Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

ita ba,kamar yadda tayi amanna ba zata iya goga kishi da kyakkyawa kuma me aji irin qawarta unaisa diyar minister ba.

_ba'asan maci tuwo ba sai miya ta qare,muje zuwa_

**********Ƙarfe hudu na rana agogon turkey,biyu na rana agogon nigeria jirgin Turkish airline ya sauka a filin sauka da tashin jirage na malam aminu kano,dauke da tarin passengers,ciki harda jabir usma khalid akko da ja'afar marwan khalid akko.

Dukkansu sanye suke da wasu lafiyayyun Italian suit,kalolin da suka dace da gayu aji da kuma kyansu,duk wanda ya kallesu sai ya maida kansa ya dada kallonsu,zaratan fulanin samari guda biyu,wadanda ilimi hutu da kuma kudi ya ratsa kowannensu,jikoki kuma jinin khalidu akko.

Zaman jiran jirgin da zai tashi zuwa gombe sukayi,wanda duka duka bai wuce awa guda ba suka daga zuwa gomben.

Ta gefan idanu jabir yaketa karantar ja'afar tunda suka sauka a qasar,fuskarsa kadaran kadaham take,babu walwala hakanan ba wata fara'a bace saman fuskar tasa ba,hannunaa guda daya yana soke a aljihunsa,har zuwa sanda suke nufar motar da tazo daga gidan Dr marwan domin kaisu gida.

Muslimu driver din abbi shine yazo daukansu,cikin wata baqar range Rover,ko ba'a gaya maka kasan cewa sabuwa ce,sai qyalli take da daukan idanu,jabir yayi tsammanin samun masu tarbarsu bayan muslimun da zai tuqa su,saidai babu kowa saishi din,sai ya alaqanta hakan da shakkar ja'afar da sukeyi,don ba kasafai ko a baya zasuyi tafiya tare a samu masu tarbarsu ba.

Cikin matuqar girmamawa da jin dadin dawowarsu muslimu ya gaidasu,sannan ya sanya jakankunansu a mota,ya shiga ya tada motar suka dauki hanya.

Tunda suka hau hanyar idanunsa na bisa titunansu,yana qiyasta watanni da ya share bashi qasarsa,watanni ne masu dan dama,dashi kansa baisan gudun da suke ba sai yanzu.

Tazarar dake tsakanin gidan dr marwan akko da airport din ba mai yawa bace,dalilin da yasa basu dauki wani lokaci mai tsaho ba suka isa gidan.

Bin ginin gidan nasu yake da kallo kamar wanda a yau yafara arba dashi,ba komai yake kallo ba sai sabon fenti da yaga anbi gidan dashi duk da girma da fadinsa,cikin qanqanin lokaci yaji zuciyarsa na masa qunci,da gaske shirin bikin suke kenan,sai ya dauke kansa daga inda yake kallo din,ya sanya hannu ya bude murfin motar ya fito ya biyo bayan jabir.

Tun a harabar gidan tarin ma'aikata dake aiki a qarqashin gidan suka fara musu maraba,kusan da jabir ya barsu,dama shike da wannan juriyar,ya sanya kansa zuwa cikin gidan,a yau din da yake a cikin gidan,sai yaji wani irin kewa da zumudi mai yawan gaske nason ganin mahaifiyarsa ita da gudan jininsa amna,baisan yayi kewarsu kamar hauka ba sai yanzu da yake a kusa dasu.

Da tattausar muryarsa mai zurfin nan yayi sallama cikin falon nasa,haj aishatu dake nutse saman kujerun alfarma da aka yiwa falon nata qawanya dasu ta daga kanta daga duban farar takardar dake dauke da rubutu a hannunta tana amsa sallamar tasa,idanunsu suka gauraya da juna,ta saki boyayyar ajiyar zuciya mai nauyi

"Alhmadlh ya rabb" ta fada can qasan zuciyarta,sai ta dubi matar da suke tare

"Ki shiga ciki kice ina samra?,ta baki waje kici abinci,zan kiraki mintuna kadan" miqewa tayi tana godiya,sannan tabi hanyar da zata sadata da farfajiyar sassan haj aishatun da take kamae qaramin tsakar gida mai siffar garden da aka wadata da wasu fararen duwatsu na wuta.

Ci gaba yayi da takowa cikin falon,yayin da amma wannan karon tayi qoqarin ajjiye kunyar dake tsakaninsu

"Maraba lale,ashe kuna gab da isowa?" Wani dan qaramin miskilin murmushi ya subuce masa,ya qaraso gabanta ya zube ya soma gaisheta,tana amsa masa itama cikin kulawa tare da karantar yanayinsa.

Baiyi wata qiba ba sam,saidai jikinsa a murje yake kadan,sai kuma fatarsa data sakw fresh da kuma haske,alamin weather din qasar data karbeshi,akwai maganganu masu tarin yawa dake ran amma,saidai a yanzun kamar yayi wuri tace komai,don haka ta barwa lokaci na gaba idan suka gama warwarewa daga gajiyar tafiya.

Yadda ja'afar ya zube mata haka jabir,don marabarsa da ja'afar din daukan cikinsa ne na tsahon wata tara ne kawai batayi ba.

Kusan shi ya fara fita yabar jabiru da amma,wanda dama koda a baya abun kusan haka yake,hirarsu da amman bata qarewa,zaka sauka jabir ya haifa ba ja'afar ba.

Yana fitowa sukayi kacibus da ammi,kana kallonta kasan an fara shiga hidima,daga boys quarters na gidan take,taje ta duba yadda aka gyara gami da tsara wajen saboda saukar baqi 'yan biki.

"Oyoyo,saukar yaushe?,ina ta ciki ban jiku ba?" Murmushin gefan baki yayi,ya gaidata itama a girmame kamar yadda suka saba

"Me zakuci?,don gidan gaba daya a hargitse yake,banjin zaku samu kalar abincin da kuke so"

"Ki turo mana hisham kawai ammi" muryar jabir dake tahowa daga baya ta bata amsa,don yasan halim ja'afar din sarai,tsaf zai iya cewa

"We are okay" bayan shi magana ta gaskiya yunwa yakeji

"Banajin zaku samu hisham cikin gidan nan jabir,gidan yau kusan babu kowa sai baqi,yana can hidimar saukar nasu baqin"

"Ba damuwa zan kirashi" jabir ya fada suka soma gaisawa sannan shima yabi bayan ja'afar wanda ya wuce sassan anni,ammi tayi gaba tana tunanin abinda zata sa a samar musu me dan sauqi da zasu iya ci.

Sanda ya sanya kai falon har yayi kamar zai koma saboda muryoyin baqi da yaji sai kuma yaci gaba da cusa kai,sai daya shiga din sannan ya fuskanci su waye a falon,anty maama ce,sai ummi badi'a matar uncle abbas.

Qaramin tsaki yaja qasan ransa,su kadai amma sun cika falon da hayaniya kamar mutum dubu,dukkansu maraba suke masa banda anni da taja bakinta ta tsuke,ya qaraso ya zauna saman hannun kujera yana amsa marabarsu,kafin dukansu su biyun su miqe anty maama tana cewa

"Anni bari muje,nan da awa biyu idan bamu dawo ba don Allah hayatu ko muslimu suje su debomin yaran nan"

"Zan gaya musu,amma kada kuje ku zauna kuma"

"Muna samo abinda mukeso zamu dawo"

"Allah ya tsare" suka amsa suna ficewa,sai falon ya rage saura shi da annin.

"Barka da warhaka" ya fada cikin rusunawa
"Barkan ka" ta bashi amsa a taqaice tana bata fuska,saidai a yau din baiji bata fuskarta ya dameshi ba kamar yadda suke da ita a baya,yana jin a wannan bigiren shi yafi cancanta ya bata fuska akan kowa

"Ina wuni?"
"Daban wuni ba zaka ganni?,ai da zamanka kayi a sassanka,ni yafi cancanta nazo na gaisheka ai,tunda yanzu ka zama uban kowa,sai abinda kakeso ka tsara zamu dinga bi,tunda kaika haifi kanka" kyawawan idanunsa ya lumshe kana ya budesu,ita tsohuwar batasan abinda yakeji bane?,batasan irin qunci da ciwon data haddasa masa ba haka siddan yana zaman zamansa yana lallaba rayuwarsa?

Muryoyin sallamarsu ta katse anni daga ruwan tijarar data debo ta shirya sauke masa su tas yau a kansa,duka 'yammatan gidan ne suka shigo,wansa dawowarsu kenan daga gyaran gashi.

Da hayaniya suka shigo saboda yadda sabgogin bikin suka fara musu dadi,amma suna hada idanu kowacce sai tayi turus,ta kuma saita bakinta,kudin goro ya yiwa gaisuwarsu ya amsa su gaba daya,babu wadda tayi gigin zama dukka suka juya suna barin sashen,daidai lokacin da amna wadda aka yiwa kanta gyara na musamman take rugowa cikin falon riqe da leda a hannunta cike da kayan qwalam tana qwalawa anni kira gami da cewa tazo suci.

Cak ta tsaya sanda tayi idanu hudu da mahaifin nata,sai kuma ta watsar da ledar hannun nata,ta take da gudu tayo wajensa tana kiran

"Dadddyyyyy...." Qasa ya sauko ya tanqwashe qafafunsa,ya kuma bude mata hannayensa gaba daya,yana jin wata irin qauna da qarfin jini dake tsakanin uba da diyarsa yana fusgarsa,ta kuwa iso ta fada jikinsa,ya sanya hannayensa gaba daya ya rungumeta cikin jikinsa yana sauke ajiyar zuciyaSosai ta qanqameshi itama kamar zata koma jikinsa

"Daddy" ta sake kira tana sauke ajiyar zuciya bayan shuru da tayi na wasu sakanni,dukka gaba dayansu shida annin sai tausayinta ya lullubesu,ya dagata sosai ya sake tallafarta yana dubanta

"Amnee" ya kirata da sunan da shaheeda kadai take kiranta da shi

"Daddy....kaima shine ka tafi ka barni?,mommy ta tafi,amra ta tafi,kaima haka?" Kai ya girgiza yana shafa sumarta da tasha gyara tana ta qyalli

"Am sorry my little angel......daddy yana neman afuwa,bazai sake tafiya ya barki ba" fuskarta ta washe sosai,da alama taji dadin maganarsa,sai kuma ta sake cune fuska

"Adda maimoon ma ta tafi,har yanzu bata dawo ba,daddy zaka je ka dauko min ita?" Anni ya kalla da alama yana da buqatar qarin bayanin sanin wacece ita,kamar kuma ya jijji sunan a bakin annin da ammansa,ganin anni bata bashi wani hint da zai gane wacece ba sai ya gyada kai kawai

"Zan dauko miki ita lil princess" qanqameshi tayi tana murna

"I love you daddy"

"Love you more amne na" sai ta shige jikinsa tana sauke ajiyar zuciya dake nuni da samun cikakkiyar nutsuwa.

Karamin tsaki anni ta sake

"Kalli.....wannan daukar hakkin har ina?,Allah ya kyauta wannan banzar zuciyar taka data kasa daukan kalar tata qaddarar" bai tankawa annin ba,don yasan jiqaqqiya ce tsakaninsa da annin,kuma ba zata qyaleshi ba tabbas sai ta maida masa kai tsaye ko kuma a fakaice.

Koda ya tashi tafiya qin yarda amna tayi ta sauka daga jikinsa,tana maqale dashi,da ita yatafi sassansa,ya samu.jabir har ya fito a wanka,yanata fama da wayoyin al'umma.

*_GARZAYA KI BIYA NAKI KUDIN KAN FARASHI KAMAR HAKA_*

Biyar:::1k
Hudu:::700
Uku::::500
Biyu::::400
Daya:::300

*_zaki saka kudin ta wannan account number din_*

HAFSAT UMAR KABIR
2270637070
Zenith bank

*Saiku tura shaidar biya zuwa ga*
07040727902

*IDAN KUMA KATIN WAYA NE ZAKU TURA TA NAN TARE DA SHAIDAR BIYAR*
09134848107

*_THANKS FOR CONTINUES PATRONAGE_*🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰

28

Wani kallo ja'afar ya watsa masa,da alama gayyar al'umma yayo musu,wanda shi baisan da hakan ba,bai kuma shiryama tarbar kowa ba,dakinsa ya wuce ya sauke amna saman gadonsa,tana ta faman zuba masa surutu,labarai iri iri,a lokacin idan kaganshi kai baka ce miskilin ja'afar din nan bane,mai yawan dakiya tsare gida da kuma shan qamshi,duk yabi ya cika fuskarsa da fara'a,hakanan duk tambayar da amna tayi masa sai ya bata amsa,saidai da yake halin a jininsa yake,ba jimawa yaji kansa ya fara cakewa da surutun amnan

"Amnee.....pls be quiet for a while,ki huta kada maqogoronki yayi ciwo,zanyi wanka,idan na fito then sai muci gaba" kai ta gyada masa,sai dai tun bai gama fidda kayan jikinsa ba taci gaba daga inda ta tsaya.

Yana daga toilet din ma yana saurarenta,murmushi kawai ya saki ya girgiza kai

"Surutun waye tayi haka?,shaheeda?,nooo....shaheeda nada hira,amma bata da surutu me yawa,salma?,laila?,hafsah?,maybe ya amsawa kansa da kansa yana tabe baki.

Sanda ya fito ya taddata da jabir,da yake shi din sarkin yara ne ya biye mata sosai sunata sabgarsu,sai ya juya ya buda walking wardrobe dinsa ya shiga yana duba kayan da zai saka,kafin ya futo sun fita,sai ya fasa shirin fitar da yayi niyya,ya saka boxer dinsa kawai ba tare daya nema ko singlet ba,turarukansa ya fesa,sannan ya shafe lallausan baqin gashin dake cike aqirjinsa wani irin azababben oil perfume,yabi lafiyar gadonsa ya kwanta,bayan ya ragewa dakin haske ta hanyar sauke duka labulayen dakin,ya kuma kashe duka fitilun dakin.

Bacci yayi sosai mai wani irin nauyi da dadi wanda ya jima baiyi irinsa ba,knocking da ya dinga ji sama sama cikin barcinsa ya sanyashi bude kyawawan idanunsa da suka qara girma saboda bacci,yadan mutstsukasu kadan,sannan ya ture lallausan duvet din daya rufe jikinsa dashi,ya zuro qafafunsa qasa yana miqewa,ya isa qofar ya bude.

Jabir ne dauke da amna,kwalliyar jikinsa ta bambanta data dazun

"Wanne irin bacci kake?,ko a masallaci ban ganka ba"

"What?" Ya fada calmly,ya aza idanunsa ga agogo,sai yaga har bakwai tayi,a hanzarce ya saki handle din qofar ya shige toilet don ya daura alwala.

"Na shirya zan fita mukaci karo da abbi yana dawowa,yace na gaya maka yanason ganinmu after isha prayer" kai kawai ya gyada masa,yana budewa amna hannunsa,ta taho da hanzari tana ci gaba da zuba masa surutunta,tare da bashi labarin inda sukaje dazun,sai jabir ya miqe ya fita ya basu waje.

Yana shirin fita sallar isha din hisham ya shigo,cikin girmamawa ya gaidashi,ya amsa masa yana sanya qaramar hular tashi ka fiya naci saman sumarsa

"Ina kaje duka yau?" Kansa yadan shafa

"Ina da patient ne yau a asibiti da yawa da zan gani,so bayan kuma na gama dasu na wuce wajen gidan yaa jabir,na sallami companyn da suka zuba home decor na gidan" kansa ya gyada kawai,hisham din ya daukar masa abun sallah suka fito zuwa masallacin suna taba hira kadan kadan.

Sai daya sake komawa ya duba ammansa,sannan ya wuce sassan anni,ya nema abinci wajen baba tabawa,wadda dama tun da can gurinta ko wajen ammansa yake cin abinci duk gidan,to sassan amman nasa yaga ya soma cinkoso,bazai iya tsayawa karbar komai na sassan ba,don bashi da tabbacin amman itace ta girka duk abinda za'a bashin.

Yana ankare da yadda annin keta faman cin magani,sai shima ya basar kamar bai gani ba,ya zauna sosai hankali kwance yana cin abincinsa,cokali daya bakinsa,cokali daya bakin amna hira,duk tabi ta cikashi da zancen adda maimoon,kome yayi mata sai tace 'haka adda maimoon takemin'.

Yana gamawa cikin sa'a yaji shigowa abbi,don haka ya miqe yana dauke da amna

"Kaje ka dawo,kazo muyi lissafin kudin kayan lefen da maama ta ranta maka ka zube mata abunta"

"lefe?,lefen wa?"

"Au da tattabaru kayi zaton za'a aura maka?,ko kuma babyn roba na wasan yara?,'ya'ya ne kamar kowa masu gata,ehe" anni ta maida masa amsa sannan ta fuske,sai kawai ya juya baice da ita komai ba ya fice,yana jin haushi yana sake cika masa zuciya.

Da sallama ya shiga katafaren falon dr marwan khalid akko,can ya hangesu saman dining shi da jabiru,da alama zamansu kenan,yayi masa izinin ya qaraso,yana jawo kujerar sake daura dashi hadi da nuna amna yace ta zauna,tayi daraf kuwa fa haye ta fara masa surutun nata,har sai da ja'afar yace cikin lallausan muryarsa,very calm

"Amnee,pls....keep quiet" narai narai tayi da idanunta,don bata gama bawa daddy dr kamar yadda take kiran abbi ba labarin da take bashi,to amma ita kanta duba daya uban nata yake mata take laushi,dole tayi shuru,ta fara saka yatsanta tana dangwalan romon pepper soup din kifi da aka yiwa abbi.

A sannan ya samu suka gaisa da abbi din,ya musu maraba,sannan ya tura masa warmers din yace ya diba abinci yaci

"Am full abbi,yanzu na gama ci wajen anni"

"Yayi kyau" yace yana ci gaba da cin abincinsa,sai dinning din yayi shuru,kasancewar dabi'ar abbi din,ba kasafai yake cin abinci kuma yana magana ba,har sai ya kammala,shurun da ya sanya ja'afar ciro wayarsa,yanajin abbin da jabir suna magana jefi jefi,wanda kusan duka kan tsare tsaren bikinsu ne.

"Bismillahi" abbi ya fada yana zama saman kujerun falon,yayin da jabir da kuma ja'afar kowanne yayi matsugunni a qasa

"Kai jabir alhmdlh,mun gama duka maganar da zamuyi dakai.....am ja'afar,abinda yasa na kiraka" abbi ya fadi yana gyara zamansa sosai,gami da cire hularsa ya aje gefe

"Inason in tambayeka......wacece ta haifeni?" Girma maganar ta yiwa ja'afar sosai,har sai daya dago suka hada ido da abbi,kana ya maida idanunsa qasa

"Anni ce abbi"

"Ma sha Allah,to ban sani ba,ko ka manta ne,dani da umar da sagir da abbas da usman.....dukkaninmu anni ce ta haifemu,kuma qarqashin ikonta muke damu da dukka abinda muka mallaka,ba zanyi magana me tsaho ba,saboda nasan kasan matsayinta a wajenmu,hatta da mahaifiyarka zabin anni ce idan baki sani ba,shi yasa ta zamto ta musamman a wajena,na kuma yi dacen da maza dubu basuyi ba,dukka hukuncin da anni ta yanke a kanka yatabbata,kuma ba komai bane ya janyo hakan ba ina da.imanin qauna ce da kuma damuwa da halin da kake ciki,Allah yayi maka wata iriyar zuciya data banbamta data kowa,amma ka sani,jajircewa da karbar al'amura a yadda sukazo suna iya kawo sauyi,hakanan lokaci yana iya warkar da kowanne irin ciwo komai girmansa,duk wani abu da zakayi a yanzu akan aurenka shizai nuna dai dai matsayin anni a wajeka,idan ka wulaqantata ko ka watsa mata qasa a idanu to ni ubanka marwan ka yiwa haka,idan ka karba abun da kima da mutunci,ka kuma riqeshi da daraja to ni ubanka marwanu ka mutunta,saboda haka zabi ya rage naka,dan halak dai shike rama halacci,anni kuwa halacci tayi maka ba butulci ba,zanga dame zaka sakawa mahaifiyata".

Maganganu ne gajeru marasa dogon zango,saidai nauyinsu yafi qarfin wani ma'auni ya iya gwadasu,shigen shigen magana irin wannan bata taba hadashi da mahaifinsa ba sai a wannan karon,nauyin maganganun da har dr ta sallamesu basu bar dukan sassan jikinsa ba,har sun kusa fita ya sake kiransa

"Ka shirya daga yau zuwa gobe,kaje gidan minister ka gana da unaisa"

"Unisa?" Ya fada cikin ransa,yana jin he knew the owner of the name UNAISA,to amma a ina?, somewhere..... somewhere,for sure,indai gidan minister ne,bu he may not remember ainihin inda yasan ta din.

Dukka wannan shi da zuciyarsa yake wannan tadin,wanda tuni ya riga yace da abbi "To" yabi kuma bayan jabir sun fice.

"Ya?,yau din zamu wuce?,don inason naje naga fatima gaskiya,i missed her badly" yana jin iya maganarsa ta yau ta qare,so saboda haka bashi da abinda zai cewa jabir din,saidai ya masa wani kallo,yana shirin yi gaba jabir din yasha gabanshi

"Shawara guda daya J.pls and pls,kayi qoqarin bin maganar abbi,indai har kai din masoyin shaheeda ne da gaske,na tabbatar da tana raye itace mutum ta farko da zata fara tursasaka kabi abinda dukka magabatanka suke so,for the first and last time may be da sukeso kayi musu wani abu cikin rayuwarka,we will see if you can do it" jabir yakai qarshen maganar yana duba yanayin ja'afar,duk da cewa ya bashi baya,kamar yadda ya zata din,baice masa komai ba sai gaba da yayi ya barshi a wajen.

Sassansu ya yanke ya koma kawai,saboda kansa gaba daya ya gama daukan zafi,tako.ina abbi ya gama daureshi,tun jabir baice komai ba dama ya riga daya yankema ransa dole ya tsaya ya fuskanci komai,zaiyi duk yadda abbi da anni keso for the sake of them.

Ya jima a haka kafin yayi qoqarin dai daita nutsuwarsa,ya daga waya ya turama hisham tex kan ya kawo masa amna,ba jimawa sai gashi da ita,ya dire masa ita ya juya.

Jaka guda ta kayan wasan daya jima yana siya ya tura mata,duk sanda ya fita yaga wani abun wasa saiya tuna da ita,sai kuma ya siya ya ajjiye,murna ta ishi amna,ta dauki wancan ta ajjiye,ta dauko wannan ta ajjiye,komai sai data nuna masa,kamar ba shi ya siyo ba.

A gaba ya sanyata yana kallo kawai,iya wannan farincikin nasa ya sauke kaso mai yawa daga cikin nashi bacin ran,abu na qarshe da yarinyar ta fada shi ya tashi zaman nasu,ya kuma dawo da mutuwar shaheeda da twin sister dinta amra danya a ransu duka su biyun,kewa da maraicin shaheedan ya kamasu

"Daddy.....mommy taqi dawowa,taqi kawomin amra muyi wasa,daddy yaushe zasu dawo?,zanyi fushi fa daddy" cikin jikinsa ya rungumeta,yana shafan gadon bayanta

"Kada kiyi fushi,kita musu addu'a kinji?,zamu hadu dasu in sha Allah sooner or later"ya fada yana qoqarin hadiye wani abu mai tauri daya tsaya masa a wuya.

Ta jima a haka kwance a jikinsa,yana jin yanayin saukar numfashinta da yadda ta qara nauyi a jikinsa ya tabbatar tayi bacci,sai ya miqe sabe da ita,daya hannun nasa kuma yana riqe da jakar kayan wasanta yayi sassan ammansa da ita.

Yana shiga tana shigowa itama falon daga ainihin qofar baya na sassan nata da zata sadaka da masaukin baqi na gidan,ita da masu aikinta su biyu,lili da laraba,suna dauke da jibga jibgan duvet da ana fiddosu yawanci a lokacin taro irin wannan musamman saboda baqin.

Jikinta sanye da Egyptian hijab daya saukar mata har qasa,duk da dare ne amma akwai eye glasses tare da ita,wanda takanyi amfani dashi lokaci lokaci idan taji bata jin dadin idanuwanta.

"Karbeta lili,ki kaimin ita dakina,idan kin shiga ki rage qarfin acn nan,don naji kaman mura nason kamata" a ladabce ta amsa,ta dauki amna da ja'afar ya shimfide mata saman kujera ta wuce ciki

"Manya" ta kirayeshi da sunan da takan kirashi dashi don ba kasafai zakaji ta kirayi sunan nasa kai tsaye ba

"Zauna muyi magana" kamar yadda ta umarceshi haka yayi,ya koma ya zauna din yana bata hankalinsa

"Kayimin wata alfarma man" sosai yake duban amman tasa,abinda yasa ta fahimci tambaya yakeson yi kan alfarmar data ambata

"Don Allah na roqeka,ka daure ka karba qaddararka a duk yadda tazo maka,kada kayi wani abu da kasan cewa ba dai dai bane,ka riqe amanar da aka baka bisa gaskiya da na sanka da ita,don Allah"

"Ku daina roqata hakanan amma,kunfi qarfin haka a wajena" ya amsa mata yana bata assurance din haka ta cikin qwayar idanunsa,ta san yana da qoqarin bin umarnin na sama dashi daman,saidai sanin halinsa yasanya mata shakku kadan,amma a yanzun hankalinta ya gama kwanciya gaba daya

"Allah yayi ma rayuwarku albarka,shikenan sai da safe"

A daren gaba daya ya gama lissafa yadda zai tafi da komai,yadda zaibi umarnin mahaifansa ta gefe guda ba tare da rayukansu sun baci ba,hakanan ba tare kuma da matan da aketa qoqarin liqa masa sun dameshi ba,don haka a washegari bayan ya shirya ya fito,ya nema ma'aikata daga cikin kamfaninsa,ya tsara musu abinda yakeso.

Cikin gidaje hudu da yake dasu ya zaba daya,wanda yake dan nesa kadan da nasu gidan,yasa aka hau aikinsa baji babu gani,don dama gidan kusan an gama komai nasa,fenti da saka qwayaye da sauran kayan qawata gidanne kadai ya rage,abinda yasa yayi saurin yin hakan,don bayason abbi ko anni wani yace su zauna a ainihin gidansa dakegovernment house road,don yafi kusa da nan gidan nasu,gidane iya gida,wanda ya amsa sunansa,kuma ya ginashi ne musamman a sannan saboda shaheeda,a sanda ta haifa masa twins,ya zuba musu komai da komai,sanda zasu tashi zuwa gidan suturar jikinsu kawai suka dauka,kuma ko bayan rasuwar shaheedan babu abinda ya bari aka taba cikin gidan,hatta da suturarta,da anyi maganan kwasan wani abun sai a rasa kansa,sai aka yanke shawarar a jinkirta ko yana kan tsinin zafin mutuwar ne,saidai har kwanan gobe komai yana nan a muhallinsa,a baya cikin gidan yake rayuwarsa,saidai yadda yake dada komawa yasa anni ta yanke shawarar ya tattaro ya dawo gida cikin jama'a,a kulle wancan gidan ko za'a samu sauqin wasu al'amuran,an dan samu din,saidai babu abinda ya canza shaheeda daga zuciyarsa har kwanan gobe ita da amransa *SO
DOWNLOAD
DOWNLOAD

2 Comments On GURBIN IDO
avatar
salima

12 months ago

Reply

Nice story

avatar
ibrahim-6-8

9 months ago

Reply

That's so amazing

Please Login or Register in order to submit comment