Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

🌀🌀🌀🌀```BOƊƊI ``` the beautiful 🌀🌀🌀🌀


Story and writing
(Z. B. M.)
09066017177


marubuciyar:

ZAINAB abu'ƙaya
BANI BA AUREN SOJA
NIMA DANAWA LAIFI
AUTAN MOMY
And now
BOƊƊI






```IN THE NAME OF ALLAH THE BENEFICIENT THE MOST MERCIFUL,```
```ALL PRISE BELONG TO YOU ALLAH LORD OF THE WORLD``` 🥰





``` ~NASA DAUKAR DA WANNAN BOOK ZUWAGA MAHAIFIYA can't luv you lees mom 🥰 heart ♥ 🍀 much luv for you 🌷 😍 ammah~





I don talk any more🤫🤥



🆓And 🆕



Page
0️⃣1️⃣......... Adamawa jihar yola ƙauyene dake cikin garin mayobelwa mai suna. Genle Sanyi da albarka ta sauka a wannan safiya mai sanyaya zuciya dake cike da kunci kara haskaka annuri mai murmushi kowane ruhi, a wannan safiya ne mutanen garin Genle suka shaida aure tsakanin ameenatu da kuma angonta Abubakar, A°mmun yasama wannan aure albarka, cikin gida kowa sai farin ciki yake yi masu bakin ciki ko na gefe,



Furera aguje ta shige gida tana rusa kuka kamar wacce aka mata mutuwa cikin tashin hankali innah tace lafiya Furera cikin kuka tace innah kamar bakijin meke faruwa a gari ba, tace to Naji amma ya muka iya da ƙaddarar Allah dolene ameenatu matar Abubakar ce, cigaba da kuka Furera tayi innah sai rarrashi take yi amma abu yaci tura can naga ta mata radi a kunne tace Allah innata dariya suka yi suka tafa, hmmmm nidai banji mesukaceba nace Intayi tsami zamuji...


Dare duk aka gama wata al'ada aka kai amarya izuwa gidanta su goggo sunyi kokarin wajen mata nasiha duk Ameenatu batada hayaniya kowa sai son barka, fatan mu Allah yakawo xuriya dayyiba,


********************************************


Wata yarinya fara mai zubin Larabawa dake sakkowa daga sama fara'a sosai a face ɗinta tana *ummu* na shirya umatanen dake zaune afalo naga duk sun Mike matar da'aka kira da *ummu* tace kai bintu, Aida mun tafi kema rigima gareki wani dake gefen *ummu* yace aike kike biye ta dama tun dazu ashe zaman giranki muke, baki ta tura alamun shagwaɓa, kowa dariya yayi sukayi hanyar fita, alama dai dukan su yaran *ummu* ne don suna matukar kama,


Airport na gihar Kano suka nufa *ummu* sai duba time take 10 minutes ya rage girji yaka raso aikuwa sunje cikin sa'a suna isa jirji yasauka,


Shine fitowar farko daga girjin wani fari zubin Larabawa shima sak yan uwansa wato *maleek Ibrahim* wanda ake kira da *Sayyid*....................



More comments more typing

Share pls 🙏



Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/ISJTXVOAvK5AlxunOo3OHZ

```BOƊƊI the beautiful.``` 🥰

group one 1⃣

wannan group na masu comments ne inkinsan ba zakiyi comments ba zakijiki awaje 🙅🏻‍♀️


Share pls
🌀🌀🌀🌀```BOƊƊI the beautiful ``` 🌀🌀 🌀

Story and writing
(Z. B. M.)



*WOMEN WRITERS ASSOCIATION*📚
_(Domin Marubuta Mata)_
✨(W.W.A)✨
https://www.facebook.com/106752595253176/posts/107924965135939/



marubuciyar:

ZAINAB abu'ƙaya
BANI BA AUREN SOJA
NIMA DANAWA LAIFI
AUTAR MOMY
And now
BOƊƊI the beautiful




```IN THE NAME OF ALLAH THE BENEFICIENT THE MOST MERCIFUL,```
```ALL PRISE BELONG TO YOU ALLAH LORD OF THE WORLD``` 🥰





``` ~NASA DAUKAR DA WANNAN BOOK ZUWAGA MAHAIFIYA can't luv you lees mom 🥰 heart ♥ 🍀 much luv for you 🌷 😍 ammah~



Happy birthday mommy ii°di milaadi sa'iid 🎂🤝💃🏼💃🏼💃🏼💃🏼💃🏼Allah yara miki lfy da nisan kwana uwata Aishatu.









0️⃣2️⃣.........bintu ce tafara hango Sayyid aguje ta isa gareshi tana "marhaban ya Sayyid tasharraftu bi ma'arifatika" murmushi Sayyid yayi wanda yake bayyana tsagwaran kyawunsa, yace da bintu kaifa anti ta mayar mishi da lastun bikhairi, lokacin sun ƙaraso ummu tace bintu Allah ya shiryeki, welcome my son hugging ɗin juna suka fara yi cikin farin ciki da ganin juna gida suka wuce domin Sayyid ya huta gajiya...




******************rayuwa ta cigaba da tafiya dadi babu dadi ameenatu na zaune tareda mijinta sun kula da juna furera kuwa na nan kan bakarta narashi son ameenatu,




Tushen labari.........



Mlm sunusu shine mahaifin Abubakar yanada mata biyu ta farko wato uwar gida kulu, itace mmn Abubakar sun daɗe kafin Allah ya basu haihuwa a lokacin ne Mlm sunusi ya karo aure ya auri innah mmn furera lokacin ma a riga an haifi furera taxo da ita gidan saboda baban furera Allah ya mishi rasuwa.

haka kulu ta zauna da innah cikin kunci domin bata jin dadin zama da ita sai abunda innah tace ake yi agidan, lokacin da Abubakar ya isa aure sai furera tace duniya shi take so kulu batason wannan hadin auren saboda haka tastaya itama sosai domin kare danta Mlm sunusi labari ya iskeshi yakira Abubakar ya tambaye shi yace idan yanada wacce yakeso to yakawo shi kuma lokacin sun fara soyayya da ameenatu ƴar A°mmun dajin labari Mlm sunusi yayi farin ciki inda yasamu kanin sa tasi'u suka je suka samu A°mmun da maganan kowa yayi farin ciki domin haɗa zuriya da mutanen kirki, ba ɓata lokaci aka tsaida magana,


Labari ya iske furera da innah tashin hankali matuka suka tsinci kansu sunyi iya shige da ficensu amma suna gani aka yi aure,


Bayan wata biyu dayin aure ameenatu tasamu juna biyu Abubakar yayi murna kulu ma tayi farin ciki sosai haka ta cigaba da renon ciki har lokacin haihuwa,



Daren Alhamis ameenatu ta kwana tana naku da duk yanda takaiga dauriya abun yaci karfin ta Abubakar yafara fita hayyaci sa yaje ya kwakwa sawa innah Ladi wacce dama mafi yawa ita ke karban haihuwa agarin, Sanyin asuba yafara ratsowa gari yacika da ni'ma Ameenatu tana cikin wani hali inna Ladi sai fama take dukan su sun hada zuwa har shi Abubakar dake kai komo awaje innah Ladi tace kuyi nishi ameenatu kai yafara fitowa ai kuwa data yunkura ɗaya biyu kawai saiga sun buleliya fara tas yarinya tafaɗo tana callara ihu masha Allah. Alhamdulillah abunda Abubakar ke faɗi lokacin da yaji kukan jaritiyarsa, zai shigo suka yi kicibus da inna Ladi tace Abubakar jira mana barina shirya su.


Cikin farin ciki yayi alwala ya nufi masallaci koda gari ya waye kowa yasamu labarin haihuwa Abubakar yafara tozali ya kyakkyawar ɗiyarsa bakin sa ba abunda yafara kira sai *BOƊƊI am* ya kalli ameenatu cikin harshen fula tanci yace nagode dawannan kauta da kika ban kunya baisa ameenatu ta dagoba, mutane kowa yaxo sai son barka bakin ciki kuwa kunsan masu ji bazai wuce furera da uwar ta innah ba.
Domin ko kowa yaxo amma bandasu.


Ran suna yarinya taci sunanta *hauwa kulu BOƊƊI*


Wato sunan mmn Abubakar kulu, amma ana ce da yarinyar BOƊƊI, haka ameenatu ta cigaba da renon yarinyar ta cikin so da kauna Abubakar yafara tafiya galingo domin kasuwanci idan yatafi yakan daɗe kafin yadawo duk abunda ke faruwa furera bawai ta hakura bane tanan tana neman hanyar da zata samu dama kuma har lokacin taki auren kowa tace ita sai abubae, duk lokacin da tayi tozali da BOƊƊI sai ta jefeta da mummunan kalma domin ana kawo ta wajen ta kwarar ta, BOƊƊI kamar yar Larabawa kyau kam ba'a magana ga kwantattacen gashi akanta farace tass Zara zaran gashin ido, dogon hanci kai sai son barka amma BOƊƊI the beautiful ce.



Lokacin da su Sayyid suka isa gida wanka yayi ya fito domin kowa gira shi yake bintu ce ta kamo hannun sa tana masa shirmen data saba, ummu ce ta hau mata fada cikin larabci, bayan sunci abinci ne sai Sayyid yace ummu inaso nadan shiga gari zamu hadu da wanine ummu tace Haba ya Sayyid yaushe kadawo bazaka bari ka hutaba, ai ummu abunne ba hutu kinsan aikin namu sai a hankali farouq ne yayi sallama..........




Share pls 🙏
🌀🌀🌀BOƊƊI the beautiful 🌀🌀

Story & writing
(Z. B. M)
09066017177


*WOMEN WRITERS ASSOCIATION*📚
_(Domin Marubuta Mata)_
✨(W.W.A)✨
https://www.facebook.com/106752595253176/posts/107924965135939/


I don't talk any more 🤫 🤥



Page0️⃣3️⃣

................ Farouq ne yayi sallama suka amsa ummu tace yau Kaine muke gani wato Sayyid yaxo yana sosa keya ya gaishe ta Sayyid yace yauwa bari mu fita ummu tace to sai mun dawo
Bintu Naji ta taso tana zata bisu ummu tayi mata tsawa Takoma Farouq yayi dariya yace gaskiya Sayyid Bintu na burgeni allah yasa idan ta girma zaku bani ita, Sayyid yace yanxu saika zauna ka jira Bintu she's just a 5yrs yace zan jira mana Kaga yanxu muna 25 ai zaiyi, hmmmm kazaji dashi.



Tun fitan su Sayyid sai karfe 9pm suka dawo ummu ce tasameshi yace *abbu* yadawo yana jiranka a falo ba jimawa da fitan ta ya tashi ya nufi wajen *abbu* da sallama yashiga cike da farin cikin ganin juna suka gaisa abbu yaji daɗin ganin son din nashi *maleek* domin yafara girma sunyi taɗi sosai har ummu taxo tasa mesu abbu ne yace to yanxu inaso nan da 2 weeks zaka wuce can wajensu *jaddun* inaso kayi masters ɗinka acan batare da hayyaba yace to abbu Allah ya tabbatar da alkharinsa, bayan fitan Sayyid ummu taxo ta zauna kusa da abbu yace Meyasa ba kaso *maleek* yazauna tare damu yayi karatu yanxu kam ina bukatar shi yafara girma aka mata Ace yazauna shima mushaku abbu yace cikin yare larabci ya ummi shin yanxu maleek ba gida zai komaba kinsan Nigeria ban yarda zaman Sayyid ananba su *jaddun* suna bukatar sa suma domin zai debe musu kewa,




. *******************************Asalin ummu safeeyah yar Saudi ne inda shi kuma abbu ibraheem dan Nigeria ne jihar Kano shima abu kara tune yakai shi can inda ya haɗuda ummu har suka fara soyayya yasanarwa iyayen sa bayan ya shawo kansu da kyar suka yarda kan cewa zasu dawo nan Nijeriya su zauna, aɓangaren ummu itama iyayen ta da kyar suka amince dake rabo dangin ajali haka suka hakura tareda sanya albarka, a daura aure asaudi ango da Marya suka ran kayo Nigeria, bayan shekara biyu Allah ya axurtasu da yaro namiji wanda shine maleek Sayyid , sai kuma sun ƙara samun Aleeyu haidar daga nan basu kuma samun haihuwaba sai nan kusa suka haifi faɗeematu Bintu, Sayyid yayi karatu har zuwa secondry Nigeria daganan yakoma UK yayi degree to yanxu yadawo zai tafi Saudi domin yin masters, shi kuma Aleeyu anan Nigeria aka barshi domin yayi sabo da gidan kakaninsa. Sai Bintu yar nursery!




*************************wata rana wacce ameenatu bazata taɓa mance shiba lokacin BOƊƊI tanada shekara daya da rabi aduniya Abubakar yatafi jalingo wajen kasuwan ci sauri take domin anyi aihuwa a ana gidan su ta shirya BOƊƊI tayi kyau abun ta itama ta shiga wanka tabarta tana wasa ba tareda takawo komai a ranta ba, jim kadan ta fito sai bata ga kowaba kuma da tana ɗan jin mostinta, cikin sauri ta saka hijab ɗinta ta fito waje amma ko alamun BOƊƊI bata ganiba yara tasamu suna wasa awaje tace ko kunga BOƊƊI suka ce bawanda suka gani tashin hankali ba'a sa masa rana.


Sauri take kamar zata kife tabi jeji ita kanta bata san inda take biba............




Share pls
🌀🌀🌀🌀```BOƊƊI the beautiful ``` 🌀🌀 🌀

Story and writing
(Z. B. M.)



*WOMEN WRITERS ASSOCIATION*📚
_(Domin Marubuta Mata)_
✨(W.W.A)✨
https://www.facebook.com/106752595253176/posts/107924965135939/




marubuciyar:

ZAINAB abu'ƙaya
BANI BA AUREN SOJA
NIMA DANAWA LAIFI
AUTAR MOMY
And now
BOƊƊI the beautiful




```IN THE NAME OF ALLAH THE BENEFICIENT THE MOST MERCIFUL,```
```ALL PRISE BELONG TO YOU ALLAH LORD OF THE WORLD``` 🥰





``` ~NASA DAUKAR DA WANNAN BOOK ZUWAGA MAHAIFIYA can't luv you lees mom 🥰 heart ♥ 🍀 much luv for you 🌷 😍 ammah~





I don talk any more🤫🤥



🆓And 🆕




0️⃣4️⃣.........tayi nisan na ban mamaki domin tuni tafice cikin gari bakin wani dan duste da ruwa ke fitowa ta wajen ta ajiye BOƊƊI ta dauki kara taba ta domin yin wasa, ba tausayi juya ta kama hanya izuwa gida dafarin ciki fall domin tasan dole inda ta ajiye BOƊƊI tasal wanta, furera kenan.



Abun fa ya faskara domin a yanxu labari ya isa ga jama'a BOƊƊI ta ɓata, jama'a sai alhini ake kowa da abunda yake faɗi ameenatu tafice daga hayyacinta domin taruɗe matuka, Mariya ce zata gona taci karo da furera cikin son gulma tace ke furera daga ina? Kallon banza Tamata wani irin rashin mutunci ne wannan furera nifa shiyasa banason Higa harkarku kidubeni kinkai kimin raini ne yar yarinya dake, Mariya tace Allah yabaki hakuri furera dama zan faɗa mikine BOƊƊI yar gidan ameenatu ta bace yanxu haka cikin gari sai neman ta ake, furera takara haɗe ranta, toni meya shafeni nan lambun buba nashiga tun safe na ɗebo gajiya kin tareni da shirme ta buge Mariya tayi wucewarta kasan zuciyarta kuwa dariya ne. Mariya tace Allah ya kyauta amma furera har yanzu ba hankali nagama abokiyar dabin tace ameenatu, na dauka ko idan na faɗa mata zan samu wani abun, harda min faɗa batason raini to ninace kar tayi aure har mu isota, haka dai ta cigaba da faɗanta itama.




Yau kuma ina zaku haka Farooq naganka da sassafe, nasan dai wannan sammako bahaka kawai ba, cewar *ummu* data fito daga
kitchen, Farooq yace eh *ummu* wlh akoi wani abu important da zamujeyi, Allah yasa dai Sayyid ya tashi *ummu* tace to sai ka rasa ciki kagani, sama ya haura inda room ɗin Sayyid yake yasa meshi yana tace kansa mai launin na Larabawa domin Sayyid ba inda yabaro ummu mahaifiyarsa, saidai stayinsa na *abbu* ne, yace yauwa yanxu dama zan kiraka kada muma kara, fitowa suka yi atare *ummu* mene ne haka Allah yasa dai ba tafiya zakuyi ba baku yi break ba, Sayyid yace wlh zamuakarane ummu akoi nisa inda zamuje, bintu ce ta fito da alamu lokacin ta tashi barci, tana ganin farouq tace ya Farouq ina zakuje ne yace my bb have you wake up, kai taɗaga masa, yace "kaifa anti, bintu tace" ana bi khairi, farouq yace that's my bb, ya farouq "ila Aina anta zahibun" ummu ce ta karbi zancen ta hanyar cewa bintu taje tayi brush sai taxo ba wani waje su Sayyid zasuba, bintu tayar da tana murna, Sayyid yace ummu "ma'assalama" tace to hazzan sa'iidah, sahibat kas salamah" da murmushi a face ɗinta har wajen mota tara kasu tana koro addu'a da larabci, abun gonin burgewa inji jidderh dama Ace sheikh ɗintane 😂lol


Tafiya suke yi ba wasa domin farouq ya rikewa motar fire kusan karfe uku suka iso jejin cike yakeda abubuwan burgewa saida suka samu wajen wani bishiya mai sanyi suka yi sallah sai Farouq yafara gudanar da aikin sa suna tafiya yana ta observing dajin abun sha'awa Sayyid na biye dashi suna dan hira


************************************* baffa am, miɗo nana ɗonka, miyiɗi diyam cewar wata bahillatana daganinsu irin borinnan masu yawo da shanu domin kuwa ga shanun masu yawa suna kiwatawa, su biyune itada baffanta, wajen da taga ruwa na gudu takara sa jin sanyin waje yasa tace kai baffa wlh nagaji, yace kin fiye lala ci cikin yaren fulanci daidai ruwan takara sa tozali tayi da wannan kyakkyawar halitta wato BOƊƊI!! Itama abunda ta furta kenan dukda bata santaba amma ji tayi wannan sunan shiya dace da ita abunka da fulani sun saba ganin abubuwa a daji., ba wani tsoro takara sa tana murmushi ta kai hannu tadauketa tanamai kwalawa baffa kira yace lfy irin wannan kiran tace baffa Kaga nasamu *ɓingel boɗɗi* baffa saida ya duba gabar ya duba yamma baiga alamun waniba yace to yanxu ya zamuyi kenan, madara *dijah* ta dama ta sto tace baffa barina bata nasan tabajin yunwa, bayan yagama bata madaran, baffa yace kodai zamu shiga kauyukan gefe nan muduba ko zamu samu wanda yasanta, aiko *dijah* tatire furr bata ga mai rabata da BOƊƊI ba domin ita tasamu yarinya,. Haka ko suka tafi da ita gashi tafiyar tasu da nisa gabar zasu yi,.


Sayyid sun gama abunda yakawo su dajin suka kara kama hanya domin basaso Ace dare ya musu, cikin gudun farouq da baya duba gaban sa kawai ji suka yi karar buge abu burki ya taka dukan su sunyi bala'in tsorata.............







Share pls 🙏
🌀🌀🌀🌀```BOƊƊI the beautiful ``` 🌀🌀 🌀

Story and writing
(Z. B. M.)


marubuciyar:

ZAINAB abu'ƙaya
BANI BA AUREN SOJA
NIMA DANAWA LAIFI
AUTAR MOMY
And now
BOƊƊI the beautiful



Follow me on what'sapp 09066017177
Whatpad
Zainab7177
Gmail zbala0512@gmail.com





🆓And 🆕


I dedicated this page to you my sister's I miss you alot Allah yakare ku aduk inda kuke. 💃🏼🥰😍🥰💕 💞 ❣️



0️⃣5️⃣.........A gigice suka fito *Dijah* tamike ta falala da gudu domin tsoron daya kamata duk da ciwon da taji a ƙafarta baisa ta tsayaba Baffan tama kafin su Sayyid su juyo gareshi yakaɗa yan shanunsa sunyi cikin daji,


Farouq ne yafara bin bayan sa yana masa magana amma inaa tafiyar tasu tayi nisa.,

Dawowa Farouq yayi har zasu shiga Mota suka ji kukan jariri ya agefen titi wajen da kukan ke fitowa suka suka ƙarasa BOƊƊI ce kwance domin lokacin da Dijah ta fadi BOƊƊI dake hannun ta gefe tayi,

Cikin sauri Sayyid ya ɗauketa wani mai mota ne ya tsaya daidai su yace lfy kuwa kodai kuna bukatar tai mako ne, Farouq ne ya faɗa mishi abunda ya faru kuma yace gashi sun tafi sun bar yarinya, mutumin yace gaskiya yaka mata ahan zarta muje asibiti saboda kar wani abu yasa meta. Ni sunana Brister Sani,


Tare Da Brister suka ƙarasa asibiti dake nan wani Kauye kusa, dukda ƙauyene amma an kula da BOƊƊI sosai don likitocin daga cikin gari suke zuwa, bayan andubata an tabbatar ba komai lokacin har *magrib* ya kusa Brister yace to yanxu kuɗin inaso Naji daga ina kuke, Farouq ne yayi magana yafaɗa masa daga inda suke kuma da abunda ya kawo su,

Yace to gaskiya yanxu kuxo muje gidana banisa sosai kuma kan hanyar kuce inyaso gobe saiku wuce da farko sun ki kan zasuje hotel su kwana amma ganin Brister ya dage suka amince,.

Batun BOƊƊI kuwa Brister yace zai ɗauka kafin ayi cigiyar iyayen ta gashi ba'a san wani gari fulanin nan suke zamaba hasalima basu da wajen zama ɗaya, dagani masu tafiyane.



Sunje gidan Barrister an musu kyakkyawan tarba, koda gari ya waye sun shirya tsab domin tafiya, matar Barrister ne ta fito ɗaukeda BOƊƊI ahannunta an mata wanka ansauya mata kaya "tayi matukar kyau" lokacin Sayyid da Farouq su kayi tozali da BOƊƊI kallon juna sukayi, Farouq baiyi kasa aguiwaba yace, "amma wannan yarinyar muka xo da ita kuwa?


Barrister ne yayi dariya yace itace dai kunga ta BOƊƊI da yawa ko! Sayyid yace BOƊƊI me hakan yake nufi, Barrister ya bashi amsa da kyakkyawa, sunan kyakkyawan yaringa mai mai tawa cikin zuciyarshi, Domin a yanxu yaji yana matukar son yarinyar domin akoita da kyau gata fara wannan ya kenan idan ta girma.


Tun lokacin da aka ambaci kyakkyawa matar Barrister ta ɗaure fuska.............




Tofa.....akoi CA kwakiya kubiyoni domin yanxune aka fara wasan 🏇🏻🏇🏻🏇🏻🏇🏻



Comments naku shine karfin guiwana, nagode da kaunarku gareni, 😍


Share pls 🙏
🌀🌀🌀🌀```BOƊƊI the beautiful ``` 🌀🌀 🌀

Story and writing
By
(Z. B. M.)


marubuciyar:

ZAINAB abu'ƙaya
BANI BA AUREN SOJA
NIMA DANAWA LAIFI
AUTAR MOMY
And now
BOƊƊI the beautiful



Wannan page na sadaukar ƙyauta gareku masoya littafin BOƊƊI the beautiful, Allah yabarmu tare.




🆓And 🆕




0️⃣6️⃣.........Matar Barrister ta ɗaure fuska lokacin da taga su Sayyid na kokarin tafiya ta tada bori., Ba kunya tace BOƊƊI baza ta zauna agidan taba. Barrister yayi magana amma tace sam ita ba tasan zancenba.,

Sayyid ne yaraba faɗan yace mungode Allah ya saka, Barrister amma ka kawota mune mukayi sanadin, Saboda haka zamu tafi da ita, kai kuma idan kaji wani lbr gameda yarinyar muna sauraro.


Farouq ma abun ya masa daɗi domin shima yanaso Ace su tafi da BOƊƊI, Babu yanda Barrister ya iya haka ya basu BOƊƊI suka yi sallama tareda musayar Number suka ɗauki hanyar TADABO TUNBIN GIWA. 🐘


***********************************Ɓangaren Ameenatu kuwa abubuwa sun caɓe, duniya tayi masu zafi, ƴa daya tilo garesu amma an wayi gari ta bace babu lbr, kuka take mai tsuma zuciya kulu ce dake zaune agefenta itama sharar kwalla take, amma tayi karfin hali tace "waɗu muyal usani" Abubakar ne yashigo shima kallo ɗaya zaka mishi Kaga damuwa ƙakara afuskarsa, haduwa suka yi suna ta jimami, kowa yaxo amma ita Furera da mahaifiyarta babu abunda yadame su sai harkar su suke yi, suna ganin burinsu ya
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment