Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE



You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

yau ze d'aura aurenmu da Hussaina.

"Alhamdulillahi mama tafad'a tare da d'aga hannuwanta sama tana godema Allah, kai Amma naji dad'i wannan abu ai abun farincikine dama kullum Addu'ata be wuce inga aurenkaba, Allah sanya Alkhairi yabaku zaman lafiya.

"To amma mama kina ganin babu wata matsala, "wace matsala haba jabeer me kanema karasa inaji kadade da kammala gidanka, kuma Hallacin da Alhj mansir kamfani yayimana ai kobakada kome yace ka auri d'iyarsa ka aureta kazubama sarautar Allah ido dan nasan baze barka hakaba,
"To mama Allah dai yasa haka shine mafi alkahiri,
"Ameen haka nikeso naji kana fad'i.
Daga nan yafita zuwa d'akinshi ya canja kaya sannan yakoma yayima mamarsa sallama tare da sanar da ita zeje ya d'auko mutum ukku dangin babanshi sannan mutum ukku a dangingin ita mamar tashi, fatan Alkhairi tayimashi sannan yafita.

⏱. *Misalin 'karfe 3:00pm*


Aka taru a masaalacin dake 'kofar gidan Alhj mansir mutane 'kalilan suka sheda d'aurin auren Jabeer Suleiman tankuri da Amaryarsa Hussaina Mansir kamfani, bisa sadaki dubu hamsin.

Bayan ankammala Alhj mansir yasa aka gabatarma duk mutanen dasuka halarci d'aurin auren abun lasawa take away akayima akaiyma kowane suka wuce suna sanya Albarka.

Bayan ankammala wannan daddy yashiga gida da sallama, su duka falo ya taraddasu zaune Momy ce ta amsa sallamar, Hassana tace "daddy sanu da dawowa "yauwa ya amsa,
Hussaina kuwa daddy nashigowa jikinta yafara kyarma dan wani masifaffen tsoronshi takeyi, cikin muryar tsoro tace "d...dad...daddy sannu da zuwa.
Wani matsiaycin kallo ya watsamata sannan yawuce d'akinsa batare daya amsa sannu d'inda tayimashiba.

Can bayan kimanin minti baiyar yafito ya kalli Hussaina "ki shirya yanzu inaso zan fita dake kuma minti talatin nabaki, kinajina "inaji daddy tafad'a tare da mi'kewa tanufi d'akinsu jiki na kyarma.

Daddy kuwa fita yayi harabar gidan, waya yakira jabeer "ya masu aikinnan sun kammala kuwa,? Ya tambaya
cikin ladabi jabeer yake magana "Eh Alh sunyi kusan minti sha biyar ma da gamawa.
"Sun had'a kome dai yanda yakamata ko?
"Eh sun had'a kome 2 bedroom ne da falo 2 sai kitchen ba abinda ba'a zubaba na bu'kata.

"Owk to anjima ka shiryar tarbar Amaryarka,
Kasa magana jabeer yayi saboda kunyar Alhj yakeji sosai.

"Basu dad'e da kammala wayaba wata had'addiyar mota tayi parking 'kofar gidan sannan wasu maza suka ri'ka jido akwatina suna shigowa dasu saida suka shiga da guda goma manya- manya, sannan sukayima jabeer bayani Alhj mansir yace akawo kayan amaryane.
Mamakine yahana jabeer magana danshi harga Allah yayi niyyar had'a wannan kayan Amma Alhj yahashi had'a kome.







Love u all my Fan's πŸ’ƒπŸ» shoki πŸŠπŸ»β€β™€
[1/5, 8:31 AM] Zee Elkaseem: πŸ‘­ *AUREN TAGWAYE* πŸ‘­
πŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•Έ
πŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•Έ
πŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•Έ
πŸ•ΈπŸ•Έ
πŸ•Έ
*Written & Story by*
*Zee Elkaseem*
*{Mmn khady}*



*Dedicated to All member's group of Ciwon "ya mace* πŸ‘©πŸ»



Page......................17



Da misalin 'karfe biyar na yamma Hussaina tafito cikin shiri sanye take da riga da zani d'inkin simple atamfar brown colour haka takalmin 'kafarta yayi kala da kayan jikinta sai 'katuwar hijab data sanya, ahankali take takowa hartazo gaban dadynsu cikin ladabi tace "na shirya daddy
"Owk muje ko, yafad'a yana nunamata 'Kofa.
Ganin tana tafiya Ahankali kamar kazar da Kwai yafashemawa a ciki yasa daddy yayi gaba ya zauna a mota yana jiran fitowarta.

Fanin fitarsa yaba Hussaina damar yin magana "Momy wai ina zamu?
Momy tace "kin tambayi kaza hanyar rafi.....
Ni kaina da kike gani bansan meke wakanaba nidai kawai abinda nasani naga tunda Alhj yatashi yau yaketa hidima ko zama yaci abinci beyiba.

Hassana dake zaune tace Allah dai yasa Alkhairi ne, ni kaina ina mamakin yanda daddy yace Hussaina ta shirya su fita batare daniba, Alhalin nasan ko'ina tare muke zuwa.

Momy tace "to wannan abu dai Allah kad'ai yasani, kiyi sauri kibishi kada kuma yaga kin 6atamai lokaci.
Juyawa tayi tafita daga falon batare data 'karayin wata maganaba.

A mota ta iske daddy zaune yana jiran fitowarta, gidan gaba tanufa da niyyar tashiga harta kama murfin motar zata bud'e daddy ya watsamata wani matsiyacin kallo "koma baya.
Jiki na 'kyarma takoma ta bud'e bayan motar tashige, sannan daddy yatayar da motar Malam bala yabud'emasu get yana d'aga masu hannu suka d'au hanya sannan yamaida get d'in yarufe Yakoma kan d'an bencinsa ya zauna yana cewa "gaskiya Alhj ya iya maganin d'an iska, wato yarinyar nan wlh da Alhj beyi saurin Aurar da itaba saita d'aukomar abin kunya. Kodayake bansaniba shin itace koba itabace oho nikam bani ganesu, radio shi yajawo ya kunna yacigaba da sauraron abinshi.

Daddy kuwa ba inda ya zarce da Hussaina sai unguwar dutsin safe malali Quarter's inda nan tangamemen gidan jabeer yake, bakin get yayi horn da sauri megadi ya bud'e mashi ciki yashiga ya ajiye motarshi inda aka tanada dan ajiye motocin, fitowa yayi sannan ya umarci Hussaina data fito itama, ba musu tafito tunda suka shigo take yaba kyan gidan, saikuma yanzu ta'kara ganinshi sosai tsarin gidan ya burgeta, a zuciyarta tace "nan kuma ko gidan waye? Amma ko gidan abokanin daddy ne bamu ta6a zuwaba, kuma sabodame daddy yaza6i yazo dani ni kad'ai banda Hassana Alhalin duk inda zamu tare muke tafiya da ita......

Daddyne ya tsinkemata tunanin datake ta hanyar cewa "shigo mana.
Ba musu tabi bayanshi wata 'Kofa yabud'e wacce tasadasu da babban falon gidan me d'auke da maka-makan kujeru irinna zamani a tsakiyar falon gefe kuma kan wani step kujerun dining ne da 'katon table d'insu, daga gaba kuma inda suke facing wata 'katuwar TV ce plasma ma'kale jikin bangon sai manyan speaker's (Home theaters) gefensu kuma wasu kyawawan flower's ne masu d'aukar ido, duka kayan falon sun kasance purple colour hatta da pentin d'akin kalarsa kenan,

Daddy yace "to Hussaina wannan gidan da kike gani bana kowa bane face gidan mijinki......
Dammmm gabanta yayi wani mummunan fad'uwa da sauri tad'ago ta kalli daddy ganin ba wasa tattare dashi yasa tamaida kanta 'kasa gabanta nacigaba da fad'uwa.

Daddy yacigaba da magana "naza6i na aurar dake dakijawomin abin kunya, saboda nan shine gidan aurenki, ki zauna kibi mijinki kiyi mashi biyayya Aljannarki tana 'kar-kashin tafin 'kafarsa idan kinbishi kisamu idan kuma kin baud'e wannan kuma Allah yasan hukuncin daya tanadar maki.
Saboda haka iname umartarki daki zama me biyayya a gareni ni mahaifinki dakuma mijinki ki zauna lafiya.

Nan daddy yayimata nasiha me ratsa jiki kafin yayimata bankwana ya ajiyemata bandir d'in kud'i yan dubu yace "saboda idan kina bu'katar wani abu bance ki matsama mijinkiba,
Bayan tafiyar daddy kasa tashi tayi daga inda yabarta, tunani take "wannan wane irin aurene daddy yayimin kamar auren wasa, to wai yaushema aka d'aura auren? Kuma waye mijin? Ina daddy yasamu mijin daya yarda da aure cikin kwana d'aya tak? Haka tagama jerama kanta tambayoyi amma batada amsarsu kuma batada Wanda ze amsa mata, hakan yasa tafashe da wani irin kuka, tana cewa "shikenan yanzu nasan daddy baya 'kaunata menayi....menayi daza'a yankemin wannan hukuncin.






Love u all my Fan's πŸ’ƒπŸ» shoki πŸŠπŸ»β€β™€
[1/7, 10:28 AM] Zee Elkaseem: πŸ‘­ *AUREN TAGWAYE* πŸ‘­
πŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•Έ
πŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•Έ
πŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•Έ
πŸ•ΈπŸ•Έ
πŸ•Έ
*Written & Story by*
*Zee Elkaseem*
*{Mmn khady}*



*Dedicated to All member's group of Ciwon "ya mace* πŸ‘©πŸ»



Page......................18



Kuka take iya 'karfinta babu me rarrashinta sai da tayi me isarta sannan ta tashi falo na biyu tashiga wanda shima yaji set d'in kujeru da kayan kallo amma sai dai shi bekai na farkon haduwaba shikuma kome nacikinsa green colour ne, tsayawa tayi ta'karemashi kallo sannan tanufi wani d'akin nan kuma bedroom ne wanda aka zubama kaya yan Dubai ba 'karamin kyau d'akin yayiba, fitowa tayi daga nan tanufi gudan d'akin ahanakali tatura 'kofar tashiga nan ma karo tayi da wani 'kawataccen d'akin kwana shikuma duka kayan yan Nigeria ne aka zuba amma harma sunso Sufi na Dubai d'in kyau.

Bayan tabi ko'ina na gidan ta'karemar kallo dawowa tayi a bedroom ta zauna tsakiyar gadon tare da rufe fuskarta da hijab d'inta, take tunanin Hafiz ya dirar mata a zuciya, wani irin kuka tafashe dashi a zuciyarta tana cewa "yanzu shikenan anrabani da Hafiz mutumin danafi so nafi 'kauna akan kowane namiji, bazan iya zaman aure da kowane namiji ba bayan Hafiz yazanyi da rayuwata, haka tacigaba da kuka tana zancen zuci.

"Yanzu ni waye wanda daddy yaza6amin anya zan iya zama dashi, ita ko kad'an bata kawoma ranta jabeer ne wanda aka d'aura mata auren dashiba.

Zaune take tabuga uban tagumi hannu bibbiyu ba abinda ke mata yawo a kwalwa sai kalar salon soyayyar da Hafiz ke nunamata, yanzu shikenan anrabamu baze 'kara shayar dani zumar 'kaunarsaba.

Mi'kewa tayi tsaye kamar wacce aka tsikara "baze yiyuba tafad'a a zahiri bazan iya rabuwa bada Hafiz ba ko ana ha maza ha mata, Hafiz shi kad'aine namijin dazan aura in kasance cikin farin ciki, ko waye wannan yayi gan-ganci daya yarda da aurena, tabbass zesan abinda ya auro ya kawo gidanshi.

********

Momy da Hassana kuwa tun bayan fitar daddy da Hussaina suketa sa'ke-sa'ke da kwancewa sun rasa ina daddy zashi da Hussaina batare da yar'uwartaba Alhalin shine yasaba masu da duk inda zasu tare suke tafiya.

Da sallama ya shigo falon suduka binshi sukayi da ido ganin yadawo batare da Hussaina ba,
Momy ce tayi 'karfin halin tambayarsa "Alhj ina Hussaina take naga ka dawo kai d'aya kuma bayan tare kuka fita.

"Tana gidan mijinta, yabata amsa a takaice sannan yawuce d'akinsa, binshi tayi daga baya zuciyarta cike da mamaki.

Hassana dake zaune tanajin abinda daddy yafad'a itama tashi tayi tanufi d'akinsu tana cewa "innalillahi wa'innalaihirraji'un "Gidan miji.... tafad'a cike da mamaki, yaushe aka d'aura auren sister bamu saniba dan gashi alamu sun nuna itama momy batasan da zancen ba,
"Ya salam tafad'a tare da dafe kanta da hannu biyu dataji yana saramata kamar ze rabe biyu, fad'awa tayi kan gado tana zubar da hawaye.


: Cike da 6acin rai momy take magana "haba Alhj ban fahimce inda zancenka yadosaba.

Juyowa daddy yayi ya kalleta tare da yin wani murmushi, sannan yace "baki bu'katar in maimaita maki abunda nafad'a d'azu saboda inada tabbacin kinji kome nafad'a.

"Lalai Alhj yanzu ka tabbatar min da baka 'kaunar Hussaina akan me zakayimata irin wannan hukuncin, aure cikin kwana biyu kamar auren d'iyar kara, haba Alhj kuma amatsayina na mahaifiyarta yaci ace nasan da maganar amma bansaniba kuma banida labari kawai saika tafi da yarinya kace wai wani ka kaita gidan miji, gaskiya ni ban yardaba kawai kafad'amin inda d'iyata take inje in d'aukota idan kai baka sonta ni ina sonta, duk wannan maganganun da momy keyi tanayinsune cikin 6acin rai da d'aga murya.

"Dakata Maryam, daddy yafad'a cikin d'ga murya "wannan auren na d'aurashi kuma yariga ya d'auru ba wanda ya isa ya war-wareshi, ince idan yarinyar nan ta jawo mana abin kunya zagin daza'ayimin baza'ayimaki rabinshiba, saboda haka nariga na yanke hukunci idan kinji hukuncin danayimaki bemakiba zaki iya kama gabanki hanya a bud'e take yara kuma nawane inada iko akansu.

Tunda daddy yafara fad'a momy ke kallonsa cike da mamaki a zuciyarta tace "lallai Alhj da gaske yake kuma ba wasa tattare dashi dole nima inbi ahankali.

Cikin langa6ar da kai momy tamatso kusa da daddy ta dur'kusa gabansa "Haba Alhj meyakai na 6acin rai haka, indai kan wannan maganar ne inshaAllah kome ya wuce Allah sa haka shine mafi Alkhairi a rayuwar Hussaina, itakuma yar'uwarta Allah kawomata miji na gari.
"Ameen daddy ya amsa tare da shigewa toilet ya watsa ruwa sannan ya d'auro Al'walar magrib dan lokacin sallar yayi.
Itama Momy d'akinta tanufa ta d'aura Al'wala ta kabbara sallah bayan tagama ta dad'e kan abin sallar tana kwararo addu'a ga yaranta.





Love u all my Fan's πŸ’ƒπŸ» shoki πŸŠπŸ»β€β™€πŸ”«
[1/8, 9:50 AM] Zee Elkaseem: πŸ‘­ *AUREN TAGWAYE* πŸ‘­
πŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•Έ
πŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•Έ
πŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•Έ
πŸ•ΈπŸ•Έ
πŸ•Έ
*Written & Story by*
*Zee Elkaseem*
*{Mmn khady}*



*Dedicated to All member's group of Ciwon "ya mace* πŸ‘©πŸ»



Page......................19



Zaune take cikin d'akin tarasa mekemata dad'i a duniya, wayarta ta Dauko sunan zuby ta lalubo sannan ta danna kira, bugu d'aya zuby ta d'auka.
"Hellow 'kawata kin 6oye kwana biyu.
"Hmm kedai bari kawai zuby idan ana sallah ba'a magana.
"Banganeba 'kawata wani abune yafaru dake?
"Abubuwa da dama sun faru dan ahalin yanzu wayar nan damuke dake ina gidana.
Saurin tashi zaune zuby tayi daga kwancen datake "bangane gidankiba 'kawata, gidanki ko gidanku?
"Hmm gidana dai dan daddy yamin aure kuma yau natare.
"Aure kuma Hussaina, to waye angon zuby ta tambaya gabanta na dukan ukku-ukku kada Hussaina tacemata Hafiz ta aura, idan ko haka ta kasance da ba abinda ze hana abkuwar 'karamin ya'ki tsakaninta da Hussainar.
Hussainar ce tadawo da ita daga duniyar tunanin data lula,
"Wlh nima har yanzu bansan ko waye mijin ba, amma inaso kizo gobe,
"To shikenan 'kawata zanzo amma wane unguwane?
Nan Hussaina tabata full address sannan sukayi sallama kowanensu ya tsinke wayar.

Zuby kuwa tashiga tsananin rud'ani, tashi tayi tsaye tafara kai komo cikin d'akin "tabbass idan har tunanina ya tabbata Hussaina Hafiz ta aura tofa sainayi yanda nayi narabasu koda kuwa ta Hanyar salwantar da rayuwartane, inason Hafiz ina 'kaunarsa bazan juri ganinshi tare da wata maceba bayan ni, wasu zafafan hawaye suka zubo daga idonta tasa hannu ta goge,sannan tanufi lokar dake jikin gadon d'akin tasa hannu ta fiddo kwalbar kodin ta tuttule a bakinta ta shanye sannan tafad'a gado tana mayarda numfashi kafin bacci yayi awon gaba da ita.


: Hussaina kuwa cigaba tayi da bin d'akin da kallo kad'an-kad'an takai dubanta ga 'Kofa tana jiran ganin shigowar angon nata.

Ringing d'in wayarta tajiyo da sauri tasa Hannu ta d'auka dan tana tunanin zuby ce takirata kozata gayamata wani abu amma sai ganin sunan Hafiz tayi 6aro-6aro yana yawo kan screen d'in Wayar, sai da gabanta yayi mummunan fad'uwa bin wayar tayi da kallo har kiran ya tsinke sake kira akayi karo na biyu nanma batayi gigin d'aukaba dan ganin kiransa kayar mata da gaba yakeyi, duk dahaka beha'kuraba ya'kara kira karo na ukku hannunta na rawa ta daure ta danna OK tare da karawa a kunnenta batayi maganaba sai shi yafara magana.
"Hellow babyna kina lafiya?
Shiru tayi duk illahirin jikinta kyarma yake dan jin muryar Hafiz kad'ai jefata yake cikin wani yanayi me wuyar fassarawa.
Magana ya'karayi karo na biyu "hello babyna ko bakyajinane.
Sannan ta daure murya can 'kasa-'kasa tace "ina jinka.
"Amma kuma kikamin shiru, kinsan kuwa yanda nadamu dake, kinsan halin dana fad'a na rashinki danayi kwana biyu......

Cikin d'aga murya da masifa Hussaina tafara magana "dakata Hafiz bakada wani dad'in baki dazakayimin bayan ka cuceni ka cuci rayuwata karabani da abinda duk wata mace take ta'kama da tin'kaho dashi a duniya.
Amma bakome ba laifinka bane laifinane dana d'auki yardata nami'ka maka d'ari bisa d'ari, gashi yanzu ina gidan mijina banida wata daraja da 'kimar daze kalleni da ita.

Dakata Hussaina nifa bangane inda maganganunki suka dosaba,
"Tunda ka yaudareni ka kaini gidanka da sunan zan gaisheda hajiyarka ashe da wata manufar ka kaini danka ketamin haddi.......

Jitayi ana doka sallama daga falo hakan yasa tayi saurin kashe wayar baki d'aya ta turata 'kar'kashin filo, sannan tayi saurin janyo hijab d'inta tarufe fuskarta dashi.

Jitayi annufo d'akin datake hakan yasa fad'uwar gabanta ya yawaita,
"Assalamu Alaikum warahamatullah, yafad'a tare da 'karasowa cikin d'akin ya zauna bakin gado.
Koda jin muryar kunnenta ya tabbatar mata da tasan me wannan muryar jin 'kamshin turarensa yadaki hancinta ya'kara tabbatarmata datasan kowaye,
Saurin bud'e lullu6in datayima fuskarta tayi dan tabbatarma idanunta abinda take tunani.
Tana bud'ewa kuwa sukayi ido hud'u da jabeer, a firgice ta nunashi da hannunta tana fad'in "Jabeer dama Kaine mutumin dayaimin yankan 'kauna, karabani da Wanda nakeso, kasa daddy yayimin aure irinnan d'iyar wasan yara aure cikin kwana biyu, bayan nadad'e da sanar maka inada wanda nakeso bakaiba, to ina me tabbatarma saikayi danasanin aurena dakayi, idan kayine dan farincikin rayuwarka nikuma ka ba'kantamin rayuwa to wallahi kaima ze zama ba'kin ciki a gareka.

"Haba hussaina banyi haka dan in ba'kantamikiba, kuma da banisonki bazan aurekiba inaso ki d'auki wannan a matsayin 'kaddarace agaremu kuma muyi fatan Allah sa tazamar mana Alkhairi a rayuwarmu.

Wani irin kuka tafashe dashi dan tunawa datayi batadafa wata daraja da 'kimar da sauran mata keda ita barantana tayima jabeer wula'kancin dataga dama abinda yafi kawai tabada kai bori ya hau, sannan tayi biyayya ta zauna lafiya ko Allah zesa yarufamata asiri, goge hawayenta tayi tace "to Allah shigemana gaba kuma Allah tabbatar mana da Alkhairi cikin wannan zama namu.
Jabeer ya Amsa da Ameen har cikin ranshi yaji dad'i da kuma mamakin saukowar Hussaina haka.







Love u all my Fan's πŸ’ƒπŸ» shoki πŸŠπŸ»β€β™€πŸ™Š
[1/8, 8:40 PM] Zee Elkaseem: [08/01 8:15 pm] Zee Elkaseem: πŸ‘­ *AUREN TAGWAYE* πŸ‘­
πŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•Έ
πŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•Έ
πŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•Έ
πŸ•ΈπŸ•Έ
πŸ•Έ
*Written & Story by*
*Zee Elkaseem*
*{Mmn khady}*



*Dedicated to All member's group of Ciwon "ya mace* πŸ‘©πŸ»



Page......................20


Daga nan ya umarceta dasu gabatar da sallah su godema Allah kamar yanda addini ya tanada, ba musu tanufi toilet ta d'auro Alwala sannan shima ya Shiga ya d'auro tasa Alwalar suka gabatar da sallar nafila, bayan sun kammala ya dad'e yana kwararo masu addu'oi kafin su shafa.

Sannan ya d'auko ledar daya shigo da ita ya ajiye tsakiyar carpet d'in dake malale a bedroom d'in, da kanshi yanufi kitchen ya d'auko masu palate da cup, gasashiyar kazace guda ukku yabaje kan tire tare da fresh milk da lemun 5alive.

Juyowa yayi ya kalli Hussaina wacce take takure duk tabi ta raina gaskiyarta binshi kawai take da kallo, a zuciyarta kuwa tunanin abinda ze biyo baya takeyi bayan Jabeer ya kusanceta yajita ba cikakkiyar budurwaba, wasu guntayen hawaye suka zubo a idonta tayi saurin sa bayan hannunta ta goge batare da jebeer d'in ya luraba.

Jabeer d'inne ya maidota daga dogon tunanin datake ta hanyar matsowa kusa da ita "bismillah gimbiya saurautar mata nasan dai kinajin yunwa yakamata ace kinci wani abu kafin ki kwanta.

Kad'a kai tayi kamar 'kadangaruwa "a'a ni banajin yunwa.
"Ban yardaba gaskiya da ganin wannan cikin ya dad'e rabonsa da abinci, yafad'a tare dakai hannunsa kan cikinta.
Ture hannun nashi tayi "nifa banajin yunwa,
"To naji bakijin yunwa amma ban yarda ki 'ki cin komeba, kawai dai inajin sarautar takice ta motsa, uwar gida sarautar mata, yafad'a cikin tsokana.

Hannu yasa ya yago naman yanufi bakinta dashi da niyyar yabata tayi saurin kauda kanta,
"Haba Hussaina bekamata ace kin'ki kar6ar komeba idan kikayi haka nikam bazanji dad'iba, dan Allah badanniba ki taimakamin ki kar6a.

A hankali ta juyo yafara bata abaki saida ya tabbatar data 'koshi sannan yazubo fresh milk nanma da kyar ta shanye cup d'aya.

Shima sama-sama yaci naman kajin sannan yakora da lemu, d'akinsa yanufa yacire kayan jikinsa yafad'a toilet yashe'ka wanka.

Hussaina kuwa tana ganin fitarshi tanufi wadrope tana bud'ewa taganta ma'kare da kaya, batayi mamakiba dan daddy yafad'amata babu abinda ba'a tanadar mata a gidan ba.

Wata fitinanniyar rigar bacci ta d'auko wacce zamu iya kira akwai ya babu, ta sanya sannan tabi duk illahirin jikinta ta feshi da sassayan turare, sannan tabi lafiyar gado tayi kwanciyarta batare data rage Hasken d'akinba kuma tayi hakane dan tanajin tsoro ganitake kamar idan ta kwanta a duhu-duhu wani abu ze sameta tasaba kullum tanajin motsin Hassana kusa da ita, yau gashi zatayi kwanan kad'aici dan taga Alamar Jabeer banan ze kwanaba tunda gashi yatafi gudan d'akin yabarta, da wannan tunanin bacci 6arowa yayi awon gaba da ita.

Sanye yake da best da short niker, farare 'kal jikinshi sai tashin 'kamshin turarensa yake me suna *story of love* yanufi d'akin.

Ganin d'akin da haske ya tabbatar mai da Hussaina batayi bacciba, da sallama yashiga jin bata amsaba yasashi dubawa kobata d'akinne, can ya hangota kwance kan lafiyayyen gadonta tanata sharar bacci hankalinta kwance, karsa shiga yayi cikin d'akin sannan ya maida 'kofar yarufe, kafin ya isa gareta ya'karemata kallo, yanda rigar baccin jikinta take sharara ba abinda be bayyanaba na surar jikinta, take yaji wata matsananciyar sha'awarta ta kamashi rage Hasken d'akin yayi tare da kunna masu fitila me sau'kin haske, ya haye gadon ya rungumota gaba d'aya jikinsa.










Love u all my Fan's πŸ’ƒπŸ» Shoki πŸŠπŸ»β€β™€β›„
[1/9, 8:14 AM] Zee Elkaseem: πŸ‘­ *AUREN TAGWAYE* πŸ‘­
πŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•Έ
πŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•Έ
πŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•Έ
πŸ•ΈπŸ•Έ
πŸ•Έ
*Written & Story by*
*Zee Elkaseem*
*{Mmn khady}*



*Dedicated to All member's group of Ciwon "ya mace* πŸ‘©πŸ»



Page......................21



A hankali yafara shafa lallausar fatar jikinta, yayinda ya tsinci kanshi cikin wani irin farin ciki marar misaltuwa.
Can cikin bacci Hussaina taji Alamar mutum kusa da ita ahankali ta bud'e idonta, tozali tayi da jabeer Wanda ya lula cikin duniyar 'kaunarta yana aikamata da sa'konni soyayya masu wuyar fassarawa, wani irin dad'i taji cikin ranta wanda ita kanta batasan dalilin hakan ba, 'kara shigewa tayi jikinsa tare da sakar mashi duk wani sashe na jikinta, shikuma yacigaba da sarrafata da kwarewarsa da gogewarsa, Hussaina kuwa mamakin jabeer ne yacikamata zuciya "wai dama haka jabeer ya iya soyayya ya iya salo daban-daban amma lokacin kafin suyi aure yake nunamata shi ustaz ne kullum beda magana sai wa'azi da nasiha.
Da wannan tunanin kawai ta ida mallakamashi kanta, a daren sukasha amarcinsu ranar jabeer yasan Hussaina mace, kuma ba 'karamin farin ciki yayiba na yanda ya sameta cikakkiyar budurwa.

Hussaina kuwa banda kuka babu abinda takeyi saboda zafi da rad'ad'in datakeji, jabeer kuwa rarrashinta yari'kayi, dan wani sabon shau'kin sontane ya'kara kamashi.

Tashi yayi yanufi toilet yayi wanka ya tsarkake jikinsa, sannan yahad'a wani ruwa me d'umi ya dawo ya d'auki Hussaina yanufi toilet d'in da ita, zaunar da ita yayi cikin ruwan dan tad'an gasa jikinta, sannan yafito ya gyara gadon tare da canja masu bedsheets, bayan yagama yakoma toilet d'in lokacin Hussaina tagama wankan zuwa yayi da niyyar ya d'aukota amma saita kauce ta ma'kale kafad'a bataso, be matsamataba tunda ta nuna bataso hannunta yakama suka fito tana taku ahankali, kan gado ya taimaka mata ta kwanta sannan ya 'kuremata a.c d'akin kasancewar lokacin ana zafi.

Komawa yayi toilet ya d'auro wata sabuwar Al'wala sannan yazo ya kabbara sallah, nafila yari'ka jerowa saida yafarajin bacci sannan ya sallame ya dad'e yana kwararo addu'a kafin ya shafa, sannan Yakoma kan

Please Login or Register in order to submit comment