Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE



You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

mal bala me gadine ya le'ko cikin girmamawa yafara magana "Alhj lafiya kuwa naganka haka kamar hankalinka a tashe?
"Mal bala yarinyarnan ni zata rainama hankali ni zata maida mutumin banza cikin garinnan, da darajata da 'kimata ace wai har kamar 'yanzu 'karfe goma da minti ashirin da takwas yarana suna gantali a gari.
Mal bala yace "amma Alh ai naga kamar sundawo ko? "Gudace tadawo yanzu jiran dawowar d'ayar nake.
"To Alhj Allah maidota lafiya, Allah sa duk inda take tana lafiya.
Komawa mal bala yayi daga ciki ya zauna kan d'an bencinshi, yanda hankalin Alhj yatashi shima duk sai yajishi cikin damuwa, saboda Alhj mutum ne harda rabin mutum.

Da misalin 'karfe sha d'aya saura minti goma, lokacin Alhj yagaji da zarya tsakanin wajen get d'in gidan zuwa cikin gida, yana zaune kan bencin mal bala, tsayuwar mota yaji dai-dai get d'in gidansa da sauri Alhj ya mi'ke le'kawa yayi lokacin Har Hussaina tafito daga motar me motar yayi gaba abinsa,

Momy kuwa da Hassana suna cikin gida hankalinsu a tashe, Hassana banda kuka ba abinda takeyi.

Hussaina kuwa bayan Hafiz ya ajiyeta ya wuce sai lokacin wani mugun tsoro ya dirar mata cikin zuciya, jikinta yafara 'kyarma, hankalinta be 'kara tashiba saida taduba agogo taga 'karfe sha d'aya na dare, ahankali tafara buga get d'in gidan, da sauri mal bala yazo ya bud'e mata tana Shiga,tafara tafiya da sauri tana wai-waye saida tazo gab dashiga falon gidan ta tsaya tacire takalminta dan kada ajiyo 'karar tafiyarta, ri'ke takalmin tayi a hannu sannan tatura 'kyauren falon ahankali.






Love u all my Fan's πŸ’ƒπŸ» shoki 🏊🏻
[1/2, 7:21 AM] Zee Elkaseem: πŸ‘­ *AUREN TAGWAYE* πŸ‘­
πŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•Έ
πŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•Έ
πŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•Έ
πŸ•ΈπŸ•Έ
πŸ•Έ
*Written & Story by*
*Zee Elkaseem*
*{Mmn khady}*


*Dedicated to All member's group of* *Ciwon ya mace* πŸ‘©πŸ»


Page-------------------------6



*Bayan sati d'aya*
Hassana da Hussaina sun daina fita konan da can kullum sai dai idan zasu islamiyya, maganar fitar da miji kuwa kullum sai daddynsu ya tinasar dasu,

Yauma kamar kullum zaune suke kan had'addun kujerun dake zagaye da babban falon gidan, Hassana ta kalli Hussaina, "nikam sister inaso muyi wata magana dake,
"Ina jinki Hussaina tafad'a,
"Wai meyasa kikacema Abba kun 6ata da jebeer Alhalin ba abinda yashiga tsakaninku,
Murmushi Hussaina tayi sannan ta d'au 'kafa d'aya ta d'ora kan d'aya tana girgizawa "ba wani dalili kawai tsuntsun 'kaunarsane ya canja she'ka.

Tana fad'in haka ta maida hankalinta kan wayarta wacce suke chat itada Hafiz suna tattauna yanda za'ayi su had'u dan tun ranar da daddy yahanasu fita tasanar dashi, shikuma kullum sai yakirata yakai sau goma yanamata magiya akan dan Allah tayi dabarar dazasu had'u koda na minti biyar ne.

Sauke ajiyar Zuciya Hussaina tayi, tace "amma Hussaina idan kikayima jabeer haka kinci amana, kinriga kinsan irin so da 'kaunar dayake nunamaki, zeyi wuya kisamu namijin daze soki kamar jabeer.

"Ba wani wuya, Hussaina tafad'a saboda nadad'e dasamun wanda ya mayemin gurbinsa, cike da mamaki Hussaina ta kalleta wannan wanene wanda yayi 'karfin halin raba Zukatan dasuka dad'e suna maradin zama abu guda,

"Murmushi Hussaina tayi tare da mi'kewa tsaye tayi taku biyu zuwa ukku sannan tajuyo ta kalli Hassana wacce kebinta da ido tana jiran jin amsarta "Ba wani bane kinsanshi, Hafiz Wanda muka had'u dashi gurin *dinner* itama Hassana mi'kewa tayi ta isa inda Hussaina take cike da mamaki "indai Wannan Hafiz d'in kike nufi wlh inabaki shawara da kada kiyi sakin na hannu kamun na guje danni wannan Hafiz d'in da kike gani kwata-kwata be kwantamin araiba da ganinshi yafi kama da yan abi yarima asha kid'a,

Hannunta takai kan kafad'ar Hussaina ta dafata "sister iname baki shawara kada kibari jabeer ya su6uce maki dan samun namiji kamarsa a wannan zamanin sai antona......

"Ke dakata, hussaina tafad'a cikin d'aga murya, kada ki kawomin 'kabli da ba'adi nace banison jabeer idan ke kinasonshi ki aureshi mana wani yahanaki, "Hmm aini tun farko bani yace yansoba, amma in bancin haka banga abin 'ki gareshiba.

"Mtsswww, Hussaina taja wani dogon tsaki sannan tanufi bedroom tabar Hassana nan tsaye cike da mamakin hali irin na 'yar'uwarta.

Hussaina kuwa tana shiga d'aki kiran Hafiz yashigo wayarta, cike da farinciki ta d'auka bayan ta sumbaci wayar dan a kullum 'karajin son Hafiz takeyi cikin zuciyarta.

"hellow babyna,
"uhm my dear ya kake tafad'a cikin shagwa6a.
"Eh to gaskiya ba lafiya...
"subhannallah meyasameka tafad'a tare da gyara zamanta.
"kin'ki muhad'u dan baki d'auki son danikemaki a bakin komeba.
Wata nannauyar ajiyar zuciya ta sauke "Haba my dear dan saboda wannan zakace bakada lafiya, indai wannan ne ka kwantar da hankalinka yau idan nafito islamiyya zamu had'u.
"Wow babyna amma naji dad'i, 'karfe nawa kuke fitowa?
'Karfe hud'une mukoma shidda, kaga wannan lokacin ya ishemu mud'an gaisa.
"Eh to hakane amma kinsanfa nayi missing d'inki sosai.
"Hmm sai munhad'un kawai tafad'a
"Owk bye "muaaah yasakar mata wani kiss ta wayar sannan ya tsinke kiran, wani dad'i taji ya ziyarci zuciyarta rungume wayar tayi cike da Farin ciki, harta 'kosa Hud'u na yamma tayi sufita zuwa islamiyya.






Love u all my Fan's πŸ’ƒπŸ» shoki πŸŠπŸ»πŸ˜‚
[1/2, 7:21 AM] Zee Elkaseem: πŸ‘­ *AUREN TAGWAYE* πŸ‘­
πŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•Έ
πŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•Έ
πŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•Έ
πŸ•ΈπŸ•Έ
πŸ•Έ
*Written & Story by*
*Zee Elkaseem*
*{Mmn khady}*


*Dedicated to All member's group of* *Ciwon ya mace* πŸ‘©πŸ»


Page-------------------------7


Da misalin 'karfe hud'u saura minti goma Hussaina tagama shirinta tsaf na islamiyyah cikin uniform kalar ruwan 'kasa,

"Kallon yar'uwarta tayi wacce ke 'ko'karin d'aura farin d'an kwali, tace Hassana kiyi sauri kinga bana bu'katar zuwa a makare, kallo kawai Hassana tabita dashi "Tofah yau kuma kece me cewa bakison makara ince kullum saina gama shiryawa sannan inyi zaman jiranki,
"Naji dan Allah yanzu dai kitaho mutafi kina 'kara tsyar damu, ......
Dai-dai lokacin kuma wayarta tayi ringing dubawa tayi jiki na kyarma takai dubanta ga Hassana wacce tagama shirinta tsaf tana jiran sutafi.

Sunan Hafiz tagani yana yawo kan wayar, dama kuma kobata dubaba tasan shine dan tsakanin 'karfe ukku da Rabi zuwa yanzu 'karfe hud'u yayimata kira yakai tara,
"Hellow yanzu zamu fito daga gidan, tafad'a tana kallon Hassana ta wutsiyar ido,
"To babyna dan Allah kiyi sauri wlh na matsu na ganki dan bakisan yanda nakejibane shiyasa kikai har yanzu baki fitoba.
"Sorry dear ina hanyafa nace ka saurareni mana.
"To shikenan ina gurinda nagayamaki,
To sainazo tafad'a tare da kashe wayar.

Tana juyowa suka had'a ido da Hassana saida gabanta yayi 'yar 'karamar fad'uwa saboda kallon tuhumar dataga tana mata.

Nunawa tayi kamar batasan kome kenanba tace "muje ko kada mu makara naga yau baki bu'katar muyi latti,
"Owk muje to.

Haka suka jero gwanin ban sha'awa kome nasu iri d'aya ga tsananin kamanni dasuke farinsu d'aya tsawonsu d'aya haka zubin jikinsu d'aya, suna matu'kar kamanni wanda hakan kesawa mutane da dama basa gane Hassana basa gane Hussaina, hatta da iyayensu basu cika ganesuba saita gurin halinsu daya bam-bamta.

A falo suka tarar da Momy, cikin ladabi suka isa gabanta "Momy mutafi islamiyyah
"To Allah bada sa'a Yakuma tsareku, Allah yayimaku Albarka, Adawo lafiya.

Amsawa sukayi da Ameen sannan suka fice, suna fita sukasamu me napep suka gayamashi sunan islamiyyar daze kaisu,

Sun fara tafiya Hussaina ta Kalli Hassana tace "sister dan Allah kiyimin taimako d'aya sonike inje gidansu zuby kuma kinsan gida baza'abarni infitaba inaso me napep ya saukeni acan sai awuce dake islamiyya idan antaso kimin waya sai muhad'u mutafi gida.

Da Hassana kamar bazata Aminceba saikuma tace "to shikenan Amma dan Allah kada ki wuce lokacin tashinmu islamiyya, kinsan dai daddy ba sauki.
"InshaAllah kinamin waya zanzo, "to shikenan.

Hassana aka fara saukewa islamiyya sannan aka wuce da Hussaina unguwar Barhim dake wajen Gari, dai-dai inda Hafiz yagayamata yananan nan kuwa tasameshi.

Tana fitowa daga napep ta hangoshi tsaye jikin motarshi ya hard'e duka hannayenshi a 'kirji, sanye yake cikin bakin wando, da yellow riga, sai ba'ka'ken takalmi, sannan ya d'ora wani ba'kin glass Wanda ya'kara fitowa da ainafin kyawunsa.

Yana hangota yafara jefarta da 'kawataccen murmushinsa, itama maida mashi martani tayi harta isa gurinshi suna musayar murmushi.

"Welcome babyna yafad'a tare da rungumata a jikinshi, saurin tureshi tayi tana waige kada ace mutane suna kallonsu. *{Hmm Hussaina kenan idan mutane basu ganinku ai Allah yana ganinku}*

"kada kidamu babyna ba mutane sosai a unguwar, kodama wani yaganmu ba wanda ze shiga harkarmu, amma tunda naga kamar kina tsoro shigo daga ciki, "dadai yafi, tafad'a
Sannan yabud'emata motar tashiga shima yashiga.







Love u all my Fan's πŸ’ƒπŸ» shoki 🏊🏻
[1/2, 7:21 AM] Zee Elkaseem: πŸ‘­ *AUREN TAGWAYE* πŸ‘­
πŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•Έ
πŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•Έ
πŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•Έ
πŸ•ΈπŸ•Έ
πŸ•Έ
*Written & Story by*
*Zee Elkaseem*
*{Mmn khady}*


*Dedicated to All member's group of* *Ciwon ya mace* πŸ‘©πŸ»


Page-------------------------9


Bayan shigowar jabeer suka gaisa da Momy sannan tashige d'akinta tabasu guri, Hassana ce tacika gabanshi da kayan ciye-ciye dana sha, sannan tad'an zauna domin su gaisa, lokacin Hussqina tana zaune tabi ta had'e girar sama data 'kasa sai danne-danne take a wayarta,

Shiru ya gifta nayan wasu mintoci, Hassanace ta katse shirun ta hanyar cewa "Yaya jabeer ina wuni,
"lafiya lao ya Amsa yana 'karemata kallo, a zuciyarshi yana cewa wannnan itace hassanar kokuwa Hussainar ce, saida yaji tami'ke tsaye tana cewa "to nikam nashiga daga ciki sannan yagane ashe ga mutunniyar tashi nan gabanshi wacce tunda yashigo ko kallo be ishetaba, taunar cingam kawai take sannan hankalinta duka yana kan wayarta tana ibadar wato chat da Hafiz.

Shiru sukayi suduka anrasa wanda zefara magana dan Hussainama yau ko arzi'kin gaisuwa Jabeer be samuba, illah wani irin haushinsama datakeji dan tadad'e dagayamshi maganar soyayyarsu ya janye ya nemi wata Amma dayake shine d'an anace sarkin naci ya'ki ha'kura.

Jabeer ne ya katse shirun ta hanyar cewa "jiya naga fitarku lokacin zaku islamiyya naso inyimaku magana amma sainaga rashin dacewar hakan kasancewar gurin dazaku yanada muhimmaci bekamata ace na tsaidakuba.
"Hmm aikode, kawai tafad'a tare da yamutsa fuska ta juyar da kanta gefe tana taunar cingam 'kas-'kas
Har cikin ranshi yaji haushin yanda tayi Mashi magana amma sai ya danne kasancewar anason namiji yazama me shariya akan wasu 'kananan abubuwa, magana ya'kara karo na biyu.

"Gaskiya inajin dad'in yanda kuke zuwa islamiyyah fatana akodayaushe kafin Aurenmu ace kunyi safka kunyi hadda koda hizif talatin ga sauran litattafan addini, kinga ko'ina zanyi Alfahari da matata tanada ilimin addini, sannan kuma uwa uba yaranmu zasu koya a gun mamarsu kafin suma asakasu tasu islamiyyar.....

Dakatar dashi tayi ta hanyar d'aga mashi hannu tana magana cikin masifa "dakata malam, wai akan wa kake magana? "Ni, tanuna kanta da hannunta, to indai nice kama daina wannan tunanin kacire soyayyata daga cikin zuciyarka, danni yanzu batakai nakeyi 'karama kanemi me sonka tunda wuri kafin lokaci ya'kurema.

Haba Hussaina donmi kike nema ki gujeni? Menayimaki? Kadafa ki manta mundad'e muna soyayya kullum burinmu be wuce muzama mata da mijiba, amma yanzu Cikin 'kan-'kanin lokaci kina nema ki canja ra'ayi.

"Oh nema manake incanja, tobari kaji in gayama ba nema nakeyiba nama canja gaba d'aya yanzu baka cikin tsarin mazan danike burin aure...
Tuni kuma wani ya maye gurbinka acikin zucyata saboda haka kaje kawai kanemi wata,

Cike da mamaki da takaicin yanda Hussaina ke gayamar magana yabar gidan, dan kosamun damar yin bankwana da Momy beyiba,

Dai-dai harabar gidan suka had'e da Zuby tana shigowa "tana ganin jabeer ta washe baki "a'a'a Manya kenan anzo gun mutuniyar, dariyar ya'ke kawai ya 'ka'karo Wanda hakan baze hana kagane cikin tsananin damuwar dayakeba,
"Eh wlh kuma gashi harna fitoba, to shikenan agaida gida.

Tana tsaye yashige motarsa yatayar da ita Malam bala me gadi yabud'emashi get yanatayimar fadanci dan yasaba duk ranar dayazo yakan bashi nacin goro amma yau sai yaga Alamar ranshi kamar a 6ace yake, haka yabar gidan Malam bala yamaida get yarufe sannan yakoma kan bencinsa yazauna yana cewa "ho yar nema yau ta6atama mutumin rai 'yan aninnan danike samuma yau bansamesuba, sannan yajawo redio ya kunna yana saurare.

Zuby kuwa taso taji wani abu daga bakin jabeer amma ganin ranshi a 6ace kuma bebata fuskar hakanba yasa tayi ciki tana zumud'in ji daga bakin 'kawarta.










Love u all my Fan's πŸ’ƒπŸ»shoki 🏊🏻
[1/2, 7:21 AM] Zee Elkaseem: πŸ‘­ *AUREN TAGWAYE* πŸ‘­
πŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•Έ
πŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•Έ
πŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•Έ
πŸ•ΈπŸ•Έ
πŸ•Έ
*Written & Story by*
*Zee Elkaseem*
*{Mmn khady}*


*Dedicated to All member's group of* *Ciwon ya mace* πŸ‘©πŸ»


Page-------------------------8


Rungumota yayi jikinsa tare da d'ora lips d'insa kan kumatunta yasakar mata kiss,
"Kinsan wani abu babyna? Yafada cikin had'addiyar murayarshi me kashe mata jiki.
"A'a saika fad'a my dear.
"Gaskiya naji dad'i nayi matu'kar farinciki yanda kika amince kikazo inda nake yanzu na'kara yarda da 'kaunar da kikemun hundred percent, wani irin dad'i taji har cikin ranta sannan tafara magana cikin kasalalliyar murya,
"My dear inaso ka yarda dani kamar yanda na yarda dakai,
"Na yarda dake babyna yafad'a tare da saka hannunshi d'aya cikin hijab d'inta yafara wasa da dukiyar fulaninta, hannunsa d'aya kuma nakan cikinta yanamata wani salo wanda ke 'kara rikitata,

Suduka sun lula duniyar soyayyar shan minti, bakajin komai sai numfashi dasuke maidawa sama-sama, haka sukayita wasanni tsakaninsu tare dajin dad'in kasancewa da juna.


Hassana kuwa tana islamiyyah suna karatu, bayan malamin dake d'aukarsu darasin Qur'an yafita sai me d'aukarsu hadith yashigo, saboda haka tana ganin haka tasan lokacin tashinsu yakusa dan dama hadith shine period d'in 'karshe kuma baya dad'ewa lokacinsa ke 'karewa saboda haka kafin yafara karatu ta d'auko wayarta sunan Hussaina ta lalubo sannan ta dannan kira.

Lokacin Hussaina na jikin Hafiz yariga yagama tayar mata da hankali kwata- kwata bata cikin hayyacinta har wayar takaraci ringing d'inta tagama bata d'agaba, sai a kira na ukku sannan tad'aga
"Hellow sister antashine, "eh kitaho muhad'e yanda zamu koma gida tare.
"Owk ganinan zuwa.

Bayan ta tsinke kiran ta maida dubanta ga Hafiz "yauwa my dear dama inason magana dakai,
"Ina jinki babyna.
"Bawata magana bace dama daddynmune yace yabamu wata d'aya mu fitar da miji, nikuma ba wanda nakeso sai kai shine nace yakamata ka gabatar da kanka gareshi.

Shiru yayi kamar me tunanin wani abu, itakuma ta zubamar ido tana jiran amsar daze bata, ganin beda niyyar yin magana yasata ta6oshi "dear lfy naga kayi shiru kobakaji me nake fad'a bane.

"Murmushi yayi "najiki babyna, kada kidamu aini dama irin wannan ranar nake jira, zanzo inshaAllah kada kiji kome aini me 'kaunarkine.
"Wani irin murmushi tasakar mashi cikin farin ciki sannan taduba wayarta 'karfe shidda saura minti goma a gaggauce sukayi bankwana yabata iyayen kud'i ta'ki amsa saboda tana tsoron gida aganta dasu.
Me napep ta tsaida tashiga zuwa gidansu.

Yana ganin tafiyarta ya kece da wata irin dariya tare dakaima sitiyarin motarshi duka "wow Allah kai damo ga harawa kobeciba yayi birgima, kowa yagayamata zan iya auren macen danagama lugui-guitawa a waje, aini sai kamilar mace wacce tasan darajar kanta ba irinkiba wacce zatabi namiji har inda yake.
A haka yatashi motarsa ya 'kara gaba ranshi fari tass.

Hussaina kuwa napep na ajiye Hassan itama ana ajiyeta, saboda haka tare suka shiga gida babu wata matsala.

*washe Gari*
Da misalin 'karfe hud'u da rabi na yamma Zaune suke falo suna kallon gidan tv startime tashar farin wata suna shirin addini da Alqibla, kasancewar yau Alhamis ba islamiyyah suduka hada Momy duk sun maida hankalinsu kan shirin amma banda Hussaina wacce hankalinta yana kan waya tana chat da Hafiz Wanda yawanci magan-ganun duk na shan mintine sukeyima junansu.

Tsayuwar mota sukaji a harabar gidan, da sauri Hassana ta le'ka ta window kafin tadawo ta zauna ta dubi Hussaina, tace "jabeer nefa yazo, cigaba da chat d'inta Hussaina tayi bata ko kalli Hassanaba barantana tabata amsar maganar datayimata.

Ganin batada niyyar motsawa yasa Momy cewa "ba magana ake makiba kobakijine jabeer ne yazo,
Turo baki tayi ni wlh momy wannan jabeer d'in yadameni nifa nagayamashi yanzu bani sonshi ko ana dole ne......
Bugemata baki momy tayi "banison sakarcin banza idan kince kin daina son jabeer wa kike dashi wanda yafishi, yaro mutumin kirki me hankali ga nutsuwa, saboda hakama mahaifinku yad'aukeshi tamkar d'an cikinsa.

Tashi tayi tana dira 'kafa cikin shagwa6a ni Momy nafad'amaki inada Wanda nakeso kuma ai yace zezo ya gabatar da kanshi gurin daddy.
"Keni rufemin baki sakaran banza.

Momy ta kalla Hassana "jeki shigo dashi,
"To tafad'a sannan tanufi 'kofa tana kallon Hussaina
Wacce tadage ita a dole batason jabeer hadda yan guntayen hawayenta.






Love u all my Fan's πŸ’ƒπŸ»shoki 🏊🏻
[1/2, 7:21 AM] Zee Elkaseem: πŸ‘­ *AUREN TAGWAYE* πŸ‘­
πŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•Έ
πŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•Έ
πŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•Έ
πŸ•ΈπŸ•Έ
πŸ•Έ
*Written & Story by*
*Zee Elkaseem*
*{Mmn khady}*


*Dedicated to All member's group of* *Ciwon ya mace* πŸ‘©πŸ»


Page-------------------------10



Da sallama Zuby tashiga falon gidan Har yanzu Hussaina na zaune inda take sai cika takeyi tana batsewa, kallonta Zuby tayi "kawata lafiya naganki haka ko wani abune yafaru.

Kedai bari 'kawata wancen mutumin mana yazo ya dagulamin lissafi,
"Wane mutumi kuma Zuby ta tambaya tare da nuna rashin gane inda abin yadosa.

Haba wane mutumifa banda jabeer, nafa dad'e da gayamashi na daina yayinshi yaha'kura Amma yanacemun,
"haba 'kawata miye aibun jabeer da zaki 'kishi jabeer kau ai namijine na nunama tsara, ga kyau ga wayewa.

"Amma kuma kwata-kwata be iya soyayyayba, Hussaina tafad'a ni kalar soyayyarshi bataminba, kinsan nasha gayamaki nafison namiji d'an life wanda yasan takan love.

"To amma tuni baki gane hakaba kike tare dashi sai yanzu.
"Kwaraiko saboda yanzu nasamu wanda ya iyane shiyasa nagane shi be iya komeba.

'Kara matsowa Zuby tayi tare da d'ora hannunta kan cinyar Hussaina "Amma 'kawata wanene wannan wanda yayi sa'ar saye zuciyarki cikin 'kan'kanin lokaci.

Wani 'kawataccen murmushi Hussaina tayi "Hafiz" wani mummunan fad'uwar gaba Zuby tayi dukda ta dad'e da sanin akwai soyayya tsakanin Hussainar da Hafiz,

"Wane Hafiz ? Ta tambaya danta 'kara tabbatarma kanta abinda Hafiz d'in yagayamata gaskiyane, Hafiz mana Wanda Muka had'u ranar *dinner* wani busashshen murmushi Zuby ta 'ka'karo "kai amma dole kike susucewa 'kawata ai Hafiz gwanine kan soyayya ga kud'i ga kyau ga kuma harkar wayewa.

"Shiyasa ai nakamu da sonshi cikin 'kan'kanin lokaci saboda iya soyayyarshi amma kin had'a da wancen bagidajen shi kullum yazo beda magana sai wa'azi da sauka da Hadda kamar shine yasakani islamiyyar, kwashewa sukayi da dariya tare da tafawa, "wlh kuwa 'kawata yo ko dady dayasakamu islamiyyar beyimana bin diddigi irin nashi.

Sai gab da magrib sannan zuby tabar gidan, Zuciyarta tana tunanin Hanyar dazatabi ta 'kuntatama Hussaina tunda harta yarda tayi soyayya da Hafiz mutumin datafiso tafi 'kauna akan kome da kowa,


*Bayan kwana hud'u*

Zaune Suke a mota itada Hafiz suna soyayyarsu kamar yanda suka saba.
yauma sunfito islamiyyah tayima Hassana 'karyar cewa Zata gano mamar Zuby da aka kwantar da ita asibiti, shinefa tataho inda suka saba had'uwa.

Rungume take jikinsa da kyar tasamu ta kwace daga jikinsa sannan tamaida dubanta gareshi,
"Nikam Hafiz narasa gane kanka koda yaushe idan nace kanasona kace kanasona amma har yanzu ka gagara zuwa gidanmu ka gabatar da kanka ga mahaifina kullum ina sanar dakai lokacin da aka ebar mana yakusa 'karewa ko jiya saida daddy ya'kara mana tuni saura kwana goma idan bamu fito da mijiba ze za6a mana da kanshi, nikuma kasan bazan iya rayuwa da wani namijiba idan bakaiba.

"Kada ki damu babyna nima ina sonki kuma bazan iya had'a soyayyarki data kowace maceba, maganar gabatar da kaina ga iyayenki kuma akwai dalilin dayasa kikaga har yanzu banjeba.

"Haba my dear wannan wane daliline haka?

Kinsan dad d'ina yana 'kasar Cairo hajiyatace ke mana kome to jiya nayimata maganarki shine take cewa inkawoki Ku gaisa kafin manya sushiga maganar, tonikuma ina tsoron gayamaki dan naga had'uwarmuma dayaya mukeyi barantana kuma ace zakije gidanmu.

"Haba my dear indan wannan ne kada kadamu zanzo "haba yaushe to?
"Yaushe kakeso inzo
"Zaki iya fitowa gobe,
"Badamuwa kajirani anan, amma sai antashi islamiyyah zantaho, "to badamuwa.

Da haka sukayi sallama tahau napep tanufi islamiyyarsu suna isa ana taso dalibai saboda haka Hassana suka d'auka sannan suka wuce.







Love u all my Fan's πŸ’ƒπŸ» Shoki 🏊🏻

πŸ˜ƒ *Kada kudamu da shokina reader's sanyine kawai ke aiki* πŸ˜‚
*08166169254* for comment
[1/2, 7:21 AM] Zee Elkaseem: πŸ‘­ *AUREN TAGWAYE* πŸ‘­
πŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•Έ
πŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•Έ
πŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•Έ
πŸ•ΈπŸ•Έ
πŸ•Έ
*Written & Story by*
*Zee Elkaseem*
*{Mmn khady}*


*Dedicated to All member's group of* *Ciwon ya mace* πŸ‘©πŸ»


Page-------------------------12


'Daukarta yayi d'af daga kan kujera yanufi bedroom da ita, shimfid'ar da ita yayi kan gado ranshi fari tas wasanni yafara mata yana shafa jikinta ko'ina yakai kimanin minti talatin yana mata haka, lokacin yagama rikicewa yakai 'kololuwa gurin sha'awa, juyar da ita yayi sannan ya zuge zip d'in rigarta kasancewar zip d'in irin me 6allewane yasa besha wahala gurin cire ainafin rigar dake jikintaba, sannan ya kwance mad'aurin zaninta yarage daga ita sai breaziya sai kuma undi 'ko'karin ciremata undi yashigayi, saida yarabata da kome na jikinta bayyanar surar jikinta ya'kara rikirkitashi, yashiga aikamata da sakonni yana wasanni da ita.

Lokacin shima yacire duk wani kaya dake jikinshi shorniker kawai yaragemar, yana 'ko'karin cire shortniker dinne dan yamatsu yacimma burinshi na sanin Hussaina a matsayin mace, lkoacin kuma wayarshi tashiga ringing.
Hannu yasa ya d'auka ganin sunan 'kanwarsa na yawo kan screen d'in wayar yasa yayi saurin d'agawa tare da karawa a kunnensa "Hellow Fatima ya'akayi? Ya tambayeta cikin tsananin jin haushin kiran datayimashi lokacin dayake burin cimma manufarshi.
Cikin muryar kuka Fatima take magana "Yaya kayi sauri kazo gida yanzu jikin hajiyane yatashi ahalin yanzu batasan inda kanta yakeba.

Subhanallah yafad'a tare da saurin mi'kewa ya rarumi kayanshi ya maida bekobi takan Hussainaba wacce taketa sharar bacci

Please Login or Register in order to submit comment