Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

na gefe suna matsar hawaye.
Daga kansa yayi yana kallon Ladidi dake tsaye tsakanin wayoyin dake kewaye da gurin ta raba k'afafun ta gida biyu d'aya a cikin gidan d'aya a waje.

Sosai yake mamakin yanda a kayi ta hau gurin tunanin yake ya za'ayi ya fuzgota daga gurin, futa yayi waje da sauri, Haladu na tsaye hankalinsa na sama yana gadin LADIDI ko da zata fad'o sai ya tare ta.


Cikin ikon Allah hankalinta na cikin gidan General ya dauke mata hankali gurin magana, Hakkim yace da Haladu yayi masa dokin wuya aikuwa haka aka yi dokin wuya yayi masa jikin duguwar gatan gar akwai guraran rodi da a had'a dasu ba gurin gini nan Hakkim ya kama cikin dubara ya haure katangar hannunsa suka cake da k'ananun k'usosi jini ya fara zuba!

K'afar ta guda ya fuzgo da k'arfi ta kifo jikinsa suka fad'o k'asa tare. General da sauran mutanan gidan suka runtumo da gudu suna salati domin su duk a tunanin su ta fad'a ne kamar yanda take fad'a musu.

Sai suka gan ta kwance saman ruwan cikin Hakkim, Wanda yake mata wani irin mugun kallo na tsana idonsa yayi jawur!! Ga hannunsa yana d'igar da jini.

Ladidi idanunta a k'ek'ashe take kallonsa, babu alamun risina a tare da ita,Hakkim ya mike a zafafe! Ya watsar da ita a gurin.

Ta mike da sauri hade da d'ibar k'asar gurin kamar yanda ta saba ta watsa masa a jikinsa ta runtuma da wani irin gudu ta dauki hanya ...... Da gudu ya bi bayan ta, General ya zube a gurin hade da dafe kansa Cikin tsantsar tashin hankali.

Salima tace"Dady dama na fada maka wannan yarinyar zata iya d'ora wa mutum hawan jini Dady tun kafin ta jawo mana wani bal'in gwara gobe a mayar da ita gudansu.

Hajiya Asiya kuwa ta daina matsayar hawayen yanzu abun tsoro yake bata sosai take zargin yarinyar da motsuwar k'wak'walwa idan ba haka ba kuma to tabbas da akwai aljanu a kanta.

Gudu take kamar wata filfilwa, Hakkim ya k'ure gudunsa domi ya tadda ita Sam baya son ta futa titi a haka yasan ba k'aramin kunya bane a ganshi yana falfala gudu kamar wani zararre. Duk iya gudu irin na Hakkim kasa cin mata yayi, ya sare mutuka yanzu ya kara tabbatar wa da cewar yarinyar annoba ce a gare su.

Cak!!!! Ta tsaya jin haushin karnuka wan! Wan! Wan!wan! Haushin ya cika gurin.
Tana haki! Ta waiwaya bayanta ta hango Hakkim ya kusa cimma ta, ta kalli gabas kudu a rewa babu gurin b'uya ga karnuka sun taso mata, ihu!! Ta kurma hade da d'ora hannunta a kanta tana fad'in"Wayyo Allah Mai koko Wayyo na Iya shikkenan mun rabu da juna sun kawo ni gidan yankan kai, Dama sai da kika ce kar na zo nace sai Nazo shikkke....... Bata karasa ba ya k'araso gurin yana wani irin huci! Ya sanya hannunsa ya kwad'e mata bakinta da. Mugun k'arfi
Bakin ya fashe da sauri! Ta sanya hannunta ta Dan gwalo jini daga bakinta. Wani razanannan ihu! Ta kurma Wanda har sai da gurin ya amsa! Dan dai unguwar ma ta masu hannu da shuni ce ko wane gate a gark'ame da irin unguwar yaku bayi ne da tuni ai gurin ya cika da 'yan kallo.


Blet din jikinsa ya cire ya fara zabga mata a jikinta kamar Wanda Allah ya aikoshi, dukan ta yake babu sassauci ita Kuma tana ihu! Hade da zaginsa tana yi masa Allah ya Isa.

Bai fasa dukan ta ba har sai da yaji bakinta ya mutu ta kwanta a gurin tana nishi hade da ne kare kanta sannan ya mai da blet din jikinsa, ya bar gurin a fusace.



Motar su Dady ya ci karo da ita tsananin b'acin ran da ya ke ciki bai sa ya tsaya ya saurare su ba ya wuce abunsa.

Tun daga nesa suka hangota kwance hasken Fitilar motar ne ya nuna musu General ya kara sauri har suka Isa inda take kwance nuffashin ta na futa sama-sama a gigice general ya dauke ta ya shiga motar da ita.

Hajiya Asiya ta dawo mazaunin dravar ta kunna motar, da sauri General Yace. " Maza mu tafi babban asibiti yarinyar ta suma."!!! Hajiya Asiya ta k'ara k'arfin motar tana fad'in *"Innalillahi wa'inna ilahi raj'inun*







*BINTA U ABBALE*
https://m.facebook.com/Zamaniwritesassociation

*🌚🌚🌚LADIDI🌚🌚🌚*
*πŸ§Ÿβ€β™€πŸ§Ÿβ€β™€πŸ§Ÿβ€β™€K'WADAGAπŸ§Ÿβ€β™€πŸ§Ÿβ€β™€πŸ§Ÿβ€β™€*



~*NA*~
_BINTA UMAR ABBALE_




*ZAMANI WRITES*
*ASSOCIATION🀝🏻*
___________________
```We are here to educate motivate and entertain our readas```
____________________
*Fadima Ummul hasnaini ya tsokar jikin Habibi*
____________________




*DEDIGATED*
*TO*
*RAHIMA ALIYU*
*ABUJA*




```BISIMILLAHIR-RAHAMANIR-RAHIM ```






*πŸ…Ώ37*





D'aya daga cikin likitocin dake duba LADIDI ne ya futo yana goge gumin fuskar sa, General ya mike da sauri tare da tarar gabansa hankali a tashi yace." Dr ya jikin yarinyar ne."?

Cikin yanayin damuwa Dr ya kalli General yace." Gaskiya yarinyar tayi dogon suma sosai duk iya bakin kokarin munyi domin ta dawo hakan bai yi wu ba, but kwantar da hankalin Ku, zata dawo normal insha Allahu daga nan zuwa gobe."


General ya share gumin dake tsatstsafo masa a goshinsa hankalin sa a tashe yake fadin"Innalillahi wa inna ilahi raji'un."


Dr ya gyada kansa cike da jimami yace." Yarinyar ta furgita ne kuma anyi mata dukan mutuwa sosai ta jikkata gaskiya duk Wanda yayi mata wannan duk bashi da imani, yarinya k'arama anyi mata duka irin na masu laifi."


General Yayi shiru domin bashi da ta cewa Dr ya girgiza kansa kawai ya bude ofis d'insa ya shige. General zubewa yayi a gurin hankalinsa ya tashi mutuka yanzu yake da ya sanin dauko yarinyar ganin tsautsayi yana nema ya haushi.



Hajiya Asiya tazo ta zauna kusa dashi tare da dafa kafad'ar shi muryar ta a sanyaye tace." Dady ka kwantar da hankalin ka insha Allahu komai zai zo da sauki na lura yarinyar bata da cikkakiyar lafiya, sai futuna da ibilici ina ganin Idan komai ya dai-dai ta mai zai hana ka kirawo Liman ya duba ta sosai nasan Idan akwai wani jinnu da suke damunta to zai fada kaga sai mu san ta inda zamu fara."



General ya dago kansa yana kallon matar tasa Yace. " Babu babban Mara hankali irin Hakkim da zai kama d'iyar mutane ya dinga jibga kamar Wanda Allah ya aiko shi, yanzu idan wani Abu ya samu yarinyar ba fata nake ba, in je in ce da iyayen ta me."?



Hajiya Asiya tace." Dady ka manta Halin yarinyar ko? Ni a ganina abunda Hakkim yayi mata shine dai-dai in ba haka ba baxa ta tsaya ba, yanzu idan ta gudu ta ina za mu fara neman ta cikin wannan gari mai girman gaske."



General girgiza kansa kawai yake tabbas shawarar da matar shi ta bashi itace abun dubawa tunda ya Riga ya dauki amanar rike yarinyar tsakani da Allah kuma ya dauko ta daga gurin iyayen ta Dole yanzu duk wani nauyi ta yana kansa.




Hakkim kuwa ranshi a masifar b'ace ya koma gida diract part d'insa ya wuce Salima ta biyo shi a baya tana tambayar sa ladidi wata irin shegiyar tsawa ya buga mata, wacce ta sanya ta rugawa da gudu part dinsu. Ya ja tsaki ya wuce part dinsa .

takalmin shi bai cire ba ya kwanta rigingine kan bed dinshi yana sakin ajiyar zuciya kana ganinshi kasan a cikin b'acin rai yake, ya rasa wane irin mutum ne Dady dinshi daka ganin sarki fawa sai zak'i, haka kurrum ya d'ako musu alak'ak'ai cikin gida, Ladidi Annabo ce,domin shi kwata-kwata baya yi mata kallo mai hankali ta yaya zasu yi rayuwa da mahaukaciya, dole ma ya bar garinan. Domin bazai iya zama inuwa guda da yarinyar ba, yana jin wata irin tsanar ta cikin zuciyar sa.



Kusan awar shi guda a kwance yana sak'e-sak'e daga bisani ya mike jikinshi duk babu dad'i ya fada toilet dinshi ruwa ya hada mai dumi yayi wanka, ya futo daure da towol mai girma wani rataye a wuyan shi, ko mai bai shafa ba, ya zura boxer hade da singilet yayi kwanciyar shi kan bed yana lumshe idon sa, wayar sa ce ta fara ringing yana dubawa yaga Dady ne , gyada kansa yayi yace." Dady kai ka jawo wa kanka wannan masifar wallahi babu ruwana, gobe iwar haka ma ni na bar garin."



Har wayar ta tsinke ba dauka ba, wani kiran ya k'ara shigowa hararar wayar yayi, yace." Nasan kan yarinyar zai yi min magana yanda na kwanta ina hutawa ta,wallahi bazan tashi ba." Juyawa yayi hade da gyara kwanciyar sa.



General ya kira wayar yafi sau biyar Hakkim bai dauka ba, kuma yana ji, Dan ma kar ya kashe wayar ne General din ya fuskanci wani Abu shiyasa ya k'yale ta, gobe yana tambayar sa yasan k'aryar da zai shirga masa, amma shi babu yadda za'ayi ya tada hankalin sa, kan wata banzar yarinya kidahuma 'yar kauyen k'ayau.



General da Hjy Asiya haka suka kwana cikin tashin hankali da damuwa, b'angaran Hakkim kuwa baccin sa ya shirga babu abunda ya dame shi, a subar fari ya tashi, yayi wanka kamar yadda ya saba ya wuce masjid, k'arfe shida shaura ya shigo gidan, ya fara shirinsa domin Sam baya so Dady ya dawo ya tadda shi gidan, yasan wata masifar ce, cikin wasu suit ya futo black and White sunyi mishi kyau sosai ya matse wuyan shi da necktie lafiyayar sumar shi tasha gyara sai kyalli take, kafarshi sanye da helf cover black sai shaining yake yi yayi kyau sosai kalar fatar shi ta futo kamar wani black america haka ya futo hannunsa rike da wata k'aramar jaka.




Salima da Baito mai aiki suna Palo Baito na gurin daining tana gyarawa Salima kuwa na zaune kan kujera cikin damuwa kana kallonta kasan bata yi baccin kirki ba, ta na ganshi ta sauke ajiyar zuciya hade da fadin "Broth barka da Safiya ."



Nazarinta yake ganin yanda tayi figai-firgai yace." Barka kadai, ni zan wuce idan sun dawo ki Sanar musu, bakinta na rawa tace"Bro ladidi fa har yanzu bata farfad'o ba." Wata irin muguwar tsawa ya buga mata tare da fadin"Don Ubanki ni ina ruwana! Da zaki wani dame ni ki damu kanki, ko wa ya siyi rariya yasan zata zubda ruwa kuje Ku k'arata da ita tunda kune kuka dauko ta ni nayi tafiya, wallahi ko da wasa kika kara yimin maganar mahaukaciyar yarinyar nan sai na ballaki! Wallahi Idoit kawai !."""
Yana gama maganar shi ya fuce a fusace!

Salima tayi tsuru-tsuru tana bin hanyar da wuce da kallo ita kanta tana jin tsoron masifar yayan nasu hade da b'acin ransa, lallai yau zuciyar sa a tunzure ta, tana ganin ko Dady ne yayi masa magana zai iya fada masa magana me zafi indai akan LADIDI ne.







*BINTA U ABBALE*
https://m.facebook.com/Zamaniwritesassociation

*🌚🌚🌚LADIDI🌚🌚🌚*
*πŸ§Ÿβ€β™€πŸ§Ÿβ€β™€πŸ§Ÿβ€β™€K'WADAGAπŸ§Ÿβ€β™€πŸ§Ÿβ€β™€πŸ§Ÿβ€β™€*



~*NA*~
_BINTA UMAR ABBALE_




*ZAMANI WRITES*
*ASSOCIATION🀝🏻*
___________________
```We are here to educate motivate and entertain our readas```
____________________

```Shugabar mataye Binta taga mala'ika da idonta, ba shamaki ba tafinta, har ya aike ta gun Habibi```
*Fad'ima Umul Hasnaini ya tsokar jikin Habibi*
______________________



*DEDIGATED*
*TO*
*RAHIMA ALIYU*
*ABUJA*




*BISIMILLAHIR-RAHAMANIR-RAHIM*





*πŸ…Ώ39*





Cike da rashin tsoro general ya tsuguna kusa da Ladidi dake wani irin Abu da idonta, yace." Kuji tsoron Allah da manzo sa ku rabu da wannan 'yarinyar marainiyar Allah me tayi muku? Kuka yi aure kuka tare a kanta, shine me zaku cewa ubangji ranar alkiyama."?

"Hahahahaha!! Suka ji wata mahaukaciyar dariya, Ladidi nayi, tafi minti uku tana yi daga bisani tayi d'if!! Gurin yayi shiru
Lokacin Salima sai da ta saki futsari a wando. Tsoro duk ya cika zuciyoyin su daga ita har Momyn ta Hjy Asiya..... General ya fara tofa mata dukanin addu'ar da tazo bakin sa. Ya kai
Kusan 30minutes tsugune gaban Ladidi yana tofe jikinta da addu'a, sannan ta bude idon ta, gami da yin wata irin mik'a! Ta mike zaune zumbur!
Kuka ta fashe dashi tana waige-waige a gurin. Su din dai ta gani a tsaitsaye sun zuba mata ido.
Take kukan ta ya kara k'arfi tana nuna kafarta duk bakinta yayi mata nauyi so take tayi magana amma ta kasa.

General ya fahimci ta dawo dai-dai sai ya fara kokarin daukar ta cike da tausayin ta, domin ya lura aljanun da suke kanta manya ne sosai Dole ta kasa motsa jikinta.

Jiki babu k'wari su Hjy da Salima suka bi bayan general Wanda ke rungume da Ladidi a jikinsa ya nufi cikin gidan da ita.

Hjy da Salima Dan babu yanda zasu yi da sun hana general shigar musu da Ladidi gida saboda tsaro , Salima tsoron mutum me aljanu take.


Kan kujera ya aje ta ya kara k'arfin AC ya kalli Hjy Asiya tare da fad'in ki hada mata ruwan ka tayi sai taci abunci."

Hajiya Asiya ta wuce kicin jikinta duk babu k'wari, ita kuwa Salima zama tayi ta k'urawa Ladidi ido babu abunda take tsoro da fargaba sai dare domin tasan Dady zai ce Dole sai ta kwana d'aki daya da Ladidi.


Kamar me k koyon magana tace"Zan sha ruwa."
General da kansa ya nufi furji ya dauko mata ruwan gora mai sanyi bayan ya bude murfin ya mik'a mata.
Tunda ta kafa kanta kan robar ruwan bata d'ago ba sai da ta shanye shi tas! Sannan ta jefar da robar hade da yin wata shegiyar gyasa lumshe idonta ta fara yi, tuni ta b'ingire a gurin nannayaun bacci yayi gaba da ita.

General ya saki ajiyar zuciya ganin bacci ya dauke Ladidi ya mike yana niyyar barin gurun, da sauri! Salima ta mike hade da rike rigar shi ta baya tana tafiya tana waiwayen Ladidi.
General ya juyo yana kallonta da murmushi a fuskar sa yace." Na lura dake da Momy taki tsoron Aminta kuke yi tun d'azu naga sai zare ido kuke yi."
Salima tace."Wallahi Dady da gaske tsoran ta nake ji, yanzu haka jikina a jike yake ban San sanda futsarin tsoro ya kuffe min ba." Dariya general yasa yace." Ho Salima sarki tsoro ki daina jin tsoron Aljan babu abunda ya Isa yayi miki Wanda Allah bai miki shi ba, ke kike da makamai a hannun ki, kina fara karatun ayatul kursiyo sai gudu." Salima tace"Duk da haka dai Dady wallahi tsoro nake ji, mu kam Big broth ya jawo mana, Dady kana jin abunda fa aljanun suke cewa zasu masa, wai sai sun dauki fansar abunda yayi mata."
Murmushi general yayi a lokacin da suke taka steps yace." Duk abunda suka yi masa shi ya jawo kanshi babu ruwana. " cikin Salima ya karta!!! Cike da tsoro tace"Please Dady ka basu hakuri don Allah kar su tab'a mana bro." Salima iya Gaskiyar ta take magana. General kam dariya yake mata sosai har suka hau sama, ko wanne ya shige dakin shi.

Hajiya Asiya na futowa daga kicin taga parlor babu kowa Sai Ladidi a kwance kan 3sitar wata irin fad'uwar gaba taji, da sauri ta fara hawa step ta waiwayen Ladidi dake kwance

General ta samu zai shiga bathroom tace"Yallab'ai gashi ruwa har yayi zafi kuma naga tana bacci a k'asa. " Yana kokarin shiga toilet din yace." Ai bacci shine samun nutsuwar ta, ki k'yaleta tayi kar Wanda ya tashe ta, sai ta tashi Dan kanta. "

Hajiya Asiya ta zauna bakin gado tana al'ajabin wannan Abu.


******

Hakkim kam ya manta da wata Ladidi don Ku da suka gama waya da Dadyn sha. Ya fada masa tayi dogon suma bai damu ba, shi tunda ya bar k'asar shikkenan, suje su k'arata su da suka daukota.

Wasu had'andun gidaje ne company da suke wa aiki ya raba musu kyauta, plate uku ne shi d'aya Salmanu d'aya Bash d'aya, gidane me girman gaske babu abunda babu na more rayuwa swimming shi kanshi uku ne da gurin motsa jiki uku gurin wassanin yara iri-iri a gurin. Yanda company ya basu gurin zasu iya yin aure su tare da iyalinsu zaman america har a bada su da iyalinsu.
Tofa Bash tun da suka je ya samu sake wa ya fara sha'anin shi da 'yan mata kala-kala, shi kuwa Salmanu baya Neman mata amma fa shaye-shaye babu irin Wanda baya yayi, Bash kullum da daddare yana night club, sai dare ya raba yake dawo wa gida, wataran Salmanu yana binsa yaje yayi kallo ya dawo gida a buge.

Hakkim ya rasa yanda zaiyi musu kullum Cikin yi musu masifa yake sai dai suyi masa dariya kawai suna fadin "Har yanzu kanshi a tukunya yake bai san yaya duniya take ciki ba.

Tunda suka Isa garin na america yau kwanaki takwas kenan wayoyin sa suke kashe, yau ta kama Sunday babu aiki duk suna gida yace bari ya kunna wayar tasa, dama saboda fad'an Dadyn d'insa ya kashe wayar ya San dai yanzu ya huce fushin sa.




*24/11/2019*




*BINTA U ABBALE*
https://m.facebook.com/Zamaniwritesassociation

*🌚🌚🌚LADIDI🌚🌚🌚*
*πŸ§Ÿβ€β™€πŸ§Ÿβ€β™€πŸ§Ÿβ€β™€K'WADAGAπŸ§Ÿβ€β™€πŸ§Ÿβ€β™€πŸ§Ÿβ€β™€*



~*NA*~
_BINTA UMAR ABBALE_




*ZAMANI WRITES*
*ASSOCIATION🀝🏻*
___________________
```We are here to educate motivate and entertain our readas```
____________________





*DEDIGATED*
*TO*
*RAHIMA ALIYU*
*ABUJA*




*BISIMILLAHIR-RAHAMANIR-RAHIM*





*πŸ…Ώ40*





Ko da General yaga kiran wayar Hakkim kin dauka yayi. Hajiya Asiya ta shigo ta same shi zaune ga waya nayi tace"Dady kana ganin kiran waya fa." Yace." Ki dauka in zaki dauka yaron ki ne sai Yau ya ga damar tunawa damu. " Hajiya Asiya ta dauki wayar tana fad'in "Ni kam zan dauka mu gaisa dashi." Hararata general yayi tare da fadin" Ke akan 'yaya bakya jin kunya ai." Dariya tayi ta d'aga wayar, b'angaran hakkim kuwa jin muryar Maman shi sai ya saki fuska cikin shagwaba yace." Mama Duk kun manta dani ko? Sai da na gaji don kaina na kira wayarku babu Wanda ya kirani yaji ya na sauka lafiya." Hjy Asiya tayi 'yar dariya tare da fad'in"Nasan kana cikin koshin lafiya my son, duk laifin ka ne, kaje ka sumar da yarinyar mutane ka gudu yanzu inda bata dawo nutsuwar ta ba me zaka ce umm? Don Allah ka rage zafin zuciya myson." Yace." Momy daga taimako sai ace na sumar da ita, ni wallahi da zaku bi tawa da Ku mai da yarinyar nan domin Zata jawo muku masifa." Hjy ta kalli gen dake kallon TV tana jin tsoron kar yaji abunda hakkim din yake cewa, da sauri ta katseshi ta hanyar fadin"Kai ka fiye Abu myson babu wani Abu insha Allah." Yace." Shikkenan tom ni dai babu ruwana inanan." Dariya Momy tayi tana tambayar sa aikinsa yace." Alhmdullahi Momy komai ya kammala muna aiki har sun bamu gurin zama. " Momy tace"Tom Allah ya taimaka yayi jagora ." yace." Dady ne."? Gashinan zaune." Yace." Yawwa bashi wayar mu gaisa. " general ta mik'awa wayar ya karba a nutse suka gaisa dashi ya tambaye shi aiki kamar yanda Momyn shi ta tambaye nan yayi masa fatan alkairi sannan suka yi sallama.

****
*K'auyan d'an kunkuru*

Tunda Ladidi tq bar K'auyan Dan kunkuru hankulan jama'ar garin ya kwanta kowa ya sake yana rayuwar su nan suka k'ara tabbatar wa da cewar Ladidi annoba Ce a garin, wasu kuwa fad'i suke ai Mai koko ta tura Ladidi birni domin tayi iskanci ne wasu kuwa saboda jahilci cewa suke yi ai Mai koko da D'alha sun siyar da Ladidi saboda su hutawa da masifa kowa da abunda yake cewa. D'alha ya samu aiki a cikin birni sai ya daina sana'ar sai da d'ata da gobe yana zuwa cikin gari yayi sati d'aya biyu uku ya dawo gida, Mai koko kuwa har yanzu tanan tana sana'ar kokon ta, tayi kewar Ladidi ta gaji wani lokacin in ta tuna da ita har hawaye take yi tana tunanin ko a wane hali take ciki oho, gashi D'alha baya zama amma tayi alk'awarin wannan dawowar in yayi dole zata turasashi ya kai ta inda Ladidi take ta ganta.


****

Yau watan Ladidi biyar a abuja za kuso kiga yanda ta sanja tayi wata kiba mai ban sha'awa farar fatar ta ta murje, duk wannan ramar babu ita sumar kanta ta futo sosai domin har tafi ta da, sai dai ko da wasa bata bari a tab'a mata kanta da sunan kitso duk ranar da akayi tsautsayin tab'a kan kuwa aljanunta sai sun buge ta yini suke yi Abu d'aya dole sai an kira malamin dake tsaye a kanta yazo yayi mata addu'oi sannan suke gusawa ta kwana tana bacci sai don kanta ta tashi.
[11/28, 9:34 AM] BintuUmarAbbale Shiyasa suke taka tsantsan da abunda zai bata mata rai indai tace bata son Abu to Dady zaiyi ta fada kar ayi mata shi, lokacin general ya sanya Yusuf dake gari ya nemo mata makaranta mai tsada akayi komai da komai general da kanshi yake kai ta ya dauko ta duk da cewa akawai direbobin sa kusan uku, shi dai bukatar sa Aminatu ta samu nutsuwa, cikin ikon Allah da taimakon Liman Ladidi ta samu ta nutsu ta daina shirme da shiririta yanzu kallo ma bai dame ta ba kullum in ta dawo daga makaranta suna tare sa Salima tana nuna mata abunda bata gane ba.
Yusuf dake shirin kai kud'in aure yaji duk duniya babu yarinyar da yake so kamar Ladidi yana mamakin asitaccan kyawun ta don a k'auye ta ke ne shiyasa komai ya b'uya, sai ya zamana bashi da gidan zuwa sai gidan su Hakkim yana fakewa da cewa yazo gaishe da General ne, nan kuwa Ladidi yake karewa kallo dukaninsu basu gane ba, lokacin suka yi wata irin sha kuwa da Ladidi itama in bata ganshi ba ta dinga cigiyar sa kenan..... Yusuf ba kullum suke waya da Hakkim sai jefi-jefi domin wani lokacin shi hakkim din bashi da time kullum suna aiki yafi samun sakewa Duk weak end sai su sha hirarsu a waya yayi ta tsokanar sa cewar ina bagidajiyar budurwar sa, shi kam Yusuf dariya yake yana fadin "Na wuce babinta yanzu na sanja wata zukekiya zan turo maka hotonta ma ka gani." Hakkim mamaki yake sosai yace."Yanzu duk irin son da kake wa Naja'atu ka daina kalli ka cika mayaudari." Yusuf dariya yayi yace." Na samu wata wacce ta fita komai da komai akan me bazan rabu da ita ba." Tsiya Hakkim yake masa yace ." ka turo min inga hoton yarinyar da ta rusa gwamantin Hafsa a zuciyar ka." Yusuf Yace. " zan turo maka amma ba yanzu ba." Haka suka yi sallama cike da barkwanci da kaunar juna.







*28/11/2019*





*BINTA U ABBALE*
*🌚🌚🌚LADIDI🌚🌚🌚*
*πŸ§Ÿβ€β™€πŸ§Ÿβ€β™€πŸ§Ÿβ€β™€K'WADAGAπŸ§Ÿβ€β™€πŸ§Ÿβ€β™€πŸ§Ÿβ€β™€*



~*NA*~
_BINTA UMAR ABBALE_




*ZAMANI WRITES*
*ASSOCIATION🀝🏻*
___________________
```We are here to educate motivate and entertain our readas```
____________________





*DEDIGATED*
*TO*
*RAHIMA ALIYU*
*ABUJA*




```BISIMILLAHIR-RAHAMANIR-RAHIM ```





*πŸ…Ώ41*





A takaice dai sai da Hakkim yayi shekara guda sannan ya dauki Hutu ya fara shirye-shiryen zuwa gida Lokacin ya kara wani kyau da waye wa.... Ya fara soyayya da wata Aboki yar aikinsa 'yar Ghana Sarah kenan tun da taga Hakkim ta kwallafawa ranta shi. Tun Yana share ta har dai yaji ta kwanta masa da ya fuskanci tana da nutsuwa da kamun Kai sam bata iya shirme irin na 'yan matan ZAMANI ba. Yaji zai iya auranta ko don kyawawan haleyen ta. Ganin ya dauki Hutu yasa Sarah itama ta dauki Hutu a rana daya suka tafi filin jirgi sukayi sallama da juna kowa ya nufi kasarshi cike da kewar juna.


Labarin zuwan Hakkim gidan yayi mugun d'agawa Ladidi hankali domin mata mance dashi ba s gidan sosai yanzu ta tsani abunda zai sake hada ta dashi ko da can ma rashin hankali ne amma yanzu ji take bata da babban makiyi kamar shi.... Duk taki sakewa a gidan Sai nukufurci take yi, Cikin su babu Wanda ya fahimci abunda take wa fushi Hjy Asiya dai hankakin ta ya tashi tana jin tsoron kar aljanu su buge ta domin duk ranar da ta tashi da fushi da nukufurci yini take tana tayar da aljanu sai an dauki malamin ta sannan suke gusawa,
DOWNLOAD
DOWNLOAD

1 Comments On LADIDI KWADAGA
avatar
north

1 year ago

Reply

dadi

Please Login or Register in order to submit comment