Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

one minute kamin ki rashi plz” ya kalli faruk yace “mie last abunda da kaci jiya “? 

Sai a lokacin faruk yayi magana “cake ne da drinks” ” hannun wa yafito 

Kallon dinah yayi dake jingine jikin bango tana hawaye yace “ni na dauko da kaina” malik ya daga mishi kai “ok toh………” momi ta daga mishi hannun “no malik plz bai dace ka masa wannan tambayar yanxu ba” hannuwansa ya daga sama yana murmushi yace “am srri akwai abunda nake son sani shiyasa but na daina” 

Yana kaiwa nan ya nufi kofar fita momi ta rufa masa baya,

Suna fita dinah ta dawo kusa da faruk ta zauna cikin kuka tace ” wlh yaya na rantse da Allah bansa maka guba  ba wlh wlh yaya kuma bansan akwai ta acikiba “

Ajiyar zuciya ya sauke yace “haba dinah ya za aiyi kiyi haka dan Allah kibar wannan maganar kar wani yaji kinji”


Dinah tana kokarin magana wayarta tayi ringing, 

Faruk ya kalleta “dauki wayar mana” kai ta daga mishi tana share hawaye ta kara wayar a kunne “hello hello ” duo2 taji wayar ta katse 

bata bi ta kanta ba ta kalli faruk zatayi magana aka sake kira sai a lokacin ta duba bakuwar number ta gani

 tana kokarin dauka kiran ya katse ba tare da ta kalli faruk ba tace “ina zuwa yaya ” tashi tayi ta nufi kofar fita

Karo sukayi da dr dake kokrin shigowa da sauri ta kalleshi tace “am srri” 

kai kawai ya daga mata yana murmushi ta fice shi kuma ya shiga dakin momi na biye dashi, 

Saida tayi nisa da gurin sosai sannan ta shiga kiran number 

Kin shiga kiran yayi sai rubuto mata ake Number busy

Kamar zatayi kuka ta shiga magana da kanta “ni wlh ban yafe ba koma wanene yake son yimin shari kaine ma kake son kashe yayana ka lakamin kajamin matsifa”

 ta karasa maganar tana hawaye 

Zabura tayi jin message ya shigo wayarta da sauri ta buda 

            ” HI LOV

AI NA FADA MIKI KI KULA DA YAYANKI KIKA KI KUMA BANI NASAWA YAYANKI GUBA BA BUT IN KINA SON SANIN WANDA YASA MASA KINA DA ADDRESS DINA AI “

                       #HUG

Jefar da wayar tayi har screen ya fashe wani irin tada hanta take tana hararar wayar kamar mai fada da zaki, 

Bata ankara ba taji an dafata da sauri ta waigo 

wata matace sanye da uniform din nurse da dan karamin hijab dinta,

Matar tace ” are u okay ” kai dinah ta daga mata “yes I’m fine ” “okay control urself nan asibiti ne” 

Nan ma kai dinah ta daga mata

Nurse din tayi murmushi

Dinah ta duka ta dauki wayar ta fice. 

Parking space ta nufa daidai inda tayi parking din motar ta

Tana isa ta bude ta shiga tasa mata key ta shiga driving 

Bata tsaya ko inaba sai gida tana yin parking ta fito uzurce ta nufi parlour, 

Tana shiga zulaiha da nafisa suka shiga tambayata jikin faruk gazarce ta amsa musu ta nufi stairs, 

Tana shiga dakinta ta wurgar da wayarta da pose

 ta nufi wardrobe ta bude ta dauko hijab brown color tasa kato ne daya rufe mata kafafu 

A hankali takai hannu ta dauko address card din ta aje karkashin kayanta, 

Ya juya da sauri tabar dakin 

Downstairs ta nufa tana kawo wa parlor zulaiha ta tare ta da sauri “plz dinah nima zanje asibitin dan naga jikin faruk “

Harara dinah ta watsa mata tace ” ai kinsan ba lokacin ganin marasa lafiya bane yanzu tunda kinsan dokokin uduth basai an fada miki ba ” 

Tana kaiwa nan ta  bata jira mie zata ceba ta ratsa gefenta ta fice

Tana fita ta ta nufi motarta ta shiga maigadi ya bude mata gate ta fice,

Gudu ta shiga yi kamar tashin hankali tana yi tana duba card din 

Bata tsagaita ba saida ta shigo mana babba sannan ta samu gefen t-t tayi parking 

Jingina tayi da kujerar motar tana sauke ajiyar zuciya

Ta dade a haka can kuma ta dago ta duba card din dake rike hannunta 

Sannan ta hau t-t wannan karon a hankali take driving 

Batayi nisa ba naga tayi parking kusa da wani mai kifi ta sauke glass din motarta ta masa sallama 

Bayan ya amsa tace ” malam dan Allah tambaya nake “?

” toh Allah yasa nasani ” ” dan Allah ina ne demon house yake”?

Ido ya tsura mata yayi shiru har saida ta sake maimaitawa sannan ya shiga mata kwanace ” wannan kwanar zakibi sai karya dama ki mike tsaye kamar zaki bar unguwar kusan karshe t-t zakiga wani katon gida da masu gate nan ne gidan zama kiga an rubuta shi wannan abun da kika tambayeni “

Busar da iskar bakinta tayi tace ” na gode malam” 

” babu komai Allah dai ya tsare ya kare adai bi ahankali” 

A hankali ta hau t-t 

ta bi hanyar da ya kwatanta mata cike da kasala take driving

Saida ta kusa kaiwa karshen t-t sannan ta fara hango gidan 

A hankali naji tana fadin ” hasbunallahu wani’imalwakil ” 

Tun kamin ta karasa gurin tayi parking tana kallon masu gadin gidan 

Daga ganinsu kasan kabilune kidin2 dasu kamar kajin turawa 

            in banda daya ke cikin shiga ta hausawa riga da wando na shadda

Ganin nayi ya taso ya nufo gurin da dinah tayi parking 

Tun kamin ya karaso dinah karance2 addu o i kawai take intayi wannan tayi wannan 

Yana karaso ya kwankwasa glass din motar a hankali cike da tsoro ta sauke shi tana addu’ah 

Murmushi yayi yace ” hajiya ki karasa ciki munsan da zuwanki” bai jira mie zata ceba ba juya ya koma inda ya fito


Saida ta bawa Allah zabi sannan ta sawa motarta key ta nufi gidan 

Tana isa suka bude mata gate cike da tsoro ta kunna kai cikin gidan 

Wani irin katon gidane da ya kusa rabin wata karamar unguwa 

Dinah sai rabon ido take har ta hango parking space 

Bayan tayi parking ta dade cikin motar sannan ta fito ta jingina jikin motar tana karewa gidan kallon 

Kamar daga sama taji ana mata magana ” this way miss ” 

Razana tayi lokacin da ta kalleshi wani katon mutun ne cikin suit yana nuna mata hanya kai ta daga mishi ” ohhh oook….” 

Ya wuce gaba ta rufa masa baya zuciyar ta sai bugawa take kamar zata fito

Saida ta bawa Allah zabi sannan ta sawa motarta key ta nufi gidan 

Tana isa suka bude mata gate cike da tsoro ta kunna kai cikin gidan 

Wani irin katon gidane da ya kusa rabin wata karamar unguwa 

Dinah sai rabon ido take har ta hango parking space 

Bayan tayi parking ta dade cikin motar sannan ta fito ta jingina jikin motar tana karewa gidan kallon 

Kamar daga sama taji ana mata magana ” this way miss ” 

Razana tayi lokacin da ta kalleshi wani katon mutun ne cikin suit yana nuna mata hanya kai ta daga mishi ” ohhh oook….” 

Ya wuce gaba ta rufa masa baya zuciyar ta sai bugawa take kamar zata fito

Wata katuwar kofa ya nufa dinah ya biye dashi tana karanta addu’o i har suka shigo wani parlour da tsayawa fada muku yadda kyausa da tsarinsa yake bata lokaci ne 

Saida ya kusa kaiwa kashen parlour sannan naga ya dauki wata hanyar

 corridor ne yana gaba dinah na binye dashi sai leke leke take 

Har suka sake karya wata kwanar 


Tsoro dinah ta fara ji da sauri ta riko rigarsa kamar zatayi kuka tace ” plz don’t hurt me owk ”  ture mata hannun yayi ba tare da yace da ita komaiba ya cigaba da tafiyarsa 

Ita kuma kamar wadda aka cilasta ta rufa masa baya tana hawaye,

 har suka bullo wani katon garden da babu abunda babu ciki sai kukan tsuntsaye kakeji tana ganin ya tsaya ita ma ta tsaya sai rabon ido takeyi hawaye shanana a fuskarta 

Ta waiga nan ta waiga nan Har ta hango zaune saman kujera sanyi da dogon wando jean dark blue sai farar vest jikinshi ko ina Tattoo ne 

Wani katon Rattlesnake na gefensa yana cin anta

Ba shiri dinah ta saki wata irin kara ta juya zata bar gurin cikin zafin nama mutunen da ke kusa da ita ya fisgo hannunta ya rike gam

Dinah ta gagara tsayuwa saboda tsoro kafafunta suka kasa daukarta 

Zubewa tayi zaune still yana rike da hannunta 

A hankali ya Juyo ya kalleta yana murmushi  idonshi na shiga cikin tana ta kara sakin ihu 

tasowa naga yayi ya nufo ta yana dariya yace ” i knew it i knew it baby daman nasan wannan ranar zata zo the game is over “,



Ido dinah ta sarka masa tana hawaye har ya kawo kusa da ita.

Kallo daya yayiwa katon mutume ya sake ta 

Shi kuma yasa Hannu biu ya rikota ya tadata tsaye 

Yana murmushi yace “kina jin tsoro ko “?

Batace dashi komai ba sai kokarin tsayawar take itama

Dakar tayi tsaye da kafafuwanta

Kallon mutunen dake kusa da ita yayi yace ” i can go ” ya rika hannun dinah ya nufi wata kofar da ita. Cikin kasalalliya murya ta shiga masa magana “no plz gida zani” 

Juyowa yayi ya kalleta yana murmushi ” no no no dia ba yanzu ba ai kinsan zuwa kika dan kusan wasu abubuwa da suka shige miki duhu ko”

Girgixa masa kai tayi “nafasa wlh na fasa bana son sannin komai” 

Ido ya tsura mata sannan yace “ki kwantarda hankalinki babu abunda zamu miki kinji “?

Bai jira mai zatace ba yaja hannunta kamar wata karamar yarinya suka karasa shiga kofar.

 nan ma corridor ne babba mai jere da dakuna sunyi kusan minti 15 suna tafiya sannan suka bullo wani parlor mai kamada fada mutanene cike a cikin shi kusan mutun 20 yawan cinsu matasane suna zazzaune saman kujeru da alama meeting suke, 

Dinah saida ta kare musu kallo sannan ta fashe da kuka. 

Daya daga cikinsu ya kalleta fuska a hade yace ” gud job sanar da ita abunda take son sani kamin mu aiwatar da aikin mu” 

Kamar daman umarninsu yake jira yaja hannunta yabi wata hanyar da ita,

Sai kuka takeyi

Nan ma sun dade suna tafiya sannan naga ya tsaya bakin wata kofa ya bude ya shiga da ita,




Parlour ne madaidaici mai tsarin turawa. 

Zaunar da ita yayi saman wata kujera shi kuma ya zauna a kujerar dake facing din tata,

Ya dura kafafunsa saman center Table yana kare mata kallo 

Sunyi 10  minutes a haka sannan ya sarka mata murmushi yace ” dinah kenan kinzo sannin wa yake son kashe yayanki ko? kuma mie yasa nake bibiyarki ko”?

 Kai ta girgixa masa alamar a a.

Ya gyara zamansa yana dariya yace ” matukar kina son nabarki kije gida dole ne ki tambaye ni abunda kike son sani”

Hade yawu tayi da sauri tana maida numfashi ta shiga masa alama da hannun dan magana taki fita,

Daker ta furta masa “da gaske zaka bari naje gida”?

Kai ya daga mata “yes in kikayi abunda na fada miki ba”

Muryarta na rawa ta shiga jero masa tambayoyi ” waye kai mie yasa kake bina ya akayi kasan wasu abubuwa game dani kuma wayak…….. “

Hannun ya daga mata yace ” relax my lov one by one “

” ok ya akayi kasan ni da kuma wasu abubuwa game da ni kuma mie yasa kake bibiyata”?

” nasanki tun kina secondiry school a lokacin na ganki lokacin na fara son sosai dan ban taba jin son wata ba ya mace ba sai ke”,,


Dinah kamar zatayi kuka tace ” to mie yasa baka fada min ba kuma kake bina haka “?

       Ba tare da ya kalleta taba yace ” saboda kunciyarmu bata yarda Conductors suyi soyayya da wadda ba dan kungiyar ba”.

“Kuma nasan wasu abubuwa game da ke ne lokacin da nake bibiyar “

Cikin tsoro tace ” mie yasa kake bibiya ta”?

” saboda kungiyarmu nada bukatarki munyi duk wani abu da zamu iya dan ganin kinzo gare mu ba tare da kin kawo kanki ba amman abun yace tura. 

Duk dare mukan kira sunanki amman karfin addu’ar ki ya hana kijimu bare ki amsa da tuni mun gama dake”

Kallon rashin fahimta ta masa,

Yayi murmushi yace ” jininki akeso dinah kungiyarmu tace dole na kawo ki kuma tamana alkawura da yawa akanki

Nayi duk yadda zanyi ban samu damar kawoki ba shiyasa nasa wasu daga cikin members namu su suyi min aiki akanki “

Wani irin bugawa zuciyar dinah take idonta a k'afe tace ” mie yasa kungiyarku take son jinina kuma wa kasa suke maka aiki a kaina”?


 Tabe baki yayi yace ” zulaiha member ce a kungiyarmu murtala direban ku shima member ne wasu daga cikin students din makarantarku yan kungiyarmu ne su suke bamu kabari akanki da kuma duk abunda kikeyi wani lokacin kuma ta tsafin mu muke ganin abunda kikeyi .

Akwai kuma aljanin da muka hadaki dashi wadda shine yake aje miki wasika ta takarda in na rubuta in kuma sakon text ne na waya tanan nake aika miki shi”

Dinah tace ” har yanzu baka fada min mie yasa kungiyarku take son jini ba kuma mie yasa kake son kashe yayana”?

” dinah kungiyarmu kungiyace da in kana ciki dole ne karika bada wadda yafi kowa soyuwa aranka na bada mahaifiya ta na bada kanwata 

Yanzu kuma kungiyarmu ke takeso saboda irin son da nake miki “

” kuma nine naba zulaiha guba tasawa yayanki kuma nake miki dabo kamar aljani dan nasan dole ki nemie sanin wadda yake aikata miki irin wannan abun “……

” na kuma riga nasan duk lokacin da kika nemie sanin ko ni wanene dolene ki kawo kanki gurina kamar yadda kungiyarmu takeda bukata”



PLEASE VOTE
[11/16, 10:19 AM] Khadeeja Candy: Nuna kansa yayi yace “nine mataimakin shigaban wannan kungiyar a nan Nigeria abuja nake zama amman saboda son da nake miki yasa yana aka ginamin gida a nan sokoto kuma na tare  a nan dan na rika ganinki ” 

Hannayensa ya shiga nunu mata ” dubi rabin jikina ki gani dinah duk sunanki ne sai kuma na kungiyarmu ” 

Hawaye nabin fuskarta kamar fanfo tace ” mie yasa kai bazaka bada kanka ba anya kuwa kai kikanken musulmine kasan hukuncin wadda yake aikata wannan aiki a gurin Allah “?

Gyara zamansa yayi yana murmushi yace “ni musulmin ne sunana manir muktar mahaifiya ta ce kirsta na tashi a uku a can nasan wannan kungiyar na har na zama mataimakin shugaban “

Ta sowa yayi ya dawo kusa da ita ya rika fuskarta yace ” wlh ina sonki dinah fiye da tunaninki “


” bazan iya sadaukarda kaina bane saboda ni Conductor ne ko da na sadaukar ba zasu karba ba sai in na aikata laifi ko na…….”

shiru yayi kamar wadda ya tuna wani abu ya cige lips dinsa ya tsura mata ido. 

Ita ko sai hawaye take tana karanda addu’o’i a hankali 

Murmushi yayi ya bugar mata baki ” daina abunda kikeyi bana so ” 

Kamar shi take jira aiko ta kara karfin addu’ar tashi yayi tsaye yana dafe kansa ya juya mata baya  “ohhh dinah ki daina plz na fada miki bana so ko ” yi tayi kamar bata jishi ba ta cigaba da addu’o’inta 

Juyowa yayi fuskarsa a hade cikin daga murya yace ” dinah in baki daina ba zan daina ganin tausayinki fa kina bata mana aiki ”   yan rufe baki aka turo kofar 

Wani katon mutun ne ya.shigo sanyi da wata karuwar riga ja har kasa baki kirin dashi fuskarsa babu annuri 

Saida ya kare mata kallo sannan ya kalli manir din cike wane yare ya shiga magana dashi 

Shima manir din ya mayar masa cikin yaren sunayi suna kallonta can kuma maganar ta koma cikin fusata suke yinta

Ido dinah ta sakar musu tana ta addu’o’inta bata ankara ba taji wani irin mugun bugu a baki ,

Katon mutumen ne yakai matashi nan da nan bakinta sai jini 

Cikin fusata manir ya cigaba da magana dashi .duk da bansan mie suke fada ba amman daga gani kasan fada suke. 

Can kuma naji yace ” ok ” mutumen ya juya ya fice shi kuma ya kalli dinah tare da riko hannunta ” tashi muje ” tashi tayi cikin tsoro sai addu’ah take 

Sakin hannunta yayi ya watsa mata mari ta bayan hannu yace “nace miki ki daina bana so “,


Hannunta ya sake rokawa ya fisgeta da karfi suka bar dakin 

Wani gurin matsatsin corridor suka bi, 

Ya dade yana tafiya sannan ya shigo wani dakin da babu komai cikin sai jajayen kyalaye da kandir 

Tunda suka tamo hannya addu’ah dinah take saidai bata bari yagane ba, 

Zaunar da ita yayi ya kama mata hijab ya cire  yace ” karkije ko ina ki tsaya nan zanzo ” yana kaiwa nan ya fice 

Addu’ah kawai take zuciyarta na bugawa kamar zata fito,

Yayi awa daya da fita sannan taji kamar an taba kofa, 

Da sauri ta kalli kofa tana maida numfashi a hankali aka turo kofa wani irin kalon macijine baki kirin sai sheki yake kai 

tsaye ya nufo ta kalmar shahada ta shiga karantawa jikinta na rawa 

Saida ya kawo kusa da ita sannan ya tsaya yana kallonta idonshi jawur dinah babu abunda take fadin banda ” la’ilaha illallah muhammadu rasulilah3  ” kamar shahada dinah take ta karantawa ta matsa jikin bango ta matse kanta 

Macijin ya dawo genfenta na dama ya koma na hagu haka yayita yawo sai kalonta yake can kuma ya juya ya fice 

( yan uwa mu rike kalmar shahada babban abuce duk lokacin dakaga abunda kake tsoro ko kaga makiyinka ko wani mai mugun nufi akanka ka karnta masa kalmar shahada zakusha mamaki dan inma da niyar cuta yazo bazai iya cutar dakaiba in mafadacine ko kuma kana jin tsoronta  zakaga ya kyaleka dan kalmar shahada tana karyar da  zuciya mai mugun hali ko cuta )

Karmar shahada kawai dinah taketa maimaitawa idonta sunyi wani ja sunyi zurfi, 

Baifi minti 15 da fitaba ya sake dawowa wannan karon da gudu yayo kanta 

Ita kuma bata fasa karanta kalmar shahada ba saida ya kawo kusa da ita ya tada kansa tsaye sai leko mata harshe yake kamar zai lasheta 

Ya dade a haka sai kamar shahada dinah take karanta mishi

Faduwa yayi  riff ya fice 

Can kuma ya sake dawowa wannan karon a fusace ya shigo ya nufota 

Lauyewa ta yayi ya matseta sosai can kuma ya saketa da sauri ya fice 

Haka suka wuni ita da macijin sai yaje ya dawo yaje ya dawo tun tana iya karanta Karmar shahada har takai inya nufota saida tace ” Allah ” 

Fitar da yayi ta karshe bai sake dawowa ba sai wasu maza uku suka shigo dakin 

Kai tsaye suka nufota biu suka rikata suka fice da ita

Harabar gidan suka fito da ita suka nufi parking space dayan ya nufi wata mota cikin motocin ya yajanyota suka sakata suka shiga suma

 dayan sai zabga mata mari yake fuskarta duk ta kunbura,

Bakin gulbi suka nufa da ita suna isa suka fito da ita suka nufi gulbin da ita suna kokarin jefata wayar dayan tayi ringing 

da sauri yayi picking yana karawa a kunne ya kallesu da sauri yace ” ku dakata kada ku jefar da ita ance mu dawo da ita ” suka juyo suka nuffo motar da ita 

Gurin sakata motar abu ya zama rigima dan kasa sakata sukayi saboda wani karfi daya zo mata sai watse su take 

Kana gani kasan ba ita kadai take ba, 

sukayi2 su sakata mota suka kasa har kusan asuba ana abu daya can dayan ya ciro wayarsa dake ringing ya kara akunne

Banji mie yake fada ba dan  cikin  wani yare yake magana can kuma ya katse wayar ya kallesu suma cikin yare ya musu magana bansan mie yace musuba 

naga sun nufi gulbin da ita suka luluyata suka jefar cikin ruwan.

VOTE
[11/16, 10:19 AM] Khadeeja Candy: A hankali ta fara motsi sannan ta bude idonta tashi tayi zaune tana karanta kamar shahada, 

Ta shiga kallon mutanen dake zagaye da ita

 Matan duk suka shiga fadin ” Alhamdulillah ” dantijon cikin yace ” sannu yarinya sannu ” cikin tsoro tace ” ina nake waya kawoni nan “? Wani saurayi cikin mutane dake zagaye da ita yace ” kwantarda hankalinki mu mutanen kwaraine tsintarki mukayi bakin gulbi a yshe koda muka duba mukaga kinada rai kuma ALLAH kawai kike fadi duk da idonki a rufe yake shiyasa muka daukoki muka  kawoki nan gurin mai anguwa ” 

dafe zuciyarta tayi tana maida numfashi ta koma ta kwanta tana fadin ” Alhamdulillah2 ” dattijon ya kalli matar dake kusa da dinah yace ” kawo mata abinci ” tashi tayi tana ” toh malam ” ta nufi wani daki 

Tuwon dawa ne da miyar bushashen kubewa makota ma suka shiga kawo mata sai jere mata abinci ake kamar mai ciki goma, 

Babu abunda taci in banda yogurt da fura da mai gari yasa aka dama mata ganin ta kasa cin komai 

         Guraren 3 na rana dinah na kwance bayan tayi wanka tayi sallah 

mai gari yazo kusa da ita ya zauna duk yangidan suka nufota suka zagayeta har da makota, 

Tashi tayi xauna ta gaishe shi tare da masa godiya bayan ya amsa cikin ladabi tace ” dan Allah baba ina nn nan wane gari ne “?

” kina cikin wani kauye ne da ake kira more ” kai kawai ta daga masa tayi shiru

Can mai gari ya kalleta yace ” yarinya ya sunanki kuma maiya kawo ki nan garin “?

Gyara zama dinah tayi ta kwashe duk abunda ya faru ta fada musu duk abunda ya faru 

Suka cika da tsananin mamaki sai jinjina abun suke,,,,, 


Girgixa kai mai gari yayi yace ” lailai duk wadda ya rike Allah baya tabewa Allah yayi miki tsari yarinya Allah ya kara tsare gaba ” duk suka amsa da ” amin ” maigari yace ” yanzu zaki iya gane gida in aka tafi “?

Shiru tayi alamar tunani sannan tace ” ae zan iya ganewa ” wata mata ta kalleshi da alama matarsa ce haba tace ” haba malam wane irin ta gane gida yanxu tadai bada number waya sai akira su afada musu sai suzo suje da ita ” kai ya daga ” to ai babu matsala ” ya kalleta ” kinada numb daya daga cikin yan gidanku “? Da sauri ta daga masa kai ” ae akwai ta yayana ” maigari ya ciro wayarsa ya mika mata ” to samin anan saina kira ” tana sakawa ta mika masa ya danna kira ringing 2 ana 3 aka dauka saida suka gaisa sannan naigari ya fada masa komai 

can ya mikawa dinah wayar karbi zaiyi magana dake ” da sauri ta karba sunyi 4 suna magana sannan ta mikawa mai gari wayar ” wai yace ka masa kwatance garin ” karbar wayar ya masa kwatance sanna sukayi sallama,,,

Can guraren biyar na yamma dinah na zauna tana fira da matan mai gari. Akayi sallama da sauri ta tashi tsaye ta nufi mai sallamar tana fadin ” yaya ” rungume ta yayi ya rumshe ido yana sauke ajiyar zuciya,

ta bayanta zainab ta rungume ta tana kuka sun dade a haka sannan ta juyo ta rungume nafisa da zara, 

Tana daga kai ta hango momi tafe tana hawaye. Da sauri tayi gurin malik tana kuka tana kallon momi ” dan Allah momi kiyi hakurri wlh bansan haka zai faruba bansan ayimin wannan tarkon ba ” kama hannunta malik yayi ya rike sai a lokacin ya lura da wani farin wahala da tayi idonta sunyi wani baki sun shige ciki, 

Momi na kawowa kusa da ita ta rungume ta tana hawaye. 

Duk suka mashe da kuka har matan mai gari saida sukayi hawaye, 

Kukan da ba daina ba kenan saida abbah ya shigo, sannan suka shiga share hawayen suka tsagaita kukan.

Da gudu dinah tayi kansa ta rungume shi tana kuka 

Tsaye yayi yana shafa kanta yace ” Allah na gode maka Allah na gode maka Allah na gode maka Alhamdulillah Allah ” 

Sai kusan magariba suka dauko hanyar gida bayan abbah da malik suyiwa mai gari kyakkyawar sallama 

Koda suka iso gida ya cika da yan uwa da makota suka ganin dinah sujayi hamdala bama kamar jidda kawar dinah, faruk na ba amagana har abdallah babban yayasu yana gidan da iyalansa

Dr Abbah yasa aka kura ya duba ta

 Saida ya tabbatar masu da babu wata matsala sannan hankalinsu ya kwanta 

Washe gari suka zaune bayan sun gama karyawa, dinah take tambayar zulaiha nafisa tace ” a tun ranar da kika bata bamu sake ganinta ba ita da driver ” zatayi magana abbah ya shigo tare da malik

bayan sun gaisa ya shiga tambayar dinah yadda abun yake,, 

Nan ta kwashe komai ta fada musu tun haduwarsu da shi,

Duk suka cika da mamaki kuma suka shiga ganin laifinta na rashin fadin tun farko kuma dakai kanta da tayi 

Malik yace ” ai na fadama momi zulaiha ba yarinyar kwarai bace duk kuka karyata ni kukaki yarda ” momi da tun dazu take rike da baki tace ” shiyasa ake son bincike

Please Login or Register in order to submit comment