Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

daga hannun saurayi

"hokkoyon dunni sauro(miko min sandar can)" ya fada yana nuna sandarta dae gefe,sai data kalli sandar sannan ta maida dubanta kanshi,ya fahimci me take nufi,don haka murmushi kawai ya sakar mata,ya taka da kansa zuwa gefanta ya dauki sandar,ga bishi da kallo mamaki fal zuciyarta
"waye shi?" Tambayar da taketa nanatawa kanta kenan.

Daga nan inda take tana iya hangen yadda yake tattare mata kan dabbobin nata cike da hikima da kuma qwarewa wadda ta lunka tata,da alamu shima din gwanine wajen iya kiwo,bai dauki wasu lokuta masu dama ba ya dawo gareta,yana sabe da sandar kan kafadarsa

"indillo(Muje ko?)" Yace da ita,dubansa tayi sanna ta janye idanunta gefe daya,sam maganar batayi mata ba,ta yaya zata jera dashi har cikin gari?,akwai idanun mutane masu yawa a kanta,sannan tana da kunyar da ba zata iya aikata hakan ba

"ummadillen(Tashi mu tafi),ko ba zaki iya tashi ba?"ya sake maimaitawa a tausashe,a hankali ta girgiza masa kai

"Kaje kawai,na gode,zan qarasa kaisu gida da kaina,na gode qwarai" idanu yadan zuba mata kadan,sai ya sauke ajiyar zuciya yana sauke sandar daga kafadarsa,ya fahimci me take nufi,tabbas ga cika bafulatanar gaske.

"Shikenan,zan kora miki su,tumudilli tokkirawaya gaɗa taajan banna wala kyettaiɗo ingwandi(idan na tafi ki biyo bayana,karki damu,ba wanda zai gane tare muke)" duk da hakan yayi mata,amma kuma batason dora masa wani nauyin kuma ko dawainiyarta,saidai kafin ta sake cewa komai yayi gaba,dole ta miqe,ta dauki malfajenta ta mayar saman kanta,ta dauki jakarta ta daura tabi bayansa.

Bata sani ba ko shima ya kula,sharewa kawai yayi,ko kuma bai kula din ba.....da gaske ita daya ta lura,yadda mutane keta binsa da kallo a sanda aka ganshi yana kora shanun da ita ke da hakkin kula dasu,yayin da ita kums ke biye dasu a baya,kasan samun nutsuwa tayi kwata kwata,jinta take a daure,har sai da suka isa gida,ya miqa mata sandanta idanuwansa akanta,fuskarsa dauke da murmushi

"Sai jaaango?" Ya fada yana sake nazartar kyakkyawan fuskarta

"Miyatti" ta amsa masa a gajarce,sai ya jinjina kansa

"Alla ɗaudane jamu(Allah ya qara lafiya)kisha magungunanki da kyau"

"to Allah jaɓe" ta fada tana jin nauyin mixanin kyautatawarsa a gareta.

Ko sanda himu yake nufar gida tunaninta ne fal cikin ransa,kamar yadda murmushi yaqi barin fuska da bakinsa su huta,sosai yake ji cewa yayi gamo da Matar aure,ta kuma zo dai dai lokacin da ya kamata ace tazo din,bayajin zaiyi nauyin baki ko jinkirin shaidawa innarsa,duk da cewa babansu baya nan,amma dai yana da kyau innar ta sani,ta kuma shaidawa baban da zarar ya dawo.

Da sallama ya shiga faffadan tsakar gidan nasu,kishiyar mahaifiyarsu wadda asalin sunanta shine rahama....amma sauran dangi da 'yan rigarsu na kiranta da ramatu,su kuma yaran gidan suna kiranta da yuuma,tana duqe gaban murhu,ta kammala kwashe tuwon dare tana wanke muciyar cikin tukunyar tuwon himu ya shigo.

Fuskarta dauke da fara'a take amsa sallamar tasa,macace mai matuqar kirki haquri hagen nesa da kuma sanin ya kamata,duk da kasancewarta wadda Allah bai azurtata da haihuwar yaro ko daya ba,amma sam bata kasance mai baqin hali gabyaran mikin nata ba,mutum ce mai sauqin kai,wadda take kallonsu ibrahim tamkar ita ta haifesu,tana kulawa da kowanne daya daga cikinsu,duk da zamantowar safara'u mahaifiyar ibrahim mace mara haquri da biyema zuciyarta a wadansu lokuta,amma yuuma ta danne,suna zaman lafiyar daya sanya jama'a da dama cikin karkarar ke sha'awar zaman nasu,ba tare da sunsan cewa fiye da kashi tamanin cikin dari na zaman nasu haqurin yuuma ne ya qawatashi.

Barka da gida yayi mata ta amsa tana masa sannu da zuwa

"Inna walaɗon(inna bata nan ne?)"

"o'o immoder,one ɓayi e'ummakiɗo(A'ah tana ciki,don bata jima da tashi daga nan ba),kila barci ne ya saceta,don tacemin bata danjin dadin jikinta sosai" kai ya gyada sannan ya sake tambaya

"Yaran nan fa?,su safiya?"

"inna'onliliɓe,amma ɓeɓadake wartuki(Innar ce ta aikesu,amma suna gab da dawowa)" har ya taka zaiyi gaba sai ya sake tambayarta

"Yaushe baaba yace zai dawo ne?" Murmushi ta sake

"Yau kuma 'yan tambayar ne a kusa himu?,rana wata yau in sha Allah" kai ya gyada yana murmushi,yaji dadin jin cewa bazai jima ba zai dawo gidan,ya tafi ikko ne da wasu shanunsa zai saidasu,wanda dama.yawanci can yake kaisu,shi kansa ibarahim din yafi zama a can,mafi yawan rayuwarsa ta can ce wajen wani dan uwan baaban nasa,yanzu ma gajiya yayi da zaman can din ya dawo gida yadan huta sannan ya koma,uwa uba kuma sun samu hutun semester,don acan din bai zauna ba yana karatunsa.

Ya daga labulen dakin ya samu barcinne kuwa ya dauketa,sai ya sauke ya wuce dakinsa,yayi abinda zaiyi a ciki sannan ya fito ya fara daura alwalar magriba,bai kammala ba innar ta fito tana daura dankwalinta

"denattoi ɗa himu(yaushe ka shigo himu?)" Ta fada tana dubansa,ita din duk da bafullatsna ce amma sam ba ruwanta da wannan kunyar da kaara tadan fari

"Ban jima ba,na leqo na samu kina bacci,ya jikin naki?"

"Alhamdlh,nasha ragowar maganin nan daka taba kawomin kwanaki kafin na kwanta,kaga kuwa har ya fara sakina"

"To alhmdlh,hammiyami jula miwarta(bari nayi sallah na dawo)" ya fada yana warware hannun rigarsa,a bakin kofar shigowa gidan sukayi kacibus da qannensa,yammata masu tasowa su biyu,yace maza su shige gida an fara kiran sallah,suka amsa masa amma suna binsa da.kallo,saboda labarin da suka samu a kansa tun a hanyarsu ta isowa gida.

Bayan sallar isha'i ya shigo gidan,babu kowa tsakar gidan sai yuuma dake zaune daga bakin kofar dakinta ita daya,gabanta fitilar aci balbal ce,sai qaramar redio da bata rabo da ita saboda jin labarai,sannu da gida yayi mata,ta amsa masa tare da shaida masa abincinsa na wajen innarsa,ya amsa mata yana wucewa kai tsaye zuwa dakin innar,bayajin dadin yadda wasu lokuta safiya da zubaida ke barin yuuma ita kadai,duk da lokaci lokaci zaka samesu wajenta,yana matuqar jin tausayinta,saboda rashin haihuwa abune mai ciwo da kuma sanya mutum cikin kewa da kadaici.

Da sallama ya shiga dakin,ya taras dasu sunata hira abinsu dukkansu,safiya zubida da sadam qaramin qaninsu,sannu da xuwa sukayi masa,ya samu waje yana zama

"Ra nyam kima,hokkumoki sadam(ga abincinka,sadam mika masa)" inna ta fada,sai sadam din ya mika masa,yaja kwanon ya bude ya fara ci bayan yayi bismillah,ba qaramin son tuwon yuuma yake ba,bama shi kadai ba,hatta da jama'ar gidan,saboda yadda ta iya girki,duk da innar tasa ma ba baya bace.

A hankali yake cin abincin yana kuma jefa baki a hirar tasu,saidai fiye da rabin hankalinsa nakan ta yadda zai gayawa inna maganar dake bakinsa,a qa'ida da yuuma zaiyi zancan,amma ya sani idan yayi hakan ransa ne xai baci wajen innar,saboda batason hakan,tafiso kowace magana suke da ita su sameta kai tsaye su shaida mata,itama yuuman tunda ta fuskanci haka,da sunzo sun gaya mata zata ce

"Kun gayawa innarku?" Idan sukace a'ah,takan ce

"Ku sameta ku fara shaida mata muji abinda xata ce".

Sai da ya gama cin tuwon tas ya wanke hannu sanna ya gyara xamansa cikin jin nauyi da kunya yace

"iwodi haala kaginmi gaɗen Inna....(akwai maganar da nakeso muyi inna)"

"Shine tun daxu kaketa wani mutsu mutsu ka kasa gayamin?,tawi'aayanka,mojetta bi'owaka(idan baka gayamin ba wa zaka gayawa duk duniya?)" Ta qarashe da sigar tambaya tana kafeshi da idanu,yasan me take nufi,sai kawai yayi murmushi yana cewa

"Babu"

"iminamma(ina saurarenka)" dan jim yayi kadan sannan yace

"Inna.....na samu yarinyar da nakeso fa".

Zuba masa idanu tayi saboda yadda maganar tazo mata a bazata,bata tsammaci jin maganar ba a wannan lokacin,saboda tuntuni tana da tsari da kuma muradi a kansa,amma duk da haka saita danne wannan a ranta,tace dashi

"Emi namma,immoi 'onni?(ina jinka,wacece?)" Kansa yadan shafa kadan sannan yace

"Sunanta maimunatu"

"Maimunatu ta gidansu laulo" muryar zubaida ta ratsa hirar tasu,da hanzari inna ta juya tana duban zubaida saboda yadda maganar zubaidan ta dauki hankalinta,yayin da himu shima ya juya yana kallon zubaidan saboda baisan waye laulo din ba,saidai idan ita dince yaji dadin yin maganar da zubaidan tayi,saboda baisan ta yadda zai kwatantawa innar ita ba yadda zata fahimta

"Da gaske ita kake nufi himu?"

"Gidansu na kusa da hanyar fegin maraba" mummunar faduwa gaban inna yayi,tabbas maimainunatun ya hango,take hankalinta yayi mummunan tashi,maimunatu 'yar uwa ga gaje?,gaje dai 'yar inna furaira

"Yuuma.....yuuma.....warnano wakka haala kawela(zo kiji wani mummunan labari)" ta fara qwalawa yuuma dake xaune qofar dakinta kiran,abinda ya sanya himu zubawa innar idanu cike da mamakin meye ya gigita innar tasa haka?,har take irin wannan kiran?.

"Ku tashi ku fita" innar ta fada tana waiwayawa gasu safiya dake zaune tun dazu suna kallon kallon a tsakaninsu,tsam suka miqe suna masu ficewa kowacce bakinga fal da magana,dai dai sanda yuuma ta shigo dakin a rude

"Lafiya kuwa?" Ta tambayi inna tana laluben wajen zama hankalinta a tashe,sai da inna taja wani dogon numfashi mai nauyi ta furzar da iska sannan tace

"Yaron nan ne yakeson dauko mana jaraba rana tsaka" sake tashi hankalin yuuma yayi tana duba inna tace

"Subhanallahi,jaraba wacce iri?" Kai inna ta gyada cike da jin xafi tace

"Wai yarinyar nan maimunatu ya gani yakeso?"

"Maimunatu?....maimunatu?" Yuuma ta maimaita sunan tana son tuna aka wace ake magana

"Diyam ta gidansu laulo" take yuuma ta fahimta,sunan kuma ya fado mata a rai,saboda ita daya keda sunan kaf rugar,hakanan kuma mahaifiyarta kadai ke kiranta da sunan,sai ta sauke ajiyar zuciya,alamun tashin hakalin da ya taso tun daga zuciya zuwa fuskarta ya fara zagwanyewa

"Hankalina ya tashi sosai innar sadam,na dauka wani abun tashin hankalinne"

"Yo akwai tashin hankalin da yafi wannan yuuma?""ai abinda yasa nace haka innar laulo.....kaf fadin rugarnan anyi ittifaqi babu yarinyar dake da nutsuwa da kuma kamun kai da tarbiyya irin maimunatu....."

"Amma kinfi kowa sanin ainihin wacece ita ko?"

"Wannan duk camfi ne ko ince hasashe....duk cikin masu hasashen babu wanda yake da tabbas kan abinda yake fada koda kuwa a gaban Allah ne,dukka abinda al'umar rugar nan keyi ba komai bane illa jahilci zalla da kima gurguwar fahimta gami da mummunan zato,koda ba zato bane hakanne,babu wanda ya taba kama maimunatu da wani mummunan aibu da za'a qita,a karan kanta maimunatu bata da wata matsala ko illa....." Idanu inna ta zubawa yuuma,a hankali a kuma sanyaye tace

"Yuuma...kodai don bake kika haifi himu ba kike qoqarin wanke maimunatu gami da kore kowanne aibu daga gareta?" Ba yuuma kawai ba,hatta da ibrahim sai da maganar ta tabashi,qas yayi da kanshi yana jin babu dadi a ransa,yayin da yuuma ta rintse idanu,maganar tana sauka saman zuciyarta da wani irin dafi mai zafi,dai dai maganar take da saukar mashi saman zuciyar tata,duk yadda take zaman kawaici da innar laulon....bata taba gwaba mata magana me zafi akan yaranta ba irin wannan

"Kaico!....kaico!" Yuuma ta fada tana girgiza kanta

"Inama ace Allah ya bani d'a na cikina wanda yakai shekarun ibrahim....kai koda ace bai qarasashi ba,matuqar ya isa a daura aurensa,da ba shakka na tabbatar miki da cewa magana nake Miki da zuciya daya.....Allah ya kyauta,kiyi haquri bisa shishshigin da nayi miki" yuuma ta fada bayan ta yunqura ta miqe,zuciyarta na wani irin tafasa,wanda tana fita qofar dakin hawaye ya silalo mata.

Shuru ne ya ratsa dakin na wucin gadi,cikin ranta innar laulo tana jin kamar bata kyauta ba,wata zuciyar kuma na gaya mata daidai ne abinda tayin,zallar mugunta ce kawai tasa yuuman bada wannan shawarar a gaban himun,bayan tasan kowa gudu da qyamar yarinyar yakeyi,ko ita bata sake ganinta tana hulda da yarinyar ba


"Amma inna abinda kika yiwa....."
"Kaga dakatamin" inna ta tsaida ibrahim dake Shirin nuna mata rashin dacewar abinda tayin

"Kada kace min komai,maganar maimunatu kada na sake jinta a bakinka,domin kuwa ba kai ba,koda wanda na isa na gaya masa yaji ne bazan bari ya aureta ba,bare kai dan cikina,bama maimunatu ba,banason ka sake kawomin maganar kowacce yarinya,na riga na zabar maka matar aure tun shekarun baya.....kaje gidansu maimunatun ka nemi gaje ku dai daita".

Tsaf kwanyarsa fa birkice,ta yaya zaizo da maganar maimunatu inna ta umarceshi da auren gaje?,gaje dai da ya sani?,ya akayi suka zama 'yan gida daya ita da maimunatun?,babu kama ta siffa ko dabi'a ko qanqani a tsakaninsu,wanne aibu ne ma wai da innar ke magana a kai da har zai zama hujjar raba sabuwar tarayyar da yanzu aka fara kiwonta tsakaninsa da maimunatu?.


*FREE PAGES ZASU KARE NE ZUWA GOBE IN SHA ALLAH,ZAKI IYA BIYAN KUDINKI TA WADAN NAN HANYOYIN*

Hafsat umar kabir
2270637070
Zenith bank

*Saiki tura shaidar biya ta nan*
07040727902

*Idan katin mtn ne kuma zaki tura ta nan tare sa shaidar biya*

09134848107

*Thanks for choosing zafafa biyar*

*_GURBIN IDO_*
*LAST FREE PAGE 05*

*AREWA BOOKS::HUGUMA*



Cikin kwanakin da suka biyo baya gaba daya kusan rabi da rabi na dawowar maimuntu daga kiwon ibrahim ne,wasu lokutan yakanyi gaba wani lokaci kuma tana biye dashi a baya,har sukai gida,ya tayata daure na daurewa ko sharar wajen idan bata samu tayi ba,sudan taba hira sannan ya wuce zuwa gida. Duk da cewa fiye da rabin hirar shi kadai yake abarsa,na maimunatun baya wuce eh ko a'ah. Haka kawai fa tsinci kanta da jin dadin tarayyarsu ita dashi,sai takejin wani canji na zuwa ma zuciya da rayuwarta,gaba daya wannan kadaicin babu shi,tana jin kamar ta samu wani bango da zata raba ko ta jingina dashi ko yaya yake,sabanin daa da bata da wanda zai magana da ita,magana da ake kirame dadi,idan taji magana daga bakin wani to fada ne,idan taji hira akanta to ta tsangwama ce,wani lokaci takan jima kwance duk sanda taje bacci,tana tuno irin hirarrkinsu da ibrahim,wani abun takan saki murmushi ne ta kuma juya ta gyara kwanciyarta.

Ta bangaren ibrahim din wani matsayi na musamman yakeji maimunatu na sake damu cikin ruhi da zuciyarsa,a dan zamansu ya fahimci abubuwa masu tarin yawa tattare da ita,ta banbanta qwarai da duka yaran rugar tasu,tana da wata irin nutsuwa da fasahar magana wadda ya jima baiga irinta jikin wata 'ya mace ba,komai nata na hankali ne da sanin ya kamata,yakan zauna yana kallon yadd take iya controlling dabbobinta da baki kawai ta hanyar basu umarni,lokaci dai daiku ne takanyi amfani da sandarta wanda xaiyi wuya ma kaga hakan.

Yadda take tausayin dabbobin kamar 'yan adam,bayan dukka alamu sun nuna sun fita samun gata da kulawa,duk da har yanzu bata taba bude baki tayi masa wata magana data shafi gidansu ba,yadda take communicating dasu kawai abun burgewa ne,duk da shima cikakken bafullace ne amma ba kasafai yake ganin hakan ba,lokuta da dama idan ya tsokanetan saidai tayi murmushi kawai,wanda kusan wannan din dabi'arta ne.

Ko sau daya himu baiyi nufin zuwa ga gaje ba kamar yadda daada ta buqata,wani lokaci ma sai ya rako maimunatu yake tunawa da batun,saidai yana ganin ba abu bane mai yiwuwa,yana da tabbacin komai zai daidaita da zarar bappansa ya dawo,wanda ya qara kwanaki kan wadanda yace zai dawo,saboda jiran haduwar kudadensa dake hannun mutane.

**************Yammacine lis,wanda yake busa wata ni'imtacciyar iska me dadi,yanayi ne da ya yiwa halittu da dama dadi,bawai ga dan adam kawai ba,hatta da sauran tsirrai da kuma dabbobin daketa kai kawo suna kiwo a farfajiyar wajen da ya zame musu wajen yini.

Daga can qasan bishiyar idan kakai kallonka wajen,bafullatana maimunatu ce cikin baqin saqinta,zaune saman koren hiramin da himu ya shimfida mata,shi kuma yana zaune daga gefanta saman wani dan mulmulallen dutse da bai cika girma ba.

Murmushine ke fita daga saman fuskarta,murmushin da kana kallonsa kasan kunyace cike dashi,ko a iya zamanta idan ka.kalla da kyau kasan a takure take,hannayenta sarqafe cikin juna tana kallonsu,yayin da shi kuma ibrahim ya zuba mata dukka idanunsa yana jiran amsar tambayar daya jefa mata.

Wani irin nauyi ibrahim din ke aza mata duk lokacin da ya zaunar da ita irin haka yana karanta mata kalaman soyayya......daga qarshe kuma a yau din ya tirketa kan lallai sai ta furta masa da bakinta tana sonshi,saboda bai taba jin hakan daga bakinta ba.

Wani abune kuma ita din da bata jin zata iya gaya masan,kalma ce data ji ta girmi kanta matuqa,koda baya kallonta ba zata iya fada ba,bare yadda yake zaune yana kallonta.

,sirara kuma jajayen labbanta ta motsa a hankali

"midelli...yamma tayi" dauke idanunsa yayi daga kanta yana murmushi,duk da yasan yau din sun gota lokacin komawarsun,amma tayi hakanne don ta kaucewa tambayarsa,yana mamakin kunya irin tata kawaici da kuma kamewa,sai ya miqe kawai ya dauki sandarta da a yanzun shike amfani da ita idan zasu koma gida.

Kamar ko yaushe ya tayata suka kammala komai,yayi tsaye daga jikin wata rusashiyar bukka dake daura da wajen yana dubanta cikin murmushi

"Shikenan,tunda ba zaki bani amsa ba maimunatu zan tafi,sai jaaango?" A kunyace tayi murmushi tana kauda kanta gefe daya,ya sauke qafarsa da ya harde waje daya ya fara takawa a hankali yana barin wajen

"Ka gaida gida" ta fada cikin siririyar muryarta da ba kasafai ya fiya jinta ba,sai daya waiwayo cikin jin dadi ya kalleta yana jinjina kai sannan yaci gaba da takawa,hakanan taji kunya ta kamata,abinda yasa ta juya da sauri da nufin shigewa zuwa shiyyar da dakunansu suke. Saidai kuma cak ta tsaya,saboda ganin inna tsaye daura da ita,da alama taji komai ta kuma ga komai.

Kallon da innar kawai ta tsareta dashi ya sanyaya mata gwiwa ya kuma sanya mata fargaba me tarin yawa,gabanta ya fara faduwa da wani mugun qarfi,duk da haka ta ari dakiya taci gaba da nufar inda innar ke tsaye tana ci gaba da kallonta

"Immoi'onni?(waye wancan?)"innar ta fada a tsawace cike da tuhuma da kuma zargi,yanayin yadda tayi mata maganar ya jefa tsoro a zuciyar maimunatun,ta qanqame jikinta waje guda,tana jiran jin saukae duka daga wajen innar,don wannan din ba sabon abu bane a wajenta

"Tambayarki nakeyi waye wancan din?"

"Sunansa ibrahim.....ya tayani qaraso da dabbobi gida ne"

"Meye hadinki dashi?" Inna ta sake tsareta da tambaya,saboda zargin da ya shiga ranta,taso taha fuskarsa amma kuma haqarta bata cimma ruwa ba,saidai batajin wanda take tunani dinne,don bata da shakka akan alqawari da yarjejeniyar dake tsakaninsu

"Babu komai" ta amsawa innar kanta a qasa,tana matse hannayenta waje guda,tana jin yadda zuciyarta ke ci gaba da bugawa fat fat

"Yauwa.....gwara ki rufawa kanki asiri,ke ta buɗeri ce,shi daya zai iya rufa miki asiri ya aureki,don haka kada ma ki batawa kanki lokaci ki yaudari kanki kice zaki saurari wani,kaf fadin karkarar nan bana jin akwai wanda zai iya daukarki idan bashi ba,koda an samu to yayi miki qarya,saboda haka ki kiyaye" daga haka tayi gaba zuwa garken dabbobin,tabi tana dubasu daya bayan daya tana kuma irgasu kamar yadda ta saba duk sanda maimunatun ta dawo,kai zaka zaci tana duba kaya data bawa qasurgumin barawo ajiya ne.

"Wuwuɗandu(ki share wajen)" ta bata umarni tana fita daga garken tayi gaba abinta,duk yadda takai ga gajiya hakanan dole babu yadda zatayi haka ta laluba kayan sharar ta fara gyaran wajen,duk da cewa a dazun kafin su tafi ta gyara wajen,batasan me ya bata wajen hakan ba,duk da tasan ko ba yaro idan innar taso bata wahala,zata qirqiro mata aikin ko kuma wanda yayi kama dashi,duk dai don kada ta huta,bata qaunar ganinta a zaune ko da na minti daya ne.


°°°°°°°°°°°°°°

A nutse yayi sallama cikin rumfar innar yana yafe da koren hiraminsa,dawowarsa kenan daga sallah sadam yace masa innar tana kiransa.

Abinda ya bashi mamaki shine ganinta da yayi a tsaye tana kai kawo daga wancan bangon zuwa wannan,idanunta dake cike da fushi ta daga ta dubeshi,ba tare data amsa sallamarsa ba kai tsaye tace dashi

"Joɗa(zauna)" kasa zaman yayi,sai ya duqa daga gefe kawai yana kallonta,ta tako gabansa a hankali tana dubansa

"Inaso naji bayan ni wace mahaifiyar kake da ita?" Sosai tambayar ta bashi mamaki,har ya tada kai yana dubanta sosai kafin ya kauda kansa ganin itama shi take kallo,yaro ne shi mai tsananin biyaya,don haka bazai iya hada idanu da daadan ba

"Babu daada....amma wani abune ya faru?" Sake baci ranta yayi

"Ni kake tambaya wani abune ya faru himu?,ashe ni ba uwarka bace?,ashe ban isa na gaya maka magana kaji ba?,tun a waccar ranar ban rabaka da maimunatu ba?,ban gaya maka babu kai babu ita ba?,shine kasa qafarka kayi wancankali da maganata akan diya mace saboda bani da wani muhimmanci a wajenka?"

"Ba haka bane inna..."
"To yaya ne?" Shuru ya gifta wanda bai gaza qasa da second hudu ba

".......ko kuwa maganar yuuma ce ta shiga kunnenka fiye da tawa ni mahaifiyarka?" Girgiza kansa yayi da sauri

"Ko kadan.....kada ki saka sunan yuuma don Allah daada,ba ruwanta,batasan me akeyi ba tun wancan ranar data fita a dakinki"

"Ibrahim!" Ta kirayi cikakken sunansa,abunda ya sake tabbatar masa zata yanke tsatstsauran hukunci ne,kuma kowanne irin hukunci ne hakan zata fadeshi ne ba da wasa ba

"Daga yau.....idan ka sake ka sake zuwa inda maimunatu take Allah ya isa ban yafe maka ba,sannan koda bayan raina ka sake ka aureta ban yafe maka ba" qarasa zama dirshan yayi a qasa maimakon tsugunon da yayi,ba qaramin kaduwa da hukuncin nata yayi ba

"Innalillahi wa inna ilaihi raji'un" ya dinga maimaitawa kansa a qasa,bai taba zato ko tsammanin hukuncin innar zaiyi tsaurin haka ba

"Don Allah inna ki sassauta kiyi haquri,maimunatu bata taba yi miki komai ba,banda......." Tsawa ta dakeshi tana katseshi

"Banason na sake jin komai daga gareka,wannan shine hukuncina na qarshe,tashi ka fita!" Ta fada a zafafe tana nuna masa qofa,sai da ya dafa qasa sannan ya miqe

"Himu" ta kirashi sanda yakai qofa

"Na baka kwana hudu kacal,ka shirya fara zuwa wajen gaje kamar yadda na gaya maka,umarnine nake baka" bayajin xai iya cewa da ita komai,don haka kansa da yayi masa nauyi kamar ya dauki kaya ya gyada mata sannan ya fice daga dakin yana jin jikinsa kamar zazzabi na shirin rufeshi.

**********Sake juya rufaffen takalmin danqon hannunta tayi don ta tabbatar dabarar data yi masa zata kaita gida,ita kanta batasan adadin liqin data yi masa ba,wani gurin da garwashin wuta da leda,wani gurin kuma tana samun zaren lilo ta zarge inda yake shirin rabewa dashi.

A hankali ta duqa ta ajjiye takalmin a qasa ta zura qafafunta,tadan motsa qafar ta tabbatar yayi,sai ta sauke ajiyar zuciya,tana godewa Allah da ya sake fiddata a yau dinma dai still,takalmin bai mata tutsu ba,batasan ya zata kasance mata duk randa hakan ta faru,itadai shi daya ta sani a matsayin takalmin da take dashi,wanda ita kanta batasan adadin kwanakin ko shekarunsa ba a duniya bare ta iya tantancewa.

Sake waiwayawa tayi hagunta da damanta,har yanzu bata debe tsammani da ganin himu ya bullo ba,duk da cewa lokacin zuwan nashi ya gota sosai,tana da tabbacin babban abune ya tsaidashi,saidai tana fatan koma meye ya kasance yana lafiya qalau.

Waiwaya tayi sashen wata saniya ke zaune,gefanta jaririn san data haifa ne a dazu jimawa kadan bayan isowarsu wajen,ta tabbatar inna batasan cikin ya isa haihuwa ba,da ba zata bar mata ita zuwa wajen kiwo ba,dole idan lokaci yayi himun baizo ba,haka zata hada da kula da sauran dabbobin,da ita wannan sabuwar haihuwar su wuce gida,yau din tana jin gajiya sosai a jikinta,ita kadai cikin wajen,cikin tsoro da fargaba saniyar tahaihu a wajenta,wanda ita kanta tasan babbar kasada tayi,saboda samuwar matsala ta mutuwar uwar ko abinda aka haifa,dai dai yake da samuwar matsala cikin tata rayuwar,ko daya innar batasan wata aba wai ita
DOWNLOAD
DOWNLOAD

2 Comments On GURBIN IDO
avatar
salima

12 months ago

Reply

Nice story

avatar
ibrahim-6-8

9 months ago

Reply

That's so amazing

Please Login or Register in order to submit comment