Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE



You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

irin mutum ne mara fasali sanin hakan ma ya samo asali ne daga bakin d'aya daga cikin yaransa da Allah ya bamu ikon kamawa a shekarun baya, shine yake sheda mana kammaninsa, a lokacin da al'amarin ya faru, banyi 'kasa a gwiwa ba na samu yaron daya haddace zane ya zana min kammaninsa domin samun sauki gurin binkice a kansa, amma abin mamaki! a yanzu wanda yake gabana a yanzu kuma muke hasashen cewa shine wanda muke nema ruwa a jallo kammaninsa yasha bambam! da wannan hoton zanen da nasa aka zana min a shekarun baya."

Mai girma governor yace." Asp ya akayi hakan ta faru? kana so ka sheda min cewa bashi bane."?

Ya mi'ke tsaye da wayar a kunnasa, kujerar ya janye ya fito daga tsakankanin kai tsaye inda yake zaune ya nufa!.......Yana wayar yana kokarin kwance masa fuska dake d'aure.

Tsaf ya warware d"aurin fuskar, idanuwansu suka hadu guri guda, kujera yaja ya zauna suna fecing din juna.

Ya cigaba da cewa." Gani gashi a halin yanzu kuma yanzu zan dauki hotonsa na turo maka dashi domin ka sheda maganata, amma duk wani binkice zanyi a kansa domin samun tartibiyar magana."

Mai girma governor ya sauke ajiyar zuciya da fadin." Okey to babu damuwa ina tsumayinka." sallama sukayi kafin ya kashe wayar, ya tsira masa ido! shima nasa idon ya tsira masa suka dinga kallon kallo suna nazarta juna, shi Asp din shine ya fara janye idonsa daga kanshi, ya jima kanshi a kasa kafin ya dago ya sake mai da idonsa gareshi yace." Inaso naji cikakken sunanka gami da jin asalin tarihin rayuwarka."?




*#500 via 0542382124...Binta umar gtbank, idan kati zaki tura ki min magana ta WhatsApp da wannan number... 07084653262........Mutanan Nijar ku tuntunbi wannan number....*
*22796074090* katin mov ko airtal.
[3/29, 8:15 AM] Surayya Dee.: *GOJE!*🏹
🐕‍🦺🐕‍🦺🐕‍🦺
_(SADAUKI OMAR RETURN👑💫_)

*BINTA UMAR ABBALE🍒*

*_MANAZARTA WRITERS ASSOCIATION🖊️📚_*
_____________________


FREE PEGE



*19&20*
Cikin tsantsar tashin hankali! da gigita suka gurfana a gabansa kafin su sheda masa abinda yake faruwa.............."Ya wani mike a fusace! tare da mi'ka tafkaken hannunsa wanda yatsun ke cike da zabban zinare da azirfa! wani irin bahagon mari! ya dinga kifa musu kafin ya sanya kafarsa ya tunkudesu duka suka fadi wanwar! a gurin. gabadaya suka
Sunkuyar da kansu, jikinsu in banda rawa babu abinda yake.

Ya takarkare! da karfi! ya kurma uban ihu!!! lokaci k'ank'ani gabadaya kaf yaransa suka kewayeshi! ya goya hannu a baya yana kai kawo a gurun!

Tsit! gurin yayi babu mai kwak'wk'waran motsi a cikinsu.

Lokacin da yake kai kawo a gurin kallonshi nake ina mamakin muninsa! baki ne sosai gashi gajere dab da kasa, yana da katon kai da tafkekiyar fuska, gabadaya hallitunsa masu girma ne bayan gajartar da yake da ita, bakinsa kato haka nan hancinsa kwala-kwala idonsa kadai ya isa firgita yaro! jajawur! dasu, kasumba tayi kaca-kaca a fuskarsa babu kyawun gani!
kallo guda za kayi masa ka tabbatar da rashin imaninsa.!

Cikin kaushin murya! ya fara magana kamar haka." A jinin jikina naji cewar akwai ayarin da suka shirya min! Yau tsayin sati guda kenan idan na kwanta bacci nake ganinsu a idona! babu wani shirinsu da zai firgatani! na shiryawa zuwansu! na kuma yiwa kaina alkawari cewa duk yawansu sai naga bayansu! babu wani mahalukin daya isa ya tunkari inda nake ba tare da she'kashi barzahu ba! nafi karfin hukuma! ballanatana wani dan adam! saboda haka dukkunanin ku na umarceku da cewa ku zauna cikin shiri babu wanda zai fita da rai a cikinsu."! jiki na tsuma! yake maganar yana wani irin huci! gabadaya ya burkice sakamakon jin abin da yazo masa a bazata!


********
Saboda tsabar kwarjin da yayi musu sam sun kasa hada ido dashi, suna gurfane a gabansa, yayin da shi kuma ke kai kawo a tsakaninsu kafin yaja tunga ya tsaya a gabansu, hannuwansa ya goya a baya, babu wasa ya fara magana kamar haka." "Ya sunanku."?
babu wanda yayi magana a cikinsu. Ya sake maimaita maganarsa! uffan basu ce ba.
Ya juya baya yana kallon jama'arsa dake tsatstaye kowanne a cikin shiri.

"Alba bani wannan dorinar." yafada yana kallonsa.
Da saurin gaske ya ciro bulalar daga cikin gidanta, kaurinta ya isa! nayi imanin za ta iya dauke fatar mutum.

Ya gyara rikonta a hannunsa, cikin wani irin hargagi! wanda yasa gurin amsawa! yace."Ba zaku bude baki kuyi magana ba ko."? Duk da sun tsorata da yanayinsa, amma hakan besa sun magantu ba.

Ya zabura! ya juya tare da kiran Alba! yana zuwa ya umarceshi da ya cire musu kayan jikinsu kaf!
Alba yabi umarni!

Ya kai ya kawo ya gurin jikinsa na wani irin karkarwa! tsumin ne ya tashi! ganin haka ya sanya wasu daga cikin yaranshi suka bara buga gangi!!! da bushe-bushe? Ya sake rikicewa! wani irin tafka! yake musu! suna ihu! da birgima a gurin!
Birgima suke a gurin suna gurnani! yana binsu da tafkekiyar dorinar dake hannunsa yana tafka musu, wanda ya janyo tsiyayewar idon daya daga cikinsu.

Hankalinta a masifar tashi taje tana kokarin rike masa hannu kuka take kariris! tana bashi hakuri sunyi bala'in bata tausayi! bata san bashi da imani ba sai yau!

Tureta yayi ta fad'i kasa ta rirrike kafafunsa "Kayi hakuri wannan rashin imani ne, ka zubar masa da ruwan ido ga jini yana fita a jikinsu kada kayi kisan kai." Wannan maganganun nata besa ya fasa abinda yake ba, ya sanya kafarsa ya taka gwiwar wanda yake kokarin gudu! ya murza da karfin gaske! wani marayan ihu! ya saki kafin ya zube a gurin yana karkarwa jiki yace." Yi hakuri kada ka kasheni zanyi ma bayani."

Ba tare da cire kafarsa ba, ya buga musu tsawa! da fadin" Ya sunanka."? baki na rawa yace." sunana Yakubu ." Ya kalli dayan da yake matagugu a kwance "Kai fa."? Yace." Sunana Sulaiman."

Kafarsa ya cire yana wani huci! ya barsu a gurin.......Saman wani icce! ya zauna! wasu daga cikin yaranshi suka bishi! da ruwa...

Wasu na masa fifita wasu kuma na kara kambaba darajarsa!

Nad'in kansa ya warware kafin ya sunkuya tare da bada umarnin a zuba masa ruwa a saman kan.

Ya dago kan yana girgije ruwan sumarshi mai laushi tabi ta kwanta tana digar da ruwa. Alba yasa abu yana tsane masa ruwan.

Har yanxu babu sassauci a tare dashi, idonshi na tsaye a inda suke. tana tsaye a gabansu, magana a suke a tsakaninsu amma basa iya jin abinda suke cewa.

Ranshi ya baci da ganin abinda take, yarinyar ta nema ta lalata masa aiki. mikewa yayi da bulalar a hannunsa ya karasa gurin, kallon mara imani take masa, za tayi magana kenan, a zabure! yayi kanta da bulalar!! ta matsa gefe da sauri! gabanta na bugawa! jajayen idanuwansa ya tsira mata cikin mashahuriyar tsawar data kusa sanyata sakin fitsari yace." Wuce ki bani guri."! kafafunta na rawa ta bar gurin, bai ta'ba firgitata ba kamar yau.

Ya kallesu kafin yace." Ku tashi tsaye! suka yunkura da kyar suka tashi! gabadaya jikinsu ya sauya kama saboda duka! yayi musu wani kallo kafin ya juya da basu umarnin bin bayansa.


Ba tare da iya kallon fuskarsa ba ya fara yi magana kamar haka "Aikinmu shine ta'addanci! rai ba abakin komai yake ba a gurunmu, sannan muna tarewa jama'a hanya cikin dare mu farauci dukkanin guzirinsu, muna rabasu da matansu da 'ya'yansu, mu kwanta dasu, kamar matan auranmu daga 'karshe mu 'kona gawarwakinsu ko kuma mu fito dasu kan hanyar mu yasar! duk wanda ya shiga komarmu bama saurara masa muna da muggan makamai kuma muna da daurin gindi daga sama, kamar yanda ka sani cewa masana sunyi hasashen cewa gurin da muke rayuwa akwai albarkar kasa, to tabbas hakane akwai! amma maigidanmu yaci alwashin cewa babu wani mahalukin daya isa ya amfana da albarkar dake wannan guri sai shi da ayarinsa, yawancin mu musulmai ne magoya bayanshi, amma ya haramta mana ibadah! bama sallah bama salati da duk wani abu da ya cancanta, burin mu ako yaushe mu kashe duk wanda yayi yunkurin shiga gonarmu, maigidanmu yaci alwashi mai zafi! akan duk wanda yayi yu'kurin ganin bayan rayuwasa." Ya k'are maganar tare da sake risinar da kanshi kasa.

Beyi mamakin da jin wannan jawabi ba, hausawa sukace da dan gari akan cin gari, a jawabin da sukayi masa ya fahimci cewa gabadayansu musulmai ne amma suka yarda suka bada goyon bayan ta'addanci a kasa.

Ya girgiza kanshi da fadin." Yakubu-Sule daku aka hada baki wani wawa! zindiqi! mushiriki! ya addabi! kasa da al'ummar dake cikinta, shin me kuke nema a duniya da har kuka mayar da zubar da jini! abin banza? a matsayinku na Musulmai masu amsa sunayen annabawa! shin ya cancanta ku aikata wannan ta'addanci."!

Gabadaya suka shiga girgiza, jikinsu yayi wani irin laushi, yaja numfashii ya fesar! kafin ya cigaba da cewa." Dukkaninku baku cancanta da cigaba da rayuwa a duniya ba domin barin irinku a ban 'kasa had'ari ne."!

Jin abinda ke fitowa daga bakinsa ya firgitasu, a tsoroce! suka shiga bashi hakuri suna kiran sun tuba!!

Wani mugun mari! ya kifa wa daya da jikinsu, 'yar hantsile yayi ya kifa yaci da kasa! tsaye ya mike! yana zagaye a kansu. gabadaya sun tsorata da yanayinsa, su kansu yaran shi basu taba ganinshi a cikin irin wannan yanayin ba, jikinsa in banda tsuma! babu abunda yake, Zinat kuwa addua take a zuciyarta kada Allah yasa ya aikata kisan kai!

Da jan ido ya kallesu, da fadin." *Ni! ne zan kawo karshen ta'addancinsa! *GOJE!!* *Nake mai maganin wani takadiri! Nayi tawa! nayi ta wasu! wannan haka yake! ba'a zubawa dani a kwashe lafiya! *Billahil-lazi hurramanu!* *nayi wa kaina alkawarin ganin bayansah"!* Yanda yake maganar yana zazzare ido shi tabbatar da abinda yake cikin zuciyarsa hakan yake babu 'karya!

Shar'bebiyar wukar dake rataye a kafad'arsa ya fizgo! daga gidanta, wani masifaffan ihu! ya kurma!!! kafin ya fara dadura! wukar a wuyansa!!
Tashin hankali kenan! gabad'aya gurin ya kacame! dan yaran sa ma manyan wukake! suka fito dashi suna gurzawa a kowane sassa na jikinsu! . shi kuwa a wuyansa yasa wukar ya zage karfi sosai! yake gurzawa.!

kuka wiwi! ta dinga yi tana kallon badakalar dake afkuwa, ita tsoronta kada su kashe kansu, ta rasa ya za tayi da rayuwarta a cikin wannan mashahurin dajin!

Tana kuka na fitar hayyaci ta karasa inda yake gabanta na lugudan duka! hannu na karkarwa take kokarin rike damtsan hannunsa, "Ka bari don Allah! ka daina! ka umarci yaranka su daina kada ku kashe kanku."!!
Ko sauraranta beyi ba ya cigaba da abinda yake, jikinta na wani irin rawa ta rumgumeshi tsam! tana kuka tare da dukan bayanshi. wannan ya janyo sadudarsa! ya cake! wukar! a gurin tare da danneta da tafin hannunsa!
Numfarfashi kawai yake gumi na yankowa daga kowane sassa na jikinsa!

Tsit! gurin yayi sakamakon umarnin da ya basu, suka mayar da wukaken jikin jikinsu.

Har yanzu tana manne a kirjinsa ta kam'kamshi shi da yayi wani motsi zata kai masa duka! kuma bata fasan kukan ba.

Hannu yasa ya d'ago fuskarta, suka tsirawa juna ido! ya jima yana kallonta kafin yasa hannu ya goge mata hawayen da suke ta zuba! yayi namijin kokarin cireta daga jikinsa! ta sake kokarin rungumeshi! duk a kokarinta na hanashi aikata wani abun.
Hannu ya daga mata da ido! ya gargade ta, sai ta sunkuyar da kai! amma har yanzu bata dawo daidai ba.


Ya kalli Alba da fadin." Bani abun rubutu."

Da sauri ya fito da takarda da biro! ya mika masa.
A takaice ya rubuta."


_*(KA SHIRYA YAKI DA MAKASHINKA!!!)*_


Wanda yake da d'an sauran kuzari ya mikawa takardar da fadin." Sa'kona ne wannan kana isa ka bashi, cewa daga ni *MAKASHIN MAZA!*

Da kyar! ya mike ya kama hanya yana tafiya tare da waiwayen d'an uwanshi dake kwance cikin halin rai da rayuwa!


Koda ya karanta wasikar sai kawai ya fashe! da wata mahaukaciyar dariya! da mike tsaye tare da dukan! girkakken dutsen dake gabansa!

Hannuwansa yasa ya tallefe 'keyarsa! tare da sunkuyar da kanshi kasa!

Ya jima a haka kafin ya d'ago yana kallon yaranshi dake kewaye dashi, gabad'ayansu suma jikinsu yayi sanyi da wannan al'amarin.

Ya kalli Nuhu dake rakube! gabadaya kammaninsa sun sauya saboda wuyar da yasha, ranshi ya sake 'baci! kawai ba tare da kowa ya ankara ba, ya fille wuka! tana! walwali a wuya ya burma masa! a take ya fara shure-shure a gurin jini sai tsartuwa yake, kafin wani lokaci rai yayi halinsa!

Ya juyo kansu a sukwane! yana kallonsu da kwala-kwalan idanuwansa! Sun tsorata mutuka gaya da ganin tashin hankalin maigidansu.

*"Cike da cin laya yace."Kamar yanda na soke! wuyan wannan shashashan! to haka zan soke! wuyan wannan marakunyar yaron daya tunkari inda nake! Ni! nayiwa kaina wannan alkawari!! saboda haka zamuyi kwankwance! kafin mu afka inda suke da yak'i."*

Suka hada baki gurin fadin."Yanda kayi shine daidai maigida muna goyon bayanka ako wane yanayi."

****
Tun bayan tafiyar Nuhu! babu wani abu daya gilma, hakan besa sun saki jikinsu a gurin ba, sai da duhun dare ya shiga sannan suka fara neman abinda za su ci.

Ita dai 'ya'yan itacuwa kad'ai ta iyaci, tana zaune tana kallonsu sun tada wuta sai gashe-gashe sukeyi da kallon ikon Allah! da kudirarsa, ace wai mutum ya gasa majici gafiya da sauran dabbobi marasa kyau yana ci a cikinsa.

K'auri da karni! duk ya cika gurin! dole ta tashi domin sauya gurin zama, domin mutukar tana shak'ar hayaki da kaurin dake tashi agurin zata iya amayar da abinda taci.

Ido ya bita dashi! be dauke ba har sai da ta samu guri ta zauna can nesa dasu, inda Allah ya takaita akwai hasken farin wata a gurin.

Ta jima a zaune a gurin tana sakawa da kwancewa! sai yanzu ta san ya rayuwa take, ta taso cikin kulawa da gata da komai na jin dadin rayuwa, tunda take bata ta'ba tsammanin cewa akwai ranar da za tayi rayuwa mai muni irin wannan ba! babban tashin hankalinta rayuwa da d'an ta'addah! irin wannan, duk abinda yake a kanta bai janyo masa 'kima da mutunci ba, domin kuwa shine mutum na farko wanda yayi sanadiyar tagayyara rayuwarta, hakika ta tsorota da rayuwa da duniyar ma gabad'aya, A yanzu babban burinta ta samu ku'bta daga cikin wannan dajin, sannan tayi wa kanta al'kawarin ganin ta jefa rayuwarsa cikin kunci da tashin hankali kwantankwacin yanda yayi mata.


Saukar wani abu taji saman wuyanta, da sauri tasa hannu ta buge! ta mike tsaye! wata lafceciyar tsutsa ce ta fado daga saman bishiya.

Rintse ido! tayi tana kiran sunan Allah! kafin taji zirrrrrr a kan kafarta, tayi tsalle ta matsa gefe tana kallon gurin, ashe gabadaya gurin tsutsutsine suke yawo.

Jiki na wani irin rawa ta bar gurin, tana isa inda suke ta iske sunyi shimfida sun gatange gurin da itacuwa tare da rufe gurin da Net!

Tsayawa tayi a gurin ta kasa shiga, domin gabad'ayansu mugun haushinsu takeji! daga nesa ta hangoshi ya nufo gurin, d'auke kanta tayi tare da jan tsaki a cikin zuciyarta.


Koda ya iso gurin bece mata komai ba, ya kama hannunta! kallonshi tayi kamar za tayi magana sai dai tayi shuru, jan hannunta yayi suka shiga gurin.

Guri guda ya zaunar da ita, muryar rarrashi da kwantar da hankali ya aro yace." Ki kwanta anan gurin nayi miki alkawai cewa babu abinda zan bari ya sami rayuwarki."

A maimakon hakan ya faranta mata sai kawai taja masa tsaki! ta kawar da kanta tana zumbura baki!

Hakan da tayi ya bata masa rai amma sai ya danne! be dauki mataki ba ya fara kokarin barin gurin, ta bude baki da fadin." Mamugunci! insha Allah sai naga karshenka."

Maganar ta bashi mamaki mutuka! sai ya juyo da wani irin murmushi a fuskarsa ya nuna kirjinsa da fadin." Me yasa kike so ki kaga bayana."?

Ta zabura! da fadin." Saboda kai din azzalimi ne macuci.!!

Ya jima yana kallonta da mamakin furucinta" Saboda kai din azzalimi ne macuci."! to wai shin da take kiransa da wannan sunayen wane irin zalinci yayi mata tun farkon had'uwarsu?

Still murmushin ya sake kafin ya furzar da iskar bakinshi, cikin gaggawa ya fita ya bata guri domin yana ji idan ya kara second a gurun zai iya nakastata.

Ya jima yana fesar da hayaki kafin ya samu sassauci a zuciyarsa, zazzafar ajiyar zuciya ya sauke! yana me sake jin sautin muryarta na amsa kuwwa! a kunnanta a cikin kunnuwansa, tunda ya taso lokacin kuruciya da girma gwargwamaya yake da *Maza!* bai ta'ba sanya mata a cikin al'amuranshi ba, saboda sanin hallayarsu! yana da tausayi mussaman akansu amma baya yarda da raini daga garesu, mace daya ce yake jinta a cikin zuciyarsa, domin duk ta tara abinda yake da bukata, hankali nutsuwa ilimi tarbiya da sauransu, ita kad'ai! yake ji a zuciyarsa zai rayuwa mai tsayi da ita, ya kai ma'kura a gurin iskancin da yarinyar nan take masa, yana tausaya mata amma ya lura ita bata gani ta daukeshi a matsayin macuci! to yana ganin zai fita daga harkata domin ya samu zaman lafiya. tare da gudanar da aikin dake gabanshi.


*#500 via 0542382124...Binta umar gtbank, idan kati zaki tura ki min magana ta WhatsApp da wannan number... 07084653262........Mutanan Nijar ku tuntunbi wannan number....*
*22796074090* dala dari katin Mov ko airtal
a
[3/29, 8:15 AM] Surayya Dee.: *GOJE!*🏹
🐕‍🦺🐕‍🦺🐕‍🦺
_(SADAUKI OMAR RETURN👑💫_)

*BINTA UMAR ABBALE🍒*

*_MANAZARTA WRITERS ASSOCIATION🖊️📚_*
_____________________



*JAMILA MUHAMMAD-ALI*
_(( (MMN BOBO💞) )_
Ina gaisuwa gami da fatan alkairi, Nagode sosai da kulawa da shawarwari Allah ya raya zuria, ya jikan MAMA yai mata rahama🙏🏻


FREE PEGE
*27&28*
Ya jima kansa a 'kasa tun bayan 'kare maganar Asp din yake cikin nazari da tunani, kafin ya d'ago kanshi ya fara magana kamar haka............Sunana *UMARUL-FARUKU* Ni d'an asalin wannan jaha ne wato jahar katsina.".........Asp din ya kalleshi na 'yan sakkwani kafin ya mayar da hankalinsa kan takarda da biron dake hannuna, yace."Ina sauraranka." numfashi ya fesar kafin ya cigaba da cewa." Kamar yanda na fada maka hakane an haifeni a karamar hukumar malumfashi cikin wani k'auye mai suna *'Kafur* ban taso na iske mahaifiyata a raye ba amma na taso da mahaifina da kakata wacce ta zama garkuwa a gare ni, mahaifina asalin sunansa Tanimu, amma da yawa jama'ar gari sunfi kiransa da *mai jakai!* dalilin sana'arsa ta jidon 'kasa akan jaki domin siyarwa da masu aikin gini da sauraransu. mahaifina ya bani dukkanin wata kulawar da ta cancanta ya ilimatar dani ilimin addini daidai gargwado yanzu haka ina da izifi sittin na al'kur'ani maigirma, duk da acikin k'auye muke sai da yayi k'okarin ganin na samu ilimin zamani (boko) hankalinsa bai kwanta ba sai da na kammala 'karamar makaranta wato secondary school............bayan hakan sai ya fara koya min sana'a domin dogoro da kai, a lokacin dana kai shekaru ashirin da biyar a duniya sai tunani na ya sauya wani guri, a zahiri dai kowa ya sanar sana'ar mahaifina wato *Jaki da mangala* ban gaji farauta ba, amma sa'i guda na tsinci kaina dumu-dumu a cikin harkar, mahaifina baya so ko kad'an saboda yayi wa harkar mummunan fahimta, dalili duk wata nutsuwa da nagarta ina da ita, amma daga ranar dana fara harkar farauta sai wasu daga cikin dabi'una suka sauya, ni zanyi shedar kaina cewa tunda na fara wannan harkar ban ta'ba haura gidan wani nayi sata ba, ban kuma ta'ba tarewa wani hanya nayi masa k'wace ba sannan kuma ba'a ta'ba kamani da laifin fyad'e ga yaran mutane ba, wannan sune munanan laifukan da zan aikata a kira ni da wani mummunan suna! busa hakin sigari ko Shakar Shisha wannan sanya kai ne ga wanda yayi ra'ayin hakan. wannan dabi'ar da nakeyi sai ta janyo cecekuce da surutai a gari cewa na zama d'an iska takai ta kawo babu irin sunan da mutane basa kirana dashi, mahaifina ya d'au damuwar hakan yasa a cikin ranshi har ciwo ya kama shi wanda shine ya zama ajali a gareshi, lokacin da ya fadi ya mutu jama'ar gari suka dauki mutuwarsa suka ala'kanta ta dani cewar b'acin raina ne ya kashe shi, a duk lokacin naji wannan maganar hankalina yana tashi mutu'ka! ni dai na san babu wanda ya isa ya kashe kuma babu wanda ya isa ya raya sai Allah! amma jama'a sun juya maganar domin wani sa'in ma ita kanta kakata Uwale takan jefeni da maganar a duk sanda ranta ya b'aci dani.........Da yawa yawan mutane suna ganin rasuwar mahaifina zata karyar min da gwiwa na janye kudirina sai abun ya basu mamaki! domin ana adduar bakwai na cigaba da harkoki na! idan na fita farauta na kanyi kwanaki ko satittika a daji! kuma da ikon Allah na kan farauci duk abinda nakeso kuma nayi guzurin magunguna iri-iri! ba zance maka ga iya adadin mutanan da suka samu lafiya ta dalilina ba, ina kar'bar 'karamar sadaka na bada magani daga cikin irin ilhamar da Allah yayi min, wannan hanyar itace ta zama hanyar abincina, domin ko bana gari kakata takan bada magani tayi d'awainiya da kanta bayan 'yan sana'o'in da take........Tafiya tana 'kara tafiya ta kowanne fanni ana samun cigaba da tarin masoya da kuma tarin ma'kiya domin duk abinda zaiyi ba zai rasa d'aya daga cikin abinda na fada a yanzu ba, shekara biyar da ta wuce ina fita farauta ni kad'ai! cikin ikon Allah sai na fara samun magoya baya a hankali a hankali na tara jama'a da yawa wanda muke tafiya tare dasu wannan harkar! jama'ar gari suka dauke mu mutanan banza saboda muna yawo da karnuka bayan haka kuma shaye-shayen magungunan tauri da sauransu, yanda jama'a suke kallonmu muma haka muke kallonsu a hangunce! domin mu mun san bama aikata wani mugun aikin da zai janyo mana zubewar mutumci wannan harkar ba *Daba!* bace, ba kuma *Ta'addanci* muke ba, muna neman halak dinmu ne domin mu tsira da mutuncin mu." Cike da karsashi da kwarin gwiwa ya 'kare maganar!

Shuru ta ratsa gurin tun bayan 'kare maganarsa Asp din yake rubuce-rubuce yayi 'yan mintina a haka kafin ya d'ago kansa suka had'a ido! ya d'anyi murmushi da fadin." *UMARU-FARUK!* Maja ya'ki! ni Asp Musa Baharu! nayi imani da cewa babu *RAGO!* ga duk wanda ya amsa wannan suna domin Asali al'amarin ya dau'ko."

Murmushi yayi wanda ya tsaya kan fatar bakinsa......Asp din ya cigaba da cewa." Yanda kayi min cikakken bayanin tarihin rayuwarka cikin nutsuwa babu inda-inda yasa naji bana shakka a kanka amma ina so yanzu ma kayi min cikakken bayanin yanda akayi har ka samu nasarar shiga sansanin mutumin da jami'an tsaro suke shakkar tunkarar inda yake, hukumar tsaro tayi mutukar mamakin! yanda akayi kai da yaran ka kuka samu hanyar shiga wannan gurin, bayan baku da manyan makaman kare kanku."

Murmushi yayi wanda yake fito da zahirin kyawunsa ya tsira masa ido kafin yace." Me yasa kai ka yarda dani da sauri haka? me yasa har yanzu baka gazgata cewa Ni ne *UBAN DABA BA."?* Asp din yayi murmushi da fadin." Saboda sanin makamar aiki shiyasa kallo guda nayi maka na tabbatar da

Please Login or Register in order to submit comment