Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

*ƘASAITA BOOK 3*


*NA*

*MARYAM KABIR MASHI*


Page 1


Lafiyayyar dardumar kafet muka dinga takawa har izuwa wajen su waziri, waɗanda su ne iyayen fada. Ya ɗan sunkuya ya gaishe su, nima sai na yi yanda na ga ya yi. Madadin na ga sun amsa cikin nuna isa,su manya ne, sai na ji sun yi masa ɗan ƙaramin kirarin yabo.

Yana ɗagowa kuwa, sai na ga sun bi layin gaisawa da shi, wato ya dinga bin su ɗaya bayan ɗaya yana gaisawa da su. Ni kuwa da mun iso sai in ɗaga masu hannu. Suna gamawa dogarawan nan na zubewa ƙasa, domin gaishe da mu. Mamaki kam ya dirar masu a lokacin da suka bayyana shi a fili, shi ne amsa musu da ya yi da.

"Mun same ku lafiya?" Har da ɗan jan sunayen biyu daga cikin su. Ba su ba,ko ni nayi mugun mamaki.

Shi kuwa wucewa ya yi abinsa bai tsaya neman ba'asin mamakinsu ba, balle da ya ce su tashi mana. Me ye na saurin zubewar su ƙasa. Da ya isa ga wasu masu kayan mu na gida kuwa, ma'ana ta da ganinsu ka san ba dogarawa ba ne, ba wanda ko ni nasan na kusa da shi ne, ban dai san ko su waye su ba,abokanansa,ko ƴaƴan manyan fada. Yana isa ya rungume ɗaya daga cikinsu, kowa kam ya yi mamakin haka, ya dinga binsu ɗaya bayan ɗaya yana yi masu masabahar runguma, irin gaisuwar larabawa,su ma kuwa sun kai su taƙwas. Bayan nan kuwa muka juya motar mu wadda aka buɗe ta tun kafin mu isa gare ta.

Limousine ce, amma na san ba wacce na san Yarima da ita ba ce ba, saboda waccan baƙa ce mai ƙofa uku, kuma gabanta irin na kowacce mota ne, amma wannan ruwan toka ce mai duhu ash colour, sannan gabanta tamkar End of Discussion. Sai da na shiga sannan na ga ya zagaya shi ma ya shiga.

Subhanallahi!. Ba don kada a ce na ruɗe ba, da sai in ce motar nan ta fi jirgi daɗi da ƙyau, duk da na je ƙasashe na gano kala-kalar motoci da jiragen sama kansu.

Lulluɓe muke ta ko'ina, ba mai ganinmu. Na ja jiki na isa na ƙwanta kafaɗar mijina. Ya ɗago goshina kaɗan ya sumbace ni.

"Thank you. Au! Ɗan ɗaga ina zuwa, kada na yi laifi biyu." Ya ɗan ware ƙafafunsa, sai na ga ya janyo wani abu kamar ƴar sabuwar alkyabba mai ruwan hoda, ya dinga zarowa har da ɗan mayafinta, shi ma mai ruwan hoda.

Ban da takalma da jaka masu ruwan ƙasa,jakar wata ƴar maƙalalliya ce,a silin hannu kawai ake maƙala ta.

"Cire ta jikinki ki saka wannan. Gidan Mai Martaba za mu wuce mu gaishe shi,mu gaishe da Mama." Ya janyo ni ya ja hancina.

"Har wajen Daddy za mu fa yau." Ina zaro idanuwana.

"Me ye?"

"Ni kunyar shi nake ji." Na faɗa cikin shagwaɓa.

"Me yasa ki ke jin kunyar shi?"

Na ɗan harare shi irin hararar da na san zata sa idanuwana su yi mishi ƙyau. Ya yi dariya.

"Kin san kullum ina ƙara son ki da ɗokin ki Yasmin,saboda yanda ki ka mayar da ni autan ki."

"Na daina,ni dai kada a je wajen Dad."

"Ba zai yiwu ba,watan mu nawa da aure har yau ba ki taɓa zuwa gida ba. Ko a da da kika ga naƙi kai ki, tsoro nake ji kada in na kaiki ki ce ba ƙya dawowa. Ki sani na koma uku saura ƙwata a garin nan. Yanzu kuwa ko kin ce ma na san yanzu ina da garanti ɗin bin ki duk inda ki ka nufa, yanda suka ba ki ɗaki, nima haka za su ba ni,in ba haka ba ƙwanan falo ya kama ni. Ke ni ko kicin ma na dinga ƙwana,ai dai ina ganin ki kullum."

Na ɗan ture shi kaɗan tare da ɗan narkewa alamar shagwaɓar da na san tana sa shi ya ji daɗi. A take ya yi ƴar ƙara kaɗan.

"Ina! Ashe da nayi sakaci a baya da ƘASAITA ta janyo mini haɗarin da yafi na mota wahala. Rasa ki Yasmin ai wani babban gurguntar rayuwa ne."

"Ni?"

"To ya isa, na daina."

"Na ɗora saman kayan jikina,dama kuwa wani material ne mai ƙyan gaske (yadi), shi ma naga ya cire ta jikinsa ya saka fara tas. Dama kayan jikinsa boyal ne baƙi,safari da wando irin ɗinkin sarauta, sai ya ɗora ruwan tokar alkyabba yanzu ya tuɓe ta ya ɗora fara.

Na zaro foda mai tafi da madubinta, na ƙara gyara fuskata na ƙara rangaɗa ƙwalli wanda dama ni kaina na san na yi kalar ja, tamkar jini zai fito daga jikina. Na ƙara gyara gashin idanuwana suka miƙe tsaye, ban da baƙi da suka ƙara, juyowar da zan yi sai na ga Yarima ya rabga tagumi ya ƙura min idanuwansa, tamkar mutum-mutumi, saboda ko ƙiftawa ba ya yi.

Sai da na kai ga taɓa shi, sannan na ga ya yi irin murmushin nan mai nuna alamar daɗi, ya yi masa yawa, ya ɗauko turare ya fara yi min fesar nan tasa. Duk fesawa ɗaya tare da sumbata ɗaya, wuya, baya saman ƙirjina, zuwa bayan kunne, wanda a ƙarshe ya kan ajiye turaran ya rungume ni da jikinsa,ko ma ya ɗauke ni cak ya tafi da ni, inda zuciyarsa ta fi so.

Amma yanzu na yi saurin ɗago shi daga ɗan ƙaramin fita daga hayyacinsa da ya yi, idanuwansa a lumshe, na sa yatsuna biyar na wara su saman fuskarsa na shafa zuwa ƙasa.

"Honey, we are in the car, wake up."

Ya buɗe idanuwansa da suke a lumshe ya yi murmushi, tare da lakatar hancina.

"Ba ƙya ji."

Na yi murmushi haɗe da ɗan fari da idanuwana, ya zame jikinsa ya ƙwanta a cinyata.

"Har na ji na gaji."

"Aikin me ka yi? Kai da Allah ya gama haɗa maka daɗin duniya, sauran ka fa lahira da addu'ar mata ta gari, ƴaƴa na gari."

"Mata ma na samu, ƴaƴan ma ina sa ran matata zata iya yi mini tarbiyyar su da irin tata tarbiyyar mai ƙyau."

Tsayawar mota ita tasa ya yi wani saurin tashi zaune cikin sakan ɗin da bai fi rabi ba, tare da gyarawa yana saka gilashin fuskarsa. Ana buɗe ƙofar nan da nan na ga har ya rikiɗe ya tafi cikin jinin sarautar sa. Kafin na ƙarasa kallon ikon Allah har an buɗe mini nawa ɓangaren take na tunano irin tawa ƘASAITAR a baya. Na yi saurin juyewa ni ma.

Ina kunno kai wajen motar nan na ga taron mutanen da sai ka ce wani biki ake,ko gagarumin taro. Yana tsaye har sai da na zagayo sannan muka jera da shi cikin kunya da naji. Muna isa cikin fada aka wuce kai tsaye,fadar ma ta waje, ba ta cikin gida ba.

Allah Sarki. Gaskiya Sarki yana son Yarima,son da na rasa cikin mu uku nawaye ya fi ƙarfi. Mama ko Mai Martaba ko ni? Wannan tunanin ya faɗo mini ne a daidai lokacin da muka shiga fada na ga Sarki ya yi saurin miƙewa tsaye yana fara'ar da ta bayyana a filin fuskarsa. So da so ya haɗe,a take Yarima ya yi saurin isa yana murna, ya tsugunna a gaban mahaifinsa, tsugunnon girmamawa, Mai Martaba ya sunkuya tare da dafa kansa.

Fadawa suka ɗauki roƙon kirarinsu, "Nan Sarki ya amsa."

Mai martaba ya ɗago shi, madadin ya sake shi, sai kawai na ga ya rungume shi. Fada ta ɗauki ihun murna har da tafi. Ni kuwa wani irin daɗi ya saukar mini a lokaci ɗaya, saboda Yarima na ɗagowa sai ya nunawa Sarki ni. Ganin haka yasa na isa na yi saurin tsugunnawa a gabansa. Ya dafa kaina nima. Gaba ɗaya fadawa suka ɗauki maganarsu.

"Sarki na amsawa, Gimbiyar mata wacce ta isa, gaba sarauta baya mulki,so da ƙauna dole a yi miki shi."

Ina tsugunne Sarki ya koma ya zauna, sannan duk faɗar aka zauna har da shi Yarima, ya tsugunna kusa da ni. A nutsuwa Sarki ya fara magana, wanda ƴan jarida da ƴan ɗaukar hoto da na talabijin sun zagaye fadar.

"Na godewa Allah da ya kawo ni wannan ranar ta farin ciki, shi ne ranar da Yarima mai ci gaba da mulkin mutanena ya dawo lafiya tare da iyalansa. Allah yasa masu albarka ga auren su. Ya yi tafiya ta hutu tare da iyalansa ta tsayin watanni uku. Allah ya dawo mana da shi lafiya, Allah ya bashi ikon riƙe iyalinsa lafiya da kuma al'ummar garina.

Na gode da irin karancin ƙaunar da ku ka nuna mana,ni da iyalina gaba ɗaya, Allah ya saka, ya kuma kawo mana canjin rayuwar jin daɗi a nan gaba. Kuma buƙatar da iyalinshi suka buƙata a takardar da ta iso min daga hannun jakadiyarsu,an gama ta tun wata biyu da suka shige, daga yau kuma iyalinsa na da iko da ƴancin zartar da hukunci a kan kowa,ko da kuwa hukunci a kan abin da suke son yiwa mutanena ne. Yanda suke son tsarin bayin gidansu, da masu kulawa da su ya koma a hannunsu. Na gode ƙwarai da ba ni haɗin kai da ake a game da hukuncin da na yanke,ko na gindaya. Yanzu za su shiga ciki domin ganawa da jami'ar da suka daɗe ba su gani ba."

Daga haka Mai Martaba ya yi shiru,ko motsi ban ƙara ganin ya yi ba. Duk da kaina a sunkuye yake, ganin Yarima ya matsa kusa da kujerar mulkin Sarki, ya dafa kansa ya miƙe tsaye,ni ma shi yasa na matsa aka dafa nawa kan, na miƙe na bi mijina da yake tsaye dama yana jirana.

Cikin gida kuwa, kamar ranar walimar amare bakwai, saboda mata da suka yi yawa a gidan. Maroƙa mata kuwa, sai yi suke, amma Yarima ɗaga kai kawai ya yi ya kallesu, sai na ga duk sun zube ƙasa suna ƙwasar gaisuwa. Gaskiya al'amarin sarauta da akwai sha'awa, sai kuma yanzu na tabbatarwa kaina cewa ba su ne da kansu suke nuna ƘASAITA ba, musamman Allah ne ya saka musu ita a cikin jininsu.

Falon Hajiya Kilishi muka fara shiga,a inda na ga hakan ba ƙaramin daɗi ya yi mata ba. Har ƙasa muka sunkuya muka gaishe ta, cikin daɗi ta amsa, har da kamo ni da tayi ta rungume,wai ga ɗiyarta ta dawo. Cikin zolaya irin ta manya ta fara magana.

"Amma dai nan za ta ƙwana, saboda gajiya,ai dole ne ta ɗan samu hutu."

Shi dai Yarima sai dai kawai ya yi murmushi, "Baka ce komai ba?"

"Hajiya ai yarki ce,ga ta nan."

Amma fa ya kasa ɗago kansa. Hakan yasa ni kuma na ƙara zolayarsa.

"Dama kuwa Hajiya duk na gaji, ga zaman jirgi,Gara na huta yanzu,ko sati biyu na ɗan yi."

Ya ɗago ta gefen ido ya harare Ni, Hajiya tasa dariya.

"Daina hararar ta,ku tashi ku je tunda ka yi mini rowar ta."

Ya miƙe yana kiran, "Hajiya ba da ke nake ba, da ita nake,. Manya na magana tana saka musu baki."

Aka saka ƴar dariya, muka fito.

Manyan mata kenan, iyayen gidan Mai Martaba,su Mama. Zaune take kamar yanda muka samu Hajiya Kilishi, cikin sakan ɗaya suka yi gaisuwa duk suka fice ɗaya bayan ɗaya, suna fita ta taso ta rungume ni jikinta.

"Your are welcome my daughter."

"Nifa mama?" Ya faɗa cikin ƴar shagwaɓar da yake yi mini. Kamar dai yanda na ga ya yi mata farkon zuwana gidan.

"Ina ruwana da kai ni kuma, sai ka koma can wajen Hajiya."

"Kai shi kenan,kun haɗe mini kai. Ita ma Hajiya cewa ta yi ta samu ƴa."

"Sai ka koma wajen Mai Martaba,ƙila shi yana so."

"Kai Mama."

Muka ɗan yi dariya, sannan na ga ya zauna ƙasa yana gaishe ta. Hakan yasa ita ma ta zauna tare da ni a kusa da ita.

Ƴan nasihohi ta yi mana na mu zauna lafiya, kada ta kuskura ta ji wata matsala ta taso a tsakaninmu. Nan ta ce mini idan har na ga tana shirin tasowa na bugawa Hajiya Kilishi waya ko na nemi shawarar jakadiya. Nan take ta ba mu labarin cewa, bayan tafiyarmu an ƴanta bayin gidanmu, amma da sunan za su cigaba da aiki, amma a dinga biyansu albashi. Na gidana kuwa,an ce su nemo miji a yi masu aure, wacce mijinta ya bar ta ta cigaba da zuwa, wacce ya hana ta ta yi zaman auranta,ko yanzu haka ake ciki.

Ƴan gidan yari kuwa, Mai Martaba cewa ya yi sai kin dawo za'a sallame su, shi ne zasu bi layi a karanta miki laifin kowa, wanda ki ka ga ya dace ki sallame shi,ki sallame shi, wanda bai dace ba ki san ya zakiyi da shi. Na ji daɗi kuwa ƙwarai da gaske,a inda murnata ta ɗan fito fili.

A lokacin dai har Mai Martaba sai da muka ƙara keɓewa da shi na musamman, muka gaishe shi a fadar cikin gida. A lokacin ne ma na samu na yi godiyar abubuwan da ya yi mini, waɗanda na buƙata.

A nan shi ma ya yi mana nasihohi irin nasu na manya. Sannan ya ce Yarima ya yi taka tsantsan da rayuwa, saboda Abdulrahman ya zo da baya nan, har ya dinga rabon kuɗi a can gidan namu, ya ce a ɓangaren gidan Ahmad ya zauna. Sai da na ɗan nisa sosai, sannan na tunano wanda Sarki ke nufi, wanda Mama ta bani labari cewa ɗan Sarki ne, amma baya sonsa, baya son ma a ce ƴaƴansa ne, kenan ɗan Hajiya Asabe.

Sai bayan da aka idar da sallar la'asar, sannan muka yi sallama da su. Ban tashi gane ina mota ta tsaya ba sai da aka buɗe mana ƙofa,kawai sai na ganni gidanmu. Na yi saurin kallon Yarima, sai na ga ya sha kunu, alamar babu wasa,ya ma yi gaba abinsa. Kafin ya kai ga ƴar matattakalar da ke ƙofar shiga gidanmu sai ga su Mamee sun fito, ita da Dad suna fara'ar murna.

Kunya ta yi saurin dirar mini,tare da murnar ganin iyayena da na yi, wata uku har da ƙwanaki da dama ban gansu ba, balle ma Dad ɗin da ba na iya ƙwana uku a da ban ganshi ba,ko tafiya ya yi saboda ni baya daɗewa, ya san har kuka nake yi masa a waya.

Yarima na isa na ga ya tsugunna ƙasa yana gaishe su. Shi kuwa Daddy sai naga ya ɗaga shi ya rungume, irin dai gaisuwar nan ta larabawa.

Dad cewa yake, "Oh! My Son, welcome back,I am happy to see you."

Ni kuwa ina isowa na faɗa jikin Mamee wacce kai tsaye tana dariyar murna. Ta ɗan riƙe ni tana dariya, daga baya kuma sai da ta taɓa ɗan wasan da ta saba.


######
[2/18, 09:13] Ummi Tandama😇: *ƘASAITA BOOK 3*


*NA*

*MARYAM KABIR MASHI*


Page 2


"Ke tashi daga jikina,ko ƴata ba ta zo ta haye mini jiki ba sai ke."

"Kai!" Na faɗa cikin yanayin jin kunya da shagwaɓa."

"Ke zo nan ƙyale ta dama ita haka take."

Cikin jin kunya, na isa wajen Daddy, Amma sai ga ni na tsugunne a ƙasa, saboda kunya da ta kama ni. Ya sunkuyo ya ɗago ni ya rungume a jikinsa. Ƙamshin turaren sa na ji ya dakar mini hanci. A take na ji kaina ya sara. Cikin sakan ɗaya na ji ina juyawa tamkar wacce ta yi hajijiya ta gaji (Katantanwa), wani amai na ji mai zafin gaske yana taho mini. Tun ina ɗaurewa har na ji gashi nan ya gangaro a bakina. Na zame jikina daga rungumar da Dad ya yi mini,na ruga a guje ga famfon da ake bawa fulawowi ruwa, na tsugunna. Wani irin mugun amai na dinga ƙwaranyawa. Ni dai na ji an riƙe ni, amma ban iya ɗaga kai ba ballantana in ga waye mariƙin nawa.

Tun ina yi daga tsugunne,sai ga ni na durƙushe sosai, shi kuwa aman nan ya ƙi tsayawa ko shan iska ma in yi. Na ƙwashe tsayin minti goma ina ƙwaranya amai. Sai ya yi kamar zai tsaya, sai kuma in ji wani sabo ya taso. Muryoyin sannu kuwa,ta ko'ina a kunnuwana, mai dafani kuwa, sai na ji ya tsugunna ya rungume ni a jikinsa.

Jin aman ya tsaya, yasa na samu na miƙe na isa na buɗe famfon na kuskure bakina, tare da wanke fuskata, saboda hawayen aman da suka tsattsafo ga idanuwan nawa. Sai da na juyo na ga mutane tsaye a kaina kusan mutum goma sha,ƴan aiki, masu gadi.

Mamee ce rungume da ni. Dad kuwa yana tsaye yana kallon ikon Allah, dukkansu suka yi mini sannu. Daga nan Mamee na ɗan riƙe da ni har cikin falon Dad ɗina. Na ɗan kishingiɗa kaɗan a kujera,Dad ke tambayata me ya ke yi mini ciwo? Na ce ba komai, sai dai kaina kawai. Cikin rawar jiki Daddy ya ɗauko magani ya miƙa mini. Mamee ta karɓa.

"A'a ba a shan magani ko sai an ga likita. Ka bari in sun tafi can su ga likita, sai ya rubuta musu magani."

Nan take na ji Dad ya fara faɗa, "Ya ma za'ayi a ce sai ta ga wani Likita,ai kowa ya san maganin ciwon kai."

"Ka zo ciki Alhaji." Ta yi ciki. Na san ɗakin Daddy suka nufa. Nan fa Yarima da ke zaune gefe ɗaya ya yi ɗan ƙaramin zaman makokin cutata, ya samu damar saurin isowa gare ni, ya kama ni ya rungume ni da rawar jikinsa.

"Ya ya me ke miki ciwo? Ki gaya mini kin ji Yasmin, talk to me please."

"Bana jin komai, sai dai kaina da ya yi mini nauyi kamar yana ciwo."

Ya sake ni ya durƙusa a gabana, ya rike hannayena duk biyun, "Please Yasmin, tell me the truth."

"Ba komai,ni bana jin komai."

"Yasmin look at me." Na ɗago na kalleshi.

"Kada ki ɓoye mini Yasmin,ki kalleni ki ga yanda na koma a yanzu kawai. Kina tunanin in ki ka ɓoye mini ya zan koma a nan gaba?"

Ya sumbaci hannuwana. Na zame hannu ɗaya na shafi gefen fuskarsa, tare da sunkuyowa na sumbaci laɓɓansa cikin kunya.

"Ba zan taɓa yi wa mijina ƙarya ba saboda ina son shi ba zan so in ga hankalinshi ya tashi ba. Ka amince da abin..."

Motsin da muka ji yasa ya yi saurin tashi ya koma inda yake zaune. Shi ne kujerar da ke nesa da ni.

Dad ne ya shigo, amma sai na ga damuwar fuskarsa ta gushe, wanda take kaɗan ya yin da Mamee ta biyo bayansa. A nan Mamee ta ce mu shiga ciki mu bar su nan. Na miƙe tare da satar kallon Yarima, saboda in karanto me ke fuskarsa. Cikin maganar raɗa ya ce, "Take care." Na lumshe ido alamar na amsa masa na wuce cikin gida.

Mamee ta zaunar da ni ta dinga yi mini ƴan tambayoyi kamar su, "Ba komai dai zaman ki da mijinki? Ya ya yanzu kun daidaita ko? Ya gida? Sarautar ba dai matsala?"

Duk na amsa mata da eh kawai. Saboda na san ni yanzu ba ni da wata matsala dama matsalata ɗaya ita ce Yarima, yanzu kuwa ni kaina na san ina son Yarima. To ballantana shi wanda na lura da zai iya rasa rayuwarsa idan har ya rasa ni.

Sai ƙarfe uku muka bar gidan, amma kafin in tafi tamkar ban taɓa yin komai ba, saboda sai da ma na ci abincin Mamee na ƙoshi. Lafiyata ƙalau muka yi sallama da su. Duk da sai da na nunawa Yarima ya bar ni gida tsayin ƙwana baƙwai,a lokacin muna falon Mamee. Wannan ne ma ya baiwa Yarima damar cije mini laɓɓana da harshensa kada ma na sake faɗar irin wannan mummunar maganar. Na ɗan narke masa tare da cewa.

"Gidan mu ne fa! Yanzu shi ne mummunar maganar?"

Bai ma ba ni amsa ba, sai dai ya ɗan kama hancina ya ja ya tafi falon Daddy,wato manufarsa baya son maganar ma.

Muna shiga mota na ƙwanta daidai lokon motar.

"I am tied." Har da ɗan canja yanayin fuskata. Bai fi minti ɗaya ba na ji Yarima na kiran sunana. Na juya na kalleshi, sai na ga ya ware hannuwansa, alamar in isa gare shi. Na ɗan kaɗa idanuwana na gyara ƙwanciyata sosai, alamar dai ba na zuwa.

"Honey please come on. Ina son jin ɗumin jikinki a kusa da ni."

Na matso na faɗa ƙirjinsa na ƙwanta tamkar ba ni ba, ina jin shi ya sumbaci goshina. "I love You Yasmin,I can't explain how much I love you. Amma ke kina ɓoye mini me ke cikin zuciyarki.

Yasmin kin san ba zan iya yin komai ba sai kina kusa da ni. Me yasa za ki takura mini in bar ki gida? Wallahi ba zan iya ba,in ba so ki ke inyi ƙwanan ƙofar gidanku ba, amma na lura ranki ya ɓaci don na hana ki. Yasmin ki yi tunani, ba ki da lafiya fa, ya zan iya ƙwatanta ƙwanan da zan yi a yau in na tuna haka?"

Jin maganganun za su yi yawa na san halin Yarima, yanzu zai iya shiga matsananciyar damuwa idan na yi masa shiru. Na ɗago nasa tsinin hancina a daidai bakinsa.

"Ka yi haƙuri ba zan ƙara ba. Wallahi nafi son ganin farin cikin ka fiye da nawa. Na fi kowa baƙin ciki idan na ga kana cikin shi. Ka yi mini afuwa,ɓata maka ran da na yi ba zan ƙara maimaitawa ba...."

Ya ɗago ni, "kin ci abinci?" Na ɗaga masa kai.

"Are You sure?" Na ɗaga kaina.

"Ai na yi wa likita waya, har ma na gayawa Mama na ce ta shaidawa Mai Martaba cewa ba ki lafiya za mu koma gobe."

"What? Haba Yarima, daga ɗan amai kuma sai ka damu haka."

Na sassauta murya, "Ka yi ƙoƙarin ɓoye sona

Please Login or Register in order to submit comment