Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

baze iya biya ba don Allah ka basu hak'uri."

  "Hak'uri won't fix anything the only thing that could fix that mess is ayi replacing da sabo."

  "Ya Afzal wallahi ko nan da shekara ka bani bazan iya siyan sabo ba."

  "Then tun da wuri kisan yadda zakiyi hakan kokuma ki shirya zuwa gidan yari."

   "Ya Afzal don darajan Allah ka taimaka min ka rufa min asiri ka basu hak'uri."

  "Kinsan wani abu? Inda wata ce chan ta rusa koda k'awar kice for example da tuni na bada kud'i an sai sabo, kinsan dalilin dayasa bazan taimake ki ba?"

"Saboda na maka rashin kunya, na 6ata maka mota nayi maka abubuwa kala-kala amman don Allah kayi hak'uri wallahi ban k'arawa na tuba."

  "Jeki kira k'awarki dake la6e achan" ya buk'aceta. Falmata na ganin Amal na nufo inda take la6e ta shiga neman hanyan gudu da k'yar Amal tasamu ta amince ta biyota.

  "Gata nan" cewar Amal.

  "Dude kana cin abin nan ko?" Afzal ya tambayi Sultan yana nuni da soyayyen gyad'an dake kan Falmata wanda 'yan Maiduguri ke kira da mandawa.

  "Yes?" Sultan ya amsa sa cike da neman k'arin bayani.

  "Alright, k'irga gyad'an nawa ya rage duka" ya buk'aceta, nan ta sauk'e tray natan ta k'irga "Na d'ari biyar da hamsin ne N550."

  "Good amshi tray d'in Amal" ba musu tayi yadda ya buk'ata.

  "Good inason ki zauna- no ki tsaya anan k'ark'ashin ranan nan ki shiga gyara gyad'an nan kina tarasu cikin leather daban, idan kin gama ki kawo min ciki and mind you ko alaman 6awo na gani aciki aikinki ia ruined zan saki a hannun securities d'innan suyi duk abinda sukayi niyya dake" ya fayyace mata muryansa ko alaman wasa babu bale Amal tace almarai yake bata. Ba ita kad'ai ba harta Sultan da Falmata seda suka sake baki ganin yawan mandawan da Afzal ke shirin sa Amal gyarawa. Mandawan da ko leda d'aya akace mutum ya gyara seya galabaita.

  "Duka na kan tray d'in?" ta tambaya cike da rashin yarda.

  "Yes you heard me right, haka ma zakiyi gobe da jibi in fact for a whole month or two only then zan amince in biya kud'in board d'incan da kika rusa. Kekuma Falmata ko?" Ya juyo kan k'awar nata "Daga yau kina ajiye min gyad'an nan naki na d'ari biyar and make sure kin taho tare da Amal, kina ji na?"

  "Eh, eh naji" ta amsa.

  "Good oya kekuma me kike jira da baki fara gyarawa ba? ga chan tap (famfo) a chan go and wash your hand da akwai sanitizer a gefe kiyi sanitizing hannunki. Securities you can go back to your posts zanyi handling mess d'in."

  "Alright sir" suka amsa tare da ja da baya.

  "Toh Ya Afzal amman naga kaman gyad'an d'ari biyar yayi wa Ya Sultan yawa ina laifin in 6are mishi na d'ari??" Amal ta tambayesa cikin best lady like manner nata.

  "Sauran inga kina tayata kekuma" yace da Falmata totally ignoring Amal, "I'll be inside duk abinda kukeyi anan zan hangoku daga ciki don't think of messing with me, guy let's go."

  "Mu nemi inuwa toh mu zauna" cewar Amal tana mey neman inda akwai rumfa.

  "Baki ji me nace bane? Nan k'ark'ashin ranan nakeso ki tsaya kiyi abinda na saki, ko jinguna naga kinyi jikin bango toh zan fasa biyan kud'in in kuma sasu su kaiki police station."

  Miyau ta had'iye "Allah sarki don Allah ka tausaya min." Be sake yi ta kanta ba shida Sultan suka wuce ciki. Tun Falmata na iya juran taya Amal tsayuwa k'ark'ashin ranan taga bazata iya ba ta nemi inuwa ta zauna, Amal baiwar Allah se gyaran gyad'a take ko 6awo bata bari kaman yadda Afzal ya buk'ata. Tayi leda shida (6) ta soma jin jiri saboda zafin ranan, ji take kaman ta tsala ihu amman ba daman yin hakan. Haka abin tausayi seda ta kwashi kusan awa biyu k'ark'ashin rana me tafasar da k'wak'walwar mutum sannan ta samu ta gyara duka. Alokacin har ta gama kod'ewa idanunta sun kad'a sunyi ja, bayanta wane ze 6alle se gumi da zufa take had'awa. Security tasa yayi ma Afzal magana nan ma seda ya gama ja mata aji sannan ya fito da wani saucer a hannunsa kad'an daga cikin gyad'an ya d'iba ya kira Falmata ya mik'a mata ragowan "Ga wannan kici wanda zaki iya ci sauran ki kai wa k'annenki a gida kokuma kiyi sadaqa dashi a layi. hungo kud'in ki."

   Baki bud'e cike da mamaki Amal ta tsaya tana kallonsa. Yanzu duk uban wahalan nan d'an abinda ze d'iba kenan? Ina laifin ita data sha wuyan gyaran ne ma ze ce mata ta tafi da ragowan amman seya kama ya bawa Falmata??? Ji take kaman zuciyarta zata k'one don tafasar da takeyi. Na farko duk a sanadin Falmata ne wannan abu ya faru se gashi yanzu ta kwashi awa biyu tana aikin sarrafa gyad'a daga k'arshe kuma a bawa Falmata wai taci? Riba biyu fa kenan, ga kyautan sarrafaffen gyad'a ga kuma yanzu ba se tayita yawo a gari tana talle ba lokaci guda za'a siye mata fiye da rabin gyad'anta. Lallai kuwa daga yau tayi hankali wallahi duk wani abinda bai shafeta ba ba ruwanta dashi.

   ***
   Kaman yadda Afzal ya tsara haka Amal da Falmata suka zo ma yau, yadda akayi jiya haka a ka kuma yau, gyad'an d'ari biyar (500) tas ta sarrafa tsaye k'ark'ashin rana me uban tafasa k'wak'walwar mutum, sanin kowa ne yadda ranan Maiduguri yake daban da na kowani gari. Bayan ta k'are ya fito ya bawa Falmata duka mandawan yau kasancewar Sultan baya nan shi kuwa be iya ci ba, itade Amal k'una ne kawai zuciyarta batayi idan taga yabawa Falmata gyad'an dake d'aukanta awa biyu ko fiye tana gyarawa.

    Anyi hakan na kwana hud'u Amal taga fa idan ta cigaba da haka toh wallahi setafi gawayi bak'i, ga shi tun ba'a je ko ina ba bayanta ya soma mata ciwo, kuma gashi tasan taurin kai da zuciya irin na Afzal ko mutuwa zatayi ta sake dawowa ba canza mind nasa zeyi ba tun akan abinda ya faru a asibiti ranan ta gano hakan, ta sani ras seta cika wata ko watanni biyu da ya yanke matan sede dukda hakan bazata kariya ba zata basa hak'uri.

    Washegari bayan sun isa ita da Falmata sega Afzal na fitowa daga office da alama masallaci ze zarce yayi sallah, bayan ta jira ya idar ya fito ta taresa ta shiga basa hak'uri harda guntun hawayenta amman kaman yadda tayi tsammani haka ko kallonta beyi ba balle ya tausaya mata yaja baya da wannan punishment. Haka tana kuka ta koma k'ark'ashin ranan ta cigaba da gyaran daga inda ta tsaya. Bayan ta iso gida ta tsaya a shagon Usama ta sai 40 leaves. Bayan sallan Isha ta d'an huta sannan ta d'au littafin da biro ta shiga rubuta, "I'M SORRY YA AFZAL I WILL NEVER DISRESPECT YOU AGAIN" layi-layi tun daga fejin farko har seda ta kai na k'arshe, ko bacci bata samu tayi ba daren ranan se bayan sallan Asuba data gama.

   Yau bayan ita da Falmata sun isa office nasu Afzal me gadi ya isar mata da saqon da Afzal ya bada a mik'a mata, na cewa baya nan ya fita meeting amman yasa asa mata ido kar ta kuskura ta ko tsuguna bale tayi tunanin shiga inuwa kokuma ta rok'i Falmata data tayata. Bayan kuma ta gama gyarawan ta d'iba rabi ta bawa Falmata rabi ta ajiye masa. Hakan tayi bayan tagama ta had'a masa rabin da littafin data siyan ta bawa me gadi sannan suka fice.

  Se chan kusan yamma Afzal ya dawo office, bayan me gadi ya miqa masa saqon ya buk'acesa littafin kuma daga gun waye ne? A takaice ya amsa shi yace daga gun 'yan matan ne. Documents nasa ya tattara ya dawo gida inda ya kaiwa Ummi gyad'an.

  "Prince mandawa dayawa haka kuma gashi har an 6are an gyara" fad'an Ummi tana k'ok'arin kai amount data d'iba baki. "Gaskia nagode."

  "You're welcome lemmi rush to my site."

  "Kaifa bazaka ci ba? Gashi ya soyu dai-dai be k'one ba."

  "Nahh ban iya ci ba."

"Yo baka ta6a ci ba dama taya zaka iya? Kade gwada kaji Allah da dad'i."

  "No thanks" d'iba tayi a hannunta "Bud'e bakin in sa maka kaji" seda tayi dagaske ta samu ya bud'en tasa mishi se kuma ya mishi dad'i ashede for all these he's been missing alot. A saucer ta d'iba masa ya wuce site nasa dashi. Bayan ya watsa ruwa ya fito da alwala sannan ya shirya yaje masallacin unguwa yayi sallah. Wayansa ya had'a a charging ya shiga viewing Instagram feeds nasa yana jefa gyad'an time to time a baki. Chan ya mik'a hannu ya jawo littafin da me gadi ya basa na cewa Amal ce tace a bashi. First page d'in ya bud'e ya soma cin karo da kalmomin hak'urin data rubuta. Murmusawa yayi tare da flipping next page d'in nan ma haka, tsallakawa yayi ya kai tsakiya yaga har nan hak'urin take basa. Murmushin yake har yanzu ya shiga bi daga farko zuwa k'arshe sannan ya mik'a ya ajiye inda yake keeping important documents nasa. Ashe tasan yin rashin kunyar da take ba kyau amman takeyi, da kyau.

A tsammanin Amal washegari idan taje ze ce mata ya yafe sauran punishment d'in ta tafi sede ta tarar da opposite d'in hakan. Sam yi yayi wane saqon nata be iske sa ba, don dad'in da gyad'an ya masa jiya yau har cikin office nasa ya shigo dasu da ta gyara kad'an se ya kwashe yaci, kafin su hankara Afzal ya cinye gyad'an d'ari uku da ashirin (N320) shi kad'ai. Sai the following day ne bayan sunzo ya saye gyad'an har Amal ta fara gyarawa yace masu ta bari su tafi ya yafe mata. Dad'i sosai taji ashe de yana sauraron hak'uri lallai kuwa ta kama kanta kar ta sake yi masa abinda ze fusatar dashi if not itace zatayi bearing consequences. Don ta lura duk wani iskanci da rashin ji da take ji dashi Afzal yana gaba da ita.

   Tun daga ranan kullum Falmata ke kawo wa Afzal gyad'a wani sa'in Amal kan biyota while most of the times ita kad'ai take zuwa. Anytime kuwa suka zo tare da Amal a bakin gate take la6ewa gudun kar ko kallonsa tayi yace ze bata wani punishment d'in, abu kaman wasa Afzal ya zama addict na gyad'an Falmata har idan gari ya waye beci ba baya jin dad'i.

   Rana d'aya ko mey ya buga kan Amal kawai ta buk'aci Falmata da ta bata mandawan Afzal, zama tayi ta gyara masa su tsaf ko 6awo d'aya babu sannan ta baiwa Falmata da ta kai masa kaman kullum yau ma ta tsaya bakin gate tana jiran fitowarta. Sosai Afzal yasha mamaki bayan da Falmata ta mik'a mishi gyararren gyad'a cewa kuma daga Amal ne. Lallai yarinyan tayi hankali yayi tunanin haka a ransa kode she is upto something not good again ne? Waya sani ko ta barbad'a masa maganin da ze rud'a masa ciki yasa masa diarrhea (gudawa) amman kuwa idan har tayi kuskuren yin hakan se tayi nadaman shigowa duniya.

  "Kikace Amal ce ta gyara duka wannan?" Ya sake tambayan Falmata yana mey bin mandawan da kallo.

  "Eh" ta amsa tana kallonsa.

  "Yau ma tana wajen ne?"

  "Eh."

  "Jeki kira min ita."

  "Toh" da haka ta sauk'a k'asa sede sam Amal tak'i biyota, da k'yar Falmata ta samu Amal ta amince bayan rantsuwan da tayi ta mata na cewa ba abinda Afzal zeyi mata. Ita Amal gabad'aya cikinta ya d'au ruwa gudunta wai kar yace tayi gwaninta yace ze sake bata wani punishmennt d'in. Bayan knocking da Falmata tayi Amal tayi sallama sannan suka shiga ciki. Yau kaman ba Amal ba harda durk'usawa da zata gaishe da Afzal, dama bahaushe yace fad'an da yafi k'arfinka dole ka mai dashi wasa. Yau duk taurin kai da rashin ji irin na Amal ta tarar da wanda yafita hakan.

   "Ke kika gyara?" Ya tambaya yana tura mata ledan gyad'an gabanta. Kai ta gyad'a a hankali.

  "Meyasa?"

  "Kawai."

  "Nace me yasa?" Ya kuma tambayarta.

"Allah babu."

  "Zo ki d'auka kici I don't trust you."

  "Wai tunani kake zan cutar dakai in sa maka wani abin a ciki?" Ta tambayesa da mamaki.

  "Thank god you know."

  "Wallahi ba abinda nasa ciki."

"Then zo kisa a bakinki kici in gani." Sanin ba abin cutarwan da tasa a ciki ta k'arisa ta d'iba kad'an ta kai baki ta tauna sannan ta had'iye, duk anan kallonta Afzal yake. "Kaga ba komai wallahi."

  "Thank you" yace da ita.

  "You're welcome" ta amsa.

  "Baki amsa min tambaya na ba har yanzu why did you do it?"

  "Ya Afzal bana son mu zame annabi da kafiri a matsayin mu na musulmai, nasan nayi maka laifi but like I said I'm sorry bamu san wa ze amfana da wani ba wataran kuma ni bana son in mutu sanin cewa wani ya rik'eni a zuciya, ko baka fad'a ba nasan ka tsaneni kana jin haushina but I'm sorry I promise never to disrespect you again."

  "Hah!" Dariya kad'an ya saki yana mey juya kansa akan office chair'n da yake zaune akai "So kinsan cewa disrespecting na gaba da kai ba kyau?" Ya tambaya had'e da d'age gira.

"Eh na sani kayi hak'uri" ta amsa a nitse tare da sunkuyar da kanta.

"Meyasa kikeyi then? Saboda mutane suyi miki baki? Kinsan sharrin bakin mutum kuwa?"

   "I'm sorry" ta furta tare da pouting bottom lip nata.

  "We're good" ya fad'a bayan tsawon lokacin daya d'auka yana mey wasa da pen da yake rik'e dashi a hannunsa.

  "Dagaske baka tsane niba yanzu?"

  "I never said I hate you."

  "Thank you Ya Afzal" ta fad'a wanda yasa sa murmusawa kad'an. Dubu ya zara ya mik'a wa Falmata "Ya Afzal ba canji" tayi saurin cewa.

  "Ki bawa Amal change d'in ta rik'e in kin samu."

  "Name nikuma?" Tayi saurin tambaya. Wani banzan kallo ya watsa mata wanda yasa tuni ta shiga yi masa godiya ba tare da tasan tayi hakan ba. Aikin gabansa ya cigaba da yi yana cin gyad'an da Amal ta gyara masa time to time.

****
Haka nan tun daga ranan anytime Amal is less busy zata d'au lokaci na musamman ta gyara gyad'a wa Afzal gyad'a rananda batada lokaci kuma haka Falmata ke kawo masa atimes ta gyara mishi most of the time kuma yace karta damu zeyi da kansa.



  *** GIDAN ALHAJI ABDALLAH ***

  "Ina Nazeefan ne wai kam?" Cewar Mummy tana me lek'an k'ofa ko zata ganta. Bada dad'ewa ba sega Nazeefah tafe, ba shakka tunanin auren da ta sa a gaba ne ya zubar da ita haka dan kuwa har duhu ma tayi sekace ba ita ba. Ga kwana biyu ta rage jin kid'i da sauran rawan kan da ta saba, a takaice de ta sauya halayenta cikin samarukanta befi d'aya zuwa biyu suke huld'a ba yanzu, batun aure kuwa bata sanar da kowa ba banda Rumaysa k'awarta.

  "Khaleefah be fad'a miki ina kiranki bane kam?" Abinda Mummy ta fara ce mata kenan.

  "Ya fad'a gani" ta amsa tana neman zama gefen Mummy akan bed bench dake d'akin.

"Batun auren naki ne dama kun kusa gama semester'n nan ko?" Kai zalla ta gyad'a.

  "Good tun last two to three weeks Daddy ya tura saqo wa Afzal amman se shekaran jiya ya bada amsa."

"Amsan mey?" Tayi saurin tambaya.

"Game da ranan aurenku da Daddy ya buk'acesa yayi fixing, kaman yadda zaki Hajj this year shima Afzal hakan Abbansa ke shirin kaisa so yace bayan ya dawo ze bada specific date kinga by then kuna hutu kuma ko?"

  "Wannan cin fuska da mey yayi kama? Shin keda Daddy kuna son Afzal ya mutuntani ya ganni da k'ima kuwa? Yanzu Mummy ace ko ranar aure na Daddy baze bari inyi deciding da kaina ba komi se abinda Afzal yace, ba damuwa" ta k'are maganan hawaye na ciko mata a ido.

  "Toh ya muka iya Nazeefah? Ko ni ban goyi bayan shawaran nan ba amman Daddy'nki koni ya dena jin maganata hak'uri ya zama dole, kede kawai ki cigaba da addu'a Allah yasa Afzal ya rik'e ki amana ya kula mana dake."

  "Da abinda Daddy keyi ko nine shi Afzal d'in bazan rik'e matar da iyayenta ke nunawa batada k'ima kona misqala zarratun da amana ba" ta fad'a chan ciki-ciki sanin sarai Mummy zata jita sannan a fili tace "Ni zan koma d'akina."

  "Tsaya tukuna kinsan gobe first of Ramadan ko? Daddy yace zan tayaki mu had'a kayan shan ruwa wa Afzal."

  "Wallahi ni bazanyi ba" nan take ta rushe da kuka. "Wallahi bazan yi ba."

"Nazeefah da hankalinki?"

"Mey hakan kuke shirin min keda Daddy please? Sekace wata bazawara second class slut wacce bata da k'ima da daraja a idanun jama'a. Haba Mummy koda Daddy ya amince be kamata ke ki biye masa ba, saboda farin cikinku na yarda na amince da auren dolen nan da kuke shirin min dukda cewa kun sani wallahi yau idan na kai k'arar ku gun ko wani malami ne a garin nan hana aukuwan auren nan za'ayi saboda ko musulunci ya hane yin auren dole amman duk baku ga k'ok'ari na ba? Haba mana! Yanzu kuma zaku sake tilasta ni in kai masa abinci? Shi waye? Mijina ne shi? Ko nid'in nace muku ina son shi ne da kuke ta nema min gindin zama gun shi haka?"

   "Allah baki hak'uri nide saqon da aka bada na isar miki idan kinga bazaki iya bi ba fine Nazeefah kece da rayuwarki kuma dama kin saba yin abinda kika ga dama ba abinda iyayenki sukeso ba, go ahead sue us to court if that will please you" Mummy ta sanar da ita rai a 6ace sam bata ji dad'in abinda Nazeefah tace mata ba, eh auren dole ba kyau amman ai kuma ita ta janyo komi wa kanta kuma tasani koda ba'a tone zuciyan Daddy ba, tasan bawai da son ransa yake yin abubuwan da yakeyi ba, he is only doing what he thinks is right as a father.

"Ki tashi kina iya tafiya" ta sanar da ita ba walwala a fuskanta sam.

"Kiyi hak'uri" daga fad'in haka ta mik'e da hawaye na bin k'uncinta ta fice.

  Washegari Daddy da kansa ya tura Nazeefah kitchen ta samu masu aiki da Mummy suka had'a had'add'en kayan bud'an baki wa Afzal. Daddy ya bari masu aiki su kai mai ma yak'i wai sam se de Nazeefah in kuma bazata kai ba tabar masa gida.

Ita Nazeefah ko a mafarki bata ta6a kawowa a tunanin ta cewa Daddy ze juya mata baya haka ba. A da se abinda tace da kuma abinda takeso yakeyi amman yanzu ko damuwa da feelings nata baiyi, abinda ya mishi kawai yakeyi regardless of her feelings. Bayan kukan data dad'e tana yi a bayi ta wanko fuskanta sannan ta fito ta sanya hijabi ta d'au basket d'in ta fice. Wani sabon kukan ta soma yi a bakin gate d'in, seda ta gama shan kukanta sannan ta k'arisa. Site na Ummi ta nufa inda Afzal ke zaune kan two seater ya mik'ar da dogayen k'afafunsa kan centre table se faman latsa waya yakeyi. Sallama tayi ya amsa ba tare da sanin wacece ba, ganin itace yaja k'aramar tsuka tare da kawar da kansa idan da yasan ita tayi sallamar da be amsa ba. Wayansa ya cigaba da latsawa tamkar ba mutum bane ya shigo parlourn. Tafi minti biyu tsaye bakin k'ofan ta na neman koda inuwan mutum ne sede ba Ummi ba masu aiki da alama duk suna kitchen ne suna aiki, taso ta nufi kitchen d'in saidai kuma ba dad'i ka fad'a kan mutane suna ciki aiki.

Tsayuwan ta cigaba da yi tana jira
Ko Afzal zey mata magana sede sam abun ba haka yake ta fannin sa ba. Chan da tsayuwan mutum ya ishesa a ka ya mik'e da niyan zarcewa site nasa. Yazo gab da wuceta ta danne zuciyarta tayi masa magana, "Ina Ummi please?"

  Bayan tsawon lokacin da ya d'auka yace, "In yau kika fara shigowa gidan let me know excuse me" ya sanar da ita cike da gadara ba tare da ya ko kalleta ba.

  "Gashi inji Daddy a kawo maka" ta kuma danne zuciyarta da take yi mata k'ona.

  "You can keep it on the table tell him nagode ya sha ruwa lafiya." Dab ya kaiga fita kenan sega Ummi ta shigo from nowhere.

  "Ahh ahh Nazeefah kece a gidan namu yau" abinda ta soma cewa kenan a yayinda take sa kai cikin parlourn.

  "Ina yini Ummi?" ta durk'usa har k'asa ta gaisheta.

  "Lafiya k'alau Mama na ya kike ya azumi?" Nan de suka gaisa. "Prince shine baka sanar cewa Nazeefah ta shigo ba?" ta juyo tana kallonsa.

  "Barin je in watsa ruwa it's getting to Maghrib" ya fad'a tamkar bey ji abinda Ummi ta fad'a ba. Kai kawai ta kad'a ta bisa da kallo yayinda ya fice. Pepper chicken da fruit salat ta d'iba wa Nazeefah kan ta kaiwa Mummy.

Bayan an sauk'o daga sallan Maghrib Afzal ya dawo site nasa da shirin cika cikinsa saboda ba k'arya azumin yau ya d'an garasa kasancewar ya kwana biyu beyi azumin Mondays and Thursdays da yake d'anyi ba. Har ya zauna kenan se ya lura da kulolin dake jera akan table d'in ba shakka sune wanda Nazeefah ta shigo dasu d'azu dan kuwa Ummi bata da kalan kulolin nan.

"Aikin Ummi" ya furta a fili. Yasan ba wanda zeyi masa kalan d'anyen aikin nan se ita. Sarai da gan-gan tayi hakan, rasa nayi yayi dan kuwa ko za'a had'a sama da k'asa baze ci girkin Nazeefah ba yasan wani concussion d'in tayi ciki? Fridge nasa ya nufa ya zaro wata silver flask daga gun freezer wanda Amal ta basa d'azu. Babban cup ya ciro daga cabinet ya juye kusan rabin zo6on aciki sannan ya shiga kwankwad'a be cire daga bakinsa ba sanda ya shanye nan ya sake cika rabin cup d'in ya kuma juyewa a cikinsa sannan ya d'an jisa da seti. Cookies ya d'aura a kai chan bayan Isha ya fita ya wuce restaurant inda yaci abinci, wanda Nazeefah ta kawo kuwa masu aiki ya kira yasa su suka zauna suka cinye tas sannan suka fita da kwanukan bayan warning daya kashe musu na cewa komin yaya kar Ummi tasan cewa bashi yaci abincin ba.

   Washegari shi kad'ai ya yini a office kasancewar Sultan yana meeting. Amal kuwa ko mey ya hanata shigo masa yau se Allah if not yawancin kullum tana bin Falmata su taho tare, ko da Falmata ta koma makarantar kwana kuwa Amal bata fasa kawo masa ziyara bayan sati sati ba, se gashi yanzu kusan kullum seta shigo masa ta taya sa hira da wasu k'ananun aikin office wanda baza a rasa ba. Cikin d'an k'ank'anin lokaci suka saba suka soma sakewa da juna unlike Afzal, Amal nada saurin sakewa da sabo da mutum saboda iya zuba surutun ta. Wajajen hud'u Afzal na shirin barin office sega Amal ta shigo, ganinta kawai da yayi se yaji dad'i ya ziyarci zuciyansa atleast zata d'anyi masa lighting mood nasa.

   Bayan sun gaisa ta zauna a kujeran data saba zama kullum, "Bade shirin tafiya kake ba Yaya?" Ta tambayesa.

  "I thought you weren't coming today" ya amsa a takaice.

  "Mami ne ta aikeni wallahi taji nace zan maka kunun aya shine itama wai senayi musu da Papi ta sake aika na kasuwa" tayi maganan tana ajiye masa wata medium sized silver flask a kan table. "Ka
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment