Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels


*THE GOVERNOR'S WIFE*
...... MATAR GWAMNA






Bismillahir Rahmanir Rahim









Book one









*Godiya ta tabbata ga Allah wanda ya bani iko da kuma damar fara rubuta wannan labari. Ina addu'ar Allah ya sa yadda na fara lafiya na ƙare shi lafiya. Amin*



*wannan labari zai zo daga kashi na ɗaya zuwa kashi na uku Insha Allah. Na ɗaya zai zo a kyauta yayinda kashi na biyu da na uku zai zo na kuɗi a farashin 400*



*wannan labari ƙirƙirarre ne, idan yayi kamaceceniya ta wani fanni da rayuwar wani, wata ko wassu to bisa kuskure ne, ba ayi dan cin zarafin kowa ba*







01







(CONGO STATE is a fictional state in Nigeria. Jahar Congo ƙirƙirrerren Jaha ce a Nigeria)



*MAFARI*






Da ƙyar kyakykyawar matashiyar budurwa da ke riƙe da hannun Mahaifiyarta ke jan numfashi da dogon hancinta da ya zauna ɗas a tsakiyar fiskarta wanda ya ƙara ƙawata ma ta fiskar sosai. Iskar asibitin wanda ke gauraye da warin magunguna, allurai, jini, fitsari da sauran su shi ya ke yiwa mutum iso a duk lokacin da ya kusancin farfajiyar asibitin. Ansan Asibitoci da wari amma wannan warin na sa ya fita daban. Ko dan Asibitin ta gwamnati ne, oho. Rabonta da zuwa General Hospital Congo tun wani ciwo da Abba yai kusan shekaru biyar da su ka wuce.



Ba su jima da zama a wajen reception ba wata mata mai ɗauke da jaririya ta fito daga office ɗin Likita ta ce " wai Zainabu Inusa ta shiga"



Budurwar nan ta kama hannun mahaifiyarta su ka shige ofishin Likitan.




Lokacin da su ka shigo Likitan yana ta cike-cike a file ɗin su. Ba tareda ya ɗago ba ya ce "Malama Zainabu mi ya ke damunki?"



"Ciwon ciki"



Da sauri Likitan ya ɗago fiskarsa saboda yadda muryar budurwar ya shige shi, bama wannan ba, a file ɗinsu an rubuta Zainabu Inusa matar aure ce mai shekaru talatin da takwas wannan budurwa kuwa da ƙyar idan ta haura shekaru ashirin da ɗaya.

Lokacin da ya haɗa ido da budurwar sai da numfashin sa ya tsaya na ɗan wasu sakanni. Muryar da fiskar ba baƙon sa ba ne amma wannan ne karo na farko da ya ke ganin ta gaba da gaba.



"Mu ne wanda Dr Ubaydullah Gidaɗo ya turo" ta faɗa da siririyan muryarta me ratsa zuciyar mazaje.




"Masha Allah! ke ce ƙanwar mu kenan. ya jikin Umma?"



Sai da ta yi murmushi kafin ta amsa mi shi da cewa jikin Umma da sauƙi.

Duban Umma Dr Hassan yai ya ce "Umma tun yaushe kika fara jin ciwon cikin?"

Ido kawai Umman ta bishi da shi har ya gama maganar sannan ta maida dubanta ga 'yarta wacce ta fara ma ta bayani da yaren kurame. Dr Hassan ya sake baki yana kallon ikon Allah, sai yanzu ya gane dalilinta na iya sign language na kurame dan watarana a wani rahoto da ta naɗa ta yi amfani da shi wajen yiwa wani kurma tambayoyi. Abin ya burge mutane da dama amma yanzu da ya ke ganinta tana yiwa mahaifiyarta tafintan (interpreting) duk abinda ya ke faɗa sai tausayinta ya kama shi. Bayan ya gama sauraron bayanen ta ya ma ta tambayoyi sai ya rubuta mu su takardar scanning ya ce su je su yi su kawo ma sa ya gani.




Ba su suka bar Asibitin ba tun takwas saura minti biyar da su ka shigo har sai ƙarfe shaɗaya da minti biyu.

Lokacin da su ka fito daga Asibitin Keke daban-daban su ka hau saboda sauri da budurwar ke yi dan ta je wajen aiki yayinda Ummanta ta wuce gida.






Da gudu-gudu sauri-sauri ta shigo cikin ma'aikatar ta su, kai tsaye studio na biyu ta wuce domin yau ne za ta fara gabatar da sabon shiri da za a fara a tashar su. Ƙarfe shaɗaya da rabi saura minti huɗu ta gani lokacin da ta duba agogon hannun ta. Ta ja dogon numfashi kafin ta buɗe studio ta shiga.



Zaro ido waje ta yi ganin wanda ke zaune akan kujera tareda baƙon su na mako.



Gefen C Y ta tsaya wanda ke ta faman saita Camera dan fara ɗaukan shirin.




"C Y mi yake faruwa? ya na ga Iklimah a nan"



"Sorry Sweery, Oga ya chanja ki"




"Amma..."



"We are going live in one, two, three" C Y ya faɗa yana ɗagawa Iklimah hannu.



Iklimah ta yi wani fari da ido ta fara bayani kamar haka: ma su kallon mu kuna tareda gidan Talibijin na HILL TV, inda a dai-dai wannan lokaci mu ke gabatar mu ku da sabon shiri mai suna BAƘON MU wanda ni Iklimah Jibril zan gabatar. To a yau dai mun taho mu ku da babban baƙo. Jajirtaccen Ɗan kasuwa wanda duniya ta ke damawa da shi. Baƙon na mu dai shine Alhaji Isa Madara...




Juyawa ta yi cike da ɓacin rai ta bar cikin studio ɗin. Wannan wani irin walaƙanci ne Oga ya ma ta haka.

Kai tsaye ta wuce sama inda office ɗin Ogan su ya ke.



Gaisawa ta yi da Sakatariyar sa wata mata wacce za ta iya kaiwa shekaru Arba'in zuwa Arba'in da biyar.





"Madam Deborah Oga na nan?"



"Yana ciki" ta amsa tana cigaba da latsa na'urar computer da ke gaban ta.



Wucewa ta yi ciki zuciyar ta cike da jin haushin Ogan na su.

Office ne da ya fi kowanne girma a cikin kamfanin. Mamallakin office ɗin na zaune kan kujera yana duba wa su takardu.

A ɗan ƙaramin katako da aka ajiye a tsakiyar table da ke gaban sa an rubuta *MD Adamu Ribaɗo*



"Ina kwana Sir"



"Lafiya"



"Sir na ga Iklimah ta karɓi shirin BAƘON MU"



"Eh" ya faɗa ba tareda ya ɗago ya kalleta ba.



"Sir amma ni aka ba wa shirin nan, ranan Jummu'a kai da kan ka ka jaddada mini cewa ni zan fara shirin nan, ni na tsara tambayoyi, ni ne na kira Alhaji Isa Madara..."



"Kin zo da wuri?" Yai tambayar yana ɗago ma ta ƙananun idanun sa.





"Sir inada uzuri, na yiwa C Y text tun da sassafe, kuma na zo kafin lokaci ya cika"



"So?"



"Sir wannan ba adalci ba ne, kuma..."



"Fita" ya faɗa da ɗan ƙarfi.



Ranta a ɓace ta fice daga office ɗin da sauri. MD ya bi bayan ta da kallo yana ƙara yabawa da wannan halitta ta Asiya.



Kai tsaye office ɗin su ta wuce wanda su takwas ke amfani da shi. Mutum biyu ta tarar a wajen ta gaishe su kafin ta wuce kan madaidaicin desk ɗinta ta zauna, ta ajiye jaka da wayoyin ta sannan ta kifa kan ta a kan desk ɗin.



Idan mutum ya ce yana son ka ka ƙi shi shikenan sai ya zama abin damuwa. Tunda ta fara aiki a wannan waje MD ke takura ma ta.



"Da wani ƙaton tumbinsa a wajen" ta furta a fili tareda jan dogon tsaki...



Yinin ranan gaba ɗaya a hasale ta ke saboda abinda MD ya ma ta. Ita gani ta ke ma da gangan yai hakan, dama tun asali Iklimar ya ke so ta yi shirin ba ita ba. Dama ƙwalele ya ke son yi ma ta...



Kusan ƙarfe biyu na rana su ka fita ɗauko rahoto chan wani ƙauye. Faɗa ne ya ɓarke tsakanin manyan ƙabilu guda biyu da su ke wajen.

Sun samu sun tattara bayanai sannan sun yi hira da mutane da dama a ƙauyen kasancewa an ɗaura labarin ne life. Faɗa ne da ya faro daga ƙona gona guda ɗaya sai abin ya zamo rikicin ƙabilanci akayita ƙone-ƙone.



*"bayan Gwamnatin Jahar Congo ta turo jami'an tsaro zuwa wannan ƙauye, ƙura ta fara lafawa, yayinda iyayen da aka yi awun gaba da 'ya'yan su su ke cikin Alhini. Na tambayi wani jami'in tsaro wanda ya tabbatar mini da zaran sun gama bincike sun tabbatar babu hannun yaran nan guda biyar a sakawa gonar Malam Bala wuta za su sako su wa iyayen su. Muna fata dai wannan abin da ya faru zai tsaya a iya haka domin zaman lafiya ya fi zama ɗan Sarki. Ta ku ASIYA-SHAHIDA FARUQ BABA, tashar Hill TV"* ta ƙarasa maganar tana murmushinta mai shiga rai.



Ajiyar zuciya ta sauke lokacin da C Y ya ce cut. Ba yau ta fara kawo rahoto ba amma yau tunda ta fara ta ke jin ƙirjinta na mata nauyi. Ko dan ranta a ɓace ya ke oho. Ta ɗan ɗaura hannunta a ƙirji tana jin yadda ya ke bugawa da ƙarfi. Ikon Allah! Ko ranan da ta fara tsayuwa gaban camera ta kawo rahoto shekara ɗaya da ya wuce bata ji irin wannan tsoron ba. Lokacin da ta ke kallon camera ta sani tana fiskantar duniya ne, amma yau ji ta ke kamar mutum ɗaya ta ke fuskanta, kamar wannan mutumin da ke kallonta koma wanene idonsa yana ma ta nauyi, ya saka ma ta tsoro, ya kassara duk wani ƙwarin gwiwa da ta ke da shi.

Za ka fahimci halin da ta shiga ne kawai idan har ka tuna yadda ka ke ji idan wani mutum da ka ke tsananin jin kunya ya zuba maka ido. Kana jin idon sa na yawo a ko'ina na jikin ka har hakan ya saka ma ka kasala har ma ka kasa iya aiwatar da komai, idan ma kana wani abu to ka dinga kuskure kenan.

To ko dai Ubayd yana kallon news ɗin nan ne? Ta tambayi kanta.





"You Ok?" C Y ya fargar da ita daga tunanin da ta ke yi



Ta gyaɗa ma sa kai tana murmushi.



"Ko dai saboda abinda MD ya miki ne? Yau gaba ɗaya kin yi wani iri. Babu wani spark lokacin da ki ke camera"

Yana maganar yana lanƙwasa doguwar tripod da aka ɗaura camera a kai.



"Ban san mi ya ke damuna ba, its like kamar mutumin da na ke jin kunya yana kallon program ɗin nan. I'm feeling his eyes all over me"



"Ba ma her ba, his eyes. Lallai Aseey, ko kin yi sabon crush ne" C Y ya faɗa yana dariya.





Ba yau Ubayd ya fara ganin report ɗinta ba. Infact akwai ranan da ya ke wajen ma ta ke ba da rahoto a gaban camera ɗin kuma bata taɓa jin irin haka ba. Idan ba Ubayd ba waye? Certainly not Umma da Abba saboda su kam tun ma kafin ta fara aikin sun kasance confidante ɗinta. Ta iya tuna ranan da aka ƙara mata matsayi ta zama field reporter sai da ta kira suka boosting confidence ɗinta kafin ta fara aikin.

Idan ba Ubayd ba idan ba Abba da Umma ba, to WAYE? Ta faɗa tana kallon motar su da su C Y ke faman saka kayan aikin su ciki...







***





GOVERNMENT OFFICE, CONGO STATE,













dif...dif...dif... ƙarar da yatsar sa ke bayarwa kenan lokacin da ya ke buga table ɗin gabansa da yatsarsa manuniya. Tunda aka fara rahoton ya ke kallo bai ɗauke idon sa ba sai da mai ba da rahoton ta faɗi sunan ta sannan aka ɗauke wajen zuwa announcer da ya ke chan studio yana ƙara commenting akan abinda ya faru a ƙauyen.

Ya bibiyi labarin ne saboda shine abu na farko mai mahimmanci da ya aiwatar a wannan shekara wanda har an kusa cin rabi cikin ta.

Mutane dayawa kallon hoto su ke ma sa. It has being a challenge lokacin da aka kira shi da gaggawa aka sanar da shi faɗan daya taso a ƙauyen Kayal ɗin. Gwamna baya ƙasar dan haka shine ya ke da damar ba da umurni a aiwatar da duk abinda ya dace gameda matsalar.

Tuni ya rattaba hannu a takarda wajen tura jami'an tsaro ƙauyen domin daidaiton lamurra a wajen. Ya ji daɗi da reporter ɗin ta yabawa Gwamna duk da dai shi da yai aikin ba Gwamna ba ne, da alama ko dai ta manta cewa Gwamna baya gari ko kuma dai ta furta Gwamna ne a matsayinsa na wakilin Gwamna ɗin.

Gidan Talabijin na HILL TV ba ta Gwamnati ba ce shiyasa ya damu da ganin rahoton daga tashar maimakon CONGO NEWS wacce ta ke gidan Talabijin na gwamnati ba lallai a yaɓawa Gwamnati baƙin fenti ba idan har ba su yi abinda ya dace ba sai ma ayi ƙoƙarin kare su.



Bai ida wannan tunanin ba wayar sa ta hau ringing. Mr Governor ya gani ɓaro-ɓaro a screen ɗin. Da sallama ya amsa wayar cikin muryarsa mai sanyi.

Daga ɓangaren Gwamna kuwa ko amsa sallamar bai yi ba ya ce ma sa maganan Albashi da zai sa hannu akai ya bari sai ya dawo tukunna.



Deputy Governor ya ce "Mr Governor nan da kwana shida fa kenan "



"To mutuwa za su yi kafin kwana shidan?"



Bai ce mishi komai ba har ya gama magana ya kashe kiran.

Yayi tunanin ya kira ne domin yai ma sa magana akan faɗan da aka yi a ƙauyen Kayal may be ma ya yaba ma sa akan ƙoƙarin da yai wajen daƙile faɗan da wuri amma shi damuwar shi kada ya saka hannu a bawa mutane Albashinsu har sai ya dawo. Yau Albashin ya shigo daga gwamnatin tarayya, kwanan wata ya kama ashirin da bakwai idan aka ƙara kwana shida zai zama uku ga wani watan kenan, mutane za su ji jiki.

Minene amfaninsa idan har a matsayinsa na mataimakin Gwamna ba zai iya aiwatar da komai na cigaban al'umma ba idan Gwamna baya nan. Ya tabbata kenan shi hoto ne.







***







Lokacin da Asiya su ka koma office har anfara kiraye-kirayen sallar Maghriba. Tana shiga office ɗin su aka sanar da ita saƙon MD da ya ke nemanta. A gajiye ta wuce office ɗinsa, ta sani ƙorafi ne zai yi ba komai ba. Tunda a wajensa kullum ba ta iya aiki ba.



"Miye matsalar ki ne Asiya?. Today's report was full of crap, sati biyu Gwamna baya gari amma kina ta faɗin Mai girma Gwamna ya turo jami'ai, Mai girma Gwamna ya damu da talakawansa. Give credit to whom credit belongs. Kina ganin da Gwamna Saminu Bacci ne zai tura jami'an tsaro cikin ƙanƙanin lokaci haka? I'm dissappointed in you"



Ita kwata-kwata ta manta da cewa Gwamna baya ƙasar to ko yana nan ai Deputy Governor hoto ne. Ba abinda ta taɓa jin ance yayi sai shegen yin ado kaman mace. Indai SSK ne ko mace sai albarka wajen iya ado.



Chief Editor na su da ke zaune a office ɗin ya kalli Asiya ya ce " miya faru na ga rahoton ki na yau ba wani armashi, ba ki da lafiya ne?"



"no Sir, Ummata ce ba lafiya" Asiya ta faɗa ranta a ɓace.



"Allah ya bata lafiya"



Ta amsa ma sa da Amin. Da hannu ya ma ta nuni da ta fita daga office ɗin. Bayan ta fita Chief Editor ya kalli MD ya ce " mutumina ka mata a hankali. The girl is good ba wanda ya fi ƙarfin kuskure"



"Idan har bama nunawa jama'a goodness na Mataimakin Gwamna kullum kallon hoto za a dinga ma sa. Wallahi da shine Gwamna da jahar nan ta fi haka cigaba cikin shekaru ukun nan. S S Kachallah mutum ne da ya san darajan ɗan Adam, he's a man of vision and mission"



"Ni zan gaya maka halin Prof Kachallah tunda ya koyar dani lokacin ina Masters ..." daga nan su ka buge da hiran mataimakin Gwamnan.



Asiya na fita daga office ɗin MD ƙasa ta koma wajen office ɗin su ta ɗau jakarta ta fito. Wani mahaukacin yunwa ke cinta ga gajiya a haka tafito daga farfajiyar gidan Talabijin ɗin. Da Ubayd na gari da shi za ta kira ya zo ya ɗauketa amma yanzu sai dai ta nemi abin hawa. Tana tsaye C Y ya fito da tsohuwar baƙar roba-roba ɗin sa.



"Ke kalar mota ce da na miki lift zuwa gida" ga faɗa yana dariya.



"Ƙaniyarka C Y, kana nufin tafiya za ka yi ka barni kenan"



Ɗan dawowa yai da baya ta hau mashin ɗin sannan ya ja suka tafi. Suna tafiyan suna taɗi saboda Clement Yohanna (C Y) akwai surutu shima kamar Asiyar shiyasa ma tasu ta zo ɗaya.



A ƙofar gidan su ya sauketa yana faɗin ta gaida ma sa da Umma.

Da sallama ta shiga gidan na su, Inna Yaha na faman jan ruwa a rijiya amma ba ta amsa sallamar ba. Ko ba ta leƙa kitchen ba ta san sai yanzu za'a ɗaura abincin dare ko kuma yanzu aka fara girkin.



Sannu da aiki ta mata duk da ta san ba amsawa za ta yi ba. Wucewa ta yi ɗakin Ummanta wadda shine ɗaki na biyu cikin ɗakuna uku da su ke jere waje guda. A kan sallaya ta samu Umman ta idar da sallah tana jan carbi, ta san ba za ta amsa gaisuwarta ba har sai ta gama azkar ɗinta shiyasa ma ta wuce wajen wardrobe ta buɗe ta fito da wata doguwar riga mai laushi, rigar guntun hannu gareta. Kayan jikinta ta cire ta saka doguwar rigan. Lokacin da ta zauna bakin gado tana naɗe wandon jeans ɗin da ta cire ne Umma ta fara mata magana da yaren Kurame inda ta ke tambayarta ya aiki, obviously ta ga rahoton da Asiyan ta kawo ɗazu a TV. Itama Asiyan ya jiki ta mata tareda tambayarta ko ta sha magani.



Ƙarfe bakwai da rabi da minti takwas bayan ta idar da sallan Isha Cornflakes ta haɗa da madara ta fara sha tanayi tana danna wayarta. Kiran Ubayd ne ya shigo wayarta amma har ta katse ba ta ɗauka ba saima tsaki da ta yi. Bayan ya jera kira biyu ba a ɗauka ba sai a na ukun ta ɗauka amma ba ta yi magana ba.

"My Aseeya" ya faɗa da murya mai sanyi.

Tasirin da sunan yai ma ta ne ya sa ta yin guntun murmushi.



"Tuba na ke ranki shi daɗe. Na san na yi laifi amma a bani dama na faɗi uzuri na"

Still shiru ba ta ce komai ba



"Mine kina ji na?"



"Mine"



Asiya ta ɗan jinginar da kanta jikin gadon Umma sannan ta ce "ni mi zan ce tunda Matan Lagos sun ɗauke mun kai. Yau tun da sassafe da muka yi waya ba ka sake waiwaya na ba sai yanzu. Na san ka kalli report ɗina na yau amma ko ka kira ka tambayi lafiyata, you dont even care ko na dawo lafiya ko ban dawo ba, kawai kai..." haka ta yi ta rantings har sai da ta gaji da kanta ta yi shiru, a lokacin ne kuma Ubayd ya samu damar lallaɓata dan ya san halin kayan sa indai tana kwarwa to ba a katseta har sai ta gama.

Bayan ta karɓi haƙurin sa ne suka bige da hiran masoya ba ta ma ji shigowar ƙaninta Aliyu ba sai kawai gani tayi ya ɗauke kofin cornflakes da ke gabanta ya fara sha. Tana ma sa magana da hannu amma inaa bai kulata ba sai ya ma koma gefe ya shanye cornflakes ɗin tas.

Bayan ya gama kuwa ya dangwarar mata da kofi a wajen yai gaba. Shigowan Umma ɗakin ne ya sa ta yi sallama da Ubayd akan za ta kirashi anjima.

Da hannu Umma ta gaya ma ta cewa ta je ta samu Abbansu a falo yana nemanta.

Sanda za ta wuce falon Abban ta kula da Inna Yaha da ke ta kwaran-kwaran a kitchen tana rabon abinci, babu wuta kuma torchlight da ta ke amfani da shi ya dafe ba haske sosai. Ba ta taɓa gajiya da mamakin halin Inna Yaha.



Asiya ta yi sallama bakin ƙofar falon Abba. Abba ya ce ta shigo.

Abba dattijone da kallo ɗaya zaka ma sa ka san ya doki shekaru sittin da biyu zuwa da biyar. Fari ne sosai a lokacin ƙuruciya amma yanzu ya fara dafewa, fiskarshi da kanshi yana yalwacce da gashi wanda kusan ya riga ya zama fari gaba ɗaya sai tsilli-tsillin baƙi da ba za a rasa ba.



Bayan ta gaisheshi ne ya ke tambayarta gameda ƙauyen da su ka je yau ɗauko rahoto. Bayan sun yi alhinin abinda ya faru tare ya sanar da ita musabbabin kiranta da yai. Magana ce akan admission da ƙaninta ya samu a Congo University wanda ya dage akan ba zai zauna a hostel ba sai dai ya dinga jeka ka dawo, shawaran Asiya ya tambaya ko dai ya siya ma sa babur kaman yadda Habib ɗin ya buƙata ne?.



Abba ya jima da retire har yanzu kuɗin pension ɗin sa su ke lallaɓawa. Ba dan Allah yayi ita da Umma suna sana'a ba da abubuwan ba za su zo da sauƙi ba. Ubayd ma yana nasa ƙoƙari akan mahaifinsa sosai.

Bikinta da na Faty da za ayi Abba ke yiwa taru dan haka maganar siyan Babur bai taso ba. Za ta yiwa Habib magana, gigin samartaka ke ɗibanshi yana ji yanzu ya gama sakandare zai shiga Jami'a.



Bayan ta bar wajen Abba ɗakin su ta koma inda Umma ke faman tura tuwon da aka miƙo ma ta. Sau ɗaya ta kalli tuwon ta kauda kai. Ga abinci ba za ayi da wuri ba gashi ba zai taɓa yin daɗi yadda ya kamata ba.

Kafin ta kwanta sai da su ka sake yin waya da Ubayd sannan ta kira Queen Bee su ka yi maganar Salon ɗin su...


*THE GOVERNOR'S WIFE*
...... MATAR GWAMNA....







*©Azizat Hamza*



wattpad Azi_zat





Bismillahir Rahmanir Rahim









Book one











02



***









A chan wani ƙaton gida da ke GRA wasu manyan mutane ne guda huɗu ke zaune a wani katafaren falo daya amsa sunan falo saboda girma da kuma irin kayan alatu da aka zuba a ciki.

Ɗaya daga cikin su wanda kusan shi za a kira da babban su ya kalli wani da ke sanye da farar shadda da farin hula ya ce "Kachallah kana ganin za mu samu abunda mu ke buƙata a wajen sa?"





Kachallah ya ce "inada

Please Login or Register in order to submit comment