Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

abinda ya fad'a.

"Hak'uri? Ni de baka ban hak'uri ba" cewar Amal tana murgud'a baki. "Allah ya karya min k'afa kar ki jisa Mami."

"Baby kallen shin bawan Allahn nan karya miki k'afa yayi ko kuwa targad'en ce kamar yadda ya fad'i?"

Ganin fa an ganota ta soma kame-kame "Toh ni ina zan sani ko had'a baki sukayi da likitan don ya rufa mai asiri-" bugi Mami ta kai mata a cinya interrupting her, wanda a sanadin hakan ta sa ihu.

"Yanzu haka kawai kima bawan Allah sharri ya karya miki k'afa Baby? Shin yaushe zakiyi hankali?" Baki ta zumb'uro tana kukan munafirci a yayinda Mami ta juyo kan Afzal da yayi jugum yana kallon ikon Allah.

"Bawan Allah don Allah kayi hak'uri wallahi haka take gagara da rashin ji toh wane akanta akayi wahayinsa."

"Ba sekin fad'a ba naga hakan a tattare da ita" ya fad'a yana meyi wa Amal kallon rainin hankalin dayasa ta murgud'a mai baki. "So am here to say sorry and take full responsibility" ya numfasa "Ga magunanta nan" anan ya miqa wa Mami leathern inda ta amsa "Dr yace karku tada hankalinku she's going to be alright kuma gobe idan Allah ya kaimu zan dawo in maida ta asibitin don a sake dressing ankle natan kaman yadda likitan ya buk'ata. Za a cigaba da yin hakan na sati daga nan in shaa Allah k'afan zai warware." Kafin Mami da akayi ma bayani tayi magana Amal ta hau k'orafi.

"Ni wallahi ban komawa asibitin" ta fad'a tana buga d'ayan k'afanta a k'asa stubbornly.

"Rufa min baki do Allah!" Mami ta ce da ita amman still se gunguni takeyi dake sam bata tsoron idon Mami. "Allah sarki bawan Allah lallai ka cika d'an halas mun kuma gode sosai, ina me sake baka hak'uri kuma."

"Ba komai Mami ya wuce nine da godiya."

"Allah yima albarka Babana."

   "Ameen" ya amsa da murmushi kad'an.

   "Nace ba kar ka damu ba seka kuma dawowa bama anan tsallake gun wanzami zan kaita a sake duba k'afan nata gobe in shaa Allahu."

"No Mami, I promised to take full responsibility so karki damu and here" ya fad'a yana ajiye ledojon a k'asa "Sakamakon hatsarin abubuwan da kika aiketa siya suka tarwatse so gasu I'm able to get some wad'anda ban samu ba kuma zan baku kud'in seku siya in kuka samu lokaci, I'm sorry" hannu ya zira a aljihun sa don ciro wallet nasa inda yaji wayam holy sh*t ashe ya baro sa acikin mota. "Excuse me please let me get my wallet."

    "Haba bawan Allah ai da ka bari, hakan ma mun gode wallahi ni na yafe sauran" fad'in Mami.

"Ni ban yafe ba" cewar Amal wane da ita aka kasa, ko ta kanta Afzal beyi ba yayi saurin katse Mami dake shirin yima Amal fad'a "No Mami please I insist, ai hak'k'in kune."

"Toh shikenan tunda kace haka mun gode" ta fad'a tare da kewayo da kallonta akan Amal "Ke tashi ki bi bayansa ba seya sake shigowa nan inba yayi sahu biyu tunda duk ke kika jawo komi" cewar Mami.

   "Taya ni na jawo? Ni na kaisa kad'eni?" Ta tambaya cike da rashin kunya.

"Da bance kibar aiken ba se da yamma kika k'i?" Zata kuma magana Mami tayi yunk'urin gwa6e bakinta nan take tayi shiru. Afzal da yayi shiru yana kallon su ne ya nisanta yace, "Karki damu Mami, let her be."

"A'a don Allah kar muyi haka da kai. "

"Mami-"

"Don Allah fa nace" hakan yasa yayi shiru.

"Toh shikenan" ya fad'a a hankali.

"Yauwa bari Baby ta bika seta amso kud'in tashi mana Baby" ta fad'a tana dawo da kallonta akan Baby dake faman zumbure-zumbure ko yunk'urin miqewa batayi ba. "Ko baki ji ni bane?"

"Toh ai bazan iya tashi ba."

"Uhn uhn fa Baby kin san ni."

"Don kinga Papi bai nan ba? Allah ze dawo dashi kuma wallahi sena k'irga mai komi" ba don tana so ba ta shiga miqewa wanda k'arshe saida Mami ta taimaka mata, k'ingishi ta shigayi tana takawa a hankali. Murmushi Afzal yayi sannan ya shiga bin bayanta.

"Toh gashi bawan Allah zaka tafi ban san sunanka ba." Kewayo wa yayi cike da ladabi sannan yace "Afzal."

"Afzal" ta nanata "Sunan larabawa ga me k'iran su, masha Allah" ta fad'a acikin wasa. Murmusawa yayi sannan yayi mata sallama ya fice alokacin har Amal ta isa bakin k'ofa tana tsaye tana kallon yaran dake wasa akan layi.
"Excuse me" yace da ita ganin tayi tsaye bakin k'ofan ba chance da ze wuce. Seda tayi muttering wasu kalamu chan k'asa iya jinta sannan taja gefe ya samu ya wuce. Bayan sa ta shiga bi sannan ta tsaya daga jikin wani bango a yayinda ya k'arisa gun motan nasa. Wallet d'in ya d'auko, dai-dai yazo bud'ewa kenan don sallamarta wayarsa dake inner aljihun suits jacket nasa ya shiga ringing. Ba tare da 6ata lokaci ba ya zaro, ganin Abba ke kira zuciyansa ya mugun har6awa yau ya shiga uku. Cike da fargaba ya d'aga sede kafin ya samu daman magana Abba ya riga sa.

"Yanzu Afzal in kiraka sau biyu in ce maka ina neman ka as a matter of urgency shine har yanzu ban ganka ba? Ai ko bangon duniya kake yaci ace ka dawo war haka" daga yadda yake magana mutum zaisan ransa ya 6aci matuk'a ba shakka Abban nan nashi mutum ne mai gajan hak'uri.

"Abba I'm so sorry-" katse sa Abba ya kuma yi "Wallahi ban san ka da halin nan ba, bansan kuma meyasa kake hakan ba amman karka damu ba seka zo d'inba domin shi wanda yake neman ma maganan ma ya gaji da jiran ka ya tafi" daga fad'in haka ya katse wayan ba tare da ya basa daman magana ba. Hankalin Afzal ya mugun tashi, rabon shi da ya 6atawa Abba rai irin na yau ya juma, probably tunda yake yaro lokacin da bai gama gano darajan iyaye ba. Yau ina zaisa kansa? A kullum shi me ladabi ne game da umarnin Abba, a kullum Abba na alfahari dashi se gashi yau all because of wannan fitsararriya 'yar gudun hijirar ya 6atawa Abbansa rai to the extent da har Abba ya kashe waya a kansa abinda be ta6a yi ba. Yasani kafin Abba ya sauk'o ya soma mishi magana kuma se ranan da Allah ya nufa.

   Ranshi a murtuk'e ya bud'e wallet d'in be ma san iya adadin kud'in daya d'iba ba tsabaragen all he wanted at that moment was yaga kansa a gida ya samu daman bawa Abba hak'uri tun kafin lokaci ya k'ure.

"Ke!" Ya daka mata tsawa wanda sanadin haka ta firgita. Tun da tasan kanta bayan wani PHE teacher'n su tun a JSS 3 ba wanda ya ta6a mata tsawa yakuma razana ta irin na yau. "Kinyi tsaye achan nine zan k'ariso miki da kud'in?" Ya jefa mata tambayar cike da tsiwa.

"Malam dakata fa!" ta tsorata iya tsoro amman dogon bakinta baze barta tayi shiru ba "Haka kawai bazaka sauk'e min haushin da kakeji a ka ba, a dalilin meh? Don wani ya kiraka ya 6ata maka rai se ka hau huce zafin ka a kaina kana min masifa? Da ni nace ka kad'eni kokuwa ni nace ka kawo ni gida? Ra'ayin da ya saka yin all of that shi zai sa ka tako har nan ka bani kud'in da kace zaka baiwa Mami in kai mata" ta fad'a kai a tsaye ko tsoron yadda yake kallonta cike da haushi da tsana batayi. Duban time a wrist watch dake d'aure a hannunsa yayi ganin he is running out of time yasa shi fasa aikata abinda yayi niyyan mata in ba haka ba belt nasa yayi niyyan zara ya nad'a mata na jaki a gurin tunda a gidansu ba meyi mata hakan. K'arisawa spot da take tsayen yayi sede yarinyan naku ko motsawa batayi ba dukda chan k'asan zuciyarta kuwa ta gama tsorata. A duk tunaninta mari ze kai mata setaji ya damqo hannunta, damqan da tana iya rantsewa ba a ta6a mata irin sa ba ai bata san lokacin da ta shiga ihu ba. Ji tayi k'asusuwan ta suna k'ara, wannan wani irin k'arfi yake da shi? Toh ita kam ya agaza ya rufa mata asiri kafin ya karya mata d'an hannu, ace ga kariya ga targad'e? Bazata iya ba.

"Naga alaman Allah ya had'aki da iyaye masu sanyin da ko tsawata miki basu iya yi as ko mey kikayi dai-dai ne a idansu kisani I'll not let you disrespect me and get away with it, bazan bar k'aramar k'waron da bata kai inyi immediate sibling da ita ba ta raina ni, ko ki iya bakinki ko na koya miki yin hakan, maras kunya kawai."

Sosai idonta ya cika da k'walla don azaba, "Ni ka sake min hannu kuma kar ka sake sa min sunan iyaye cikin zancenka, musamman na Abba na saboda ya rasu" ta fad'a cike da k'arfin hali. Ganin fa baida niyyan sake ta tasa ihu "Mami!" A lokacin har hawayen na neman gangarowa. Se anan ya saketa cike da wulak'anci regardless of her condition, wanda da ace ba bango a kusa da ita data fad'i a k'asa. Hannunta yaja out of nowhere tare da tusa mata kud'in aciki sannan ya juya ya kama tafiya. Kafin ya isa gun mota har Amal ta zaro kud'in ta k'irga, dubu hud'u ta gani "Hey!" Ta danna mai kira amman yayi banza da ita se a karo na biyu, nan ma ba juyawa yayi ba tsayuwa kawai yayi, "Ce ma akayi Papi na ya rasa na ciyar damu ne ko na sha da zaka wani kama ka bada dubu hud'u na abinda be taka kara ya karya ba?" Se anan ya juyo yana kallonta ashe de dubu hud'u ya zara "Zan d'au dubu d'aya, ban sani ba ko canji ze rage amman idan har ya kasance hakan, I'll return your change for you ga sauran kud'in ka" nan ta zare dubu daga ciki tare da yin watsi da sauran a k'asa ta juya da k'ingishinta ta wuce layin gidansu leaving Afzal da baki wangalau a bud'e cike da mamaki, don shock k'wak'walwarsa tama kasa fahimtar dashi abinda wannan 'yar gudun hijirar ta masa. Ji yake as if ya cafko ta ya nad'a mata na jaki shin wannan ya iyayenta suka girmar da ita? Fitsara sekace 6era, besan na gida ba balle bak'o. Lallai ta guji had'uwansu, yanzu baiwa Abba hak'uri ne ke gabansa dako seta gommaci kid'a da karatu.




*~*~*~*~*~*~*~*~*~*
So how was the chapter? One word for Amal?😂
In shaa Allahu bayan sallan azumi kuma semu d'aura daga inda muka tsaya. Na sako pages biyun nan ne domin mutane irinsu Meela da Sumayyah masu shegen maita da tak'uri 😜 se kuma don wasu fans d'ina da suka d'au cewa na daina rubutun hausa gabad'aya. Wishing you all a faithful Ramadan ahead xoxo.

RANA D'AYA
#RD
Love... miemiebee👄✨
[12/08, 22:25] ‪+234 907 483 8352‬: 🎀🎀🎀 🎀🎀🎀
🎀❣🎀
❣❣

💦💦 🍃🍃🍃
*RANA D'AYA!*
💦💦 🍃🍃🍃

_Written by Miemiebee👄_


*PAGE 0⃣3⃣*


  
_How can I turn you guys down when the love and devotion speaks this much??😩😍 Yanzu haka kuka k'i yarda a cigaba da posting RANA D'AYA after Ramadan😩 kaman maita harda masu cewa koda sau d'aya a sati ne 😂 nida mutane na se Allah but know that ina alfahari daku sosai sosai wallahi💖. Though my schedule is tight, I'll still manage and squeeze time to type once in a week like you guys requested before Ramadan approaches, so here is chapter three. Juma'ah zuwa juma'ah zakuna samun post in shaa Allah, happy reading!❤_



Ta kai ga yankan lungun gidansu kenan sega Mami tafito sanye da mayafi "Ina zaki Mami?" Tayi saurin tambaya "Maggi zan siyo nan shagon Usmanu ashe ya k'are ban sani ba gashi har miya ya kusa nuna. Kiyi sauri kije ki kula min dashi dama na rage ichen seki k'ara" Mami ta sanar da ita.

"Toh Mami ki dawo lafiya" ta amsata, da k'ingishinta ta shiga takawa amman ta tsaya chak sanadin kiran da Mami tayi mata, hakan yasata kewayowa "Na'am?" Ta amsa.

"Nace nawa Afzal ya baki ne?" Nan fa oganniyan taku ta shiga kame-kame tana ta6e baki. "Ya haka? Tambaya fa nike miki, nawa ya baki?"

  "Dubu d'aya" ta fad'a chan k'asa-k'asa.

  "Har dubu? Mu gani" ta buk'aceta, nan Amal ta d'ago ta nuna mata. "Yo shine kika tsaya kina rarraba ido kaman 6eran da aka kama yana sata?"

  "Uhnmmm ni zan wuce kar miyan ya k'one" ta fad'a tana dodging had'a ido da Mami tasan tabbas idan suka cigaba da had'a ido Mami na iya gano k'arya take, bata kai ga taka k'afanta ba Mami ta kira sunanta "Baby!" Chak ta tsaya zuciyar ta na har6awa.
   "Na'am?"
  "Juyo ki kallen" saidai ta kasa, seda ta d'au tsawon lokaci sannan ta juyon. "Fad'a min me kikayi? Tabbas babu gaskia a tattare da ke fad'i me kikayi."

  "Mami me kuwa zanyi? Ni shikenan kullum kina cikin zargi na" ta zum6uro baki.

   "Munafuka bazaki bar k'arerayin nan naki da kike tasowa dasu ba ko? Nace fad'a min me kikayi wallahi idan kika bari har Afzal yazo gobe na tambayesa naji gaskiya daga bakinsa jikinki zai gaya miki."

  "Wai duka na zakiyi? Ai Papi baze bar ki ba" da sauri ta buge bakinta tuna Papi bayi gida yayi tafiya.

  "Sam bazan dake kiba amman inada wanda ze daka min ke kaman ganga, Malam Bunu na islamiyyan ku zan kai mai k'arar ki nacewa har yanzu baki daina k'aryan banzan nan ba."

  "A'a don Allah Mami kiyi hak'uri wallahi dorinan shi me baki uku ne na tuba."

   "Yauwa fad'an me kikayi toh."

  "Ki rantse baza kimin komi ba."

  "Sa'ar kice ni? Zaki gayan ne kokuwa?"

"Mami dan Allah kiyi hak'uri."

  "D'aya" Mami ta shiga k'irge "Biyu-"

   "Zan fad'a zan fad'a" Amal ta katseta a rikice. "Dubu hud'u ya bada shine na miyar masa da sauran saboda kudin abubuwan da suka rage basu kai hakan ba."

   "Oh! Amman 'yar nan anyi wawiya wallahi shi daya k'irga kud'in ya baki besan me yakeyi bane kome? Ai da niyyan kyautatawa ya bada."

"Toh-" ta fara magana.

  "Rufa min baki da Allah!" Mami ta katseta cike da takaici "Yanzu fisabilillahi Allah ya kawo mana arziki har gida ki miyar da hannun kyauta baya Baby? Meye muke dashi da zaki miyar masa da d'umbun kud'i haka iyye?" Don takaici Mami ji take kaman ta mauje ta, tana gwada yunk'urin hakan kuwa Amal tasa ihu gashi ba halin gudu k'afarta baze barta ba, dan tausayi de kawai Mami ta barta. "Shin ya amshi kud'in yanzu?"

  "Eh mana tun yaushe ma."

  "K'arya kike nace k'arya kike. Fa bazan haifeki ki tsaya kina raina min hankali ba nace ya amshi kud'in da kika miyar masa ko ya?"

  "Ya kar6a..." hannu Mami ta d'aga kaman zata doketa "Nace ya kar6a ko be kar6a ba?" Zata kuma wani k'aryan Mami tayi kaman zata sauk'e mata mari, tuni ta shiga bada asalin rahoton "Wallahi be kar6a ba k'arya nakeyi."

   "Nasan za ayi hakan ai, ki kiyaye nifa Baby! Ki kiyayeni ina fad'a miki wallahi ranan da nace zan tarke ki a lungu bazaki ji dadi ba. Yanzu ina kud'in tunda kince be amsa ba?"

Chan k'asa-k'asa tana me zum6uro baki tace "Na yasar mai a k'asa da yak'i kar6a."

  "Kud'in kika yasar?!" Tas kukejin sauqan mari a bayan Amal daya sata sakan wani irin rikicaccen ihu bawai don marin yayi zafin da zaisa ta yin kalan ihun bane sai don shagwa6a irin nata. "Amman yau na tabbata kina da ciwon hauka maza wuce muje ki ibo kud'in kuma Allah yasa muje har 'yan tsince-tsince sun d'auke kiga abinda zan gwada miki a gidan nan yau, dama gashi Papin ki bayi nan balle ya shiga miki." Kukan munafurci kaman yadda ta saba ta shiga yi tana me maquro d'an k'wallan daya ciko mata a ido. Haka Mami ta sata gaba da k'ingishin nata suka k'arisa dai-dai spot d'inda abin ya faru wanda a dai-dai lokacin wasu almajirai suke k'ok'arin d'iban kud'in wani ihu Mami tasa "Karku ta6a zaku 6ace" ai kafin tace pim ta nemi yaran ta rasa tasan sarai idan ba hakan tace ba kwashe kud'in zasuyi su gudu su barta da innalillahi. Da sauri taje ta tattara dubu ukun cus ta k'irga, wani hamdala ta saki sannan ta amshe na hannun Amal dake faman murza idonta tun d'azun. "Maza wuce gida kuma Allah yasa miyan ya k'one kiga abinda zan miki."

  "Toh ni Allah ne da zan hana miyan k'onewa?" Ta tambaya tana zum6uro baki.

  "Zan buge bakin nan fah" da sauri ta sa hannu ta toshe bakin nata kafin hannun Mami yayi landing a kai "Maras kunya kawai wuce gida saura kuma ki tsaya hira da Azee a hanya kiga abinda zan gwada miki mutum se shegen almubazaranci." Tana kaiwa nan ta yanki kwanan shagon Usama, itama Amal a hankali ta shiga takawa da k'ingishin har ta isa gida.

Saidai wani hanzari ba gudu ba, takai gab da shiga ciki kenan sega k'awarta Azee wacce Mami ta ja mata kunne akanta, se ince kusan rashin jinsu d'aya saidai kawai ita Azee a gaban Babanta take hakan yasa tafi Amal jin tsoron ido da bakin mutum unlike Amal.

"K'awas ya na ganki da bandeji waine a k'afa?" Tayi saurin tambaya tana doso ta, idonta na akan k'afan Amal.

"Hmm kede K'awa bari kawai wani reckless bawan Allah yau Allah ya had'ani dashi, ina zaman zama na yayo kaina da mota ya bigeni."

"Subhanallah shine baki sanar dani ba? Sannu ya k'afan toh?" Nan suka hau hira Amal ko gabad'aya ta mance da miyan da Mami tace ta kula dashi.



**** ***** ****** *******

Isan Afzal gida keda wuya as tun da ya hau tuk'in yake tunanin abinda Amal tayi masa, tafasa ransa yake sosai tabbas baze bari ta gudu unpunished for what she did ba, komin ji da dad'ewa seya rama. She wants to play games? Then she got it. Yana isa gaban wata makekiyar gida da bature ke kira da mansion ya yanki corner inda ya tsaya dai-dai gaban fancy iron gate d'in. Securities biyu ne masu uniform tsaye a bakin k'ofan suna gadi, sannu da zuwa suka mar sannan suka bud'e gate d'in. Tafiya kad'an yayi ya kuma cin karo da wani iron gate d'in nan ma securities biyu ke guarding wajen bayan sun mar sannu da zuwa suka bud'e masa giving him a safe passage. Tafiya yake through the driveway a hankali exploring the beauty of the mansion. A sannu a sannu ya k'arisa last parking lot meh glassy display sannan yasa motarsa ciki ya yi parking ya fito. Makekiyar flat da me bada labari bata san daga ina zata soma labarta saba Afzal ya wuce ciki. Sashin fari ya shiga wanda ko ba a sanar da mutum ba zai san na mai gidan ne wato Abbansa. Knocking yayi bisa entrance door d'in sannan ya bud'e tare da sa kai. Makekiyar parlour ne da aka k'ayatasa da abubuwa masu tsada masu d'aukan hankalin d'an Adam. Komi aciki white, golden and red ne banda cinema'n dake manne jikin bango, ga ko ina tsaf ko dust baka gani illa k'amshin turaren wutan dake tashi.

"Sannu da zuwa Prince" wani na miji dake sanye da uniform ya fad'a yana doso Afzal da yayi zaune bisa one of the various golden X red royal chairs.

"Thank you Abba na gida?" Ya tambayesa.

"Eh yana d'akinsa" ya basa amsa a takaice.

"Good, help me speak with him please."

"Yes sir" ya amsa. Da fad'an haka ya juya ya shiga ciki ta wani k'ofa, yakai tsawon minti biyu sannan ya dawo. "I'm sorry amma kaman Master bai da shirin ganinka" mutumin ya sanar dashi. Dama Afzal yasan za'ayi hakan ba kowa yake blaming ba illa Amal ji yake kaman idan ya kamata karya saketa se ta daina numfashi, 'yar gudun hijira kawai ya furta a ransa. "Please tell him I'm sorry yayi hak'uri ya fito" ya fad'a da damuwa karara bayyane a fuskansa.

"I did amman baida niyyan fitowan ne, yak'i nakega idan Hajiya tamar magana zai sauk'o, I'm sorry excuse me" daga fad'in haka yayi kan dining table inda ya cigaba da goge-gogen da yakeyi. Ganin fa zaman da yakeyi a gun baze haifar masa da komi ba ya miqe ya fita. Side na Ummi ya nufa direct don neman taimakonta. Kaman kullum seda ya ciro hanky daga aljihunsa ya toshe hancinsa sannan ya k'arisa ciki. Ko bai tambaya ba yasan yau ma da akwai hayak'in kullum d'innan, anayin abu dai-dai amman ita Ummi idan batayi over ba bata jin dad'i. Site nata kullum yana cikin hayak'i da k'amshin turaren wuta. Had'add'en parlourn ta daya k'unshi combination na white, dark and light purple ya wuce making it to her room. Knocking yayi bayan ta amsa da 'yes' ya bud'e ya shiga, miqe akan gado da zani d'aure a k'irjinta ya tarar da ita tayi ruf da ciki a yayinda 'yan mata biyu ke mata tausa, hayaqin d'akin is indescribable ba shakka yau d'inma gyaran jiki ake mata. Shi yarasa amfanin wannan abu, shin ta gyara jikin nata takai ina? Abba deh ba saurayi bane yanzu haka zalika itama ba budurwa bace. Murmushi kad'an ya saki tuna reaction nata anytime idan yace mata ita ba yarinya bace yanzu ta tsufa. Shi de ya rasa ta ina ta zama yarinya, mutumin da ya kusan approaching 50 kam ai ya manyanta. "Waye ne?" Ta tambaya kasancewar kanta na facing opposite direction na k'ofar. Kafin Afzal ya amsa 'yan mata biyun suka rigasa "Prince ne."

"Oyoyo My Prince" ta fad'a tana k'ok'arin zama a yayinda 'yan mata biyun dake kanta suka ja gefe "Sannu da dawowa Prince" kai kawai ya musu nodding.

"Toh kuma kayi tsaye gun ka k'ariso ciki mana" Ummi ta fad'a tana janyo mayafi tare da lullu6e jikinta. Kyakkyawar mace ce me uban kyawun jiki wanda idan ba wai an fad'i shekarunta bane mutum baze ta6a sanin takai hamsin ba kaman yadda Afzal ya fad'a. Irin skin nata ake kira da kalan wankan tarwad'a gashi kuwa daya samu gyara se wani glowing yake like gold, ga k'iban nan tubarkallah nama du sun nannad'u a wuya. Kallo d'ai za ayi mata asan matar alhaji ce.

Tana da kyau sosai haka Afzal ma amman abun mamaki sam mutum baze ce mahaifiyar sa ceba saboda rashin kaman su, sam kyawunsu be zo d'aya ba. Afzal yafita haske
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment