Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ta iske hassan da husaini na alwala gindin rijiya, sai yusuf dan karaminsu dake zauna yana cin shinkafa da wake. Hajjo sai kokarin kankamta gurin murhu take.
Mik'a ta kumayi akaro na biyu, tace "Hajjo kin gama abincin kuwa, har wani jiri jiri nakeji tsabar yunwa"
"Dayake ga uwarki baiwa ko, dan ubanki kizo kice tunda ke na girkawa, yar kusun uwa" Hajjo ta fadi cike da bacci rai, bata ko kalle taba tadau lankar samirar tayi cikin daki.
Dariya Hassana ya fece dashi, aranshi yaji dadi yadda Hajjo tayi mata, "toh ayi dai mu gani ko sabulu xai daina kumfa, "
Harara Batul takai mai tasan sarai inda ya dosa, tsaki tayi tace "banza kawai, toh munyi da toka ma yayi kumfa, kuma wlh ka shiga taitayinka idan bakaso nayi kudi na manta ka kasan dai ni matar manya ce"
Dariya yayi "wazai kwashe ki badai ..
Katse mai xancen Hajjo tayi daga daki, tana fadin "baza ku wuce masallaci ba ko ?
"Zamu" husaini ya fadi hade da jan Hassan suka wuce, dan shi dama magana ce makiyinsa, idan kaga yayi doguwar magana toh da Baba ne.
Cize baki Batula tayi danba karamin shak'a tayi ba, akalla shekaru shida ne tsakanin ta da hassan amma ya mugun raina ta, yaro dan shekara sha biyu sai ki rantse dan arba'in ne yadda yake tsaro xance. kallon yusuf tayi da har yanxu ya kasa cinye yar lomar dake cikin kwanon, tace "Kai tashi amso min salad da tumatur gurin Baba"
Kafin yayi magana Hajjo ta fito, bazai jeba, "ajiye abinci ka wuce sallah" ba shiri ya karashe loman yayi waje. Ganin ba mafita yasa batul yin alwalar tayi sallah sannan ta zauna tsakar gida jiran ace ga nata abinci amma taji shuru.
Sallaman baba ne ya sata mike wa tsaye, ta amsa. "baba sannu da zuwa" ta fadi hade da amshe kwandon dake hannusa.
"Yauwa fatima, har kin dawo, ya makarantar ?
"Alhamdulilah"
Tabarma ta dauko ta shimfida ya zauna hade da shi mata albarka, itama zaman tayi tana kara mai sannu, baiyi mamakin abunda takeyii ba dan kuwa ta saba tarairayar sa, idan kuma halin nata ya motsa ko gaisuwa dakyar takeyi balle ta nuna su suka haifeta.
Fitowa da langar abincin Hajjo tayi, tamai sannu da zuwa sannan ta koma daki dauko furar dana dama mai, sannu baba" Batul ta kuma fadi akaro na biyar,
"Kinci abinci kuwa
Tace "a'a, dama kai nake jira Baba"
"Lailai kuwa kin cika yar baba, hada mata muci", ba shiri tahau zuba mai da yaji suka fara ci, Hajjo na fitowa tahau salati, dire furar tayi tahau Batul da dundun, "dan ubanki tashi nace, wannan abinci badake na dafaba, yar banxan yarinyar marar mutunci"
Murtuke wa batul tayi bata da alaman tashi,
Cikin sanyi muryarsa baba yace "waike Bareera ban hanaki zagin taba, baki san cewa wana bakin naki shine xai iya kaita ga halaka ba"
Hajjo kam ta kule "Malam ai dole nayi magana, yarinyan nan na ganina ina aiki ko sannu balle ta temakamin, nagama kuma dan batta kunya taxo ta baje tana ci".
"Ki dunga hakuri, Fatima ai yarinya ce komi tayi bai kamata ki hurar da ita da yunwa ba"
Toh" kawai hajjo tace ta koma daki ta zauna, tana jinsu suna hirar da dariya har sauran yaran suka shigo aka barke da hira.


***
Washe gari dakyar tasamu wata bakar doguwar riga ta sanya,yawanci yan atamfofin nata sun sha jiki, kunyar sasu take kar su Minal su raina ta, mayafi karamin ja ta dauko tayi rolling, fitowa tayi ta leka dakin Hajjjo ta iske tana sharar, tace "hajjo saina dawo"
Zuciyar hajjo fawas ta amsa mata da
Toh batula, Allah ya temaka, ki dawo dawuri dai"
"Amin" butula tace tana murmushi, shiyasa takeson Hajjo sam bata da riko kaman ba jiya ta kama d'addaurewa ba.

Zaure sukayi kicibis da Baba xai shigo ta gaidasa, yace da ita ta koma tasanya hijabi dan shigar ta tayau zam bata mai ba, ba musu ta sanyo hijab bayan ta saka mayafin cikim jaka, ta fito ta amshi kudin mota ta fice.
Bata sha wuyaba tasamu marwa ya kaita poly, da sauri ta wuce girl toilet ta cire hijab din tasaka mayafin sannan ta wuce zuwa hall, already su Minal sun kama mata sit, zama tayi tana wani shan kamshi ana gamawa suka fito da niyya wucewa gida kasancewar lec guda garesu.
Minal tace "Fatima yaushe zamu je gaida cousin dinki ?
Yatsine fuska tayi tace "very soon, baya gari ya raka mamansa Abuja checkup suna dawowa zamu je"
Allah ya kaimu" Minal ta fadi.
Billy tace "y not muje gidan ku"
Gaban ta ne ya fadi, aita gwamma ce su mata duka akan suje gidansu, mazewa tayi tace "okay muje, saidai Daddy baya gari yaje paris"
"Ba damuwa" acewar Billy.
motar Minal suka shige, billy abaya, Batul ta babbak'e agaba suka kama hanya, tunanin karya da zatayi kawai take, tafiya mai dan nisa sukayi har suka iso Kawo, billy tace" Minal shigar mu layin can na siyi salad da tumatur mai kyau"
"Ki bari akwai wani can gaba"
"Nidai muje can din, customer din mama ne, can take turamu siyo mata"
"Tonaji", lemcy tace hade dayin ribas, Batul jiki duk ya mutu, Allah yaaa ba gurin Baba take nufiba, bata gama tsorata ba saida Billy ta nuna Baba dake nesa tana fadin karasa teburinsa....
[10:00PM, 5/26/2017] Xarah Bukar: 💖 *INA ZAN GANSHI*💖
Rubutawa
Xarah Bukar

®NWA

xarahbukar.wordpress.com

16 to 20

Tashin hankali ne ya dabaibaye ta, tayi saurin shingid'e cikin kujerar hade da janyo mayafi ta rufe fuskarta.
"Bba ina wuni" suka gaida shi, ya amsa ciki da fara'a, dan kuwa ya taba ganin Billy. Salad da tumatir masu kyau ta siya ta bashi kudinsa, ba yadda batayi ba yabar canjin yak'iya yabata kudinta, sai sannan Minal ta tab'ota "bazaki siyi komai ba'. banxa tayi kaman bataji ba. Godiya suka ma Baba kanan suka bar gun, Baba yaso ya gane kaman itace sai kuma yayi saurin kawar da tunanin sanin cewa da hijab ta fita kuma ma ina Fatima ina yawo da manyan masu kudi haka.

Adan firgice ta yane mayafin fuskar ta, duban Minal tayi tace "kinsan mi ajiye ni nan, na msnta ashe mama ta aikeni chemist"
"Haba dai muje to" acewar Minal.
Cikin nuna damuwa tace "ku bari kawai, next tym sai kuzo, yanxu muna xuwa gida zatace na tsaya shad'anci a hanya".
"Eyya to ba komai, zaki gane gida daga nan" Minal ta fadi hade dayin parking
"Eh, gobe mu hadu skul, tnx"
Da sauri ta fito daga motan gudun karsu tsayar ta, Billy tai mata bye hade da dawowa gaba, itadai har yanxu ba wani yadda tayi da Fatima ba.

Saida taga sunja gaba sannan ta sauke ajiyar xuciya, "yan durun uwa halan hauka nake na kaiku gidan mu, yadda kuke nema Rmd nima nemansa nake, dan kuwa dani ya dace, ina xan Ganshi ?" Ta fadi hade da waiga wa kaman yana kusa.
Marwa tagani ya nufota tayi sauri tarar sa, leko dakansa yayi da niyyan tambayan inda zata sukayi ido ihu, atare duk suka ja tsaki, inda tasan wanslan matsiyacin ne da bata tsayar dashi ba, amma ba yadda ta iya.
"Layin yan wanzan xaka kaini "
Bai saurare taba ya kunna marwan sa yayi gaba, ya gwammace ya k'ona mansa akan ya dauki fitsararar yarinyar nan, yana ji tana xurfa mai zagi bai tsaya ba yayi gaba abunsa. Dakya tasamu wani ya kaita gida sam ta mance da sauya hijab, tana sauka idon Baba akanta daga can nesa yana kallonta, mamaki sosai yayi ganinta da gyale kuma babu tantama itace yagani a mota yammatan nan, ransa ya bacci ba kad'an ba, haka ya shigo gidan da magrib, yaran na gaida sa ciki ciki ya amsa, ya kira hajjo sun dade suna wata mahimmaciyar magana daga bisani kuma ya fice, Butul kam ko ajikinta aganinta can maganar da suka sabayi sukeyi, tun ba yauwa ba zataga iyayen suna tattaunawa k'asak'asa wataran harda sharar kwalla sukeyi, itadai bata san masu ba. Kayan da zata sa gobe take gogewa da dutsan guga na gwarwashi tana gama ta hange su, ta dauko sauran fanta dinta da Minal ta siya mata ta sha rabi, hade da tande baki, arziki akwai dadi da yanxu dan jolly juice zata jika tasha. Yusuf ta kwallawa kira ta bawa sauran yasha.


***
Zaune suke a dinning suna breakfast, babu mai magana cikinsu tsabar yadda suke bawa table manners dinsa, shiya fara gamawa ya mike zuwa palo ya zauna yana latsar wayarsa, sanye yake da kananun kaya dasukayi matukar amsar sa, tana gamawa Altine mai aikinsu ta kira kwasar kayan gurin itama ta koma kusa garesa ta zauna. "My boy bazaka office ba, Mardiyya tacemin kwana biyu baka zuwa da wuri ?
Fuska murtuke yace "xanje" ba tare daya dago kallan taba.
"Easy my boy, da Mom dinka fa kake magana".
Shuru yayi kaman bazaiyi magana ba yace "i know, did i say sumthing bad"
"No, amma ai saika kalle ni ko ?
Dagowa yayi ya kalleta, sam bayason yin fara'a yanxu saita kawo mai xancen Mardiyya, bama wana ba so yake kawai yasan meke tsakaninta da Hajiya safara danya tabbata itace ke uxura mata.
Kwankwasa kofar palo ne ya katse masu hanzari, Altine taje ta bude hade da gaida mai shigowa.
Murmushi Rasheed ya saki ganin daddy malam, dan saurayi ne mai shekaru 26 daganin kayan jikinsa kasan ba wasu masu hali bane sai rufin asiri. Dogon tsaki momy taja bai damu ba ya duka kasa gaidata bata amsa sa, ya nufi Rasheed suka gaisa cike da fara'ar sannan ya zauna, it seems urgent magana zasuyi saidai Daddy malam yayi shuru ganin hararar da Mom ke aikama sa,
"Muje waje " abunda Rasheed ya fadi suka mike tsaye.
Ba karamin haushi Momy taji ba, idan bata manta ita ta kawo daddy malam amatsayin mai wanke mata mota da dadadewa, tama manta dashi abunda bata sani ba ashe suna tare da Boy dinta har ila yau, ba yadda bata raba suba, sunki rabuwa. Tsaki ta buga akaro na goma tana fadin "mi xaai da talaka".

Garden suka nufa suka zauna a sit for two, Daddy malam ya nisa yace "ya gajiya ?
Lumshe idanu rasheed yayi yace akwai "stressed fah, amma am enjoying it, kamin aikin dana saka ?
"eh nayi, komai it ready".
Sun dade suna tattaunawa daga bisani suka tashi, mukullin motarsa na aljihu suka shiga motar yaja yayi dropping Daddy malam sannan ya wuce office.

***
Cikin sauri tagama shirun ta tsaf na zuwa office, dukda tayi latti bai hanata tsantsarwa kwalliya ba, harta fita ta dawo dauka wani hadaddan farin hanky dake ajiye karkashin pilonta, dauka tayi tana kallon yadda akayi embroidery sunansa RMD cikin hanky din da golden thread, ya burgeta matika, bisa hancinta takai tana shakar kamshi mai dadi dake tashi sanan tasa cikin handbag dinta ta fito da sauri, dan kuwa ostrich take son tsayawa tsiya mai kodan burger da pizza ne.
Hajiya Safara ta iske palo sai Abba dake tsaye da alamu shima aiki xai wuce, gaidasu tayi aladabce hade da masu sallama kanan ta wuce.
Abba yace da hajiya safara, "kinga yarinyar nan wlh tafiki hankali, halina ta iyo"
Harara takai mai, tace "oho dai koma miye nina haifeta ba ita ta haifeni, marasa hankali saidai ka nema a adanginka"
Kwafa yayi hade da karkata hulansa, ya fice daga palon cike da haushin yadda matarsa bata girmamasa, kaman shi mai y'a 25years amma baa ganinsa da gemu, ko dayake ya kusa tufkar hanci, maganin Safara kadai xaiyi ya huta, kuma yasan ta inda xaibi ya huce haushi.


***

Tun 8am suke zaune hall jiran lecturer yaxo, shuru bai xoba har 9 yayi, class rep yayi announcing bazai samu daman zuwa ba, watse wa kowa yayi kafin 12 lecture, Suna zaune pavement Minal ta kawo shawara suje ostrich siyan snack kasancewar ba nisa da poly. Bayan sun isa Minal da billy suka fito daga motar banda Batul da ta rike kai bata da alamun fitowa, Minal tace "bazaki shiga ba"
"Kuje dai, headach ke damuna"
"Mi zaki ci"
Fari da ido tayi, dama abunda take jira kenan, rashi kudi yasata tayi respecting kanta ta zauna, murya can kasa tace koma ma, ki hada mun da coconut ice cream"
"No p" Minal tace taja hannu billy suka karasa ciki.

Zaman mintuna uku tayi cikin motar, Mardiyah ta fito daga bakery din rike da ledar ostrich, tun daga nesa Batul ta saki baki tana kallon ta, ba karamin burgeta matar tayi ba ga wani takunta na kasaita, bata gama sakin bakin ba taga ta karaso jikin motar rav4 dake parke agefenta,
hannu tasa cikin jakarta ta ciro mukullun motar saidai bata lura da farin hanky daya fado dagw cikin jakar ba ta shiga motar taja, da azama Batul ta fito daga motar tadau ka kafin tayi taku daya zuwa uku dan mika mata tuni Mardiya taja motar da axama tayi gaba, Allah sarki ko sauri mi take, Batul ta fada tanai karewa hanky din kallo wani kamshi mai dadi ke fita daga jikinsa, warware wa tayi taga embroidery din RmD jiki kaman marar gaskia tahau ware idanu, ji take tamkar amafarki, wata mata ce wannan tahau mamaki, ita kam gaba ta kaita gobara titi jos, komawa motar tayi da sauri ta zauna ganinsu su Minal sun fito.
"Sannu kinsha zama" Billy ta fadi.
Minal ta mika mata nata ledar, ba kunya ta amsa ko godiya babu. Suna isa makaranta refreshment centre suka nufa suka zaman ci, kadan kadai Batul ta tsakura taci tabar sauran da niyyan kaiwa gida yin bagu.


***
Bata daddara ta nufo office dinsa rike da ledar ta, tura kofar yayi daidai da budewa xai fito, kawunan su sukaci karo, "auchh" ya fadi hade da matsawa baya yana mata kallon sama da kasa, tsabar rudu ko nata azaban bata jiba tahau mai sannu hade da kai hannunta gurin, "dan Allah kayi hakuri basan kana gurin ba"
Hannuta ya matsar gefe, fuska daure yace "Mardiyya ban hanaki shiko min office ba?
Amaraice tace "am sorry, dama breakfast na kawo ma" ledar ta mika mai.
Amsa yayi yace "thank you" ya fice daga office din.
Ajiyar zuciya ta sauke, ta rasa mai xatayi ya burge sa, duk gayun ta da kyan ta bai dadarasa ba, kallon jikinta ta tayi babu abun less than 100k ajikinta, sarkar wuyarta ma ta Gold ce but still abanza harara a duhu.
Ficewa tayi daga office din ta iske Charles zaune a desk dinsa yana cin abunda ke cikin ledar, takaici ne yakamata kaman tayi kuka, wato bazai ciba shine yabawa secretary dinsa, kwafa tayi ta wuce yana gaidata ma bata amsa ba.


Bayan sun gama lecture ba yadda su Minal basuyi da Batul su ajiye ta gida ba taki fir acewarta wani research xatai a library, basu kawo komai aransu ba suka wuce abunsu sannan itama ta fito waje neman abin hawa bayan kusan minti 20 da tafiyar su. Allah Allah take kadai taje gida tama su Hassan kwalelen ice cream.
Cikin sa'a kuwa tasamu Marwan daya ajiye wasu tayi azama shiga tun kafin ma tahau ciniki, tasan idan ta tsaya ciniki saita kai dare babu wanda ya dauke ta.
"Yammata drop ne ? Taji muryar sa tamkar saukar aradu a kunnuwanta, shi kansan baisan itace ta fado mai cikin Marwan ba.
Dogon tsakin dataja yasa shi kyallero fuskan ta ta mirrro, ba shiri kuwa ya tsayar da niyyar taryarwa, batare da yace uffan ba ya tsaya jiran saukar ta.
Ganin ice cream dinta xai narke kafin taje gida yasa ta sausata murya , "eh drop ne muje ko nawane xan baka, kudi ba matsala bane"
Hmm" yayi yaja Marwan suka kaman hanya da niyyan yimata rashin mutunci indai bata mai biya mai tsoka ba.
Wayarta ce tayi ringing, Dubawa tayi taga Minal ce, guntin tsaki taja gashi wayarta saida speaker akeji, idan kuma tace xata dauka zataji iskar hanya. Tsinkewa call din yayi ta kuma ringing.
"dan Marwa dan tsaya xan amsa kira"
Baice komai bw yayi parking daga gefe, kallonta yayi ta mirriro sai wani yatsine take sannan tadau call din.
"Fatima kin wuce ne ? Minal ta fadi daga dayan bangaran.
Cike da iyayi tace "eh, kuna tafiya Daddy yaxo dauka ta, ina cikin Jeep dinsa yanxu"
"Eyya Daddy ya dawo kenan?
Rike baki Batul tayi shataf ta manta tace masu yana paris, mazewa tayi tace "yau yadawo, daga Airport yaxo dauka na"
"Okay, ina gaida shi, sai mun hadu gobe"
Bye" ta katse wayar hade da sauke ajiyar zuciya, Mamuda kam ya gama tsorota da yarinya mai babban suna, karya kiri kiri ba kunya balle tsoro Allah, gashi kuma ko ajikinta, bai gama mamaki ba saida yake ta ciro farin hanky daga jakarta tana shakar kamshi jiki hade da zuba murmushi. Idanuwa kawai ya zuba mata.
"Malam karka cinye ni man, ja muje" ta fadi tana harara sa, sai sannan ya dawo hayyacin sa, yakama kan kekensa sukayi gaba.
Baba ke tsaye baki titi da tulin tumatur da tarugu a kwando yafi mintuna 30 tsaye, akalla Marwa kusan bakwai sun wuce ba wanda ya kallesa yawanci dama basu fiya daukan masu kayan miyan ba acewarsu kar Marwan su yayi datti, hango Marwan da yayi yana tohowa yasashi adduaa Allah yasa ya daukesa.
"yammata saidai kiyi hakuri, ga wani tsoho can dole na daukesa" Mamuda ya fadi
"Bangane ba, drop fah na dauka kuma kudi xan baka ba kyauta ba.
"Nasani karki manta kudi naki ne, amma Marwan nawane, kina iya sauka kibin rabin kudina"
Tsaki taja, "matsiyaci dai baiji dadi rayuwa ba"
Bai tanka ba, ya tsaya daidai ina Baba ke tsaye, ya fito yana "sannu Baba" hade da daukar gwandan tarugu yasa kan sit kusa da ita, afusace ta fito daga Marwan tana fadin "waikai wane irin wawane, zaka batamin jiki da taruugu..." Makoshinta xancen ya makale, ganin Baba agefe yana kallonta, "baba ina wuni" ta fadi tana yak'e.
Ciki ya amsa fuska daure inda gayamai akai bazai yadda yar cikinsa ke zubar da kimar ta hakaba, Mamuda kam bai kawo komai aransaba atunaninsa kawai ta gaida Baba ne amatsayin girmama babba.
"Baba muje" ya fadi bayan ya saka dayan kwando, su biyu da Baba agaba, sai Batul abaya da ta rukub'e, tsoronta daya kar Baba ya mata fada gaban matsiyacin nan.
[10:00PM, 5/26/2017] Xarah Bukar: 💖 *INA ZAN GANSHI*💖
Rubutawa
Xarah Bukar

®NWA

xarahbukar.wordpress.com

26 - 30

K'ashe gari bataje makaranta ba, fuskarta gabad'aya kumbure tsabar kuka, tana jiyo Hajjo da k'annan ta a tsakar gida suna hira taki fitowa, ga uban yunwa da takeji tun abinci jiya bata latsawa bakinta komai ba har ila yau da sakaliya tayi. Wayarta dake kashe ta kunna ta kira wani saurayinta shehu da tuni ta dade da jefasa a k'wandon shara, matashi ne irin masu son aci duniya, Baban sa mai kudi ne sosai, yana son Batul saidai son jiki irin nasa yasa Batul bata son basa fuska, bugu daya ya dauka tamkar jira yake, kirarin daya saba mata yafara tuni ta dagatar dashi, tacemai lailai yaxo bayan magrib akwai muhimmaciyar magana da takeson yi dashi, sannan kuma wen coming yaxo mata kayan dadi, naam yayi da bukatun ta cike da jin dadin kota sauya shawara game dashi.
Kaste wayan tayi taja jiki zuwa bangon dakin ta shingid'e.
Baba ke zaune daga gefen teburin kayan miyansa yana alwala, Mamuda ya karaso da Marwan sa ya faka gefe ya fito suka kara gaisawa da Baba, bai jima da bari gurin ba. dayar butar dake cike da ruwa ya janyo yayi alwara sannan suka mike zuwa masallaci dake gaba dasu kadan.
Sadaf ta fito daga dakin rike da siliwas dinta a hannu, Hajjo ke sallah tsarkar gidan, ta tako ahankali ta bayanta tayi waje da azama, ajiyar zuciya ta sauke ganin babu kowa rumfar Baba, waigawa tayi ba alamun motar Shehu sai ganinsa tayi da kafarsa yana tunkaro ta hannusa rike da bakar leda.
"Miye haka zaka zomin da kafa, ina motar" ta fadi tana karasawa garesa.
Dariya yayi.
"Popcy na yanani daukan mota saboda reckless driving danakeyi, mashin ma naso zuwa dashi"
Harara takai mai, "Allah kiyaye kazo gurina da mashin, ai aji down kenan, yanzu dai miye a ledar ?
Daf da ita ya matso, yanai kai mata wani shu'umin kallo, yace "Tukun nadai, , nifa duk kin hargitsa min kwakwalla, wace magana zaki gayamin ?
Ja da baya tayi kadan tanai mai kallon bansan haka sannan tace "Shehu temako zakamin, gobe xan kawo frnds dina gidanku su kanga amatsayin wani cousin dina"
Kallon rashin fahimta yayi mata, waye cousin dinki, ya sunan shi
"I dont know, nasan dai Rmd ake cemai, i want you to act like him idan mukazo"
Galala yake kallon ta, baiyi mamaki abunda takeso yayi ba, dan kuwa yasan halinta sarai, farkon haduwan su ba yadda bata jifan shi da karya, daya gano gidansu ne yasata saduda ta koma real Batulan ta, yanxu kuma ba mamaki wata bomb take shirin ajiyewa.
"Okay ba matsala, saikun zo din, amma nikuma mai zan samu in return, kinsan dai gwamnati ta hana aikin banza" cikin zolaya ya fadi yana kai hannu zai rikota, batare da ya kai hannusa ba ta warce ledar zatayi gaba, saurin shawon gabanta yayi yana fadin "Batula babu kodan kiss" kiris yarage yakai mata kiss tayi saurin kawar da kanta gefe sukayi ido hudu da Baba da Mamuda dake tsaye suna kallonsu. Rai bace Baba nufeta yana cewa "mia kikeyi da yaron nan, ban hanaki haduwa dashi ba"
Jiki na rawa tace "dama assignment zaimin"
"karya kike" Baba yafadi yana kallon shehu da tuni yasha jinin jikinsa, "uban mi ya kawo nan ?
Shehu kam be boye komai ba ya zayyane wa Baba abunda ya kawo shi, salati baba ya saki, wana wace irin yarinyace, shi Rmb yake kowa, wayene, ina kika sanshi ?
Tsuru tayi tana kokarin boye ledar abayanta, warcewa baba yayi ya bude yaga bankararriya kazar yahuza, innalilahi kadai yake ambata ya mikawa shehu leda hade da korarsa, fashewa da kuka tayi ta ruga cikin gida, Mamuda kam kasa magana yayi, kila idan aka duba ransa yafi na Baba bacci, tir kawai yake da hali irin na Batula, wani irin tsanar ta ke sokanshi a zuciya.
Kwafa Baba yayi yace "yarinyan nan ga karya da kwadayi, tsoro na daya karta fara sata da bin maza"
Nisawa Mamuda yayi yace, "ayi hakuri Baba, kuruciya ce zata gyara nan gaba"
"A'a dai mamuda, i dont tink fatima zata gyaru, aurar da ita xanyi gobe goban nan kafin tajaza min abun kunya, Yekuwa xa'ayi a masallaci maiso na aura masa"
"Baba ayi haka kuwa, kasan fah Batula mai kudi tasa ran aura kar talaka irina ya ansan tayin"
Kur Baba yayi yana kallonsa sannan yace "Mamuda na baka ita, dan Allah karka ce a'a kaine daidai da ita ba wasu can maisu kudi datasa agaba ba"
Gaban Mamuda ne ya fadi, shikam mai xaiyi da yarinyar nan, shuru yayi baice uffan ba banda nauyin da kimar tsohon da yake gani.
"Nasan baka sonta, dan Allah ka amsheta amatsayin Sadaqa na baka ita" baba ya fadi cikin murya kaman xaiyi kuka.
Kasa cewa Uffan Mamuda yayi har suka taka zuwa inda rumfar baba, Marwan sa yanufa ya zauna zaija ya kalli baba da shima kallonsa yake, jiki sanyaye yace "sai da safe"
Baba yace "indai ka karbi sadaqa ta gobe xan ganka karfe biyu agurin nan da shirin daurin aure, bai iya amsawa ba banda jan marwan da yayi ya wuce, jan marwan yake amma gabadaya hakalinsa ba ya jikinsa, xancesu da baba kemai yawo akai, jin awani wawa horn abayansa yasa shi dawowa hayyacinsa, parking yayi gefen hanya hade da fiddo wayarsa, dannawa yayi ya kira Daddy Malam, magana daya biyu sukayi sannan ya katse.
Bayan mituna goma da parking dinsa wata arniyar Jeep ta karaso gurin, da azama Daddy malam da wani suka fito daga ciki, gaida Mamuda sukayi, bai amsaba ya fito ya shiga cikin jeep din, dayan da suke tare yaja Marwan yayi gaba, Daddy Malam na gefe shike driving suka isa wani karamin gida mai shegen kyau.
Parking yayi suka fito atare, Daddy malam yace "Mamuda ne ko Rasheed" ya karasa maganar cikin

Please Login or Register in order to submit comment