Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

asara ba bare haquri da ita idan ta sameta,haka ta dinga kai kawo har haihuwar ta kammala.

Saman dan dutsen da himun ke zama ko yaushe idan yazo ta koma ta zauna,idanunta nakan abun hannunta na shirin duwatsu green da jaa,tasa yatsanta guda daya tana wasa dasu,ta warasu wani lokacin ta hadesu,tana tuna lokacin da innarta ta zura mata su,har yanzu lokacin yaqi bacewa cikin idanunta.

Ta jima zaune a nan,tana jin wata kewa da kadaici suna shigarta,lokaci lokaci tana daga kai ta dubi yanayin yadda dabbobin ke kai kawo sannan ta sake maida kanta.

Karo na qarshe data daga kanta ta tabbatar lokaci yayi da ya dace su koma gida,ta sauka daga kan dutsen a hankali,ta gyara zaman hularta sannan ta dauki sandanta ta fara ratsawa ta tsakaninsu tana hada kansu.

A gaba take sanyasu mafi yawancin lokuta,idan taga zasu canza hanya ko zasuyi wani abu ba dai dai ba takan tsawatar musu,suna ji kuma suna fahimta yawancin lokuta,yau dinma haka ne,hannunta na dauke da sabuwar haihuwar da daya daga cikin shanun tayi.

A hankali baqaqen lafiyayyun motocin guda biyu ke kutsowa cikin rugar,tana haura duk wani tudu da kwari da kuma kwazazzabo dake kan hanyar ba tare da mutanen dake ciki sunji komai wata jijjiga ko wahala ba da ire iren wadan nan hanyoyin ke dashi a duk sanda mota zata ratsasu ba,hakan ya faru ne sanadiyyar kyau da lafiyar motar,wanda hakan yake da nasaba da irin tsadar da kowacce mota guda daya ke da ita.

Motar farko mutum hudu ne a ciki,driver salmanu,sai wani zaune a gefansa hayatu,daga seat din baya kuwa dattijuwar macace,hakimce cikin shiga ta alfarma,kyakkyawar lallausar blueblack din atamfa ce wadda tayi matuqar haska farar fatarta,duk da akwai tsufa tattare da ita,amma yanayin da take ciki na hutu da kuma jin dadi ya hana bayyanuwar tarin shakarunta,daga shekara sittin da takwas,ya maidata zuwa 'yar shekara hamsin,idan ka cika qwaqwafi kuma ka qara mata da uku,hankalinta na ga window din motar,tana duban hanyoyin da suke wucewa,wanda sukanyi gamo da mutane jifa jifa,duk mutumin da suka gifta sai ya bisu da kallo,saboda abune baqo a wajensu,zasu iya irga sau nawa suka samu labari ko sukaga shigowar mota rugar tasu,wasu sukan cika da fargabar su waye suka shigo musu?,wasu kuma kyau da motar ke dashi ne yake daukar hankalinsu har sai tayi nisa ta bacewa ganinsu.

Daga gefan dattijuwar kuwa kyakkyawar matashiyar budurwa ce wadda duka duka ba zata haura shekara ashirin ba a duniya,shigarta kadai zai gaya maka cewa ta fito daga gidan ilimi wayewa da kuma wadata,kacokam ta tattara hankalinta ga wani littafi dake da shafuka masu dan dama,da alama nazari takeyi.

"Salmanu........saukemin gilashin nan.....naga alama wannan baqin abun da kuka lafta masa bazai bar idanuwa suyi kallo yadda ya kamata ba" ta fadi tana hade gira.

Karaf matashiyar ta daga kanta daga kan littafin

"Haba anni....me kuma za'a sauke miki kiji?,an kunna ac ne fa,ta yaya za'a sauke glass,kuma ta hakan ma ai ana ganin komai,tunda ba dare bane" harara ta juyo ta watsa mata

"Ke....kiyi ta kanki,ni ba dake nake ba,toke da wanne mataccen idon ma kike iya gani daga nan din?,idon da komai za'ayi saida gilashi?,salmau zaka saukemin ko kuwa?"

"Za'a sauke anni" yayi maganar yana sauke mata da hanzari kamar yadda ta buqata.

Sai da aka sauke mata gilasan tas sannan ta sake matsawa jikin window din tana fara'a

"Yawwa,yanzu naji batu,amma daa an qunshe mu kamar 'yan kidnapping,ni ba baqin hali gareni ba da kullum xan fita zance a rufeni cikin gilasai" sarai matashiyar ta fahimci da ita take,kuma idan da sabo ta saba ko kuma tace sun saba da halin anni,duk wanda ke zaune da itama ya riga da yasan halinta sarai,don haka sai ta maida mayafin da yake kafadarta zuwa saman kanta,ta kuma rufe littafin saboda hasken ya mata yawa,karatun bazai mata dadi ba ta maida jakarta,ta ciro wayarta a maimakon littafin ta soma qoqarin kunna data,saidai yanayin rashin network mai kyau ya hana wayar tata amfani,dole ta maidata itama jakar.

"Ma sha Allah,kai ma sha Allah,lallai na jima rabona da adamawa,wai" anni keta fadi,fuskarta na nuna alamun jin dadin tafiyar sosai.

A dan rude maimunatu ta maida hankalinta ga marabar hanyar da shanunta ke tsallakawa saboda jin wani sauti,hango motocin suna tahowa yayi matuqar daga mata hankali,na farko yadda zata tsaida dabbobin da sukayi nisa da tsallakawa ta bawa motocin dama su wuce,na biyu kuma motocin sunyi matuqar sanya mata fargaba da tsoro kamar yadda suka sanyawa mutanen da suka baro a baya,su waye a ciki?,me sukazo yi cikin rugar tasu?,wadanne irin motocine wadan nan da sam bata taba ganin koda me shigen kamarsu ba?.

Yadda suke sake kusanto inda suke ya sanyata yunqurawa da hanzarinta ta fara bawa dabbobin nata umarni da dukka salon da tasan suna iya karbar umarni da hani daga gareta,tanayi tana kutsawa ta cikinsu tare da dan daga muryarta.

"Kai salmanu......dakata" anni ta fada da sauri,idanuwanta suna sauka akan maimunatu,sosai ta zuba mata idanu cike da mamakin yadda take iya bawa dabbobin umarni da baki take kuma iya sarrafasu ba tare da takai duka ma ko daya daga cikinsu ba,idanun anni ya sauka ga dan qaramin dabbar dake hannunta,fari qal dashi sabuwar haihuwa,abinda yaja hankalinta kenan zuwa ga garken dabbobin,ta dinga binsu da kallo daya bayan daya

"Ma sha Allah,wadan nan dabbobin gaskiya na qwarai ne,sun samu kiwo da kulawar data kamata"

"Abinda nake fada a raina kenam hajiya yanxu hajiya,babban abun mamakin yadda qaramar yarinya kamar wannan take iya kula dasu gaba dayansu" cewar hayatu shima idanunsa akan maimunatu

"Bari hayatu,kaga inda ake mata,ba irin 'ya'yanmu ba cima zaune da komai suna zaune ake musu" anni tayi maganar tana tabe baki.

Dariya ce taso qwacewa matashiyar amma ta danneta,sai murmushi da ya fita a fuskarta,yayin da hayatu da kuma salmanu suka dan dara kadan,saboda sunsan da wadda take,a tsakaninsu suka dinga tattaunawa,har zuwa sanda maimunatu ta ratsa ta gaban motocin suka wuce da dukka dabbobin,tana dan duba da kuma waiwayen motar tana mamakin yadda suka dakata mata suka bata dama ta wuce.

Ajiyar zuciya ta sauke me qarfi bayan data tabbatar sun tsallake lafiya,abinda ya taba faruwa da ita shekarun baya bai sake maimaita kansa ba,wanda ita daya tasan bala'i da masifar daga fuskanta a sannan,har yanzu tana iya tuna sanda motar ta taho a guje,bata kuma damu data tsaya ba ganin dabbobi suna qetarawa,tana hango sanda motar ta banke dan dalonta da take matuqar ji dashi,ya zube a qasa jini na fita ta hanci da bakinsa,ta bishi da gudu ta tsugunna a gabansa tana kuma saboda ta tabbatar bazai tashi ba,taji mugun cin birkin da motar tayi,da fadan da wata murya ke mata tsaye a saman kanta,fadan da yafi kama da a dakeka a hanaka kuka saboda cikin xafi da fadar maganganu marasa dadi ake yinsa,abinda ya sanyata daga kanta ta dubi.mai maganar.

Kalmomin da zata gaya masa masu zafi take nema amma ta rasa,saboda ita din ba gwanar rashin kunya bace,bata ma iyata ba sam,to dawa zatayi bayan dabbobin sune qawayenta?,abu na qarshe da take ganin xata iya shine watsa masa harara gami da tsaki mai nauyi,kafin ta sauke kuwa aka sauke mata wani zazzafan mari da ya sanya wuta ta dauke mata gaba daya,ta daina gane komai,bata tashi dawowa hayyacinta ba sai bayan wani lokaci.

Ko a yanzun data tuna sai data runtse idaunta,tana tuna zafin marin saman fuskarta,abinda ya biyo baya kuwa ta gefan inna azaba ce ta cita mai yawa,bata damu da yadda fuskarta ta tasa ba saboda marin data samu akan abinda ita ke da gaskiya,ta tattara laifin gaba daya a kanta,tare d adora alhakin mutuwar dan maraqin saniyar a wuyanta.

Ajiyar zuciya ta sauke sanda suka iso gida,kamar kowanne lokaci ta daga murya ta sanarwa innar ta dawo,bata ajjiye dan jaririn a hannunta ba sai data qaraso ta miqa mata shi,bakinta har kunne,kai kace jika aka haifa mata na dan mutum

"Dama kinsan ta kusa sauka amma baki garzayo kin kirani ba?" Innar ta fadi haka cikin tuhuma,bata amsa mata da komai ba,itadai tana duqe tana daure wasu akuyoyi,banda abu irin na dan adam,ta samu uwa da dan lafiya,bata damu da yi mata sannu na wahalar datayi da naggen ba har ta sauka lafiya,ta buge fa tuhumarta,wanda tayi imani cewa inda ta barta a can ta taho kiranta wani abu mummuna ya faru,lallai ba zata daga mata qafa ba.

Tunda taji maimunatun tayi shuru tasan ba zata tanka mata ba,ita kanta ta santa da wannan halin,a wasu lokutan idan tayi mata irin hakan,yaxo akan gabar da take cikin fushi ko takejin haushinta,kamata take ta nada yadda ranta yayi mata suga.

*Daga yau free pages sun qare,paid pages zasu biyo baya in sha Allah,hanzarta biyan naki kudin koki bibiyemu ta shafukanmu dake arewabooks*

❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥

*_ZAFAFA BIYAR din samari ne a rayuwar INAYAH,kowanne a cikinsu akwai wani murdadden Al'amari da ya shata layi tsakaninsa da ita,wawakeken sirri wanda a koda yaushe take kiransa da SANADIN LABARINA_*

*_Amma babban abun mamakin a koda yaushe shine,ita dai tasan cewa BABU SO tsakaninsu MEYA KAWO SHI?_*

*_Duk da haka tana tunanin yun qundun bala ta fitar da FARHATUL K'ALB a cikin ZAFAFA BIYAR din samarinta,duk da batason su zame mata GURBIN IDO wanda har kullum ba ido bane_*

😄😄😄😄😄😄😄

*YA KUKAJI SALON MASU KARATU?*

*YADDA SALON YA BAMBANTA DAKO YAUSHE HAKA LABARAN SUKA BAMBANTA DA DUKKA LABARANMU NA BAYA*

INAYA(riba biyu)___mamughee

SANADIN LABARINA___Rano

BABU SO___Billynabdul

FARHATUL K'ALB___Miss xoxo

GURBIN IDO____Huguma

*ZAKI YARDA AYI TAFIYAR NAN BABU KE MADAM?*

*_GARZAYA KI BIYA NAKI KUDIN KAN FARASHI KAMAR HAKA_*

Biyar:::1k
Hudu:::700
Uku::::500
Biyu::::400
Daya:::300

*_zaki saka kudin ta wannan account number din_*

HAFSAT UMAR KABIR
2270637070
Zenith bank

*Saiku tura shaidar biya zuwa ga*
07040727902

*IDAN KUMA KATIN WAYA NE ZAKU TURA TA NAN TARE DA SHAIDAR BIYAR*
09134848107

*_THANKS FOR CONTINUES PATRONAGE_*🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰

*06*


"Alhmdlh" anni ta furta sanda motocin suka faka a qofar ginin gidan bappa labaran,mahaifi ga ibrahim,qafafunta ta zuro qasa tana fadin

"Hasbiyallahu la'ilaha illa huwa alaihi tawakkaltu wa huwa rabbul arshil azim" kana tayi bismilla ta yunqura,gaba daya qafafuwanta sun riqe,jikin tsufa ga kuma zaman mota

"Salmanu ku jirani,idan mun gama gaisawa inajin tare daku zamu fita can cikin gari na duba masauki" cewar matashiyar,dakatawa da tafiyar da anni keyi ta waiwayo tana yamutsa fuska

"Laila....me naji kina fada?,au dama ba rakiyar Allah da ma'aiki kika yimin ba?" Shaf ta manta da annin tana jinta,fuska tadan kwabe

"Kuma me nayi anni?,duk wannan dawainiyar?,ina cewa flight zamu bi kikace kefa sai mota,amma ban fasa rakoki ba"

"Yo rakiyar banza da wofi?,tunda ba zaki iya kwana a gidan ramatu ba" hannayenta laila ta hade waje daya

"Shikenan,zan kwana abar maganar" don sarai ta sani mitar annin ba abu bane me kyau ko dadi ba,duk da hakan taci gaba da takawa zuwa cikin gidan tana ci gaba da mitar,ta dauke kanta tana sake ajiyar zuciya,idanunta na sauka ga yaran da suka fara baibayesu suna kallonsu,sannan ta dubi su salmanu

"Kuyi tafiyarku kawai,amma ina buqatar ruwan sha"

"Akwai ai za'a samu" yahaya ya amsa mata,sai ta juya tana bin bayan anni zuwa cikin gidan.

Dai dai lokacin da yuuma ke qoqarin daura alwalar sallar magariba,wadd ta saba duk lokacin da tayi girki ta kammala,tana hadawa da alwalarta sanna ta wuce daki.

Cikin mamaki ta ajjiye butar data gama zubawa ruwa ta waiwayo da hanzari jin muryar annin

"Yafendo?,yafendo yau kuma ni kika tuna?" Yuuma ta fada cikin madaukakin farincikin da ya kasa boyuwa a fuskarta,kana ta kasa jiran qarasowa anni,ta taka da kanta ta cimmata a tsakiyar gidan

"Nice rahama,yau dai Allah ya qaddara ganawarmu,kimin aikin gafara" anni ta fada tana kama hannun yuuma,murmushi ya kuncewa yuuman,ta shiga marabtarsu,dai dai sanda aka fara shigowa da kayan amfani na abinci,wanda ya zamewa anni kamar ibada duk sanda zata ziyarcesu,takan sauke musu kayan abincin da sai su kusa shekara basu qare ba,mota biyu takeyi,daya ta kayan abinci,daya kuma wadda zata taho a cikinta.

Hajiya maryama wadda ake kira da anni,tamkar uwa take a wajen yuuma,saboda da ita da mahaifiyar yuuman 'yan mata zarr suke,'ya'yan yaya ne(namiji) da 'ya'yan qanwa,kakanninsu daya,a turance ake cewa(cousins),tun zamanin yammatanci akwai shaquwa sosai tsakanin anni da mahaifiyar yuuma,uwa uba sunansu daya,maryam da maryam,kakan yuuma asali dama bafullacene,mazaunun ruga,koda ya tashi aurar da diyarsa maryam saita auri jinsinsu,mahaifiyar yuuma a ruga tayi aurenta kamar yadda ta taso a nan,yayin da daya maryam din anni tayi aure cikin gari itama kamar yadda ta rayu a nan,saidai duk da hakan zumuncinsu bai yanke ba,duk sanda dama ta samu suna ziyartar juna su da 'ya'yansu,har zuwa sanda suka fara tara zuri'a,rayuwar mahaifiyar yuuma batayi tsaho ba Allah ya karbi abarsa,a sannan duka duka yuuma din bata wuce shekara sha biyar ba a duniya,sosai anni taso ta riqe yuuma ta kuma aurawa danta na fari,saidai kuma mahaifin yuuma yaqi bada ita,saboda ita daya ce 'ya mace a wajensa,dole ta haqura,taci gaba da kulawa da ramatu(yuuma) da kai mata ziyara har zuwa sanda aka aurar da ita ga bappa labaran,ita ta yiwa yuuma komai kamar diyar cikinta,saboda ita dinma Allah bai bata diya mace ba,sai maza da take dasu guda hudu.

Tun daga sannan takan ziyarci yuuma akai akai,ramatu yuuma ta zama 'yar gata,batayi kukan rashin mahaifiya ba ko kadan,saboda anni ta tsare mata komai,bata da matsala ta kowanne fanni na rayuwa,tun daga sutura zuwa cima,ko yaushe anni naka hanya wajen yo mata aike koda bata zo ba.

Sanda shekaru suka fara tafiya yuuma bata haihu ba hankalin anni ya tashi,ta kashe kudi sosai akayita duba yuuma,saidai ba wata damuwa data nuna wadda zata hanata haihuwa bare a maganceta,daga qarshe anni taso fita da ita waje,don tana cikin sukunin rayuwa sosai annin,dukka yaranta ba wanda bai zama wani ba cikin garinsu na gombe amma yuuma tace ta barwa Allah,kome za'ayi idan haka Allah yaso ganinta ba wanda ya isa ya canza mata qaddararta,hakanan dole anni ta haqura,da kanta yuuma ta baiwa bappa labaran shawaran qaro aure,da farko yaqi amma ta matsa ganin cewa shi ba abinda ya nuna bazai iya haihuwa ba,bai kamata ta rageshi ba,daga bisani ya haqura,ya laluba ya zabo karimatu mahaifiyar himu,sanda tazo gidan itama sai data shekara biyu sannan ta samu cikin Ibrahim,bayan ta haifeshin ma sai daya kusa shekara bakwai ta haifa safiya sannan xubaida,sai auta sadam.

Ramatu macace mai tsananin haquri da hangen nesa,ita kanta fureran tasan da haka,shi yasa itama take qoqarin kiyaye wasu abubuwan kada ta shiga haqqinta da yawa,saidai kuma Allah ya jarabceta da son 'ya'ya,sam bata iya yiwa kowa kara a kansu,tun daga sanda bappa yace zai dauki ibrahim ko safiya ya baiwa yuuma daadar himu ta runtse ido ta dunga diga rashin mutunci sai yuuma ta sake kiyayewa,kyautatawa da nuna kulawa da duk uwa zata yiwa danta idan ya ratso tsakaninta dasu tana musu,ta daukesu kamar yaranta,amma ta kiyaye duk wani abu da tasan zai bata ranta ko yaja musu cece kuce da furera,abunda yasa xaman nasu ya sake dadi kenan,zaman lafiya kuma ya wanzu tsakaninsu,duk da wani lokacin daadan himu kan dan taba,amma hausawa sukace idan kace wargi waje yake samu,kuma sai bango ya tsage qadangare ke samun qofar shiga,dole itama wasu abubuwan fureran ke kiyayewa.

Fadin irin murnar da yuuman a yau ta tsinci kanta ma bata bakine,saboda anni tadan kwan biyu batazo mata ba,ba kasafai yuuma ke zuwa wajen anni ba,saboda bappan mutum ne mai kulle sosai,itama anni bata zafafawa saboda tasan ya tsarewa diyarta komai,yayi mata riqo na amana bai barta ta wulaqanta ba,sannan ita annin a yanzu babu nauyin kowa a kanta,sakamakon mijinta ya kwan biyu da rasuwa,don haka kafin ma yuuma taje ita taje mata.

Yuuma bata dubi dare daya fara yi ba,haka ta tashi takanas ta yiwa anni sabon girki,cikin cimarsu ta fulani da tasan annin tafi so,a ranar kusan raba dare sukayi suna hira,sai gab da zasu kwanta anni tace da ita

"Wajen fa labaran nazo....."

"Lafiya yapendo?"

"Lafiya qalau ramatu,shanu nake da buqata zan qara cikin gidan gona ta,wancan yaron hamdan naso aikowa,naga zai batan lokaci nace gwara nayi tattaki nazo da kaina" murmushi yuuma tayi,tasan dramer din anni da jikokinta sarai,takan gani idan taje musu,annin irin matan nan ne da basa daukan raini,bata da haquri akan abinda tasan kan gaskiyarta take,amma tana da matuqar kirki da kuma tausayi

"Aiko dai bappansu gaba daya dabbobinsa na garin yayi kudu dasu,kwana goma yace zaiyi ya dawo kinga muna ta zuba idanu shuru,amma naji suna waya da himu yace nan da jibi ko gata zai dawo,saidai ko ki tsimayeshi,cikin rugar nan nasan zai duba miki irin wadanda kikeso din"

"Kash.....kuma sai da nayi wannan tunanin,amma bari mu gani,Allah yasa ya dawo kafin na wuce,don kwana uku zanyi,ranar litinin zan koma ga likitan qafata abuja"

"Har abuja anni?" Yuuma ta fada tana kama baki,baki anni ta tabe

"Ina zaman zamana rigimammen yaron nan ya hadani da zirga zirga,duk kusan qarshen wata sai yasa an sakani a jirgi ba gaira ba dalili na tafi ganinsa,nace ya canzamin ya kafe,wai duk nigeri shine lamba daya.....kijimin qarya ramatu" anni ta qarashe fada tana yatsina fuska da tabe baki.

Murmushi yuuma ta sake tana kada kai,tana matuqar sha'awar yadda suke kula da anni,tana jin cewa dama ace itama tana da arziqin da zata ramawa anni koda dan kadanne cikin irin alkhairanta gareta

"Tunda ya fada ai hakanne anni" kashingida tayi kan lallausan katifa da bargo da yuuma tayi mata shimfida da ita

"Ke rabu da shi ramatu,bokon tasu ma ta wannan qarnin tafi qarfin hankalinka,ke bakya ce sunyi muhammadiyya ba" anni ta fada tana fadawa wani tunani can,wanda har sai da yuuma ta ankara

"Yanzu anni har yau baki bar sana'a ba?" Idanunta ta bude sosai tana kallon yuuma

"Ramatu,kome arziqin mijinki jikoki da 'ya'ya kada ki kuskura kice zaki rabu da sana'a,duk tsiya naka naka ne,koda ba'a rageka da komai ba,amma naka yana da dadi" kai yuuma ta jinjina tana gamsuwa da zancan anni,tun tale tale anni bata saba da zaman banza ba,har kawo yau da babu abinda ta nema ta rasa,ko rai tace tana so idan ana siyar dashi za'a siya mata,amma bata daina nema ba,tana da makeken gidan gona,wanda tafi ji dashi fiye da komai nata.

Tun suna hira sama sama har bacci yayi awon gaba da anni,sai a sannan yuuma ta gyara nata wajen ta kwanta itama.

*_WASHEGARI_*


K'arfe takwas na safe yuuma ke dosar dakin daada dauke da turamen atamfa gudu hudu a hannunta da shadda ta maza yadi goma,sai takalmi na maza me kyau wanda ta tabbatar zaiwa ibrahim.

Da sallama ta daga labulen dakin daadar,safiya dake zaune tana shan kunu ta amsa mata tana gaidata,dai dai lokacin daada ta fito daga uwar dakinta tana daura zani,kafadarta saqale da hijabi.

Gaisawa suka fara yi da yuuma sannan ta'ajjiye mata kayan

"Gashi inji anni"

"Too.....anni bata gajiya,to Allah ya amfana ya qara arziqi" daadan ta fada cikin farinciki,mutum ce dake matuqar son ka yiwa 'ya'yanta alkhairi,safiya dake shan kunu tataso itama tana daga atamfofin tare da fadin

"Bara na zaba tawa kafin zubaidata iso ta dauke wadda tafi kyau......gaskiya anni nada kirki,bata gajiya" murmushi yuuma tayi ta miqe,har takusa da qofa ta juyo

"Af.....niko daada nace ba,ko ibrahim ya gaya miki inda yaje ne?,tun jiya anni keta tambayarsa,kuma kamar banga shigowarsa gidan nan ba tun shekaran jiya,abincinsa ma sai da safen nan na hada a dumame" tana shirin saka hijabinta ta amsa mata

"Eh.....na turashi gidan sukaina"
"Sukaina?" Yuuma ta maimaita a ranta cike da mamaki,saidai ba kasafai take magana akan wasu abubuwan da daada ke yankewa kan yaranta ba

"Ayyah...to Allah yasa zasu hadu,don jibi annin zata koma"

"Ba lallai gaskiya,inajin sati zaiyi acan kafin ya dawo"

"To ba laifi" yuuma ta fada tana ficewa,kanta ya daure tamau,sukainan yayar furera ce,bata da kirki ko kadan,masifaffiya ce ta bugawa a jarida,tana aure ne a wani qauye dake maqotaka da rugarsu,ta yaya za'a tura saurayi kamar himu gidan yayi kusan sati?,duk da itama tana da samarin yara kamarshi,amma kuma tafiyar ai ba ta radin kansa bane,kamar wani qaramin yaro?,da wannan tunanin yuuma ta koma dakinta,inda tabar anni da kuma laila wadda ke jira a kawo mata qosai da yuuma ta bayar a siyo mata,tace shi take sha'awa,tunda suka tashi da safen take jiyo qamshinsa.

Suna tsaka da hira daada ta shigo a shiryenta tsaf,suka gaisa da anni sannan tayi mata godiya daga bisani tace

"Zanje na dawo yuuma,ba dadewa zanyi ba" kallonta yuuma tayi cike da mamaki,ina zata da safen nan,uwa uba kuma ma kusan dokar bappa ce,basa fita unguwa a gidan matuqar ya tafi kudu irin haka sai ya dawo,kamar anni tasan tunanin da yuuman take sai tace

"Labaran ya sassauta tsaurin nasa kenan?" Tayi maganar tana dariya.

Kai daada ta kada fuskarta na nuna zallar damuwa

"Ko daya anni,dole ta kama na fita ne,zanje na yiwa wata yarinya data nacewa himu gargadi,waye zaiso hada iri da irin tsiya irin jaraba",laila dake dan sauraron voice note na watsapp ta earpiece din dake kunnenta sai ta zareshi,ta miqe ta zauna sosai tana kallon daada,saboda yadda taji maganar banbarakwai,ita kanta anni dake rayuwa cikin tsakiyar birni,cikin ahali da muhallin da wayewa da kuma boko suka yiwa katutu sai data ji maganar bawai

"Tooo....ikon Allah,to....abi a sannu dai,Allah ya maganta mana"

"Ameen ameen,sai na dawo"

"Allah ya kiyaye" yuuma ta amsa mata.

Shuru yuuma tayi tana juya batun cikin ranta,me yasa daada take haka?,akan yaranta gaba daya idanunta suje rufewa?,yanzu Allah ne kadai yasan idan taje me zasu aiwatarwa da yarinyar,tunda ta riga data sani,innar laulo qawace kuma aminiya a wajenta,ita kanta banda ubangiji ya riga da ya qaddara tafi qarfinsu,da ba qaramar wuya zata bata ba ta hannun daadan.

"Wai....nace ba" laila ta fada tana duban yuuma,sai ta maida hankalinta ga laila

"Wai daada kuwa cikakkiyar bafulatana ce yuuma?" Murmushi yuuma tayi,tasan me lailan ke rayawa cikin ranta

"Gaba da baya,har gwara ni innata itama ruwa biyu ce,amma ita babu sirki"

Tun gabanin lokacin tafiyarta kiwo yayi yau din ta shirya,da wurwuri tayi wanka don kada innar laulo ta farga ta hanata yi,ta gyara jikinta sosai,ta kama jelar gashinta ta nannadesu tayi musu wata lanqwasa me qawanya me kyau,hatta da duwatsun kwalliya na kanta da hannunta sai data qara wasu,ta sake fita bufalatana zam.

Can qasan ranta takejin cewa tana yin wannan kwalliyar ne duka saboda ibrahimu,tana ji a jikinta zaiyi wuya ace yau din baizo inda take ba,saboda yaune kwanaki uku suka cika bata ganshi ba,bata saurari wani abincin safe ba,tunda ba ita zatayi ba yau,ta
DOWNLOAD
DOWNLOAD

2 Comments On GURBIN IDO
avatar
salima

12 months ago

Reply

Nice story

avatar
ibrahim-6-8

9 months ago

Reply

That's so amazing

Please Login or Register in order to submit comment