Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE



You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

tsirara haihuwar uwarata kan gado.



A gidansu Hussaina kuwa Hankalinsu yayi matu'kar tashi ganin 'karfe goma ta gota ba Hussaina ba labarinta, gashi ko ankira wayarta switch up,

Daddy yagama 'kulewa ranshi yayi matukar 6aci.
"Lallai yarinyar nan tana nema ta maidani mutumin banza cikin garinnan, nizata jama abin magana aiko zata dawo ta tarad dani zatamin bayanin inda taje,
Sannan ya maida dubanshi ga momy "kece me babban laifi keda kikabarta tafita bayan kinsan dokar dana kafa a gidannan.
"Haba Alh sau nawa zan gayama bansan fitar yarinyar nanba, ko kana tunanin nizan bata izinin fitane, bayan nasan dokar daka kafa a gidannan.

"Zata sameni nikad'ai nasan hukuncin dazan yankemata, kuma kuduka bance wani yabani ha'kuri akan kowane hukunci zan yanke akantaba yafad'a yana nuna Momy da Hassana wacce ba abinda take sai kuka, tana ro'kon Allah ya maido mata da yar'uwarta lafiya duk inda take.

*12:30am* ⏱

Da misalin 'karfe sha biyu da rabi na dare Hussaina tafarka daga nannauyan baccin datakeyi ahankali ta bud'e idanunta a tunaninta d'akinsu take, kawai sai ganinta tayi wani d'akin daban wanda bazata iya sheda inda take.

"Subhanallahi tafad'a tare da 'karema jikinta kallo ba kome jikinta, saurin jawo zaninta tayi ta rufe jikinta tana waige-waige taga ta inda mutum zefito daga cikin d'akin amma bataga Alamar hakanba,
Ahankali tunanin abinda yafaru da ita yafara dawomata a kwalwa, sai lokacin ta tuna tazonefa gaida hajiyar Hafiz, to Amma meya kawota nan? Waye yarabata da kayan jikinta? Ganin batada wanda zebata amsar duka jerin wad'annan tambayoyin data jeroma kanta yasata aza hannuwanta duka biyu aka ta kwala wata irin 'kara.
"Shikenan Hafiz ka cuceni kagama da rayuwata ka 6atamin abinda duk wata mace take ta'kama kuma take tin'kaho dashi a duniya, jin damshi-danshi 'kar'kashinta yasa ta'kara tabbatarma kanta da abinda take zargi "shikenan Hafiz yagama dani ya 6atamin budurcina nashiga ukku tafad'a tare da sakin wani wahalallen kuka.

Ahaka ta maida kayanta ta d'auki jakarta koda ta d'auko wayarta kashe taganta baki d'aya bata tsaya kunnawaba sakata kawai tayi a jaka sannan tanufi 'kofar fita daga gidan.

Cikin sa'a taga gidan bud'e batayi wata-wataba tafito tad'au hanya dukda ba'kin duhun dake akwai ga unguwar tsit babu wani mahalu'ki bakajin motsin kome sai haushin karnuka da kukan tsun-tsaye.

Tafiya take batare datasan inda zataba, harta fito titi, nanma wani titi rami'ka batare datasan inda ze 6ulla da itaba.

Tun tana tafiya da sauran 'karfi-'karfinta har tafara gajiya tafara layi kamar wacce tasha tabugu.
Da-dai bakin wani junction taji an haske mata fuska da wata irin fitila me tsananin haske hannu tasa tana karewa muryar wani namiji taji yana cewa "hey your under arrest kune yan'iska masu shaye-shaye da yawon banza ko.

Kafin tayi wata mgana sunsakata mota sai ofishinsu.
Ganinta office d'in yansanda yasa hankalinta yad'an kwanta dan koba kome tasan ta ku6uta.







Love u all my Fan's πŸ’ƒπŸ» shoki 🏊🏻
[1/2, 7:21 AM] Zee Elkaseem: πŸ‘­ *AUREN TAGWAYE* πŸ‘­
πŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•Έ
πŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•Έ
πŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•Έ
πŸ•ΈπŸ•Έ
πŸ•Έ
*Written & Story by*
*Zee Elkaseem*
*{Mmn khady}*


*Dedicated to All member's group of* *Ciwon ya mace* πŸ‘©πŸ»


Page-------------------------11


*washe Gari* bayan sun dawo daga isalmiyyah, Hussaina taje d'akin Momy zaune ta isketa bakin gado tana nazarin wani littafin addu'oi cikin ladabi ta zauna kusa da ita.

"Momy wata Alfarma nazo nema gurinki,
"Tame ina jinki fad'i, momy tace batare data kalletaba,
Nan tashiga inda-inda tana ganin kamar 'karyar dazatayi bazata fishshetaba amma sai wata zuciyar tace "ki kwatanta hausawa sunce a rashin tayi akan bar araha.
"Dama Im...wai asibiti zamuje ganin mamar Zuby shine nakeso dan Allah ki taimakeni kibarni wlh namiki Al'kawarin bazan wuce awa d'ayaba.
"Kinga Hussaina banison abinda zezo yad'agamin hankali ina zamana lafiya, yanzu kije kisamu guri kiyi zamanki kuma mahaifinki yadawo yatarad bakinan wace amsa zanbashi,

"InshaAllah Momy bama zesan najeba,
Haka dai tayita magiya har momy tabarta tare da saharad'in idan daddynsu yadawo bata dawoba zatace batasanma fitartaba, tace ta amince da hakan.

Cikin Zumud'i takoma d'akinsu ta d'auko wani tsadadden swiss less maroon colour tasanya sannan tasanya takalmi milk jaka milk, sai tayi too much kasancewar zaren da akayi kwalliyar less d'in milk ne sannan tabi da milk d'in mayafi, _{mashaAllah koni zee dana kalleta nasan ba 'karamin kyau tayiba}_

Hassana dake zaune tana bitar littafin ibadah wanda akayimasu 'kari yau, ta kalleta "uhm sister wannan gayu haka Kuma sai ina?
"Sorry sister sauri nakeyi idan nadawo zakiji,
"To Allah maidoki lafiya
"ameen kawai tace tafice, A falo ta tarad da momy saida gabanta yayi mummunan fad'uwa dan batayi tunanin ganinta nanba,

Kallo Momy ta'karemata daga sama har 'kasa "keda zaki ganin marar lafiya kuma da wannan gayu haka,
'Ka'karo murmushi tayi "Hmm Momy kuma dan za'a ganin marar lafiya ba'a sa kaya me kyau.
"To shikenan nidai nagayamaki karki dad'e.
"InshaAllah bazan dad'eba.

Tana fita tahau napep sai inda sukayi mahad'a da Hafiz, tana isa kuwa ta iskeshi a mota, bud'emata yayi tashige sannan suka d'au hanya.

Sunyi tafiya me nisa kafin su shiga rukunin wasu gidaje da Alama estate ne, bakin wani gida sukayi parking shine yafara fitowa sannan yabud'emata tafito tare suka jera har zuwa cikin gidan,

Wani 'kawataccen falo yayimata masauki gidan tsit kamar ba mutane amma kuma yanayin kayan gidan zaka kallah kagane akwai mutane, zama sukayi suna fira sama-sama kusan minti sha biyar ba Alamar wani ze fito, nan Hussaina tad'an tsorata ta kalli Hafiz Wai ina mutanen gidanne,
Murmushi yayi haba babyna kamar ba wayayyaba hajiya tana ciki yanzu zata fito, ina zuwa yafad'a tare da mi'kewa yanufi pridge lemun _5ali6e_ ya d'auko tare da cup d'in glass ya ajiyemata,
"Bari ingyama hajiya may be bataji shigowarmu bane, wani d'aki yashiga da Alama bedroom ne bayan minti biyar yafito ya kalli Hussaina wacce kallo d'aya zakayimata kagane a tsorace take "hajiya tana wankane amma tana zuwa, wai bakisha lemunba "Uhm na'koshi nidai sonike intafi gida kada amun fad'a kagafa har bakwai da minti sha tara tafad'a tana duba agogon wayarta.
"Koma miye ai kinsha koda lemunne kinsan idan bakishaba bazanji dad'iba.

Zubowa tayi cikin cup tad'an kur6a kad'an ta ajiye
"Haba me kikasha nan?
Lemun yad'auka yacika cup d'in yafara bata da kanshi da ta'ki kar6a ganin ranshi ya 6aci yasa ta 'kar6a a hannunta ta shanye sannan ta ajiye cup d'in.

Cike da farinciki ya kalleta "kokefa babyna amma da kintsaya wani no'ke-no'ke "Uhm kawai tace dan tunda tasha lemun jikinta yamutu sai wata kasala data rufeta.

Hafiz yana lura da halin datake ciki saboda haka mi'kewa yayi tare dayin hanyar d'akin dayashiga d'azu "ina zuwa nasan yanzu tagama.

Hussaina kuwa hamma tafara jerowa d'aya bayan d'aya tana lumshe idanu cikin minti bakwai bacci me nauyi yayi awon gaba da ita.

Saida ya dai-daici maganin dayazubamata a lemu ya Isa yin aikinsa sannan yafito ganinta yayi kwance kan kujera tana shara bacci wani shu'umin murmushi yayi tare da 'karasowa inda take.








Love u all my Fan's πŸ’ƒπŸ» shoki 🏊🏻
[1/2, 7:21 AM] Zee Elkaseem: πŸ‘­ *AUREN TAGWAYE* πŸ‘­
πŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•Έ
πŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•Έ
πŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•Έ
πŸ•ΈπŸ•Έ
πŸ•Έ
*Written & Story by*
*Zee Elkaseem*
*{Mmn khady}*


*Dedicated to All member's group of* *Ciwon ya mace* πŸ‘©πŸ»


Page-------------------------13


Wani d'an sandane ya kalleta Wanda da Alama shine babbansu yace "miye sunanki?
Jiki na kyarma tabashi amsa "Hussaina,
"Ke yar gidan wacece kike yawo da wannan daren?
"Uhm wlh yalla6ai ba yawo nikeyiba, hasalima ni bansan ya'akayi nafito daga gidaba.
"Shut up, yafad'a cikin d'ga murya, ke muzaki rainama wayo, irinki-irinki mungamu yafi a 'kirga, hadama wad'anda sukafiki iskanci.
"waye zefitodake daga gidanku batare da izininkiba, kada kimanta cikin Halin da aka kamaki na maye koshima bakisan ya'akayi kikayi shaye-shayen ba?

"Wlh yalla6ai bansha komeba na rantsema da Allah,
Tassss saukar wani lafiyayyen mari taji a kumatunta wanda wannan d'an sandan ya d'auketa dashi, marinda saida ya gigitata saboda tsananin azabar tafin hannun d'an sandan ba 'karamin kato bane.

A 'kufule yace zaki fad'amana ke 'yar'waye kokuwa saina sa6amaki.
Cikin tsananin gigicewa take magana "zanfad'a.... Zanfad'a wlh.
"Oya ina saurarenki d'ansandan yafad'a tare da tsareta da manyan idanunsa masu ban tsoro.

"Ni Yar gidan Alhj Mansir company ce.
"What? 'Dan sandan yafad'a tare da mi'kewa tsaye.
"Karya kike yafad'a tare da nunata da yatsa, duk fad'in garinnan waye besan Alhj Mansir kamfaniba, mutumin kirki me halayya ta kwarai ace ke yarsace kina wannan munanan halaye.
Kuma ba wannan ba iya saninmu Alh Mansir bayada wasu 'ya'ya sai yara biyu yan tagwaye.
"Yan la6ai wlh nice ai mune yan tagwayen Nice Hussainar dan Allah Ku taimakeni Ku maidani gidanmu.

"Sajen Habu, dan sandan yakwalama wani daga cikin yansandan kira.
Da sauri d'ansandan ya iso gabanshi ya 'kame tare da saramashi.

"Maza a fiddo mota yanzu zamuje gidan Alh Mansir kamfani "yes sir yafad'a saida ya'kara saramashi kafin yafita zuwa ma'ajiyar motocin.

Dare ya tsala misalin 'karfe biyu na dare motar yan'sandan tayi parking bakin get din gidansu Hussaina, nocking sukayi lokacin mal bala yana kwance cikin d'an karamin d'akinsa yafito da sandarsa a hannu yana tamabayar "waye? Hussainace tayi magana "nice mal bala, "kece wah? Ya tambaya.
"Nice Hussaina.
"Husssaina da wannan daren subhanallah bud'e 'kofar yayi ahankali yana le'kowa yayi ido hud'u da ita da 'yansanda biyu tare da ita.

Da Sauri Hussaina tashiga gidan 'yansandan suka take mata baya, a harabar gidan suka tsaya "kishiga kiyimana magana da mahaifin naki.
Bata ko sauraresuba tayi cikin gidan da gudu,
Lokacin Daddy,Momy da Hussaina suna Zaune a falo, Momy sai Addu'a take Allah maidomata da 'ya lafiya a Zuciyarta tana cewa "danasan haka zata kasance daban amince da fitartaba.
Hassana kuwa kuka kawai takeyi, yayinda dady Zuciyarsa tagama 'konewa jiyake inama yaga Hussaina yanzu Allah kad'ai yasan irin dukan dazeyimata.

Begama wannan tunaninba yaga anturo 'kofar falon, mikewa yayi da sauri dan ganin me shigo masu gida da wannan tsohon daren, ido Hudu sukayi da Hussaina saurin isa yayi Inda take a zuciye ya dun'kule hannu yakaimata wani mugun naushi sannan yasa 'kafa ya hard'ota.
Fad'uwa tayi 'kasa tana maida numfashi sama-sama ko kukanma yakasa zuwamata saboda tsananin azabar datake ciki.

Dukda haka Daddy beyi 'kasa a gwiwaba gurin ciro cherger wata fitila dake jikin soket yarin'ka tsulamata, sai lokacin tasamu damar fasa ihu tare da d'aukewar numfashinta ta sulale 'kasa sumammiya.

Ganin tafad'i yasa Momy 'karasowa gurin tana kuka "innalillahi Alhj miye haka kake shirin kasheta, kabari mana kaji ta bakinta, "Bazanbariba da bata fitaba da hakan be faruba, kuma ko mutuwa tayi bani nadamar kasheta saboda da inyi mugun gani 'kara narasata baki d'aya.

Hassana kuwa ganin 'yar'uwarta kwance ba Alamar rai tattare da ita yasata rud'ewa tafito zuwa harabar gidan dagudu tana kuka, ganinta yasa 'yansanda sukayi saurin tarbarta a tunaninsu Hussainace saida suka kula da kayan jikin wannan basubane jikin wacce suka kawo yanzu "ke lafiya suka shiga tambayarta, a gigice take nunamasu cikin gidan tana cewa "daddy yakasheta, ya kashemin 'yar'uwa.
"What suka fad'a tare da abkawa cikin gidan baki d'ayansu..






Love u all my Fan's πŸ’ƒπŸ» shoki 🏊🏻
[1/2, 7:21 AM] Zee Elkaseem: πŸ‘­ *AUREN TAGWAYE* πŸ‘­
πŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•Έ
πŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•Έ
πŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•Έ
πŸ•ΈπŸ•Έ
πŸ•Έ
*Written & Story by*
*Zee Elkaseem*
*{Mmn khady}*


*Dedicated to All member's group of* *Ciwon ya mace* πŸ‘©πŸ»


Page-------------------------14


A gigice Momy tabi Hassana da kallo tare da 'yan'sandan dake tare da ita.
"Hassana Kina Haukane, mahaifin naki kika kirama 'yan sandan.
Cikin muryar kuka Hassana tace "Wlh momy bani nakirasuba ina fita nagansu a harabar gidannan.

Kallonsu daddy yayi a gadarance yace "waya kawoku gidana, kuma da izinin wah kuka shigo har nan? Yafad'a yana nuna inda suke tsai-tsaye.

"Babban cikinsune yayi magana "Sunana inspeter Sabi'u wale, mune wad'anda suka kawo wannan yarinyar gidannan bayan mun tsinceta cikin halin maye, bayan ta dawo hayyacinta mukayimata 'yan tambayoyi shine tasanar damu kaine mahaifinta shine muka kawota, muna tsaye a haraba munajiran tayimana magana dakai shine mukaga wannna tafito tana fad'in a taimaketa ankashemata 'yar'uwa shine dalilin dayasa muka shigo domin gudanar da aikinmu kamar yanda doka ta tanada.

"Owj naji duka bayaninku nagode, inaso kutafi kawai ni zan iya solving kowace matsala tagidana batare da wani yasamin hannuba nagode da taimakon dakukayima 'yata.

"Muma mungode Alhj Amma dan Allah ari'ka kai zuciya nesa, saboda gudun danasani....
Sai a hanzarta a kaita asibiti suka fad'a suna kallon Hussaina dake kwance bako motsi.


Bayan fitar 'yansandan momy ta kalle daddy Wanda yaketa mazurai da Alama har 'yanzu zuciyarsa bata gama hucewaba,

Hussaina kuwa har 'yanzu tana kwance batasan inda kanta yakeba, momyce tamatso inda take ta tallabo kanta ganin ba alamar rai tattare da ita yasata fashewa da kuka, "Dan Allah Ahj mukaita asibiti kada tamutu.....

"Tamutun mana, yafad'a cikin d'aga murya.
Sannan yayi 'kasa da muryarshi yana cewa "ba inda zan kaita na kwammace inrasata baki d'aya da mugun halin datake Neman jefa kanta.
Tajamani abin fad'i a gari, yana gama fad'in haka yashige d'akinshi ya maido 'kofa yarufe.

Cikin kuka Momy ta kalli Hassana tace kawomani ruwa.
Da sauri Hassana ta d'ebo ruwa cikin cup takawo, amsa Momy tayi tashiga kwarama Hussaina a jiki amma ko motsi batayiba saida ta zubamata a fuska sannan tayi firgigi ta tashi ta 'kan'kame Momy tana fad'in dan Allah kibashi ha'kuri wlh bazan 'karaba.

"Ke Hussaina kitsaya mana, ki nutsu nace ba daddynku bane nice Momy
'Kara 'kan'kameta tayi tana fad'in "wayyo Momy wlh bazan 'karaba kigayamashi na tuba.

"Cikin tsawa Momy tace "dallah ni sakeni tare da tureta daga jikinta, kinsan kina tsoro kikaje yawon har kika kai wannan lokacin baki dawoba, itama tana gama fad'in haka tayi tafiyarta d'akinta tabar Hussaina nan tana kuka itada Hassana.

Hassanace tamatso kusada ita takama Hannunta ta mi'kar da ita tsaye suka nufi d'akinsu.
Koda suka shiga d"akin zaune sukayi jugum-jugum suduka suna sharar kwallah.

Ita Hassana tana kukan halinda 'yansandan nan suka fad'i sunkama Hussaina na maye.

Itakuma Hussaina tana kukan yaudara da Hafiz yayimata har yayi nasarar rabata da budurcinta.
Wasu sabbin hawaye suka zubo a kuncinta.

Hassana ta kalleta tare dasa hannunta ta sharemata hawaye
"Dan Allah 'yar'uwata naro'keki ki gayamin gaskiyar inda kikaje har kikakai wannan lokacin baki dawo gidaba, kuma da gaskene abinda 'yansandan nan suka fad'i na kamaki dasukayi cikin halin maye?

Tana gama fad'in haka ta tsareta da idanu tana jiran jin amsar dazatabata "Hmm ko d'aya Hassana wlh bansha komeba, kuma ni ba inda naje nasan dai naje asibiti kamar yanda na tambayi momy zanje kuma ta amincemin, ana gaf da magariba nabaro asibitin ina tsaye inajiran abin hawa wani me mota yatsaya gabana yaro'keni da inshiga yaragemin hanya nikuma ganin ina sauri yasa na Amince nashiga motar to shinefa daganan ban 'kara sanin abinda yafaruba saida na tsinci kaina yashe a titi, wannan shine gaskiyar abinda yafaru.

Hassana najin haka ta 'kara fashewa da kuka tare da rungume 'yar'uwarta tana fad'in "sister Allah yasa da rabon sauran shan ruwanki a duniya, ya Allah na godema daka kwatomin 'yar'uwata daga hannun muyagun mutane.

Hussaina kuwa dad'i taji har cikin ranta dan ganin Hassana ta yarda da 'karyar data tsaramata, a zuciyartama cewa tayi aiko gobe idan daddy da Momy sun tuhumeni abinda zan fad'amasu kenan, da haka suka kwanta bacci yayi awon gaba dasu kowace da tunani barkatai a zuciyarta.


*Washe Gari.*

Koda suka tashi bayan sunyi duk abinda yadace na gyaran gida, komawa sukayi d'aki sukayi wanka wasu dogayen riguna suka sanya masu kyan gaske tare da 'yan 'kananan hijab.

Lokacin Momy tagama had'a break fast zuna zaune kan dining tana zubama daddy kasancewar tara hartayi yana sauri yafita office saboda yanada ayyuka da dama a can.

Jerawa sukayi gwanin ban sha'awa suka nufi inda iyayen nasu suke sannan suka zazzuna bayan sun gaishe da iyayen nasu.
Hussaina sai sunne kai takeyi alamar rashin gaskiya.

Bayan sunkammala breakfast ne daddy ya kalli Hussaina tare da d'dd'aure fuska kamar beta6a dariyaba yace "inaso kigayamin gidan ubanwa kikaje jiya.

"Uh...im asibiti naje ganin mamar 'kawata.
"Da izinin wah kika fita?
Kallon Momy tayi suna had'a ido Momy ta watsamata wata muguwar harara, ba shiri ta saddar da kanta 'kasa, tayi shiru.

Dadyne yacigaba da magana "koma waye ya d'aure maki gindi a gidannan kike Neman lalacewa tonidai ba agabana ba, kuma yau basai gobeba zan d'auki mataki kanki dan bazan zauna ina kallonki kijamin surutu a gariba, yana gama fad'in haka ya d'auki jakarsa yafice daga gidan ranshi a matu'kar 6ace.











Love u all my Fan's πŸ’ƒπŸ» shoki 🏊🏻
[1/2, 8:33 AM] Zee Elkaseem: πŸ‘­ *AUREN TAGWAYE* πŸ‘­
πŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•Έ
πŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•Έ
πŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•Έ
πŸ•ΈπŸ•Έ
πŸ•Έ
*Written & Story by*
*Zee Elkaseem*
*{Mmn khady}*



*Dedicated to All member's group of Ciwon "ya mace* πŸ‘©πŸ»



Page......................15


Daddy ne Zaune office d'insa yahad'a hannu bibbiyu ya buga tagumi ba abinda yake tunani sai irin rayuwar da Hussaina take neman jefa kanta,

Mi'kewa yayi tsaye ya maida hannuwansa duka biyu baya tare da fara zagaya office d'in yafara zancen zuci "yanzu wane mataki yakamata in d'auka dan ganin nayima tufakar hanci bata war-wareba, yau kimanin shekara ishirin ina tarbiyantar da yarannan amma lokaci d'aya suna nema su bijiremin, komawa yayi kan kujera ya zauna tare da maida kanshi sama ba abinda yake tunani sai abinda 'yan sandan dasuka kawo Hussaina gida suka fad'i na cewa sun kamata cikin Halin maye, wato rayuwar dazata jefa kanta kenan, wadda daga haka mutum ze iya aikata kome hatta da kisan kai mashayi na iya aikatawa batare da shakka ko shayin irin hukuncin daze biyo bayaba.

"Assalamu Alikum, da sallama jabeer yashigo office d'in hannunsa d'auke da wasu files-files, jin shiru ba'a amsa sallamar ba yasa ya'kara yin wani sallamar karo na biyu, nanma shiru daddy be amsaba dan yayi nisa cikin tunanin dayake, guri jabeer yasamu ya zauna tare da ajiye files-files d'in kan tebur d'indake gabanshi da d'an 'karfi yanda daddy zeji karar ajiyewar. Hakan kuwa ya maidoshi daga dogon tunanin dayake ya d'ago da kanshi ya kalli jabeer "Ah jabeer badai har kagamaba, "eh nagama gashinan saura wad'annan files d'inne sunada 'yar matsala akwai takardun da babu aciki, yafad'a yana ware wasu files guda biyu gefe.

"Owk to ba Matsala idan na duba zanyima magana sai a gyara, "to kawai yafad'a tare da mi'kewa ze fita daga office d'in harya kai bakin 'kofa daddy yayi kiransa "jabeer, cikin girmamawa jabeer ya amsa tare da dawowa ya zauna,

Saida daddy yayi shiru na kimanin minti biyu kafin ya sauke ajiyar zuciya "Jabeer dama inason magana dakai "to Alhj Allah sa dai lafiya,
"Eh to lafiya lao, kan maganar Aurenka da Hussaina kanasonta kuwa har yanzu?
Cike da jin kunyar tambayar da daddy yayimasa ya amsa da "eh.

"To bakada matsala inaso da anjima bayan sallar azahar kataho da magabatanka da shedu koda basu wuce mutum gomaba, nima zan sananar da 'yan'uwana za'a d'aura aurenku kaida ita, bani bukatar kome naka sadaki kawai zaka taho dashi naira dubu hamsin,
Kada kayi mamaki kan wannan abin dana aiwatar akwai dalilin yin hakan Wanda nasan koda kaji dalilin na tabbata bazaka'ki jininaba,

Jabeer dai shiru yayi yana sauraron Alhj cike da mamaki a zuciyarshi yana cewa "wannan shine ikon Allah me tsaida wando koba zariya, kome wannnagaggawar take nufi Allahu wa'alamu.

Haka ya kauda kowane tunani cikin zuciayrshi yayima daddy godiya sannan yakoma office d'inshi.
Koda ya koma tunanin dai yahanashi sukuni saboda haka rufe nashi office d'in yayi Yakama hanyar gida.

*Waye Jabeer*

Jabeer Suleman shine asalin sunanshi Haifaffen garin katsina, Alh sule tankuri shine mahaifinsa sai mahaifiyarsa Hajiya sa'ada sunada rufin asiri Bakin gwargwado amma ba'a kiransu masu arziki, su biyu iyayensu suka haifa dagashi sai 'kanwarsa Nusaiba wacce akwai tazara sosai tsakaninsu dan ahalin yanzu nusaiba bata wuce shekara sha shidda zuwa sha bakwaiba yayinda jabeer yakeda talatin da d'aya.
Tun yana d'an shekara sha bakwai mahaifinsu yarasu lokacin mahaifiyarsu na d'auke da 'karamin cikin nusaiba bayan rasuwar mahaifinsu da wata bakwai ta haifi nusaiba, haka sukacigaba da rayuwa yau da dad'i gobe babu, yayinda mahaifiyarsu ta tsaya tsayin daka dan ganin jabeer yayi karatu, da kyar da sud'in goshi sukasamu ya kammala karatunshi a F.C.Ekatsina kasancewarshi hazi'ki yasa yasamu sakamako me kyau amma dukda haka samun aiki yayi wahala kusan shekara biyu yana neman aiki besamuba, kwatsam rannan yaji ana Neman ma'aikata a Company Alhj mansir badan yasa ran zesamuba yaje yayi interview cikin ikon Allah kuwa saiga sunanshi cikin wad'anda aka d'auka aiki, sunyi matu'kar farinciki shida mahaifiyarshi da 'kanwarshi, ranar dazefara zuwa aiki mahaifiyarshi tayimashi nasiha me ratsa jiki akan ri'kon amana da gaskiya, sannan tabishi da addu'ar samun s'a.

Bayan wata shidda dafara aikinsa Alhj mansir yalura da Halin gaskiya da ri'kon amana na jabeer hakan yasa yajawoshi jiki tare da 'karamashi matsayi a office d'in Wanda a halin yanzu shine mataimakin manager company.



*Masu yimin magana ta prvt najina dasukayi shiru kwana biyu Dan Allah kuyi hakuri na rashin ganin reply d'ina naga sa'konku saidai be karantuwa kasancewar nasake download whatapp ne nagode da kulawarku.*




Love u all my Fan's πŸ’ƒπŸ» shoki πŸŠπŸ»β€β™€
[1/4, 7:48 AM] Zee Elkaseem: πŸ‘­ *AUREN TAGWAYE* πŸ‘­
πŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•Έ
πŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•Έ
πŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•Έ
πŸ•ΈπŸ•Έ
πŸ•Έ
*Written & Story by*
*Zee Elkaseem*
*{Mmn khady}*



*Dedicated to All member's group of Ciwon "ya mace* πŸ‘©πŸ»



Page......................16


Saboda haka cike da tunani barkatai jabeer ya isa gidansu, 'kanwarsa Nusaiba yafara gani zaune falo tana kallon wani Indian film me suna salam namaste, da sauri ta tarbeshi tanamashi sannu da zuwa, bayan ya amsa d'akinsa yanufa ya ajiye jakarsa sannan ya dawo falon, har yanzu dai nusaibar ce ita kadai a falo tambayarta yayi "ina mama?
"Tana bedroom,
"Owk kawai yafad'a tare da nufar 'kofar dazata sadashi da d'akin kwanan mahaifiyar tashi, da sallama yashiga d'akin zaune ya isketa gefen gado hannunta ri'ke da waya da Alama waya tagama, kallonshi tayi bayan yasamu guri ya zauna kan bedsite "a'a jabeer yanaganka kadawo tun yanzu ko mantuwa kayine?
"A'a mama ba mantuwa nayiba wani babban Al'amari ya maidoni Wanda ni kaina ya d'auremin kai,

"Wannan wane Al'amarine tafad'a tare da maida duka hankalinta gareshi,
"Watako yanzu danaje office shine Alhj yakirani yake cemin inje insanarda magabatana kuma inbada kud'in sadaki naira dubu hamsin

Please Login or Register in order to submit comment