Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

daka wawan tsalle sama kamar an wullo shi daga cikin baka bai dira ako ina ba sai a tsakiyar dakarun yana dira ya wulla bawa rakib bayan Sa tare da masa bushara da duk runtsi kada ya fado dan idan ya fado ya zama gawa ae ko sai ya rikeshi tamau jarumi Aryan ya wanzu yana mai kai Sara da suka cikin bakin zafin nama juriya da bajinta tako ina duk inda yasa gaban Sa saidai kaga maza na zubewa kasa kamar ana sassabe a gona cikin yan dakiku ya tashi hankalin bangaresa yana juyawa bayan Sa ya hango dakaru sun yanyame gimbiya sima tako ina kafin ya yi wani ynkirin kai mata dauki yaga tayi wata alkafira a sama ta zubar dasu gaba dayansu sai taki yarda ta dira agun kawai sai ta rika taka kan dakarun tana kara gaba dan su hade da jarumi Aryan aci gaba da yakin





Shiko sarki dizlan yana daga gefe yana ganin yadda ake ragargazar dakarun Sa sai yaji zuciyar s ta kama ta farfasa kamar zata kone kawai sai ya kwarara uban ihu kuma ya yi wa dakarun bushara da subashi guri tunda basu Iya wa a lokaci guda dukan su sukaja baya suka zama yan kallo kawai shikuma ya zare takobinsa sannan ya zaro wani gatari a bayan Sa ya hada biyu koh da ganin wannan Abu daya faru sai jarumi Aryan ya daka tsalle ya dira a gaban gimbiya sima yana mai da da zare wata takobin a kuybin cinyarsa ya hada suka zama biyu sannan ya tunkari sarki dizlan bada shakkar komai ba suna haduwa suka ruguntsume da wani azababben yaki suka wanzu suna kaiwa junan su Sara da suka cikin bakin zafin nama wata irin jarumta suke nunawa dan wani lokaci ma idan suka tashi sama sai sunyi kusan da kika ashirin sannan suke durowa su Dora yakin kowa kokarin chanza salon fada yakeyi amma duk salon da suka chan xa sai suka duk sun iyashi koh ganin wannan Abu sai suka ja da baya kamar hadin baki suna haki kamar zakaru suna kallon juna kowa fuskarsa a turbune





Saida suka kwashe yan dakiku a haka sannan kuma sukayi kan juna da mugun gudu kowa yasa takobinsa a kasa tana kartan kasa suna ihu sai da ya ra ge baifi saura taku uku su hadu ba sai kowa ya daka tsalle sama kamar an janye su da majajjawa suna haduwa a sama cikin mugun nufi kawai sai gani akayi sunyo kasa rikicha suka fadi shidai Aryan dantsen hannunsa na hagu y dafe inda jini keta zuba sakamakon saran da sarki dizlan ya dankara masa shukuma sarki dizlan gefen cikinsa ya dafe inda takobin Aryan ta nutse a cikin zare takobin yayi ya yar da ita tare da kwallah ihu ya zube a gurin da gudu ko wanne bangaren sukayi kan dan uwansu





Rike sarki dizlan akeyi amma shi burunsa bai wuce akama su Aryan a kulleba koh da ganin haka sai dakarun suka kuma dauki Kansu koda ganin haka sai gimbiya sima ta karanta wasu dalasiman tsafi suka bace bat kamar basu taba wanzuwa a gurin ba ko da ganin abinda ya faru sai sarki dizlan ya ta karkare ya kwarara uban ihu yana mai zubda hawayen takaici................




Comments dinku shine zaisa na Dora typing




By fast class

🏀🏀🏀🏀🏀🏀
      🏀 🏀🏀🏀🏀
            🏀🏀🏀🏀

TARTSATSIN WUTA
(adventure story)
            🏀🏀🏀
     🏀🏀🏀🏀🏀
🏀🏀🏀🏀🏀🏀

Tsara labari da rubutawa

ALIYU ISHAQ
Β Β  (fast class )
________________________________

*AREWA WRITER'S ASSOCIATION*
_________________________________
*πŸ’¦{Arewa ginshiΖ™in al'ummah}πŸ’¦*
_________________________________
https://www.facebook.com/104534761033461/posts
arewawritersassociation@gmail.com



Page 36to40


Daga marubucin
KAUNAR UWA
UMAR FAROUQ and now
TARTSATSIN WUTA
(adventure story)






Lokacin da su gimbiya sima suka bace daga kofar gidan kurkukun basu bayyana ako INA ba sai a cikin wani kunkurmin daji mai matukar ban tsoro su Kansu basu San koh a wani daji suke ba sabida tashin hankalin da suka shiga na ganin hannun Aryan na ta xubda jini ba kakkautawa cikin sauri gimbiya sima ta mikawa bawa rakib yan tagwaye ta lula cikin daji Neman mgn karban su yayi ya ajiye su akan wani zanin goyonsu ya fara kokarin tsaida jinin dake zuba a gurin ciwon nan dakyar ya samu jinin ya tsaya da taimakon wani kyalle daya yago a jikin Sa ya daure ciwo yana tsaida jinin ya sauke numfashin wahala sai a wannan lokaci yakejin gajiya a jikin sa ta yakin da suka sha duk da shi ba komai yayi ba to su wadanda sukayi fadan ya sukeji kenan ya tambayi kansa bai gushe ya na wannan tunanin ba yaji wani irin sauti na tashi sama sama nan take yaji zuciyarsa ta buga tsoro ya dabaibaye shi sabida ya gane gurnanin rikakken zaki ne Wanda ya jima bai ci abinci ba yunwa ta koroshi ba shiri ya fara Neman mafita tun kafin xakin ya gane inda suke Ashe ya makara dan tun da suka bayyana a dajin zakin yasan da zuwan su ta hanyan kanshin su daya shaka yanxun haka ma shi yana kallon su da ga inda yake amma koh kadan hankalin rakib baikai gun da zakin yake ba








Da sauri ya dauki aisar da jumaima ya fara Neman gurin buya juyawan da zaiyi yayi arba da zakin sai rabka hamma yakeyi yana lashe baki nan take hantar cikin sa ta kada ya rasa mai ke masa dadi a duniya kawai sai ya yanke shawara ba zai bari wani abu ya samu su Aryan ba koh da zai rasa ransa ne duk da yasan Aryan ba abinda zai iya sabida ciwon dake hannunsa kawai sai ya je ya zare takobin Aryan ya ruketa ya fuskanci zakin da niyyar syita ta kare a wannan lokaci su aisar na kwance a kasa sai wasan su suke irin na jarirai su basu ma San maike faruwa ba







Zakin na ganin abinda rakib yayi kawai sai ya kalli inda aisar suke ya daka wani wawan tsalle da nufin ya musu dauka daya cikin zafin nama da ko a mafarki rakib baisan xai iya ba yayi wani mugun tashi ya dira a gaban zakin kafin yayi wani yunkuri rakib ya Sa kafa ya maida kansa ma ana ya chanja masa akala zakin ya fadi chan gefe guda yana tashi ya rabka wani wawan ihu mai tarwatsa maxa mai sa mai tsohon ciki ta hau nakuda ba shiri yan tagwaye suka hau kwalla ihu sakamakon raxanan da sukayi sakamakon wannan ihun da zakin yayi shine ya jawo hankalin sima da tayi nisa gurin nemawa Aryan mgn tana kan wata bishiya dan tsinko ganyenta taji wannan ba shiri ta diro rike da ganyen ta falfalo da wani axababben gudu kai da ganinsa kasan na sihiri ne ba NATA na kanta ba







Cikin azababben gudu zakin yayi kan rakib shima yayi kundunbala yayi kan zakin suka kaure da fada su fadi chan su tashi nan zakin na kokarin kafawa rakib kaifi shikuma yana kaucewa amma yaki sakin zakin dan yasan yana sakin sa tasu ta kare suna cikin wannan hali ne zakin ya samu sanarar cixon rakib a kafada ba shiri ya kwallah ihu Wanda ya cika dajin gaba daya kuma shine ya firgita sima ta kara karfin gudunta dan tayi nisa dasu sosae







Duk da wannan cizo da zakin ya masa baisa ya sakeshi ba ana haka ne suka kai inda rakib ya yarda talobin dake hanninsa da sauri ya dauka cikin azama ya lumawa zakin ita a ido yana cirewa jini ya biyo bayanta wata Uwar kururuwa zakin yayi kuma ya dada rkicewa gurin kaiwa rakib hari duk wannan abinda ke faruwa Aryan bai sani ba dan ya jima da suma kuma har yanxun bai farfadoba








Da kyar rakib ya Kuma samun nasarar FASA dayan idan zakin fa ya haukace agun ko da rakib yaga zakin yayi kan yan tagwaye yana shi rin takasu sai ya falfala da gudu ya na zuwa ya tattaro duka karfinsa ya saukewa zakin nan kai kan yayi chan gangar jikin ta zube kasa matacciyar







Hakan yayi dai dai da isowar gimbiya sima tana ganin irin jarumta da rakib kawai ta hau rabka masa tafi da jinjina Kuma tace gsky na godewa abin bautata da ya bani miji jarumi mai da kakkiyar zuciya kasani wannan fadan dakayi shine a madadin sadakina na aurena dan dama na kudire a raina bazan ci gaba da zama da kaiba sai kayi wani abun jarumta daya birgeni kuma gashi kafin ma na fada ma ka kayi abinda ya kamata sabida haka yanxun aure kawai ya rage mu daura







Cikin matukar garin ciki rakib ya is a inda take suka rungume juna suna dariyar murna sima ta janye jikin ta ta koma inda Aryan yake tana mai cewa ya dauke aisar da jumaima an an ta sa masa mgn ta dinke raunin sannan ta fara masa firfita zuwa wasu yan dakiku ya farfado anan suka yada zango suka kafa tanti sabida dare ya soma yi a wannan lokacin suna shiga tantin gimbiya sima ta kallesu su biyun tayi gyarn murya tace mufa yanxun ba tsira mukayi ba kusani kamar yadda Aryan ya suma shima sarki dizlan ya suma kuma INA tabbatar muku da cewa sai ya shiga halwar tsafinsa dan nemo inda muke kusani ba wani nisa mukayi da birnin kisra ba dan daga nan Zuwa chan tafiya ce ta yni daya kachal idan ya gano inda muke kuwa a Daren nan zaisa abi bayan mu kinga kenan zuwa Sadiya zasu Iya riskan mu dan haka muma da asuba zu kara gaba sabida haka kowa ya kasance cikin shiri tana kaiwa nan ta samu shinfidarta ta kwanta dan ciyar da aisar da jumaima suma kwanciya sukayi dan yin bacci,




πŸ₯πŸ₯πŸ₯




Al amarin su sarki uklan kuwa tunsan da Aryan yabar Gida mahaifiyar sa ta tashi hankalinta akan wannan tafiyar saita sa kanta a daki tayi ta kuka da kyar yake lalashinta da fada mata cewa duk fa runtsi Aryan bazai mutu ba sabida haka binciken sa ya muna masa haka kuma bazai iya kashe sarki dizlan ba amma fah dole dai dauko abinda ya he nema kullum da haka yake lallashinta tayi shiru amma nadan ta yarda ba dan har yar rashin lpy ta kwanta sakamakon tafiyar sa ,wannan kenan








πŸ₯





Achan birnin kisra kuwa bayan sarki dizlan ya farfado su Aryan ne suka fara zuwa masa a rai ya yunkura dan ya tashi yaji ciwon gefen cikin sa yana masa zafi nan take abinda ya faru ya fado masa a rai ihu ya kwarara sannan ya mike dukda zafin da yakeji amma ya daure dakin tsafinsa ya shiga ya kulle kofah ya hau bincike saida ta kwashe sa a daya da rabi Shannan ya dago yana murmushi na nasara kawai sai ya fita ya na mai bawa sarkin yakin sa umarni da su hada dakarun yaki dan a je riski makiya sunan a dajin sarjim dake gabas da wannan burni sun kafa tanti kawai ga warsu yakeso aiko nan da nan sukahau shiri shima ya hau shiryawa wata shigar yaki yayi mai ban tsoro duk jikinsa ya rufeshi da kayan yaki na karfe ya kawo ta kalmi na fatar da Musa ya saka ya saka hular karfe itama baka idanunsa kadai ake gani sannan ya kawo tagwayen ta kubbah ya saka a kugunsa ya rataya wata zabgegiyar adda ya jagoranchi da karun suka fita daga brnin suka nausa cikin daji.....................







Anan ake yinta fah readers ni dai comments kawai nakeso mai xafi




By fast class
🏀🏀🏀🏀🏀🏀
      🏀 🏀🏀🏀🏀
            🏀🏀🏀🏀

TARTSATSIN WUTA
(adventure story)
            🏀🏀🏀
     🏀🏀🏀🏀🏀
🏀🏀🏀🏀🏀🏀

Tsara labari da rubutawa

ALIYU ISHAQ
Β Β  (fast class )
________________________________

*AREWA WRITER'S ASSOCIATION*
_________________________________
*πŸ’¦{Arewa ginshiΖ™in al'ummah}πŸ’¦*
_________________________________
https://www.facebook.com/104534761033461/posts
arewawritersassociation@gmail.com



Page 41to45




Daga marubucin
KAUNAR UWA
UMAR FAROUQ and now
TARTSATSIN WUTA
(adventure story)






Lokacin da su sarki dizlan suka fita daga birnin kisra suka nausa cikin daji sai suka wanzu suna masu kara kaimin gudunsu dan zuwa su riski abokan gaba kana kallon fuskan sarki dizlan kasan ransa a bace yake a wannan lokacin da wani zai masa mgn sai dai uwarsa ta haifi wani haka suka yi ta tafiya baji ba gani duk da acikin hasken farin wata suke tafiya








A daya bangaren kuwa koda gimbiya sima ta gane cewa su Aryan sun yi bacci sai ita kuma ta kasa bacci sakamon rashin yarda da gurin da suke dan tana ganin a koda yaushe sarki dizlan zai iya musu aike koh na aljani koh dai na wani mugun abun anan ta dauko mudubin tsafin ta ta shafeshi nan take hoton duk abinda ya faru a burnin kisra ya hasko a mudubin har zuwa sanda sarki dizlan ya had a dakaru suka taho gunsu nan take taji zuciyarta ta buga dan tasan indai aka kuma haduwa to da matsala tunda Aryan bazai Iya yaki ba sakamakon kafadar Sa da take da ciwo duk da tasan shima sarki dizlan ba wani karko zai yi ba tunda Ciwon Sa ma yafi na Aryan hadari sosae amma sai tayi tunanin indai aka hadu bai zama lalle su sha ba duk da tasan bazai iya kashesu ba amma ae sarki yawa yafi sarkin karfi kawai sai ta fara tunanin mafita bata gushe tana wannan tunanin ba kuwa mafita tazo mata mafitar kuwa ita ce kawai ta kira hadimin ta acikin aljanu tazo ya karasar da su birnin hairil salad kafin sarki dizlan tazo ya tadda su anan abinda yasa kuwa tayi wannan tunanin kuwa shine ba ta yadda za ai Aryan ya iya tafiya a yau sai dai zuwa gobe kuma gashi rakib bazai iya giyashi yayi doguwar tafiya ba shiyisa ta yanke wannan shawara aiko bata tsaya wani jinkiri ba ta fita wajen tantin ta tsaya tana mai rufe idanunta ta daga kanta sama ta kwalla kira kamar hada DAMGASKUS DAMGASKUS DAMGASKUS ta fada sau uku nan take sararin samaniya ya chanja launi iska ta hado mai mugun karfi zuwa chan jimawa sai ga wata shirgegiyar halitta na saukowa kasa a hankali har ta gama saukowa daga nesa idan ka kalli wannan halitta sai kayi tunanin tsauni ne ya sauka agun aljani dangaskus yana da rankwalelen kai kuma a jikin kan ido dayane dashi sai wawakeken bakinsa yana da hannu guda biyu wato hagu biyu dama biyu yana da duka fukai guda goma sha hudu ko wanne bangare bakwai kenan idan aljani DAMGASKUS ya bayyana agu indai ya had a idanu da mutum suma yakeyi sai dai in mutum ya kasance jarumi na gaban kwatan ce aduk cikin sadaukan aljanu na wannan nahiya ba aljani da yakai aljani damgaskus karfi dantse juriya iya yaki duk cikin jinsin su tsoronsa sukeji banda wani aljani guda daya mai sunana muklus shidai muklus ya kasance dan gidan sarauta wato shine mai jiran gado tare da aljani damgaskus aka basu horon yaki da su abokaine amma akan wata budurwa guda daya suka bata da juna lbrn yana da tsayi readers ,








da zuwan wannan aljani sai ya duka kasa ya kwashi gaisuwa tare da fadin ranki ya Dade mai zan miki a cikin wannan tsohon Daren haka








Cikin kakkausar murya tace haba DAMGASKUS sai kace bakasan abinda yake faruwa ba a tsakanina da makiyi na yanxun na umarceka da ka gaggauta daukemu ka kaimu birnin hairil salad wato birnin su jarumi Aryan sabida a yanxun haka sarki dizlan yana kan hanyarsa ta zuwa nan domin ya riskemu






Koda jin wannan batu sai hawaye ya ciko da ga idanun aljani DAMGASKUS sannan yace ya shugabata ki sani cewa aduk duniya yanxun banda makiyin daya wuce sarki dizlan sabida shine silar rushewar farin cikina ya kashemin mata ta kuma amaryata Dana ke mugun so a duniya yanxun ni kadai na rage a cikin zuri ar mu ma tundaga wannan lokacin nayi alkawarin daukan fansa amma me sarki dizlan ya fi karfina amma Dana yi bincike naga zuwan wadannan tagwaye duniya sai nayi matukar farin ciki Wanda ban taba yin kamarsa ba a rayuwa ta na miki alkawarin ni zan bawa wadannan yata naki horon yaki ta yadda za su zama gawurtattun jarumai a duniya baki daya kuma nine zan musu rakiya dan nemo tsumin dodo ragazalu yanxun dai kufara nawa kaina mu tafi birnin hairil salad tukunnan koda gama fadin hakan sai gimbiya sima ta haye kansa ta zauna shikuma ya saka hannunsa ya dauko Aryan rakib da yan tagwaye ya Dora a gadon bayan Sa dukan su sai barci suke yi ba suma San abinda ke faruwa ba a hankali ya fara kada fuka fukan Sa ya tashi sama yana mai tsala axababben gudu tamkar tauraruwa mai wutsuya







Bayan kamar dakika Dari uku da sitti da tafiyar aljani DAMGASKUS sai ga rundunar sarki dizlan ta karaso gurin da zuwa ya kalli gabar da gamma kudu da arewa basu gimbiya kawai sai ya zare mudubin tsafinsa ya fara binchike anan yata duk abinda ya faru tsakanin su da aljani DAMGASKUS kuma a yanxun ma har sun isa birnin hairil salad cikin matukar bacin rai ya bada umarnin koh wanne dakare ya shirya daga nan birnin hairil salad ya nufa da yaki sai ya baje birnin zai dauko maciya amanarsa ya kashesu ya dawo gida daganan Zuwa chan tafiyace ta kwana biyu babu yada zango kunga kenan a na ukun zamu isa mu farwa birnin kafin muje chan ciwona ya warke kuma nasan shima abokin gabata NASA ya warke kinga saimu taba raini ni dashi baki daya yana gama fadin hakan ya kalli bangaren yama ya dausa cikin daji ba shiri suka rufa masa baya kamar wasu turuwai........................





Ni kawai comments nakeso shine zaisa na dora typing




Muje zuwa readers yanxu ma aka fara dan har yanxun yan tagwaye basu fara barna ba tukunna dai kubiyo ni da ruwan comments na biyoku da nest page





By fast class
🏀🏀🏀🏀🏀🏀
      🏀 🏀🏀🏀🏀
            🏀🏀🏀🏀

TARTSATSIN WUTA
(adventure story)
            🏀🏀🏀
     🏀🏀🏀🏀🏀
🏀🏀🏀🏀🏀🏀

Tsara labari da rubutawa

ALIYU ISHAQ
Β Β  (fast class )
________________________________

*AREWA WRITER'S ASSOCIATION*
_________________________________
*πŸ’¦{Arewa ginshiΖ™in al'ummah}πŸ’¦*
_________________________________
https://www.facebook.com/104534761033461/posts
arewawritersassociation@gmail.com


Page 46to50



Daga marubucin
KAUNAR UWA
UMAR FAROUQ and now
TARTSATSIN WUTA
(adventure story)




Dedicated to all my fans ina yinku oba ALLAH yabar kauna










Sai da su sarki dizlan suka shafe Sa a daya da rabi suna tafiya batare da an yada zango ba kwatsam suna cikin tafiya sai sarki dizlan yaga boka kailur ya bayyana a gaban Sa fuskan Sa ba Alamar annu ri sannan yace shin mai na fada maka ya kai aboki na shin ka manta na fada maka cewa bazaka iya kashe wannan jarumi dashi da matarka ba shin banjamaka kunne akan hakan ba amma kaje kayi ganganci kasani duk naga abinda ya faru tsakanin ka da wannan saurayin sadauki Barin ka nayi ka fara gwada wa tukunna kasani idan zakuyi yaki sau dubu da wannan yaron ba Wanda zai mutu sai dai ragas wadannan tagwayene kawai zasu iya kashe ka idan suka hada karfi da karfe nasan kasan cewa gimbiya sima ta hada kai da sarkin sadukai na aljanu wato damgaskus kasani cewa kafi karfinsa nesa ba kusaba amma bazaka taba iya kashe shi ba dan shima gimbiya sima ta bashi kariya a yanxun koh kaje birnin hairil salad bazakaga makiyanka ba aljani damgaskus ne zai tareku kuma idan kayi.yaki dashi kasani acikin Ku ba Wanda zai tsira sai kai kai ma din da kyar zaka tsira yanxun shawara daya ce kabari sainan da shekara goma sha biyar saika yi gagarumin shuri ka tunkari birnin hairil salad da yaki a wannan lokacin gimbiya sima ta ba yayan ta sirri kan tsafinta kuma sunsan yadda za a samo tsumin dodo ragazalu yanxun abinda zakayi shine sai sun tafi kai kuma zaka samu aljani mai karfin gudu kalan na aljani damgaskus ka bisu a baya sai sun sha wahalar kai kuma a. Wannan lokacin da suka samo tsumin zaka far musu kasani yin fada da dodo ragazalu kamar ka fito kace zaka yaki duniya ne idan kabisu a sannu ma zai kashe maka su kazo gida ka kashe sauran makuyanka wato su sarki uklan shikenan amma fah ni shawara na baka idan kaji kasani akab cikin dakarunka ba Wanda yasan da zuwa na sai kai kadai sabida haka ba Wanda yaki abinda mika tatauna ni da kai ni dai na barka lpy kafin lokacin zamu kuma saduwa idan da rai da rabo yana kaiwa nan ya bace bat kamar baki taba wanxuwa a gurin ba haka ya tafi yabar sarki dizlan da wasu wasi sai sake sake yakeyi daga karshe sai ya dauko mudubin tsafin sa yayi binchike sosae ya ga akwai kamshin gsky a mgnr abokin NASA kawai sai ya kada kan dokin sa yana mai bada umarnin a komai birnin kisra aiko duk suka biyoshi batare da kowa yasan dalili ba tunda wannan rana sarki dizlan yake ta shirye shirye zawan wannan rana kullum yana cikin binchike har wata yar rama yayi sabida tashin hankali
WANNAN KENAN








πŸ₯







Achan birnin hairil salad kuwa gimbiya sima duk taga abinda ya faru tsakanin sarki dizlan da boka kailur haka shima sarki uklan ya ga duk abinda ya faru a lokaci guda dukansu suka tuntsire da Dariya kamar bazasu daina ba daga chan sai sarki uklan ya ce lalle sarki dizlan mugun wawa ne ya yadda da mgnr abokin sa baisan Karya ya fada masa ba lalle sarki dizlan yana cikin tsaka mai wuya kuma yayi Babban kuskure kuskuren kuwa shine barin wadannan tagwaye su girma indai sun girma to sune ajalinsa koda jin haka sai gimbiya sima tace ya shugabana ina da tambaya shin mai sarki dizlan yayi wa boka kailur haka da har yake Dora shi a keken bera







Koda jin haka sai sarki uklan yayi murmushi yace lbr ne mai tsayi yata amma dai kisani kamar yadda sarki dizlan ya je kasarku ya kashe miki iyaye ya aureki ta dole shima haka ya yi wa boka kailur dan shi nashima yafi ciwo kina jina








Akwai wata rana lokacin sarki dizlan bai karbi sarauta a birnin kisra ba to sai mahaifinsa ya turashi koyon yaki da aikin bokanci daya tashi sai ya kai shi birnin Hindu gurin wani shahararren boka anan gidan suka hadu da boka kailur nan kuwa suka kulla abota ta sanadin halinsu dayazo daya na zalunchi bayan wasu shekaru da haduwar su sai dizlan ya gano abokin NASA na soyayya da wata tsaleleliyar budurwa a garin mai suna nuraima nuraima ta kasance kyakykyawar budurwa ajin farko dan aduk birnin Hindu yar sarkin garin ce kawai ta fita kyau da chan kailur yar sarkin yakeso amma dayaga wutsiyar rakumi tayi nesa da kasa sai ya koma kan nuraima kuma sai akayi dace itama tana matukar kaunarsa kuma kowa a garin najin tsoron sa sabida zalunchin sa koda sarki dizlan ya gano wannan soyayya sai ya fara tunanin yadda za ai ya rabasu tunda yasan sunyi nisa bazai iya rabasu ba kawai sai ya yanke shawarar tunda a shekarar karshe yake abun malaminsa to bari ya hkr yasan abinda zai yi aiko da shekara ta zagayo sai dizlan yayiwa kailur dabara ta cewa yaje bayan gari ya jirashi akwai wata kyauta daya tanadar masa zai bashi idan lokacin tafiyarsa yayi aiko ba musu ya tafi bayan tafiyarsa sai yaje gidan su nuraima ya kirata ya shaida mata cewa abokin sa na bayan gari yana jiranta shine yace yazo ya kirata bata kawo komai a ranta ba ta bishi da ya tashi sai ya chanza hanyar shi kailur ya fita ta kifar gabas shikuma sai yace mata yana kofar yamma alhalin a kofar gabas sukayi zai zo ya sameshi









Saida suka yi tafiya mai nisa suka shigo cikin duhuwa sai hira sukeyi data gaji sai tambaye shi shin bamuzo gurin bane kawai sai ya tuntsire da Dariya anan yake fada mata Karya ya mata kawai ta bashi abinda yakeso su
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment