalinsa bai wuce na cewa Batul kanwar shice ba, bai taba jin sonta ba sai yanxu da yaji wai kanwar shice, wani irin sister love game da ita ke ratsa mai gangar jiki da zuciya.
Yace "Mom ki temake ni, Princess is missing, duk fadin kaduna na bincika ban ganta ba" ya fadi yana kuka, ido jajir.
Lallashi sa tahau yi tanai kara basa hakuri.
Karasa shigowa Mardiyya tayi da tuni tana tsaye bakin kofar, kuka take ta nufosa,
Mugun tsawa Mom ta daga mata hade da mikewa tsaye
"You have overstayed your welcome, pack your tinx ki barmin gidana"
Ko kallanta mardiyya batai ba tacigaba da takowa gurinsa, kafin ta kara taku daya tuni Mom tayi taku biyu uku takai mata gigitaccen marin da yayi baraxanar sanya jinin gabobin jikinta daskarewa.
Ihu ta saki tsabar raradi, kallon Rasheed tayi da bai san abunda ke faruwa ba, kuka kawai yake yana kiran sunan princess.....
[10:01PM, 5/26/2017] Xarah Bukar: 💖 *INA ZAN GANSHI*💖
Rubutawa


Please Login or Register in order to submit comment