Join Our WhatsApp Group

GOYON KAKA Complete Hausa Novel Document by GOYON KAKA


GOYON KAKA

Cover Design Copyright and attribute to Marus Graphics

Uploaded by @Taskar

Total Words: 31587



GOYON KAKA

Reading Time: 2 Hours

Added On: 07, Sep 2023

Author: Umma Yahaya ,

Ebook Compiler : Admin

Author Group : Unknown group

Author Phone : Not Inserted

Book License : Free

Category: Love Novels

File Size: 187.61 kb

File Type: txt

Views: 4691+

Download: 1778+

Last download: 18 minutes ago

Description/Story: ο»ΏGOYON KAKA
Na Umma Yahaya
Complet
Ebook creat by Shuraih Usman
Ebook publish by www.hausaebooks.com.ng
Ebook din nan yazo maku ne daga shafin www.hausaebooks.com.ng
Kuna ziyartar shafinmu don samun sababbin littatafai
Ga duk wanda ke bukatar ebooks nashi ya samu shiga cikin wepsite namu sai ya turo mana da littafin ta Email namu hausaebooks@gmail.com

πŸ’πŸ’πŸ’πŸ’πŸ’
πŸ’πŸ’πŸ’
πŸ’
*GOYON* *KAKA*
*1*
Bismillahi wassalatu wasalamu alah rasulullah,alhmdllh ayau ne Allah y bani ikon fara sabon buk dina mai suna *goyon* *kaka* Allah y bani ikon farawa a sa'a ameen.

Yarinya ce da baxata haura shekara takwas ba ta sheko da gudu cikin gdan nasu ko sallama babu,direct bandaki ta nufa abin data debo acikin rigarta ta xubesu a bakin ban dakin mangaro nagani da alama tsinkosu tayi ba wani excuse ta tura kofar bandakin saboda matsanancin fitsatin daya korota,suman tsaye tayi sakamakon wanda ta gani a bandakin saboda tsabar tsoro a wando ta sako fitsarin,a 360 ta juya kotakan mangwaron batabi ba dakin kakarta ta shige gurin buya ta shiga nema can Allah y bata sa'a ta fada karkashin gado a lokacin kakar kuwa tana baccinta batasan mai yake faruwa ba.
Wanda ta bude a bandaki kuwa ransa duk y baci saboda bakin cikin yarinyar ta ganshi ba kaya a dalilin wankan da yake a gaggauce y karasa wankan y futo ransa duk a jagule matashine da baxai wuce 22 years ba ko daki bai shiga ba y wuce dakin kakar,masifa yakeyi tun daga tsakar gda yake kwalawa kakar kira danyasan xata iya boyeta kaka!kaka!!kaka!!!wlh yau saina kusa balla yarinyar nan kowa ma y huta ayi yarinya sai hatsabibanci,dannaga iskancinnaki gaba yakeyi tinda harkin kai ki leka mutum a bandaki yana wanka lokacin y karasa shiga dan duk babatun da yake a tsakar gidane kaka kuwa bata jishi ba saboda tana wata sabuwar duniyar cikin bacci.
Kaka!kaka!!kaka!!! ya kwala mata kira da karfi a firgice ta farka a baccin tana haba mai gdan wannan tashin hankalin kira kamar an kawo farmaki,tsaki yayi mtsss yace ni ina shegiyar jikarnan taki mai siffar aljanu,bata fuska tayi tace wlh Aslam ka kiyayeni,ubanme tayi maka xaka fara xaginta yarinyar ma da bata gidannan,tsaki yadanyi yace yace ai baxaki gane ba,tace eh mai xan gane,yace yarinya bakyason laifinta nidai kawai ki futomin da ita danyau saina babballata,islam cikinta ne yace kuwwwww tana xaxxaro ido tana addu'ar yasa karya ganta,dan tasan laifin datayi masa inya kamata xai iya kasheta,dan wlh yaya Aslam mugu ne,kaka ce ta juya tayi kwanciyarta tana kayi ka gama nidai a gidannan ko mai kama da islam ban ganiba tun rana data futa.
Juyawa yayi yace wlh nafasa yin satin yau xan koma dan aljanar jikarnan taki xata iya sakamin hawan jini,kaka tace kafi ruwa gudu umma tagaida aysha kuma karka kara kiran islam da aljana in baxata kirata da sunanta ba ka bashshi ba dole bane,islam sai data tabbatar da yaya aslam y futa sannan ta fara kokarin futowa.

πŸ’˜πŸ’˜πŸ’˜
*daga* *sisin* *mama* πŸ’˜πŸ’˜πŸ’˜
[11/12, 8:52 PM] β€ͺ+234 703 443 5155‬: (1/10/2016 11:00am)na umma yahya musa

πŸ’πŸ’πŸ’πŸ’πŸ’πŸ’
πŸ’πŸ’πŸ’πŸ’
πŸ’πŸ’
πŸ’
*GOYON* *KAKA*
*2*
Kokarin futowa takeyi daga maboyar tata kakace tajiyo mutsu-mutsu a karkashin gado tace au Ashe shegen berannan bai mutu ba aikuwa yau xan saka maka maga..bata karasa magana ba taga islam ta fito tana xaxxaro ido ,kaka ta kama baki tace lah ga ja'irar kaya yaushe kika shigo,xumbura baki islam tayi tace daxu nashigo.
Kaka tace to menene y hadaki da wancan mai bakar xuciyar yadda y xuciya daya kamaki dako makota baxasu iya kwatarki ba,karamin bakinta ta cuno gaba tace to ai daga gonar malam tanimu muke shine fa fitsari y matsoni tofa bansan fa yana bandakin yana wanka ba shine nashiga duk cikin dangarta take maganar,kaka ce ta tuntsire da dariya tace kaji yar nema daman nasan laifi kikayi masa,islam itama dariyar take tace Allah bada gangan nayi ba,kaka tace toh naji,islam tace yanxu ina yaya aslam din saboda futa xanyi xamu tafi rafi yau ana kamun kifi,kaka ta karkatar da baki tace kinsan bakar xuciyarsa yace gda xai tafi,islam tace gwandama dama duk y takuramin y koramin abokanaina y hanasu shigowa gidannan sannan y hanani futa wasan dare,tashi tayi tace kaka saina dawo,kaka tace to amma baxaki hutaba naga yanxu kika dawo,tace au bari nadauko mangwaro na ki boyemin dan sai da mukayi dambe da hanne na kwato mangwaron nataho nasan intaxo tagan shi xata dauka,ta futa ta dauko ta kawowa kaka ta dauki daya tana wlh kuma kaka karki shamin kinjiko,kaka tace xancen banxa mai xanyi da kayan tsami xoki dauki abinki,dariya islam tayi tace Allah y baki hakuri kakata ta kaina ta fuce,a kofar shigowa dakin kaka sukayi kicibis da yaya aslam rangwashi y sakar mata a tsakiyar ka,wani gigitacciyar kara ta saki sanadiyyar wani masifaffen xafi da taji y ratsata,a kuje ta fuce waje taci gaba da ihu,da gudu kaka ta taho har tana tuntube xani na faduwa tana daukaπŸ˜‚ da aslam suka hadu xai shigo dakin hade girar sama da kasa kaka tayi tace me kayi mata,murmushi yayi yace haba ta wajena me kuwa xanyi mata tsorata dai tayi data ganni shine fa ta fice da gudu taxata xan daketa,dariya kaka tayi tace yauwa aina xata dukanta kayi narama mata,xaro ido yayi yace yanxu saiki dakeni tace ras ma kuwa,sallama sukaji anayi kaka ta xari mayafi aslam y mara mata baya malam tanimu suka gani y kawo karar islam da kawayenta da abokananta irin barnar da sukayi masa acikin gona,kaka tace karka yiwa jikata sharri yaushe taje gonarka,kana da wannan shegen saka idon da bakar rowa ta yaya har xasu dauki mangwaronka ka bassu,yace ai katanga suka haura,kaka tace ni islam bataxo da mangwaro ba Aslam ne y dinga bawa malam tanimu hakuri dan yace mai gari xaije y fadawa,tsaki kaka tayi tace kaje birni ka fadawa sarki ba mai gariba,dakyar Aslam y shawo kan malam tanimu dan sai da y bashi 2k y hakura dan tanimu akwau san abin duniya lol,bayan sun shigo gida dan karamin tsaki Aslam yayi yace wlh ke kika dada bata yarinyar nan in ba haka ba yaushe har tasan ta haura katangar mutum ta sato masa mangwaro dududu nawa take,kaka tace karyane fa sharri yakeyi mata,Aslam y nuna mangwaro akan gadon ta yace wancan fa,kaka tahau borin kunya tace to ayi mutum sai bakar rowar jaraba y shuka mangwaro mai warin gawasa kanshi y ishi yara y hanasu mai xai hanasu tsinkowa,Aslam yace wlh da inada iko da mayar da ita gurin aunty amarya xanyi tunda ba tarbiyya kikeyi mata ba,harararsa kaka tayi tace to ko ubanka nina raineshi kuma nabashi tarbiyya,xaro ido yayi y kama baki yace Allah y baki hakuri,kaka tace naji,yace ai yayana wlh baxan kaisu riko ba balle kuma *GOYON* *KAKA* xaki tayi tace wanema xai rikema yaya,yace eh naji kinsa ina bata lokaci sallama naxo miyi xan tafi,kaka tace haba Aslam au da gaske kake baxaka cika satin ba,yace gwanda natafi tunkan kikai ga duka tunda kin fara xagi tace nayi dukan ma indai kan islam ne sainayi maka,y futa yana kinjiko tace ga daddawa nasiya musu ka tafi da ita yace baxan dauki kayan wari ba yaja trolly bag dinsa yai gaba.

πŸ’˜πŸ’˜πŸ’˜
*daga* *sisin* *mama*
πŸ’˜πŸ’˜πŸ’˜
[11/12, 8:52 PM] β€ͺ+234 703 443 5155‬: (2/10/2016 2:00pm)na umma yahya musa

πŸ’πŸ’πŸ’πŸ’πŸ’πŸ’
πŸ’πŸ’πŸ’πŸ’
πŸ’πŸ’
πŸ’
*3*
*ASALINSU*
Malam umar shine mahaifin Abdul da Aliyu asalinsu yan jihar kano ne a karamar hukumar gwarxo,Ahmad da aliyu sun taso cikin hadin kai da gurmamawa,inda Aliyu yake bawa Abdul girma sosai da sosai,mahaifiyar su Aysha tana kokari wajen ganin tabasu tarbiya.
Mahaifinsu malam umar dan kasuwa ne yana kasuwancinsa tsakanin cikin garin kano in yaxo yayi kasuwancinsa y koma gda gwarxo haka suke xaune cikin rufin asiri,y bawa yayansa Abdul da Aliyu tarbiyya da ilimin xamani dana boko sannan ranakun hutu yana daukarsu suje kasuwa saboda suga yadda yake gudanar da kasuwancinsa,haka suke rayuwarsu har Abdul y kammala secondary skull dinshi y shiga university a lokacin Aliyu yana s.s 1.
Lokacin Abdul yana 300 level Aliyu y gama secondary shima y shiga university shekarar da Abdul xai hada degree dinsa a shekarar ciwon ajali y kama mahaifinsu y rasu sunji mutuwar malam umar saboda da wayansu ba'a tabayi musu mutuwa ba kakanninsu tun suna kanana suka rasu da taimakon Allah Abdul y samu y karasa makarantarsa yaci gaba da kula da kasuwancin mahaifinsu.
Xaune suke babarsu da suke kira da umma tace yanxu kai yaronnan dayake dan fari ne bata fadar sunansa(Abdul)girma y kamaka y kamata ka nemo mata kayi aure murmushi yayi yace insha Allah.
Kwanci tashi asarar mai rai Allah y hada Abdul da wata yarinya khadija bai sha wata wahala ba ta amince akayi bikinsu,khadija yarinya ce mai ladabi da biyayya suna xaune lfy inda yake xaune a cikin kano a unguwar ja'in dayake haya y kama gda mai daki 3 sai kitchen da bandaki,a waje ma akwai shago da bandaki ya nemi kaninsa y dawo sai da aka kai ruwa rana sannan umma a'i ta yadda y kama gaya dan da cewa tayi sai dai y dawo gida y gyara y xauna sai daya nuna mata kasuwancin da yakeyi yana da muhimmanci gwanda yana kusa dashi sannan ta hakura,Aliyu y dawo gidansa yake xaune a shago safe rana da dare khadija ce take basa abinci ko daidai da rana daya bata taba gajiyawa ba,saboda Aliyu yanayi mata biyayya kuma khadija tana da kirki.
Duk week end suke xuwa suna gaida umma a'i tanajin dadi sosai saboda yadda kan yaranta yake a hade,kuma suna kulawa da ita.
Dayake kasuwancin yanxu sai da ilimi yake tafiya kuma Abdul da Aliyu suna da ilimi shine dalilin karfafuwar kasuwancinsu,dan yanxu Abdul harya fara futa kasashen ketare domin kasuwanci yana shigo da kayayyaki kuma alhmdllh komai yana tafiya daidai saboda suna fitar da hakkin Allah.
Aliyu yana shekarar karshe a makaranta yayansa Abdul y siya musu wani tamfatsetsen fili a unguwar rijiyar xaki,tuni yasaka aka fara gini part ne 2 manya sai kuma akayi kananu guda 2 a lokacin kuma khadija tanata fama da laulayi,cikin 5 months aka gama gidan saboda akwai wadatattun kudi.

πŸ’˜πŸ’˜πŸ’˜
*data* *sisin* *mama*
πŸ’˜πŸ’˜πŸ’˜
[11/12, 8:52 PM] β€ͺ+234 703 443 5155‬: (2/10/2016 3:00pm)na umma yahya musa

πŸ’πŸ’πŸ’πŸ’πŸ’πŸ’
πŸ’πŸ’πŸ’πŸ’
πŸ’πŸ’
πŸ’
*4*
A lokacin y kira Aliyu dan yayi masa rakiya unguwar rijiyar xaki yaga sun nufa wani tamfatsetsen gida yaga y nufa dashi a machine din yaya Abdul sukaje a aljihunsa yaga y futo da key y bude gidan mamakine y kama Aliyu kasa boye mamakinsa yayi yace yaya gidan wane,murmushi Abdul yayi yace mushiga tukun shiga sukayi kowanne part an kawata shi da kayan xamani masu bala'in kyau cikin fara'a Aliyu yace yaya naga gida kuma yayi amma ina son karin bayani inji gidan wane,dariyar shima Abdul yayi yace gidanmu ne cikin mamaki Aliyu yake kallan Abdul yace eh namune rimarmu nake tarawa da tayi yawa shine nayi tunanin mai y kamata nayi shine naga y dace kawai na gina mana gda tunda kaima kaga ka isa ajiye iyali,kaga y nuna masa manyan yace wannan daya naka daya nawa,waccan na umma waccan dayan kuwa na yaranmu maxa da xamu haifa in Allah y kawo, farin cikine y lullube Aliyu y rungume yayansa Abdul harda kukansa yace ngd ngd ngd yaya Allah yabar xumunci Abdul yace ameen sai da suka koma sannan Abdul yake fadawa khadija itama taji dadi tayi fatan alkhairi kallan Aliyu tayi tace kanina saura mata ko kuma inaji ni xan samo maka dannaga kamar kanin nawa tsoron mata yake,dariya Abdul yayi yace haba aunty na waya fada miki amma dai nabaki xabi tunda haka kikace,dariya tayi tace xancena gaskiya ne kenan yace eh naji,Abdul shima dariyar yayi.
Da suka je gaida umma a wannan satin Abdul yake fada mata itama tayi farin ciki,Abdul yace umma yanxu haka ma nayo mana order motoci basu karaso bane,tace lallai kaxama magajin malam Allah y kara hade kawunan ku y albarkanci dukiyarku sukace ameen.
Abdul yace yanxu umma yaushe xaki koma can gidan murmushi tayi tace da ace malam yaso xamana a birni daya kaini tun yana da rai da y kaini birni,amma tunda bai kaini ba yanxu ba avinda xai kaini birni xama ina muku dai fatan alkhairi Allah yasa ashiga a sa'a,sukace ameen duk yadda sukaso su shawo kanta ta yadda ta koma firr taki haka suka hakura.
Aliyu yace yanxu yaushe xamu tare murmushi Abdul yayi yace ba yanxu ba ka bari sai nan...


Read / Download GOYON KAKA

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .

START READING

OR

Login Register

Please Login or Register in order to submit comment

Releted Novels

Releted Album