Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

dashi, ya kalli Mutari mai nama dake hada-hadar sallamar jama'a yace"Mutari"!!!!!





*COMMENT VOTE AND SHARE*
[9/23, 7:47 AM] 8k: https://m.facebook.com/Zamaniwritesassociation

*🌚🌚🌚LADIDI🌚🌚🌚*
*🧟‍♀🧟‍♀🧟‍♀K'WADAGA🧟‍♀🧟‍♀🧟‍♀*




*NA*
_BINTA UMAR ABBALE_
~*®BINTUBATULA👄*~



*MARUBUCIYAR*

```NANA KHADIJA```
```YARO DA KUDI```
```GIMBIYA BALARABA```
```TSANTSAR BUTULCI```

_*LOODING:*_
_*{LADIDI K'WADAGA🌚}*_




_*ZAMANI WRITES ASSOCIATION🤝🏻*_

_______________________
```We are here to educate motivate and entertain aur reades```
_______________________





_*DEDIGATED*_
*TO*
_RAHAMA ALIYU_





```Komai yayi tsanani yana tare da sauk'i, cikar muminin mutum yarda da k'addara mai kyau da mara kyau, idan ubangiji ya jarrabe ka, da musiba ka karb'a hannu biyu kar kace wani ne yayi ma, ko da wani mutum ne silar faruwar haka to kasani babu abunda bawa ya Isa yayi face da sanin mak'agin ka, Ubangijin baiwa kenan alimul gaibu washahadati, ka mik'a masa al'amarin da sannu zai yaye maka damuwar ka, Allah kasa mu dace```






_*BISIMILLAHIR-RAHAMANIR-RAHIM*_





*🅿4*





Da sauri Mutari ya juyo jin irin kiran da Halliru ya kurma masa, baki na rawa yace"Akwai wanda yazo gurin nan bayan naje guri Umaru mai rake yanzu"?

Cikin mamaki Mutari yace"Gaskiya babu wanda yazo kan kayan ka ina kallo tun d'azu"

Kamar ya fashe da kuka yace"Zo kaga abunda akai min"
Mutari ya baro gurin sa da sauri yazo yana dubawa,, salati yasa yana mamaki tare da fad'in"Wannan aikin Ladidi ne wallahi, d'azu ba kaje har inda suke ba, ina jin kana zaginta" Halliru yace"To kuma da kace baka ga wanda yazo gurin ba"

"Tabbas ban ga kowa ba, amma na tabbatar da cewar Ladidiya ce zatayi maka wannan aikin, wallahi kasan ta kamar aljana take, sam ba'a ganinta a guri" Cikin fushi Halliru yace"Billahillazi sai sun biya ni kud'in nono na, idan ta saba yi wa wasu suna k'yaleta to ni wallahi bazan d'auki asara ba"

Murmushi Mutari yayi yace"Shiyasa d'azu kamar in ce maka kar kaje inda suke saboda nasan halin yarinyar bata da mutum ci wallahi shiyasa kaga ni bana shiga sabgar ta, ko kaman ta lokacin da ta watso min ruwan kwata kaina kasan ranar har nama da gurasa basu tsira ba sai da ruwan kwatar ya same su,, ko da na je na fadawa kakarta hakuri kawai ta bani, da k'yar na kara tayar da wani jarin"


Halliru ya tsuguna yana goge gumi, Ladidi ta kassara masa rayuwa ta rusa masa jarin sa, yau-yau d'in nan ya d'auko sabon nono duro guda dubu goma sha biyu yarinyar nan ta zuba masa k'asa a ciki,, kewaye shi sukayi suna bashi hakuri wasu na bashi shawarar kawai ya tafi ya fadawa mai gari a bi masa hakkin sa.


Tana tafe tana d'aura zaninta,, gami da kad'e ragowar k'asar dake jikin zanin,, ta gyara d'aurin d'ankwalin ta,, ta cigaba da tafiya fagam-fagam! Ko tsoron dare ba tayi, Tara da rabi na dare, haka ta dunga wuce majalisa ta maza babu abunda ya dame ta,, har ta karya kwana zata nufi gida sai ta canza shawara juyawa tayi ta koma da baya, kwanar gidan kallo ta nufa,, tun daga nesa ta gango matasa sun cika rumfar kwanon ga hasken wuta nan tar! Masu gyad'a da daddafan k'wai da saurarnsu sai cini ki suke,, bayan gurin kallon bola ce,, gashi ba wani dogon gini bane wani gurin ma da langa-langa a ka rufe,, a hankali ta hau kan bolar ta daddafa ta d'ane kan k'aramar katangar,, kanta ta zura tana lek'awa, aikuwa taga matasa sun cika gurin suna zaune kan bainci wasu ma basu samu guri ba, suna tsatstsaye sai ihu! Suke da alama film din ya d'auko dad'i, sosai take zura kanta domin taga wane irin film ne da ake ihu!! Wani saurayi ne ya kare mata da tsahon sa, ji take kamar ta sauka ta zabga masa mari,, ihun da sukeyi yana hana aji komai sai wani take take ji babu alamun k'usha-k'usha,, kunne ta kasa sosai lokacin da Taji wannan saurayin yana magana dana kusa dashi "Gaskiya ina son film d'in nan wallahi, Sharukahn ya iya soyayya , nifa lokacin da ya rungume ta, he da na kusa suma dan dad'i wannan film din yayi kyau wallahi" Dariya d'ayan yasa yace" Ya sunan film din ma"? "Khoch-khoch hotaih" Hahahaha Gaskiya film din yayi ko nawa ake ce zan biya domin in kalle hi"
Ihun!! da suka ji ne yasa suka mai da hankalin su kan Tv,, Ladidi tace"Hegu "yan iska ni da nasan ba na fada bane ma bazan zo b.... Maganar ta ta katse lokacin da Allah ya bata ikon hango akwatun tv an hasko Sharukan da kajol suna soyyaya da rungume-rungume! " Kan Uba!! Ta kurma wani uban zagi,, tsaki taja tana k'okarin dura kasa tace"Allah wadaran in tsaya in kalli wannan iskancin, nifa shiyasa na tsani wannan Dan film din gwara Salman kan,, yana da mutum ci,, dura tayi k'asa tana Jan tsaki sai mita take da ta sani bata zo ba, inda ta San ba fim din fada bane,
Shiru gurin duk masu saye da siyarwa dake gurin sun tashi,wasu ma har sun soma futowa daga gurin kallon dana film din yazo karshe, ko a jikinta, ta kama hanyar gida fud'un-fud'un,, kamar daga sama, taji an cafki hannuta, ta juya a fusace! Ilu ne ya ke mata wani kallo yana lashe baki. Hararsa tayi tace"Sakar min hannu ko in ci abu ta kazar ka" Ilu yace"Ni kike zagi takand'a" ? Fuzge hannuta tayi a fusace! Ta tsani ya kira da wannan suna wai takand'a, tace"Uwarka ce takand'a bani ba"

Mari ya kai mata, ta kauce da sauri,, hannuta yaja da k'arfi ya na kokarin kai ta wani lungu ta turje tana zagin sa,, yace"Dama neman ki nake ruwa a jallo Dan uban ki, d'azu kin fasawa k'anwata baki ranan kin zage ni ,to yau zaki gane kuran ki" janta yake tana turjewa, gami da durzar k'asa da kafafun ta, duk k'arfin sa sai da ya sare, ya kama haki!! Tace"Sake ni ni ba "yar iska bace"

Yace"Sai ki gayawa wanda bai sani ba, Dan uwarki daga gidan Uwar ki kike shegiya jiki duk jijiya sai k'arfin tsiya"

"Uwarka ka zaga ba tawa ba" tafad'a a fusace! Yace"Au! Baza kiyi shiru ba" ?

"Sai kayi shiru zanyi, kuma wallahi zaka San ka zagi uwata" "To me zakiyi Takand'a" ? yafad'a yana mata dariya ta k'arfin hali, domin duk ya gaji yau ya kara tabbatar da cewar yarinyar ba ita kadai bace,, shamtar sa tayi yana fad'in "Zaga kuwa abunda zanyi yanzu" kafin ya ank'ara ta kwashe k'afafun sa da hannu daya ta zubar dashi a gurin ta falfala da gudu tana shek'a dariya babu ruwanta da dare.

Ilu ya rike bayansa yana rintse ido sosai bayan sa ya bugu da wani dutse ya Dade a kwance a gurin "yan gidan kallo na ta wuce shi a kwance,, cikin takaici ya mike tsaye yana da ya sanin kula Ladidi gashi ta ji masa ciwo a banza.



Mai koko na tsaye a soro cikin tararrabi, k'arfe goma da rabi na dare, Ladidi ba ta shigo gida ba, ta duba ko ina bata nan,, D'alha ya gama fad'an sa ya futa nema,, da ya d'auka abun wasa ne, sai da yaga an gama Taskar labarai, hankalin sa ya tashi, babu shiri ya bazama neman ta,, duk ya duba inda ya dace babu ita, ya nufo gida cikin gajiya da sarewa, zuciyarsa ta raya masa yaje ya duba gidan kallo, hanya ya kama yana tafiya yana addu'a a zuciyar sa,, da tafiyar ta ya gane ta,, b'uya yayi sai da tazo ta wuce sannan ya futo ya bi bayanta, abunda yasa ya b'uya shine yasan halinta in ta ganshi tana iya guduwa,, tana shiga soron gidan yana shiga,, ya sanya k'arfi ya k'wade mata k'eya d'ankwalinta ya fad'i kasa, ta rusa ihu! Wannan karon Iya bata hanashi dukanta ba, fad'i take " Kara mata ja'irar yarinya gantalalliya ta tayar mana da hankali"

Ladidi ta buga wani uban tsalle ta afka cikin gidan tana kurma ihu!! Kamar Wanda aka kona mata jiki da ruwan zafi,, d'akin Mai koko ta shige ta zura sakata tana ihu! Tun k'arfin ta.















*COMMENT VOTE AND SHARE*
[9/24, 10:59 AM] 8k: https://m.facebook.com/Zamaniwritesassociation

*🌚🌚🌚LADIDI🌚🌚🌚*
*🧟‍♀🧟‍♀🧟‍♀K'WADAGA🧟‍♀🧟‍♀🧟‍♀*




*NA*
_BINTA UMAR ABBALE_
~*®BINTUBATULA👄*~



*MARUBUCIYAR*

```NANA KHADIJA```
```YARO DA KUDI```
```GIMBIYA BALARABA```
```TSANTSAR BUTULCI```

_*LOODING:*_
_*{LADIDI K'WADAGA🌚}*_




_*ZAMANI WRITES ASSOCIATION🤝🏻*_

_______________________
```We are here to educate motivate and entertain aur reades```
_______________________



_*DEDIGATED*_
*TO*
_RAHAMA ALIYU_




_*BISIMILLAHIR-RAHAMANIR-RAHIM*_





*🅿5*





D'alha yace"Gashi kinji daga bakinta ko? can na gano ta ita kad'ai kan hanya tana tafiya ko tsoron dare ba tayi" Mai koko tace"Yanzu dai kayi hakuri mubar maganar sai da safe dare yayi" K'wafa yayi cike da takaici ya yar da abun dukan ya shige d'akinsa. Iya ta sassauta murya tana fad'in"Bude min kofa kinji ko,, bazan bari ya doke ki ba" Ladidi najinta tayi mata shiru,, "Na ce dake ya tafi d'akinsa ki bude min kofa nace ko" Banza tayi mata,, Sauraye sai cizon Iya suke babu abunda take so illa ta kwanta don tayi muguwar gajiya, rarrashin Ladidi take ta bude mata kofa,, k'eme-k'eme tak'i budewa, gyara kwanciyar ta tayi ta lumshe idonta bacci na fuzgarta, tana jin surutun da Mai koko take sam bai dame ta ba,, b'acin rai da takaici suka saka zuciyar Mai koko kamar ta buga gashi ko "yar tabarma babu a tsakar gidan ballantana ta shimfud'a ta kwanta,, ga duhu ga sauro ga danshin ruwa, bata so ta daga murya saboda dare kar D'alha yaji soro ta nufa a hankali ta kwanta kan dogon bainci da masu siyan koko suke zama tana addu'a a zuciyar ta, Allah ya shirya mata Ladidi.




*TUSHEN LABARI*


*K'auyan d'an kunkuru* k'auye ne dake cikin jahar kano,, ya had'a da Fulani a ciki amma ba sosai ba,, k'auye ne da yake da albarkar gonaki da filaye gami da manya-manyan bishiyun mangwaro ko ta ina,, Malam Labaran manomi ne wanda yake da gona guda d'aya yake noman d'orawa da gero a ciki,, da Abunda ya dogara kenan dashi yake ci da iyalinsa yake sauran bukatu, yana da mata d'aya da yara biyup
duk maza, matarshi sunanta Furera, mace mai Neman na kanta tunda aka kawo ta gidan Mijinta take sana'oi iri -iri , domin ta dogara da kanta, dansu na fari sunan shi Aminu yana da lalurar sikila sai Dan uwanshi D'alha shi lafiyan sa lau, abunka da k'auye San basu maida hankali gurin ciwon dansu ba, sai dai in ciwon ya motsa masa suyi masa jike-jike su bashi, Cikin hukunci ubangiji ya mike ya cigaba da rayuwa kana kallo Aminu kasan bashi da koshin lafiya tare suke tafiya gona da mahaifin sa,, ko sunje can ma baya iya aikin koma, D'alha ne me karfi,,

Malam Labaran yana da aboki D'an Fulani gurin zuwa kiwo suka hadu dashi,, inda Allah ya had'a jininsu ta kaisu ga had'a yayan su aure Aminu da Amina "yar Dan Fulani itama tana d'auke da irin lalurar Aminu, dake d'an Fulani ma'abocin jin redio ne, ya tab'aji suna fada cewar idan masu irin cutar zasuyi aure su dunga auran jinsu su, nan Labaran ya amunce, ya kuma Sanar da Aminu da Hurera duk suka amunce suna fatan alkairi,, lokacin yayi aka d'aura aure cikin aminci Amina ta tare gidan Mijinta Aminu inda gurinsa yake kewaye da langaga sai dai in zata shiga band'aki take futowa babban tsakar gida,, wata hudu da auran su, ciwon Aminu ya tashi kafin ayi wani yunk'uri ya galabaita mutuk'a jikinsa kamar babu jini ya dashe Tass,, wani makocinsu ya basu shawarar zuwa birni domin a duba shi, to suna cikin shirin tafiya ne, Allah ya amshi Abunsa , mutuwar sa ta girgiza mutane mussaman matarsa Amina tayi kuka har ta gaji " yan uwa na tasaunta tayi hakuri,, bayan sadakar uku kowa ya watse akabar mutan gida da kewar Aminu mutumin K'warai kenan, bayan sadakar ar'ba'in ne aka gano cewar Amina na da ciki, aikuwa Mai koko ta dunga kula da ita sosai har lokacin haihuwa yazo,, inda Amina ta fara zubar da jini abunda ba a so kenan ko mai lafiya balle mai sikila, hankali a tashe aka d'auke ta sai asibitin birni *(Murtala muhamad hospital)* ganin tana cikin halin taimako ne yasa suka shiga da ita dakin operation,, suka ce mijinta ya sa hannu aiki za'ayi mata,, Dan Fulani na kuka da rokon Allah ya sanya hannu Labaran ma ya sanya, to tun kafin a shiga da ita ta rasu,ganin cikin na motsi yasa suka shiga da ita cikin gaggawa aka Ciro yarinya mace, mai kama da uwarta.


Cikin halin damuwa nurse ta futo ta sanar dasu halin da ake ciki, sosai suka shiga rud'u da tashin hankali daga bisani suka hak'ura suka barwa Allah, suka karb'i gawar Amina suka tafi domin yi mata suttura, mai koko na rungume da jaririya tana kukan zuciya.



*****************

Mai koko ta d'auki son duniya ta Dora shi kan Amina da taci sunan mahaifiyar ta, dama kafin su baro asibitin sun duba ta sosai ko itama tana d'auke da ciwon sikila, Allah mai yadda ya so yarinya lafiyanta Lou sai dai k'ankanta, amma inda ans bata madara me kyau zata murmure.

Malam Labaran bai yi shawara da kowa ba yaje ya sanya gonar shi a kasuwa nan take aka samu mai siya kasan cewar gonar tana da kyau kuma tana da fuska akayi ciniki aka bashi kudinsa, ya nufi asibitin cikin gari duk abubun buk'ata ya siyowa Amina ya siyo mata madara masu kyau, da kaya niki-niki ya shigo gidan, Hurera tai yi mamaki sosai nan ya zauna ya warware mata komai, tace"Malam da kayi shawara dani da baza ka siyar da gonar ka ba" yace"Saboda haka shine mafuta asurinmu ya rufu, Kinga madarar nan tana da tsada idan ba haka ba bamu da kud'in siya, kuma ko d'aukar me shayarwa mukayi dole mu biyata, tace"Hakane kuma to Allah ya rufa mana Asiri,, nan Hurera ta kara k'aimi gurin Sana'a har ta kafu da sanar Koko da safe,, shi kuma D'alha yake sana'ar sai da D'ata goba da mangwaro asirinsu na rufuwa,, Dake ranar lahadi aka haifi Amina yasa Mai koko take ce mata Ladidi shikkenan mutane suka rike suma suke kiranta da Ladidiya,, shekararta uku a duniya Allah ya amshi ran Malam Labaran ciwon kai tafarar daya,, Mai koko nauyi ya kara yi mata yawa, dake jaruma ce, sam bata karaya ba, ta cigaba da neman kud'inta, da kanta ta kai Ladidi makarantar allo tun tana da shekaru hudu,, tana zuwa cikin yara zaka ji gurin ya kaure da kuka Ladidi Duk ta doke su, har wad'anda suka girme ta dokansu take,,Malami ya doke ta tayi masa Allah ya Isa,aikuwa ya dawo wa da mai koko ita yace"Tana hana su karatu in taje dokan yara kawai takeyi ta hanasu karatu gashi in an doke ta tayi Allah ya Isa shi kam bazai iya ba" Mai koko tace"Kaje ai ba kai kadai bane me makaranta na kai ta wata, sai da akayi wata shida tukkuna sannan ta kaita wata makarantar nan ma bata canza zani ba,, tana zuwa makarantar karatun yara ya lalace domin duk gurinta suke komawa suyi ta wasa duk tsawan da malam zai musu basa jinsa. Nan ya fahimci zuwan Ladidi ne jawo haka, tunda da yana iya tankwara su, aikuwa sai ya ware ta a cikinsu in tayi futina yaci ubanta, ita kuma ta zage shi, gashi duk dukan da za'ai mata bata kuka sai dai idonta yayi ja, malam da yaga ba zai iya ba ya tattarata ya mayarwa da mai koko ita,, abunda ta fadawa malamin farko haka ta fada masa,, shekara guda bata zuwa makaranta, sai wasa da yawo kusfa-kusfa D'alha bai tab'a Ankara ba, dake da wuri yake futa baya dawowa sai gab da magariba, ya dawo ya wuce ta makarantar Allo yaga an tashi yana ta daga kai yaga ta inda Ladidi zata b'ullo bai ganta ba, sai yayi tunanin ko ta tafi gida, yana tafiya ya hangota kan katangar wani gida ta mike tsaye tana ta tafiya tana k'yalkyala dariya kanta babu d'ankwali, sai diddigagen gashinta da kwarkwata ta cinye rabi ta bar rabi, duk k'wanta nan burjik!! Kira ya kwala mata"Ladidi"!! Da sauri ta juyo jin muryar Kawunta ta hantsilo k'asa ko a jikinta ta mike da gudu tayi gida,,, girgiza kai yayi ya bi bayan ta.

Sosai ya dunga fad'a Mai koko tace"Ai sai ka d'auke ta ta kaita da kanka ko wace makaranta aka kai ta sai su koro ta saboda tsabar bakin ciki sun tsani marainiyar Allah" Yace"Halin ta ne ya jamata zan kai ta, wata makatanar da kaina Wallahi da kaina zan dunga hukunta ta" Shiru mai koko tayi masa ya gaji ya shiru, ita ko Ladidi na bayan ta tana zumb'ura baki gami harare-harare ta tsane shi tunda kullum cikin takura mata yake. Washe gari da safe D'alha ya sa ta a gaba suka nufi makaranta ya damk'a ta a hannun Malam yace"Gatanan yayi mata hukunci in tayi laifi, kuma ya kula da karatun ta."






*COMMENT VOTE AND SHARE*
[9/24, 10:29 PM] 8k: https://m.facebook.com/Zamaniwritesassociation

*🌚🌚🌚LADIDI🌚🌚🌚*
*🧟‍♀🧟‍♀🧟‍♀K'WADAGA🧟‍♀🧟‍♀🧟‍♀*




*NA*
_BINTA UMAR ABBALE_
~*®BINTUBATULA👄*~



*MARUBUCIYAR*

```NANA KHADIJA```
```YARO DA KUDI```
```GIMBIYA BALARABA```
```TSANTSAR BUTULCI```

_*LOODING:*_
_*{LADIDI K'WADAGA🌚}*_




_*ZAMANI WRITES ASSOCIATION🤝🏻*_

_______________________
```We are here to educate motivate and entertain aur reades```
_______________________



_*DEDIGATED*_
*TO*
_RAHAMA ALIYU_




_*KU SONI TA ZARCE💝💝💝 NIMA NA NASO KU TA ZARCE❣❣❣IN HAR KUKA KUFCE! 😡😡A KANKU NI ZAUCE! 🤢 IN KUNJI😍😍*_
😃😃😃😃😄😄😄😃

I will always saying thank you to my people love you so much,, muna tare insha Allah😘




*🅿6*




D'alha ya kama hanya yai tafiyar sa, gurin sana'ar sa, tunda malam yayi mata gurin zama cikin yara take ta faman zabga masa harara sosai yayi mamakin yarinyar ko da yake dama yana da labarin ta sosai,, sai ya d'auke kansa kawai yayi kamar bai ganta ba,, ya cigaba da koyar da yara, yarinyar dake kusa da ita ta zura hannu ta mintsina yarinyar ta fashe da kuka, Sai tayi saurin cire hannunta tana kallonsa yana kallonta,, ya gane itace yarinyar ya kira da hannunsa, gurin zama yayi mata,, Ladidi taji haushin haka, tayi shiru tana zumb'ura baki, lokacin tashi nayi yayi musu addu'a duk suka mike sai ta d'auki takalmi wata ta b'oye, to yaga lokacin da ta d'auka, murmushi yayi ya kira yarinyar ganin tana kuka, Ladidi ya kira, taje tai masa k'erere aka yace"Bata takalmin ta" Zumb'ura baki tayi tace"Baya gurina fa" "Naga fa sanda kika d'auka kika b'oye bata kinji ko,, ni nasan kyautar da zanyi miki" Shiru tayi yace"Zan baki alawa" Aikuwa sai ta futo da takalmi da ta b'oye kasan zaninta ta jefawa yarinyar, da sauri ta d'auka ta sa, ta kalle shi, kai tsaye tace"Bani alawar" yace"Dama ba karatu kika zo ba" ? Daga kai tayi" yayi murmushi yace"To don Allah kiyi karatu ki nutsu kinga Kawun ki ya kawo ki kiyi karatu nayi miki alk'awarin bazan Doke ki ba kamar yarda ya fad'a" baki ta tura tace"Ko ka dake ni ba zafi zanji ba" dariya yasa yace"Nasan da haka ai,, shiyasa ma bazan tayar da hankalina ba". "Ni dai bani alawa ta" fad'a tana Sosa kanta,, Hannu ya zura cikin aljihun sa ya ciro Alawa guda biyu yace"Kullum nayi miki alk'awari zan dunga baki mutuk'ar zakiyi karatu in kin zo makaranta kuma zaki nuttsu ki daina tsokanar "yan uwan ki" Karb'ar Alawar tayi tayi tafiyar ta, ta barshi da baki a sake, girgiza kai yayi ya d'auki allon nata yana dubawa, duk girman ta, tana Alam tarakaifa. Wanda basu kai shekara goma ba ma sun shiga sabbi,, ita tana zaune, haka kawai yake tausayin yarinyar, yana fa yara guda biyar duk kamarta shiyasa in yaga yara na k'uruciya yake musu addu'ar shiriya Wannan shine silar zaman Ladidi a makaranta ko tayi nufin tsokona ko gudun makaranta sai ta fasa saboda alk'awarin alawar da Malam Salihu yayi mata, shi kuma kullum baya fashi, ana tashe zai bata,, gashi Yanzu tayi nisa a karatu ta kusa izu d'aya. Babu laifi tana gane wa.

*WANNAN SHINE TOSHEN LABARI*



Da Asubah D'alha ya futo da niyar zuwa massalaci, da cocilan a hannunsa yana haskawa, sai ya ga Mai koko na k'okarin saukowa daga bainci da alama itama tashin ta kenan, Cikin mamaki ya tsaya yana kallonta yace"Iya me kike anan"? Shiru tayi masa ta mike tana Sosa jikinta, yace"Da alama nan kika kwana meye dalili"? Cikin b'acin rai tace"Wannan ja'irar yarinyar ce ta rufe min k'ofa jiya babu yadda banyi ba ta bude min amma tak'i"D'alha mamaki sosai yake yace"Tak'i bude miki k'ofa me makon ki min magana shine zaki kwanta a soro cikin sauro Iya sai kinje zazzab'in cizon sauro ya kama ki"? K'okarin shiga cikin gidan take tana fad'in"Kai dai magana ta wuce, ai kayi tafiyar ka" Gyad'a kai kawai yayi ya wuce yana mamakin son da Iya takewa Ladidi wannan son shi a ganinshi cutar wa ne, domin shi yake k'ara lalata yarinyar. Har yaje massalaci yan sak'e-sak'en hukuncin da zai d'auka kan Ladidi domin ko me Iya zatayi sai ya doke ta ya rantse. Bayan an idar da sallah sun futo,, Halliru mai Fura ya tsaida shi suka gaisa,gani yayi Halliru na sha masa kunu yace"Malam Halliru lafiya ko" ? Halliru ya sauke ajiyar zuciya yana fad'in"Idan kaji kira daga mai gari kar kayi mamaki" Cikin mamaki D'alha yace"Me ya faru" Rai a b'ace Halliru ya kwashe duk abunda ya faru ya fad'a masa,, innalillahi wa'innailahi raji'un shine abunda D'alha yake ta Nanatawa yace"Don girman Allah Halliru kayi hak'uri wallahi in banda ka fada min ban san abunda yake faruwa ba, itama Iya ina tabbatar maka da cewar bata sani ba kayi hakuri don Allah kar ta kaimu ga zuwa gurin mai gari, wannan tonan asiri ne"


Halliru ya sha kunu yace"Inyi hakuri kamar yaya? Kana nufin in zauna bani da abinyi kome? Na fada maka fa yarinyar nan duk jarina ta rusa kaje ka tambayi Mutari me nama zai fada maka komai" D'alha ya kwantar da murya yana fad'in "Duk baza ta kaimu ga haka ba,, yanzu ya kake so ayi" ? Kai tsaye D'alha yace"Kawai mu raba asara Ku bani dubu biyar ni nayi muku lamani" D'alha ya tsaya yana tunani daga bisani yace"Shikkenan insha Allahu zamu San abun yi ka kwantar da hankalin ka"

Halliru ya saki fuska yana fad'in "Shikkenan sai na jika"
Sallama sukayi kowa ya kama hanyar gida.

Lokacin da ya isa gida, Mai koko na tsaye gaban wata k'atuwar tukunya da duguwar muciya a hannunta tana ta aikin motsa koko ga kwanuka har an fara layi,, kai tsaye d'akin ta ya nufa, sam bata yi tsammanin dokan Ladidi zai yi ba,, sai ihun ta kawai ta ji da sauri ta jingine muciyar ta shiga dakin da sauri,, tana fad'in "Au!! Dama dokan ta ka shigo kayi ko D'alha? Can na hango Ladidi k'arshen gadon k'arfen Mai koko sai ihu!! Take kurmawa babu ko k'wallon hawaye, D'alha ya zage k'arfi yana ta labta mata bulala,ya ki cewa komai,, Tace" Shikkenan kashe ta tabi iyayen ta, tunda kak'i ka saurare ni" yana haki! Yace"Da kin san abunda yarinyar nan tayi to da kin bani gudumawar abun duka" Cikin fushi tace"Kome tayi bazan bada abun duka a illata ta ba, ni dai nace ka daina dukanta in dai ni na haife ka" D'alha ya yar da abun dukan yana haki! Cikin b'acin rai yake warware mata abunda ya faru, sosai itama ta jinjina al'amarin, amma don k'arin abun haushi sai cewa tayi"Yo ai da ka k'yale shi yaje ya fad'uwa mai gari sai me, dan yaje, dubu biyar dai insha Allahu za'a bashi, ai k'imar mutum tafi kudi shi kud'i suka dama da zai zugo ka kazo kana dukan marainiyar Allah"
D'alha yace"Ko yau ta k'ara sai na doke ta, in ta kama ma in sa ta a mari sai in daure mata k'afafu sai inga k'afafun yawo"
"Tunda kai ai haka akayi maka sai ka daure ta magani" Mai koko tafad'a cikin takaici,futa yayi a fusace! Ta mai. da hankalin ta kan Ladidi dake ta faman sosar jikinta wani gurin har ya kwailaye, amma saboda dauriya da kafiya gami da jarumta ko kwalla babu a idonta k'ema gadas, sai da sunyi jajazuri! Tace"Kin kyauta kinji ko, aini kam bazan miki baki ba sai dai i n nema miki shiriya a gurin Allah idan kuma wani, shad'ainin ne yake sanya
DOWNLOAD
DOWNLOAD

1 Comments On LADIDI KWADAGA
avatar
north

1 year ago

Reply

dadi

Please Login or Register in order to submit comment