Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

sosai wasu sukan ce mar fari ma, ita kuwa tafi sa dala-dalan idanu da kuma dogon hanci. Hancinsa na nan shiba dogo ba shiba gajere ba gashi nan de k'arami acikin oval shaped face nasa.

Da hannunsa yayi mata nuni cewa hayak'in d'akin is unconducive ya mar yawa.

"Kai deh da ace kanada asthma da turaren wutan gabad'aya zaka hanamu yi a gidan nan toh ya akayi?"

"Ummi please mana! I want to talk to you" ya fad'a tare da had'e giransa, hancinsa kuwa har a yanzun na toshe da handkerchief.

"Toh ya kakeson inyi? Bawai kaman ina da k'arfin koran hayak'in nan a lokaci guda bane."

"Toh kizo muje parlour concentration d'in is less a chan."

"Halan baka ka gyaran jiki ake yimin ba."

"Fisabilillahi kullum gyaran jiki, gyaran jiki ko amarya albarka" har anan be sauk'e hanky'n daya toshe hancinsa dashi ba.

"Jimin d'a!" Tayi exclaiming full of wonder. "Da meye ce inba amaryar ba? Naga da gyaran jikin ne na iya na karkato da hankalin Abbanka kaga har yau bemun kishiya ba."

"Toh whatever ni ki fito muyi magana."

"Wai me ne da bazaka iya fad'ansa daga bakin k'ofar ba? Aure zakayi? Kuma ka bar min k'ofa a bud'e tun d'azu ko bakasan hayak'in fita yake ba?"

"Exactly ki fito muje parlour" ganin batada niyyan motsawa yace da 'yan matan suyi excusing nasu ba gardama suka fita suka basu waje, ita de Ummi binsa da kallo kawai take ko mey yake da shirin yi? K'arisowa cikin d'akin yayi da dogayen k'afafunsa tare da tsayuwa dab a gabanta sannan ya shiga janta. "Ummi dan Allah ki tashi kin de san kina da nauyi."

"God help me" ta fad'a sannan ta miqe suka fito parlourn inda suka zauna akan two seater side-to-side. "What is it?" Ta tambayesa.

"It's Abba he's mad at me" ya fad'a a takaice.

"Toh kuma har wani sabon abu ne wannan? Kade san Abbanka da zafin fushi da zuciya sekace kai anan."

"Ummi please!" Ya fad'a tare da buga k'afansa a k'asa.

"Okay, okay toh meh dalilin?" Labarin duk abinda ya faru ya bata be bar komi ba. Numfasa tayi bayan da ta gama sauraronsa tace, "Toh Allah kiyaye aukuwan na gaba amman meyasa ba ka sanar dashi abinda ya farun ba?"

"Yak'i ma ya saurareni kashe wayan yayi gabad'aya kuma yanzu ma daga site nasa nake, nasa Micheal ya mar magana still yak'i fitowa."

"Toh ni yanzu me kakeso in maka?"

"Like what a question" ya fad'a tare da juya idanunsa da suke nan farare k'al. "Kiyi mishi magana of course, he always listens to you."

"Nifa banason kana jawo ni cikin matsalarku haka kawai kazo kasa nima yak'i cin abincina na sati."

"Ummi please kinsan Abba be iya yin fushi da mutum ba yanzu ba k'aramin aikin sa neba ya daina min magana for a whole week!"

"Toh ai nima abinda nake gudu kenan kar yabar cin abincina na sati."

"Toh yau aka fara hakan ne?" Ma ta 6ata mar rai. Ai da k'yar idan Abba ya ta6a jera watanni biyu yana cin abincin Ummi ba tare da yayi fushi ba. Haka yake da an 6ata mar rai seya d'aga k'afa wa mutum, abun takaicin kuwa shine se ya nemi abinda zai fi damun mutum sannan yayi using nasa against that person. Se kuma shi gado ba gwaninta ba, shima Afzal haka yake da shegen zuciya da fushin nan irin na Abbansa ko fad'a sukayi da Ummi seya d'aga k'afa daga cin abincinta da kuma yi mata magana in banda gaisuwa ba abinda ke had'asu har se ya sauqo, shima gaisuwan don ya zamo masa dole ne. Abinda ke bawa Ummi mamaki shine bayan shi kansa Afzal d'in ya iya ma mutane fushi meye a ciki don Abbansa yayi masa?

"Aww abinda zaka ce kenan? Ashe dai ba dad'i, ashe idan aka maka haka bazaka ji dad'i ba amman kake ma mutane, ai halin Abban naka da kai seku ta fama kaga barin je in k'arisa gyaran jikin nan yau Abbanka yace zamu fita date kaga ko zama be kama ni ba."

"Ummi please talk to him ni wallahi abinda yasa hankalina ya tashi ma saboda yace akwai abinda yake son sanar dani ne kuma daga yadda yake maganar nasan magana ce me muhimmanci."

"Oh! Dam-" se kuma tayi shiru tuna yadda Abba ya jaddada mata cewa no matter what kan kar ta kuskura ta sanar da Afzal halin da ake ciki yafi son ya mar maganan da kansa.

"Dama meh?" Yayi saurin tambayarta.

"Babu bance komai ba bari in shiga daga ciki." Kafin ta kai ga miqewa Afzal ya rik'o hannunta restricting her. "Ya haka Prince?"

"Ummi there is something you're not telling me" ya fad'a yana mata kallon cikin ido don tabbatar da abinda ya fad'a.

"Kai de da assumption se a hankali ni nace wani abu ne? Sakeni du Allah."

"Ummi please tell me mene Abba keson sanar dani?"

"Wallahi prince seda Abbanka ya ja min kunne kar na fad'a maka don't worry he is planning on telling you himself."

"Taya ze fad'an bayan yamin fushi?"

"Toh ka kwantar da hankalinka zan masa magana, zan mishi bayanin komai anjima idan mun fita in shaa Allah ze sauk'o kar ka damu kaji my handsome Baby?" Ta k'are zancen tare da aza hannunta akan ha6ansa tana mai wasa sekace wani jariri. Hannun nata ya cire yana zum6uro baki ashe de shima ya iya shagwa6an shine yake ma Amal kallon bakwai saura kwata don itama tayi wa Maminta bayan gashi babba dashi shima yana yi.

"Oww had'a min rai zakayi? Shikenan sena fasa basa hak'urin" ta fad'a da gan-gam.

"A'a please don't ni ba 6ata miki rai nake ba" yasa murmushin dole. Murmushin ta mayar masa tare da pecking nasa a kumatu "An kai maka abincinka a site naka ko zakaci anan?"

"Nah am full" yayi maganan yana aza hannunsa kan flat muscled abdomen nashi.

"Toh sallah fa kayi?"

"Zanyi idan na shiga" ya fad'a tare da miqewa.

"Alright I love you."

"I love you too" ya amsa sannan ya kama hanya ya fita tare da nufan site nasa wanda shi kuma kominsa is in black and white. Abinda ya kama daga parlournsa, dining table, d'aki, closet, toilet and bathroom. Kitchen ne kawai pure white. Bathroom ya fad'a yayi alwala sannan yayi sallah ya rage kayan jikinsa tare da barin shorts da singlet zalla. Akan gado ya miqe tare da k'ure AC'n d'akin, ragowan aikin daya rage mar a office yakeson k'arisawa amman ji yayi ya gaji gabad'aya ko d'aga yatsa bazai iya ba don haka ya jawo wayansa daga kan side table tare da shiga Twitter inda ya shiga bin feeds nasa, yana gamawa dashi ya shiga Instagram se Snapchat, k'arshe ya leqa whatsapp wanda daga nan bacci yayi awon gaba dashi.

\•\•\•\•\ A cikin City star.

Zaune Abba da Ummi suke a filin da Abba yayi reserving musu. Ummi ansha kyau kaman ba gobe se k'amshi take. Tana sanye ne da royal blue lace me torches d'in yellow wanda ko ba'a fad'a ba mutum na sani kaya ne me bala'in tsada ga wani arnen d'inkin da akayi mishi wanda ya mugun kar6arta. "Kin ganki kuwa Baby? You're looking so takeaway" Abba dake sanye da sky blue half jamper ya sanar da ita yana mey mata murmushin sosa zuciya.

"Kai My Dear kai de bazaka dena flattering d'ina ba ko?" Ta fad'a cike da kunya tana blushing.

"Ai kema kin san gaskia nake fad'i gashi har yanzu koda wasa 'yan matan waje sun kasa kawar min da hankali daga gareki, ba don komi ba kuwa se don wannan kwalliya, gyaran jiki da son k'amshin naki, keep it up."

"Kai My Dear toh nagode in shaa Allahu kuma zan cigaba, amman kaima bakaga yadda kayi kyau bafa ai nasha fad'a maka half jumper suna ma kyau kak'i ji na."

"Na gano hakan nima yanzu shiyasa kika ga na sanya yau." Hira jifa-jifa suka cigaba dayi har izuwa lokacin da orders nasu suka iso. Cike da k'asaita suka shiga ci suna hirar jifa-jifan har yanzu. Sun kusa gamawa Ummi tayi gyaran murya "My Dear?"

"Na'am?" ya amsa tare da d'ago kansa yana kallonta cike da soyayya sai kace yau ya soma sata acikin idanunsa.

"D'azu Prince yazo ya sameni" ta tsaya deliberately don jin mey zaice. Shi kuwa tunda yaji ta ambaci 'Prince' yaji yayi losing appetite nasa ma gabad'aya. "Ya da tura plate naka gefe kuma My Dear? Kode na fad'a wani abu ne?" Tayi saurin tambaya.

"Na k'oshi" ya fad'a yana kawar da kansa yana me kallon gefe.

"Dan Allah kayi hak'uri nayi shiru barin sake cewa komi ba amman ci abincin kasan banason kana kwana da yunwa yi hak'uri" ta hau lalashinsa, cike da dabara ta mayar masa da plate d'in gabansa da k'yar ya yarda ya cigaba da ci seda ta tabbata ya k'oshi sannan tace, "My Dear kamar hak'uri don Allah Prince yaro ne kuma fushinka a gareshi babban tashin hankali ne wallahi, baka ga yadda ya shigo site d'ina ba d'azu cike da tashin hankali bayan yayi ma Micheal magana daya maka sallama kak'i fitowa dan Allah ka sassauta masa."

"Hmm Hajiya Mariam kenan, shin ya sanar dake abinda yayi min?" Ya tambayeta "Ya fad'a miki sau biyu ina kiransa bai d'agawa? Bayan da na samu ya d'aga kuma yace min meeting suke inyi hak'uri and I agreed saboda Prince be cika min k'arya ba sede inyi ma yaro jiran duniya da Baban yarinyan nan amman yak'i zuwa, wannan abin kunyan dame yayi kama? Haka mutumin nan ya gaji da jira ya tafi."

"Bance yayi dai-dai ba amman da kayi mar uzuri My Dear accident yayi encountering wanda daba don Allah ya tsagaita ba da sede a kiraka ace maka kazo ka d'au gawan d'anka."

"Haka yace miki?"

"Yes My Dear and ba k'arya yake ba sanin kanka ne Prince bai cika k'arya ba se idan ta kama so I believed him."

"Allah kare aukuwan na gaba" kad'ai yace.

"Ameen ka hak'uran?"

"Da hak'uri na da rashinsa ai du d'aya ne."

"Taya ya zamo d'aya kuma My Dear? Idan har ka hak'ura muna isa gida ka kirasa ka mar maganan nan da kakeson yi mar ko ze d'an samu peace of mind please." Murmusawa yayi cike da k'asaita yadda manyan alhazai keyi.

"Hajiya Mariam you're a blessing to this family, a da kafin in aureki ban zata zan iya sake walwala ba a duniyan nan, na d'au bayan rasuwan Fateemah bazan sake tsintan kaina a cikin kalan farin ciki da walwalan da nake ciki ba a yau saidai tun da akayi mana aure kika canza dukannin wad'annan abubuwa. Ke ce sanadin duk wani walwala da farin ciki da nida d'a na muke ciki a yau, you mended my broken heart. Hajiya Mariam bakida burin dayafi kiga our family stays together and happy yau nasan duk inda Fateemah (asalin mahaifiyar Afzal, yar Mariam wacce suke uwa d'aya una d'aya. Ta rasu ne bayan sunan Afzal da kwana biyu sanadin breast cancer) take tana alfahari dake, kin so Prince tamkar d'an da kika haifa."

"Dear kenan" ta murmusa cike da jin dad'in wannan kalamai daga bakin masoyinta. "Ai d'an 'yar uwata tamkar d'a na yake so kadena min godiya banida kaman ka da Prince a duniyan nan. Kuma a kullum ina godewa Allah daya bani ikon farinta maka da Prince, addu'a na kuwa baifin Allah hore mana dogon rai mai albarka in cigaba da kula daku ita kuma marigayiya Allah ya cigaba da kai Rahama kabarin ta."

"Ameen Hajiya Mariam ta" ya amsa a yayinda memories da sukayi sharing da marigayiya suka shiga dawo masa.

"Zaka mar maganan idan mun koma?"

"Queen d'ina ta sa baki ai dole na."

"Kai amma naji dad'i a ringa ma Prince sassauci please kasan yaro ne."

"Ke kuma ki cigaba da shagaltasa kinji ba?" Dariya kalan na manyan mata ta saki sannan ta zuk'e cocktail drink da take rik'e dashi. Hira kad'an suka ta6a sannan driver ya dawo dasu gida. Waya Abba yama Afzal akan yazo ya samesa a site nasa yanzu, alokacin Afzal na zaune a parlour yana playing game. Take ya kashe ya mik'e tare da zira farar jallabiyansa daya rataya jikin hanger sannan ya fito. Knocking yayi aka amsa sannan ya shiga, Abba da Ummi ya tarar akan two seater suna zaune looking so takeaway da alama yanzu dawowansu. Besan ya rayuwarsa zata kasance ba without these two: they simply complete him and he loves them so much. K'arisawa yayi ya durk'usa a k'asa tare da gaishe da Abba cike da ladabi da kuma yiwa Ummi sannu da dawowa.


RANA D'AYA
#RD
Love... King_miemiebee👄✨
[12/08, 22:25] ‪+234 907 483 8352‬: 🎀🎀🎀 🎀🎀🎀
🎀❣🎀
❣❣

💦💦 🍃🍃🍃
*RANA D'AYA!*
💦💦 🍃🍃🍃
March, 2018

_Written by Miemiebee👄_


*PAGE 0⃣4⃣*



   "Ashe abinda ya faru kenan toh Allah kare aukuwan na gaba" fad'in Abba.

  "Ameen Abba thank you" ya amsa a nitse. Numfashi me nauyi Abba ya fisga sannan yace, "I'm sorry for my outburst on you, yaci ace na baka dama kayi min bayanin abinda ya faru kafin in yanke hukunci."

  "Ba komai Abba ni ya kamata in baka hak'uri I'm sorry in shaa Allah hakan baze k'ara faruwa ba" ya amsa cike da girmamawa, kansa sunkuye a k'asa.

"Masha Allah, Dama Alhj Abdallah ne keson ganinka."
  Alhj Abdallah? Afzal ya nanata a ransa, wani Alhj Abdallah d'aya? And saboda meh?

  "Alhj Abdallah Abban Nazeefah" Abba ya sake fad'a ganin kaman ya jefa d'an nasa cikin duhu.

  "Ohh!" yayi exclaiming se yanzu ya fahimci wa Abba ke nufi. Alhj Abdallah Abban Nazeefah wanda ya kasance aminin Abba kuma second neighbour'n su, gida d'aya ne a tsakanin su. "Abba ina fatan lafiya dai ko?" Ya tambaya a takaice.

  "Eh toh it depends, kafin nan ina son muyi wata magana da kai Prince shin ka nada tsayayyiya kuwa?" Zuciyarsa yaji ya mugun har6a bade aure Abba ke shirin masa ba don kuwa be shirya ba, sam ba mace d'ayan da ta ta6a yimasa acikin jerin 'yan matan da Allah ke had'asa dasu. To cut the story short, shi baida ko budurwa d'aya ma balle ace ya cire tsayayyiya a cikin su. Ko da yake London karatu 'yan mata ke binsa and not the other way round, kuma koda wasa be ta6a saurara masu ba haka zalika da ya dawo Nigeria ma yanzu, kusan a kullum se 'yan mata sunzo gunshi a office bayan wanda ke binsa har gida. A sanadin hakan ya hana secretary'n shi barin kowa cikin office nasa in ba wanda ya sanar da ita da zuwan su ba.

  "Kayi shiru ko kafi son ku tattauna da Umminka ne tukuna?" Fad'in Abba jin shirun yayi yawa.

  "A'a Abba ba abin tattaunawa don a gaskiya banida tsayayyiya" ya basa takaicaccen amsa bayan nazarin daya samu yayi.

  "Toh Alhamdulillah" Abba ya saki hamdala wanda ya d'aure wa Afzal kai. Meh hakan ke nufi? Kafin ya kawo wani tunanin a ransa Abba ya cigaba, "Dama Alhj Abdallah ne ke tunanin had'a ka da 'yarsa Nazeefah" wani irin mumunan buguwa zuciyan Afzal yayi wanda sanadin hakan yaji zazzafan ciwon kai na neman afka masa.

  "Aure fa kenan Abba?" Ya tambaya cike da mamaki.

  "Yes Prince aure kuma kaga jifa yazo dai-dai da zama kenan tunda kace baka da tsayayyiya." Holy crap! Ji yayi kaman ya kashe kansa domin haushi, meyasa bema Abba k'arya yace mar da akwai tsayayyiyar ba a farko? But he can't blame himself saboda baida masaniya akan wannan zance Abba ke shirin sanar dashi. In da kuma k'aryan yayi yace yanada tsayayyiyar and Abba ya buk'acesa da yayi introducing nata ya zeyi? Meyasa Ummi bata sanar dashi wannan ne maganar da Abba ke shirin sanar dashi ba? Nazeefah fah? Wancan fand'ararriyar yarinyan da sama da friends nasa uku sunyi dating nata. 'Yar karamar yarinya amman se shegen rawan kai da falli, idan za'a k'irga samarukan cikin Maiduguri masu ji da kansu toh d'add'aiku ne basu fita da ita ba sam batada kamun kai ga d'an banzan rainin da take ji dashi a takaice de ya tsaneta. Meyasa Abba ze yarda da k'udurin abokin nan nasa? Meyasa ze yarda ya bada only son nasa wa 'yar da batada ko kamun kai? He need answers.

   "Prince kayi shiru" fad'in Abba sede har yanzu Afzal besan da wani bakin zai soma magana ba couple with the fact that baida ra'ayin aure ko kad'an yanzu. For crying out loud he's just 25 years old ina laifin abar shi yakai koda 30 ne. "Afzal?" Fad'in Abba for second time.

  "Nnn... na'am Abba" yayi stuttering.

  "Bakace komai ba" ya sake ce dashi.

  "Abba bansan me zance ba, Abba yarinyan can batada kamun kai dan Allah kar ka amince da wannan k'udiri" ya fad'a cike da tashin hankali.

  "Tabbas ba k'arya acikin zancen ka Prince, Nazeefah tayi zara ta fi k'arfin iyayenta kullum complain da Abbanta ke min kenan. Amman idan ka duba, rashin kamun kan nata ne dalilin da yasa Abban nata ke son aurar da ita so she can change her ways. Sanin kanka ne Alhj Abdallah d'an boko ne aurar da yaro at a very tender age sam baya d'aya daga cikin tsarinsa, dalili ne ya kawo hakan kuma kaf cikin yaran abokansa tare da ni amininsa ba wanda yaga yayi masa ya kuma yaba da hankali da tarbiyyarsa kaman kai Afzal, ka gane amincewa da wannan aure kaman yin jihadi ne. Wata k'il idan akayi mata aure zata canza wannan gur6a66iyar rayuwar data d'au wa kanta" Abba yayi concluding.

  "Abba ni kuma fah? Ban shirya yin aure yanzu ba, ban ta6a kawo tunanin aure ba a nan kusa, Abba please don't give me out" ya fad'a a maraice.

   "Kayi hak'uri Afzal am not trying to give you out nasan wannan babban abu nake nema daga gareka shiyasa naso muyi maganan as father and son insan meye point of view naka, idan har baka son yarinyar kuma baka tunanin ko a nan gaba zaka ita yin hakan, fine bazan yi maka auran dole ba. Kai kad'ai Allah yabani Afzal and da sani na bazan ta6a yanke hukuncin da zai cutar da kai ba, ina sonka fiye da duk wani mahaluk'i a duniyan nan. Sanin mune nan kaf yarinyan nan Nazeefah bata kai ta cutar da kai ba in kuwa har zatayi hakan toh wallahi bazan ma bari a yi nisa da zancen nan ba. Da tunda mahaifinta ya tunkare ni da maganar zan ja masa layi but we all know bata kai tayi ma wani abun ba. Afzal I've known Alhj Abdallah for a very long time, tun ina masters dina. Da nauyi Afzal in ba haka ba da zan koma in sanar dashi cewa lallai-lallai kai baka amince da wannan k'udiri ba, bazan bari a cutar min da kai ba Afzal. I'll appreciate it if you'll reconsider your decision amman idan har kai kaga you can't find it in your heart to love that girl zanyi iya k'ok'ari na in fahimtar da shi abokin nawa."

    A hankali maganganun Abba suke shiga jikin Afzal suna tasiri. Kaman yadda Abba ya nuna cewa rashin halacci ne ga abokinsa idan har bai cika masa wannan buri ba shima Afzal haka yake gani. Gani yake idan har be bawa Abbansa goyin baya ba toh rashin kyautatawa ne why because tun zaman shi da Abba wannan ne karo na farko Abba ke neman abu a gurinshi da ya kuma nuna muhimmancinsa haka. Tabbas auren Nazeefah baze kashe sa ba toh why can't he sacrifice his happiness for his father's??

Ya d'au tsawon lokaci yana nazari amman ya kasa deciding akan komai, ji yayi k'wak'walwarsa ta toshe gabad'aya, a sannu a sannu ya d'ago kansa dake dafe tun d'azu ya shiga magana a hankali "Tabbas k'in amincewa da k'udurin Alhj Abdallah rashin halacci ne a gareka Abba kamar yadda nima rashin baka goyin baya yake rashin kyautatawa a matsayina na d'anka. Moreover, koda ni ne na tsinci kaina a cikin wannan halin da kake ciki I would do thesame" ya tsaya. Sosai Abba yaji dad'in kalamun nan da suke fitowa daga bakin Afzal. A kullum godiyanshi kenan ga Allah na basa d'a mai hankali mai kuma tunani kaman Afzal wanda yake gudun b'acin ransa wane aikata sa6o wa ubangijinsa.
   A hankali Afzal ya shiga magana "sai dai-" wanda Abba yayi saurin katse sa a nitse.

   "Karka damu Prince ba wai don ka auri yarinyan nan hakan na nufin nan a gaba idan Allah ya had'a ka da wacce kakeso bazaka iya auranta bane wallahi ni ko bayan wata d'aya da auran naku ne ka kawo min wacce kakeso I'll respect your decision in aura maka ita kuma ba abinda Nazeefah ko iyayenta suka isa suyi da hakan, you're a husband to four wives, all I'm asking is kayi hak'uri ka amince da k'udurin mahaifin 'yar nan."

  "Abba..." ido Ummi ta masa don haka yayi shiru.

  "Ba seka amince right away ba Prince, take as long as you want to make up your mind I shall respect every decision you take fata na kawai zakayi considering wannan situation, kasani k'in amincewar ka ga auran 'yar nan kaman tozartani ne a idon amini na da kuma duk wani mutumin da labarin nan ya iske sa. Kaje na sallameka Allah yima albarka, thank you for your time."

  "Toh Abba ameen, seda safe Ummi goodnight" da haka ya miqe ya fice zuwa site nasa inda ya zube a kan gado a yayinda kansa keyi masa wani irin sara, ji yayi komi ya dena tafiya masa a duniyan. Ina ma Allah ze d'au ransa cikin wannan dare (wa iyya zubillah) don komi ya wuce. Ina ma ba a ta6a k'addaro masa da rana irin ta yau ba. Upon all the women out there Nazeefah ze aura? Yarinyar daya tsana fiye da mutuwarsa, fiye da duk wani mahaluk'i a duniyan nan kuma yake da tabbacin itama ta tsanesa as much ba don komai ba kuwa se don tsan-tsan tsana da k'yaman da yake nuna mata a fili, a bayyane a fuskan sa anytime path nasu yayi crossing. God help him. A da har ya fara gyangyad'i kafin kiran Abba amman yanzu baccin nasa ya nema gabad'aya ya rasa ba don komi ba se don tashin hankali. Ido ya zura wa ceiling yana k'ok'arin tattaro hankalinsa, ana cikin haka yajiyo knock a bakin k'ofan d'akinsa se yanzu abin ya fad'o masa ashe beyi locking main k'ofar site nasa ba.

  "Come in" ya fad'a cikin wata irin kasalacaccen murya. K'ofan na
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment