Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

KISAN GILLA 1
Littafi na biyar
Na Abdulaziz sani madakin gini
Ebook creator:- Shuraih Usman 99%
Domin download na wasu kayatattun littatafan Hausa a matsayin Hausaebooks tayadda zaku iya saukewa ku karanta acikin wayoyinku sai ku ziyarci wannan shafi www.shuraih.waphall.com Sannan ku zabi littafin da kuke so

For more download of some non- fictional hausa books as a hausaebooks so that you can download it to your phone and read it at any time (offline reading) then visit our wepsite at www.shuraih.waphall.com Adress and select your books for offline reading
Gargadi:- wannan ebook din bana sai ruwa bane kuma ba anyishi bane don batanci ga wani koh ga wata
Sannan ni shuraih Usman 99% bana tura littafi ta private kuma bana whattsapp sannan banda group a whattsapp ga wanda yaga wani kuskure da muka making acikin wannan littafi sai kiramu akan wannan nombar 08170707521

Ga duk wanda baisan yadda ake downloading na littatafanmu ba sai ya ziyarce mu akan wannan adireshin yanar gizo gizon http://keffians.xtgem.com/forum Sannan yayi tambaya in sha'Allah muku ma zamu mai bayani dalla dalla akan yadda ake sauke littatafanmu
Sannan ina kara maimaitawa bana whattsap kada wani ya ha'ince ku ta hanyar amfani da sunana a whattsap asha karatu lafiya
Hakkin mallaka (m) Abdulaziz sani madakin gini

KISAN GILLA
Littafi na Daya (1)
Part A.
.
Marubucin Littafin
Abdul Aziz Sani M/Gini
Typing AA Misau
Ke Magana
.
Labari ya isowa AA Misau cewa...
MARUBUCIN YA RARA DA CEWA,
A wani zamani can baya mai tsawo da ya shude anyi
wani babban birni mai suna madinatul haswar
a cikin daular larabawa
birnin madinatul haswar ya bunkasa a kan karfin
arziki girman kasa, karfin mayaka da yawan al umma
sarkin dake mulkin birnin madinatul haswar ya kasance adali mai tausayi da jin kan
talakawa ana kiransa da suna HISHAM IBN UBAIDA
.
SARKI HISHAM yana da matar aure guda daya jal mai suna
shamilat wadda ta kasance yar wani babban sarki mai
mulkin wata kasa da ake kira da hushush ana kiran wannan
sarki da SAHIBUL HILAYAT
sai da sarki hisham ya auri shamilat da shekaru goma sha daya sannan Allah ya
albarkace su da samun juna biyu nan fa sarki hisham da shamilat suka cika da tsananin farin ciki
domin
a duniya basu da wani buri wanda yafi ganin sun sami haihuwa saboda a shekarun
baya babu abin da basuyi ba, domin su sami
haihuwar amma abu ya gagara,
lokacin da mahaifin
shamilat ya samu labarin cewa 'yarsa ta sami juna
biyu sai ya kamu da tsananin farin ciki fiye da ita
kanta shamilat din da mijinta saboda shi kuma bashi da burin da yafi yaga jikansa
kafin ajali ya riske shi kasancewar tsufa ya
riske shi
a ko yaushe ta Allah zata iya kasancewa
Al amin Ahmed Misau, Guyson nake magana,
bisa wannan dalili ne sarki sahibul hilayat ya
tashi manzanni da dukiya mai yawa ya aiko su izuwa ga sarki
hisham yace ga wannan ayi
renon ciki kuma idan haihuwa tazo daf yana son
shamilat ta je gida ta haihu, yayin da wannan sako ya isa ga
sarki hisham sai hankalinsa ya dugunzuma domin
baya son ya rabu da matarsa dai dai da dakika daya
amma kuma yana matukar jin nauyin surukin nasa don haka
sai ya amince da hakan ita kuwa shamilat sai ta kamu
da matukar farin ciki saboda a rayuwarta babu abinda
take so sama da ta kasance tare da mahaifinta a ko yaushe
saboda ita kadaice 'yarsa a duniya
sarki Hisham yana da dan uwa yarima ZAMARU wanda
ya kasance azzalumi kuma mara imani mai tsananin son duniya
uwa daya
uba daya suke dashi da hisham, a zahiri yarima zamaru
yana nuna cewa yana matukar kaunar dan uwansa
sarki hisham amma a karkashin zuciyarsa babu
abinda ya tsana sama da shi ba wani bane ya haddasa
wannan gaba ba a tsakaninsu face kawai hassada da
kyashi da kuma tsananin son KARAGAR MULKI
TUN mahaifin su sarki hisham na raye ya futa cewa hisham
ne zai gaje shi daga
wannan lokaci ne yarima zamaru yaji ya tsani
dan uwansa sarki hisham ya fara tunanin hanyar
da zaibi ya kawar dashi daga doron kasa sau bakwai
yarima zamaru yana bayar da kwangilar a kashe
hisham amma yana kubuta kasancewarsa sadauki mai
dakawa maza gumba a hannu
Guyson nake magana Al amin Kenan
Lokacin da yarima zamaru yaga ya kasa ganin bayan
sarki Hisham sai ya
zuba ido izuwa lokacin da tsufa zasu riskeshi har
rai yayi halinsa
saboda ya tabbatar da cewa indai babu sarki hisham
dole shine zai hau karagar mulki, ana cikin wannan hali ne
na jiran lokaci kwatsam sai shamilat ta sami juna biyu
hm Al amarin da ya kara dugunzuma hankalin yarima zamaru kenan saboda ya
san cewa idan matar hisham ta haihu to fa
sarautar ta kara yi masa nisa, a ranar da zamaru ya sami labarin cewa shamilat
ta samu juna biyu sai ya kasa zaune ya kasa tsaye
har dare ya raba bai rintsa ba
Babban abinda ya kara jefa
shi cikin bakin ciki shine shima matarsa ba ta taba
haihuwa ba don haka duk ranar da ya mutu shi
kenan bashi da magajin mulki, cikin tsakar dare yarima
zamaru na kai kawo a cikin turakarsa ya kasa barci sai matarsa sarima ta farka
daga barci koda taganshi a tsaye yana kai kawo saita dube shi
cikin tsananin damuwa ta mike da sauri tasha gabansa
tana mai rike kafadunsa, tace yakai mijina menene
ya tayar maka da hankali a yau har ka kasa bacci?
Koda jin wannan tambaya sai yarima zamaru ya yi ajiyar zuciya sannan yace
baki da labarin cewa matar sarki ta samu juna biyu ne?
Sarina tayi ajiyar zuciya tace haba maigida yanzu
a kan haka ne ka tayar da hankalinka har ka kasa bacci koda jin haka
sai zamaru ya rufe sarina da fada yana cewa bata da
hankali bata da kishin rayuwarta,
sarina ta bushe da dariya sannan ta ce ka kwantar da hankalinka mijina ina so ka
sani cewa ni na san abinda ba ka sani ba idan har kana so ka san abinda na sani yanzu ka
tashi mu tafi izuwa can bayan gari wajan wani bakon boka da yazo
cikin alamun karayar zuciya yarima
zamaru ya dubi sarina yace ke nifa na gaji da maganganun bokayan nan
tunda an dade ana ruwa kasa na tsotsewa kuma na gaji da gafara sa har
yanzu banga kaho ba
Guyson nake magana, sarina tayi murmushi tace aiko bokaye
suna suka tara wannan bokan ya wuce yadda duk kake
tsammani duk wani bayani da zan yi maka ba zaka
gamsu ba don haka gani ya kori ji kawai kazo muje wajansa
yanzu a cikin wannan daren cikin sirri
koda jin wannan batu sai yarima zamaru ya cika
da farin ciki kawai sai ya mike zumbur ya kama shiri
yayi badda kama itama sarina yasa ta ta batar da kamanninta sannan sukayi
hawa suka fice daga cikin birnin madinatul haswar a sirrance ba tare da kowa ya shaida su ba
sai da suka yi tafiyar kusan rabin
Sa a sannan suka iso gaban wani katon dutse
wanda a kansa akwai wata yar karamar bukka
abinda ya daurewa yarima zamaru kai shine ganin matattakalar bene a kan dutsen tamkar sassake dutsen akayi
aka samar da ita shi dai
zamaru ya san wannan dutse sama da shekaru
talatin baya amma bai taba ganin wannan matattakala
a jikinsa
ba tabbas wannan matattakala aikin aljanu ne
bana mutum ba abinda zamaru ya ayyana kenan a cikin
zuciyarsa
bayan zamaru da sarina sun tsaida dokunansu a gaban dutsen sun sauka
sai suka daure dawakan nasu a jikin wata bishiya sannan suka taka
wannan matattakala suka hau kan dutsen
suna isa gaban wannan bukka sai sukaga bokan tsulum ya
bayyana a gabansu yana kyakyata dariya al amarin da ya dan razana yarima zamaru
kenan ya dan ja da baya kadan , shi dai wannan boka
ya kasance dogon mutum garjeje mai kirar mutanan
farko jikinsa gaba daya a murde yake alamar
karfi ta bayyana karara a tare da shi yana da yar
faffadar fuska kyakkyawa cike da kasumba da gajeran gemu
babu riga a jikinsa face wata fatar damisa
wacce ya yafata bisa kirjinsa ta zagayo izuwa bayansa
daga cikinsa zuwa gwiwoyinsa a rufe suke
da bante irin na fatar damisar da ya yafa kuma
takalmin dake kafarsa ma anyi shine da wannan fatar damisa
gaba dayan damatsansa na hagu dana dama a cike
suke da gurayen tsafi , tabbas wannan boka yana da kwarjini da cika ido kai da
ganinsa kasan cewa murucin kan dutse ne wato bai fito ba
sai da ya shirya
bokan ya dubi yarima zamaru yayi murmushi yace
kada kaji tsoro ya shugabana ni mai taimako ne a gareka
ko ince zamu yiwa juna taimako ku biyoni
izuwa cikin bukkata mu zauna domin mu tattauna sosai
koda gama fadin haka sai bokan ya juya ya shiga
cikin bukkar nan take yarima zamaru da sarina
suka bishi a baya ba tare da fargabar komai ba
da shigarsu cikin bukkar sai yarima zamaru ya sake cika
da tsananin mamaki domin kansa ne ma ya kusan juyewa
saboda ya tsinci kansa ne a cikin wata makekiyar fada wacce
ta kawatu ainun ninkin
fadar sarki hisham sau uku wadansu kuyangin aljanu sunata hidima da kai kawo
bokan yaci gaba da tafiya a tsakiyar fadar ya nufi inda karagar mulki take
su zamaru na biye dashi amma basu isa inda karagar mulkin take ba sai
da suka yi taku dari da arba in, da zuwa sai bokan ya zauna akan karagar mulki yarima zamaru da sarina kuwa sai kuyangin aljanun
suka kama hannayansu suka kaisu izuwa kan wadansu
kujeru dake daf da karagar mulkin suka zaunar
dasu
nan da nan aka kawowa yarima zamaru da sarina
ruwan inibi a cikin tambulan na zinare da
kofuna suka fara jika makoshinsu a sannan ne bokan ya dubi yarima zamaru a karo na biyu yace lale maraba
da yarima zamaru dan uwan hisham sarkin gobe
Al amin Ahmed Misau
Guyson Sunana Kenan
koda jin wannan batu zamaru ya natsu sosai
bokan ya ci gaba da bayani yana mai cewa
ka kwantar da hankalinka ya kai wannan dan sarki
kayi sani cewa matarka tazo nan kafin kai kuma
mune mukace ta kawo ka
mun san duk abin dake damunka da kuma burin dake
zuciyarka
tabbas mune zamu magance maka dukkan matsalarka muddin muma zaka bi umarnin
mu shin ka amince da wannan sharadi?
Koda jin wannan batu sai yarima zamaru ya dubi bokan cikin alamun rashin
fahimta sannan yace menene sharadin da kake so ka gindaya mun
bokan yayi murmushi yace ina so ka dauki
alkawari cewar idan bukata ta biya zaka raba birninka
biyu ka bani kaso guda na mallakeshi haka kuma zaka bani rabin dukkan
dukiyarka
lokacin da yarima zamaru yaji wannan batu sai
hankalinsa ya dugunzuma ainun ya rasa abin dake masa dadi yayi shiru yana tunani
bokan ya tuntsure da dariya alamun da ya janyo katsewar
tunanin yarima zamaru kenan ya dago kai a
firgice
ya dubeshi yace ni ne Hizainu ibin Markasi masanin sirrin gobe,
yakai wannan dan sarki ina so ka sani cewa babu wani
abu da mutum ke samu a saukake kuma a banza face
ya rasa wani abu
ina mai shawartarka daka dauki sharadina ni kuma na
taimaka maka na sanar dakai duk abinda zaka yi ka
samu biyan bukatarka kuma
yanzu ne kadai damarka
idan ka bari wannan dama ta wuce ka har abada ba zaka samu wata ba
sa adda yarima zamaru jai wannan batu sai ya kawo gwauron numfashi ya ajiye gami da ajiyar zuciya ya sake yin dan guntun tunani
sannan ya dubi boka
hizainu yace na yarda idan ka taimakeni burina ya cika zan raba mulkina da dukiyata
gida biyu na baka rabi amma bisa shardi guda
sharadin kuwa shine sai dai kayi rantsuwa da girman
tsafi da kuma darajar iyayenka cewar a gaba ba zaka yi yunkurin
rabani da mulkina ba
domin ka mallaki kasar gaba daya kuma ba zaka taba cutar
dani ba ko wani nawa
koda jin wannan batu
sai idanun boka hizainu suka zazzaro ya kamu da tsananin
mamaki saboda bai taba zaton cewa yarima
zamaru zai daureshi ba da jijiyarsa haka, al amarin da ya jefa
shi cikin shakku da wasu wasi kenan ya kama muzurai yana
kallon kuyanginsa dake kai kawo a cikin fadar suna hidama
sai da yayi dan tunani da nazari sannan ya bushe da dariya
nan take yayi rantsuwa da girman tsafi gami da darajar iyayansa bisa kan cewa ba zai taba neman
wani abuba daban a wajan yarima
Zamaru a nan gaba kuma ba zai cutar dashi ba koda jin haka
sai farin ciki
ya lullube yarima zamaru yace shima ya amince da bukatar
boka hizaunu
boka hizainu ya kyalkyala da dariyar murna yace
gobe da safe idan kaje fada zaka iske dan uwanka sarki hisha,
a kwance cikin cutar ajali kuma ba zai wuce kwana bakwai ba a kwance rai zaiyi halinsa
abu na biyu da nake so dakai shine a yanzu haka
matar sarki hisham ta haifi da namiji kuma har ta
gama wankan jego ta baro can birnin
darul hushush ta taho izuwa nan birnin madinatul
haswar tare da jaririnta da kuma dakaru dubu biyar masu tsaron
lafiyarta
wadanda suka kasance zakwakuran mayaka fasa taro lallai ka shirya
wadansu zakwakuran dakarun da suka fisu
jarumtaka wadanda zasu je su yake su su kashe matar
sarki ya zamana cewa baka da wata barazana a mulkinka ina mai
tabbatar maka da cewa a daren da dan uwanka sarki hisham
zai mutu ne shamilat da jaririnta
zasu iso cikin garin nan
don haka duk yadda zakuyi kusa a tare su a can cikin daji
kafin su iso kusa da wuri, kuma kada ka kuskura ka shiga
cikin mayakan da zasu je yin wannan aiki kuma ka
tabbatar da cewar anyi wannan aiki a cikin sirri
ba tare da wani ya sani ba lokacin da yarima zamaru
yaji wannan batu sai hankalinsa ya kara dugunzuma fiye da ko yaushe ma ya dubi boka hizainu cikin alamun tsananin
tsoro da damuwa yace yakai wannan boka mai daraja
yanzu a ina zan samo dakarun da zasu iya kashe
dakarun da sarki sahibul hilayat masu yiwa shamilat da
jaririnta rakiya izuwa nan birninmu? Ka sani
cewa dakarun birnin darul hushush mayaka ne na asali kada su ba wasa bane
boka hizainu ya sake bushewa da dariya lokaci guda
kuma ya turbune fuskarsa yace babu wanda zai iya
yi maka wannan aiki face sarkin yakinka amzadu ibn karlyas
koda jin haka sai yarima zamaru ya cika da tsananin mamaki gami da tsoro yace
to yaya amzadu zai amince yayi min wannan aiki alhalin kasan cewa ya kasance
babban aminin sarki hisham wanda a shirye yake ya
sallama rayuwarsa domin kare ta sarki da iyalansa
koda jin haka sai boka hizainu ya sake bushewa da dariya
sannan yace
da zarar sarki hisham ya mutu kaine sarki komai
ya dawo karkashin ikonka da mulkinka
a wannan lokaci kana da ikon sarrafa komai da kowa da karfin karagarka
a daren da sarki
hisham ya mutu ka tura akamo sarkin yaki amzadu da iyalansa a matsayin kana zarginsa
da laifin sawa sarki wannan ciwon ajali tunda kowa ya
san cewa dare da rana yana tare da sarkin
bayan an tsare su a kurkuku shida iyalan nasa sai
kasa a fito dashi shi kadai azo dashi har cikin
turakarka ka kadaita dashi a sannan ne zaka gaya masa
bukatarka ta son ya
debi zakwakuran yaransa suyi
bada da kama suje su kashe matar sarki shamilat da jaririnta
da duk dakarun da sukayi musu rakiya
izuwa nan birnin madinatul hashwar idan
kuma yaki koyayi wani abu ba dai dai ba sabanin umarnin da ka bashi
zakasa a kashe iyalansa idan kuma yayi aikin daidai
bisa nasara zaka bashi babban matsayi a fadarka fiye
da wanda yake da shi a yanzu...
.
Nan zan dan dakata Dafatan Littafin ya kayatar daku
comment da like saimu cigaba
kafin nan
Nidinne Al amin Ahmed Misau
Guyson sunana Kenan Daga
Zauran Labarai NakeKISAN GILLA
Littafi Na Daya (1)
Part B.
.
.
Marubucin Littafin
Abdul Aziz Sani M/Gini
Typing AA Misau
Ke Magana
.
Labari ya isowa AA Misau cewa...
Fiye da wanda yake dashi a yanzu.
lokacin da boka hizaunu yazo nan a zancensa
sai yarima zamaru ya kamu da tsananin farin ciki
nan take ya kama kyalkyala dariya saboda murna sannan ya dubi boka huzainu yace
yakai wannan boka mai daraja hakika ka cika makiru uban masharranta na duniya
Hm
babu makawa wannan dabara taka saita yi nasara
shin yanzu ka tabbatar mini da cewa idan na koma gari zan iske sarki ya kwanta cutar ajali
koda jin wannan tambaya sai boka huzainu yayi murmushi yace yau fa
shekara bakwai kenan ina shiri da jiran zuwan wannan
rana saboda me ma zaka rinka shakku bisa furucina ku koma
gida kuje ku sha barcinku a cikin wannan dare lallai gobe da safe za a yi kiranka izuwa fada kaga zahiri
nan take yarima zamaru da sarina matarsa suka yi wa boka
hizaunu sallama suka fito daga cikin gidan nasa suka hau dawakansu suka koma
cikin birnin madinatul hashwar ba tare da wani ya shaida suba akan hanya
.hakika masu iya magana sunyi dai dai da sukace
tsafi gaskiyar mai shi kuma maso abinka yafika dabara
Kashe gari kuwa da sassafe aka tashi manzo daga gidan sarki ya ruga izuwa gidan yarima zamaru ya sanar
dashi cewar ya rugo izuwa gidan sarauta ana nemansa yanzu yanzu
a majalisa koda jin wannan batu sai yarima zamaru
ya dubi manzon cikin alamun tsananin mamaki
da tsoro yace lafiya ake namana a fada
da sassafen nan haka
Manzon ya risina yace ai sarki ne ya kamu da wani irin ciwo
farat daya ko mikewa zaune ma ya kasa, koda jin
haka sai yarima zamaru ya dimauce ya ruga da gudu izuwa cikin turakar matarsa
sarina
da shigarsa ya iske sarina a kwance tana shirin tashi
kenan
nan take ya labarta mata labarin da manzo yazo dashi
dajin haka sai sarina ta mike zumbur daga kan gado ta daka tsalle ta rungume
zamaru
tana mai kyalkyala dariyar murna tana cewa shi kenan
bukatar mu ta biya
nan dai zamaru yayi sauri ya kintsa sannan ya
bi manzo suka wuce izuwa gidan sarauta
da isar su ya wuce kai tsaye izuwa cikin turakar
sarki inda ya iske sarki hisham a kwance bisa gado fuskarsa ta cika
da wadansu irin kuraje babu kyan gani
ga likitoci da manyan bokayan garin nan
sun taru a tsaitsaye a gefen gadon
a daya bangaren kuwa gaba dayan yan majalisar
sarkine a zazzaune suma sunyi jigun jigun cikin alamun tashin hankali
koda shigowar yarima zamaru sai sarki hisham ya
dubi yan majalisarsa da dukkan likitocin sa da bokayan
nasa har dama duk hadimansa
dake cikin turakar yace kowa ya fita ya barsu yana son
ya gana da dan uwansa zamaru
a wannan lokaci sarkin yaki amzadu na zaune daf da sarki ya rike hannayan
sarki yana ta zubar da hawaye kuma ya kurawa
sarki hisham idanu kodajin umarnin da sarki ya bayar sai
kowa ya fice daga cikin fadar amma shi sarkin yaki amzadu saiya kasa mikewa
ya fita har saida sarki ya dubeshi ya budi baki yace yakai babban masoyina ka
sani cewa a rayuwata ban taba boye maka wani al amarina ba saboda
kauna da yardar dake tsakaninmu amma yau kuma bana son ka san wani babban sirri dake tsakaninmu da dan uwana
zamaru
saboda uwa daya uba daya ya wuce wasa don haka ina son ka fita ka bamu wuri
koda jin wannan batu sai mamaki ya turnuke sarkin
yaki amzadu domin irin haka bata taba faruwa ba
tsakaninsa da sarki
cikin sanyin jiki ya mike tsaye yana waigen sarki yana
zubda hawaye ya fice daga cikin turakar
kuma ya janyo musu kofa ya rufe
ta
faruwar hakan keda wuya sai sarki hisham ya dubi yarima
zamaru ya yafito shi da hannu ya sake budar baki da kyar
yace
matso nan kusa dani ya kai dan uwana rabin jikina
cikin nuna alamun tsananin damuwa har idanun
na zubar da hawaye zamaru ya je ya zauna agefen
gadon sarki daf dashi suka kurawa juna idanu
har izuwa tsawon yan dakiku
sannan sarki ya dubeshi yace
yakai dan uwana kayi sani cewa a daren jiya na kamu da wannan cuta farat daya
kuma likitocina da bokayena sunyi iya bakin kokarinsu akan
su gano abinda ya haddasa wannan cuta da maganinta sun kasa, tabbas jikina
ya bani cewa
mutuwa zanyia cikin yan kwanaki kalilan
ka sani cewa bani da wani makusanci wanda yafika sai kuma matata shamilat da abinda ta haifa
tuni mahaifin shamilat sarki sahibul hilayat na birnin darul hushash ya aiko da manzo
cewar shamilat da jaririnta data haifa sun taho nan birnin bisa
rakiyar dakarunsa kuma zasu iso a daren kwanaki bakwai masu
zuwa
koda sarki hisham yazo nan a zancensa sai hawaye ya zubo masa yaci
gaba da cewa
a duniya bani da wani buri wanda yafi naga dana na cikina
wanda ban same shi ba sai bayan na shafe shekaru
goma sha daya dayin aure amma gashi burina ba zai cika ba
domin ina ji
a jikina cewar kafin shamilat ta iso garinnan ajali ya riskeni
Al amin Ahmed Misau, guyson nake magana
koda jin haka sai yarima zamaru ya rungume
sarki hisham yana mai fashewa da kuka yace yakai
dan uwana kayi sani cewa dukka mai rai baya
fidda tsammani rabo kuma babu wata cuta wadda bata
da magani a doron kasa don haka ni yanzu ina so ka bani dama na
garzaya izuwa makotan kasashenmu na nemo maka magani
koda jin wannnan batu sai sarki hisham ya busheda
dariya cikin
Matukar karfin hali da juriya, al amarin da yayi
matukar baiwa
yarima zamaru mamaki da tsoro kenan yaji a ransa
kamar sarki ya gane cewa yana da masaniya a kan
wannan ciwo da ya same shi, lokaci guda kuma sai yaga sarki hisham ya fashe da matsanancin
kuka na bakin ciki
da kyar zamaru ya rarrasheshi yayi shiriu
sannan ya dube shi yace yakai dan uwana tunda na hau
kan karagar mulki ban taba kamuwa da ciwon da ya kaini
ga kwanciya ba sai jiya fruwar hakan ce ta tabbatar mini da cewar nesa ta
matso kusa ina so ka sani cewa ba wani abu bane ya sa na sallami
kowa daga cikin dakin nan ba sai domin muyi wani sirri
guda daya wannan sirri ba komai bane face ina son na roke ka wata alfarma guda daya
ka sani cewa rayuwa ban taba tauye wani hakki naka ba
a matsayinka na kanina kuma baka taba neman wani abu a wajena ba wanda banyi maka shi ba tun daga kuruciyarmu
kawo izuwa girmanmu a lokacin da mahaifinmu ya ke raye da kuma ya mutu
koba haka bane?
Yarima zamaru ya gyada kai a lokacin da hawaye na gaskiya ya zubo masa
domin take yaji tausayin sarki hisham ya ratsa jikinsa
saboda sanin cewar gaskiyar ya fada sai yace
hakika ka fadi iyakar gaskiya yakai dan uwana
sarki hisham yayi dan guntun murmushi sannan yace
ni kuwa ban taba neman wani abu ba a wajanka kuma ka taba saka mini da kwara zarra ba koda karfin jikinka
bisa duk irin abubuwan alherin da nayi maka a rayyuwa
zamaru ya gyada kai yana mai nuna alamar haka ne
sarki hisham yaja dogon numfashi sannan yace alfarmar da nake nama a wajanka itace
idan har matata ta iso birnin nan a raye ita da jaririnta
kada ka sa a kashesu ko a boyesu a wani wuri bisa
tsoron nan gaba zasu iya rabaka da mulkinka
idan har ba zaka iya zama tare dasu ba kamar yadda na zauna tare dakai tsawon shekaru
DOWNLOAD
DOWNLOAD

4 Comments On KISAN GILLA
avatar
daiy

10 months ago

Reply

Good

avatar
ibrahim-9-5

7 months ago

Reply

Nice thanks a lot

avatar
taskar

7 months ago

Reply

Replying to ibrahim-9-5

Aha thanks for feedback keep following our site and enjoying our new hot hausa novels

avatar
kabir-mariya

7 months ago

Reply

Tnx alot

Please Login or Register in order to submit comment