Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

da suka sha jan lalle wanda ya sake qawata qafan,ya kuma zame mata ado sosai,sai ya janye idanuwansa,qafafun are tiny,abinda yake alamta masa tana da qarancin shekaru kenan?,haka kawai sai yaji zuciyarsa na darsa masa son ganinta da tantance wacece ita?,ta yaya zasu dubi kamarsa suce zasu aura masa yarinya kamar haka?,sakanni qalilan zuciyarsa ta kacame da wasuwasin yarinyar ce ko kuma hasashe ne irin nasa?.

Miqewa yayi yana sake jan tsaki duk a qoqarinsa nason mantawa da wannan wasuwasin da yake azalzalarsa a rai,ya taka zuwa qofar bandaki bayan ya kalli agogo yaga lokacin sallar magrib yadan gota kadan,ya daura alwala,ya sake fitowa yana sauke hannun rigarsa daya nannade kafin fara alwalar,yana son ce mata taje tayi alwala suyi sallah amma kuma ya rasa ta yadda zai gaya mata,bawai kuma baisan yadda zaice mata bane,a'ah,kawai qyashin maganar yakeji,har ya fidda abun sallah ya shinfida tana zaune,sai daya sake jan tsakin nan nasa dai,wanda ya kuma sanya maimunatu faduwar gaba ta kuma rintse idanunta kamar kowanne lokaci idan yayi tsakin,don tana jin tsakin ne har tsakiyar kwanyarta,faduwar gabanta kuma nada nasaba da muryar dake mata kama da wata firgitacciyar murya data taba ji shekarun baya da suka wuce

"Kiyi alwala kizo" ya fadi mata yana jona qaraman kettle dake a gefansa.

A hankali ta miqe,ta kuma dan ja mayafin nata baya kadan,sannan ta wuce zuwa bandakin.

Gaban madubi ta tsaya bayan ta yaye lullubin kanta gaba daya,tana sakin wata ajiyar zuciya me nauyi gami da kallon fuskarta,wadda lallausan gashinta me azabar santsi da yasha gyara daga wajen yakumbo saratu ya fito kadan ta gaban dankwalin nata,saita debe ruwan dake zuba daga famfo ta fara alwalar,tana yi tana kallon fuskarta a madubi,zuciyarta nata mata saqa abubuwa masu yawa harta gama,ta maida dankwalinta da mayafinta ta fito,ta kuma tsaya a inda ya mata nuni suka tada sallar.

Yadda yake sallar cike da nutsuwa yayi matuqar burgeta,ko banza alamune dake nuni da sanin addininsa.

A hankali ya sallame,idanunsa suka sake sauka akan dogayen hannayenta suma da suka jiqu da jan lallae cikin ado me ban sha'awa,hakanan ya samu kansa da juyowa gaba daya yana fuskantarta,idanunsa suka sauka gaba daya a kanta,ta tanqwashe qafafunta sosai tana zaune,sai ya ganta 'yar qarama a gabansa,tazarar dake tsakaninsu ba mai yawa bace

Shuru ne ya baquncin dakin,numfashin kowannensu yana fita tare sa tulin tunanin dake zuciyar kowannensu,yaci gaba da zama a haka yana fuskantarta tare da wassafa me zayace da ita?,duk sanda yadan dubi sashen da take zaune sai yaji wani abu ya tokare masa wuya,yanzun haka bayan ita akwai wata daban dake gombe tana jiransa?,for god sake anni zatayi masa haka ne wai?.

Kamar wadanda aka umarta daga shi har ita kowanne ya daga kanshi zuwa ga dan uwansa,take fuskarsu ta hade waje daya kamar yadda idanuwansu suka cudanya da juna,fari qal din idanuwan nan nata da baqaqen qwayar idanunta masu digon zaiba jiki,kyakkyawan idanunwansa dake da wani irin shape,tare da wani irin maganadisu dake cike da zallar kwarjini.

Kusan lokaci daya wani abu ya daki zuciyar kowannensu,wanda ta bangaren maimunatu ba komai bane face wani irin tsoro razani da kuma firgici da ya kusa tafiya da numfashinta,cak ta tsaya da zuqar iska zuwa huhunta na wucin gadi,hatta da ja'afar din ya karanci hakan,yayin da shi kuma zallar mamakin qananun shekarun da take dashi hadi da kamanni da tayi masa da wata suka ratsashi.

Cikin jarumta ta zuqi wani dogon numfashi ta kaiwa hunhunta cikin wasu sakanni masu mugun sauri,abinda ya tallafa mata numfashinta ya dawo da aiki,saita lumshe idanunta da kyau tana shaqar numfashin da qyar,tana kuma jin yadda zuciyarta ke mugun bugawa da sauri kamar zata tsinke daga inda take ta fito.

"Hey" ya fadi cikin mamakin yadda take wasu abubuwa kamar wadda taga giftawar mutuwarta a gabanta,maimakon maganar tasa ta taimaka wajen bude idanuwanta ko samun nutsuwarta......a'ah,sai ta sake razana,saboda muryar ta sake tabbatar mata da shi dinne dai,shine dai wannan mutumin,take jikinta ya dauki rawa,zuciyarta taci gaba da kadawa a tsakanin qirjinta,sai tayi wuf zata tashi jikinta na kakkarwa kamar wadda azababben zazzabi ya rufe.

Caraf ya damqi tsintsiyar hannunsa cike da haushinta da mamakin firgitar da tayi,riqon da yayi mata ya sanyata sakin kuka babu shiri tana dubansa,mamaki ya cikashi qwarai,sai ya janyota ta koma ta zauna a inda ta tashi.

Sosai hankalinta ya kuma tashi,ta hade jikinta waje daya hawaye naci gaba da bin kuncinta,ta yaya zata manta da wannan fuskar?,yaya zata manta dashi,mutumin da ya kusan sanadin cirewar qwayar idanunta saboda marin da ya zabga mata duka akan dabbobinta?,mutumin da ya mata barazana da kakkausar murya,wanda tun daga ranar bata sake ganinsa ba,saidai duk sanda taga mota,ko taga wani abu da yayi kama da mari saita tunda da abinda yayi mata,sau tari takan shafa kuncinta idan ta tuna da wancan lokacin,mutumin da razanata matuqa,ta tsani taba,ta kuma tsani me shanta,sai gashi ya fesar da hayaqinta saman fuskarta,abinda ya kusan haddasa mata daukewar numfashi,wanda ya aikata mata wannan duka shine zaune yanzu a gabanta,shine kuma mijinta?.

Samun kansa yayi da zuba mata idanu,abinda ba al'adarsa bace,yana dubanta tare da son tuna inda ya santa,tsahon wasu daqiqu kwanyarsa ta dauko masa komai,bafullatanar yarinyar nan,daya jima yana tunawa bayan marin da ya dauke fuskarta dashi,ya jima yana murza hannunsa a lokacin cikin fushi da jin haushinta na yadda ta qarasa tunzura fusatacciyar zuciyarsa ya aikata mata abinda ba halayyarsa bane,fuskar da yakan tunata lokaci bayan lokaci saboda qarfin halinta da kuma yadda ta bashi haushi a sannan.

Ga mamakinsa sai yaji duk wani temper na zuciyarsa ya sauka daga kaso casa'in cikin dari,zuwa kaso arba'in ciki dari,ta yaya zai zauna da wannan yarinyar?,wadda gaba dayanta baifi ya haifeta ba inda ace auren qauye akayi masa?,ta yaya zai zauna da wannan bafulatanar rugar?,wadda ya tabbatar babu abinda ta sani,babu kuma abinda ta iya?,ya aureta yace ya auri me?,ta yaya ma duniya zata kalleta a matsayin matarsa?,wanne irin rigima ce wannan ta anni?, take kwanyaraa ta hasaso masa unaisa,yayi comparing nata da wannan,sam babu hadi,ko ita unaisar bata cika mizani da ma'auni ba,tayi masa girma da yawa,don shaheeda bata kai wadan nan shekarun ba har ta rasu,barema tun halittarsa shi mace bata taba burgeshi ba,shaheeda ce mace qwaya daya tallin tal da ya taba daga kai ya dubeta da wata ma'ana ta daban,itace macen data fara bude rayuwarsa,kuma sanda ta tashi tafiya.....yanajin ta hada da muqullin komai nashi tayi gaba dashi.

Cikin rai da zuciyarsa ya dinga jin yanzu zaiyi solving daya daga cikin matsalolin kamar yadda yake kallon maimuntu da unaisa a natsayin MATSALA kuma GURBIN IDANU ne kawai,wadanda baijin zasuyi ko suna da amfani ko wata rana ga mamallakinsu,wanda dasu da babu duk daya

"Relax" ya fada idanunsa a lumshe,yana zagaya lips dinsa da yatsun hannayensa

"Yamin shuru!" Ya sake fada a karo na biyu,ganin taci gaba da rera kukanta kamar ma bataji abinda yace ba,yadda ya buqata kuwa a wannan karon....sai ta fara hadiye kukan sannu sannu har ta samu nasarar tsaidashi.

Shuru ya sake ratsa dakin,tamkar bazaiyi magana ba,kafin daga bisani ya bude dukkanin idanunsa ya watsasu a kanta

"Kinsan menene aure?" Yayi tambayar with husky voice,wani irin abu ya ratsa mata tun daga saman kanta zuwa tafin qafafuwan maimunatu,saboda girma da nauyin da tambayar tayi mata,me zata ce masa?

"Kinsan me aure yake nufi?" Ba tare da tayi dogon nazari ba ta gyada kanta alamun eh,kasancewar ba mutum ce ita wadda ta iya qarya ba.

Wani miskilin qaramin murmushi ya sake

"Okay......yayi kyau,tell me menene aure?" Ya fada yana yin qasa da muyarsa,hadi da tsareta da idanunsa nasu nauyin kallo,duk da bashi take kallo ba amma sai da taji gaba daya ta rude ta kuma daburce

"Ehhnnnnn" ya fada da madaukakin sauti,sai ta shiga girgiza kai alamun a'ah,bata sani ba

"Qarya kike kenan da farko..... okay let me show you the real definition of marriage" ya fada with confidence,zuciyarsa na gaya masa that's the only way da zai cimna gaci na abinda yakeson aiwatarwa,ba tare da yasan maimunatun was simple and peace maker ba,sai ya miqa hannu ya janyota cikin zafin nama daya sake tsoratata zuciyarsa na ingizashi,ya sanyata tsakiyar qirjinsa duk da yadda zuciyarsa ke qin hakan.

Fara yamutsata yayi,abinda yayi matuqar dukan hankalin maimunatu ya kuma kadata sosai,abinda tunda take makamancinsa bai taba faruwa da ita ba,mugun gigicewa tayi cikin tsoro da razani,ta sake sakin kuka tana riqe masa hannayensa da yakeson fara yawo dasu cikin sassan jikinta,sai ya tsaya cak numfashinsa na wani irin gudu,yana duban yadda ta riqe dukka hannayensa biyu cikin siraran tafin hannunta,jikinta na wani irin rawa kamar an kada mata gangi

"Bai kamata ba,baka kyauta ba" yaji can tsakiyar kansa zuciyarsa na gaya masa,bai musa ba,take zuciyarsa ta gamsu da cewa bai kyauta din ba,saidai kuma wannan ce hanya guda daya da zaiwa tufkar hanci,tunda baisan irinta ba yarinyar,abu daya ya sani game da ita,tsiwarsa da har ta iya buda baki tace masa Allah ya isar mata a wancan lokacin,yana jin this the only way out da zai dorata kan duk abinda ya tsarama zuciyarsa.

Saidai kash,yana shirin sakinta anty maama ta turo qofar riqe da jakar kayanta,abinda ta gani ya sanyata fadin

"Subhanallah" da sauri tana komawa da baya,abinda yaja hankalinsa,yayi hanzarin sakinta ya kuma miqe a nutse,ya isa bakin qofar dakin ya sake bude mata ita sosai,sannan ya juya zuwa bandaki bacin rai yana cinsa kan yadda ta gansu,yayi yaqinin abinda zaizo ranta daban,abinda zata rayama ranta yasha banban da abinda yake faruwa,ya tura qofar toilet din ya shige.

Gaban madubi ya tsaya yana duban fuskarsa,hannunsa yasa yana yamutsa sumarsa zuwa bayan kansa,yadan riqeta da qarfi yana jin haushin kansa da kansa,ta yaya zai riqe yarinyar cikin jikinsa har kamar haka?,sai yaja wani irin tsaki kamar zai cire harshensa,yana jin tsantsamin jikinsa dama hannayensa,duk da cewa babu abinda ke fita a jikinta sai lallausan qamshin turaren firdaus.

Wayarsa ya ciro ya turawa jabir tex kan ya shigo masa da kayan sawarsa,sannan ya ajjiye wayar,ya soma fidda kayan jikinsa yana jefarwa,ya daidaita ruwa me dumi sosai daga shower ya shiga ciki yana sabe jikinsa kamar zai cire fatar wajen.

Da wani irin nutsuwa dakiya da kuma tsare gida ya dawo dakin,bayan ya shirya cikin wata lallausar jallabiyya da aka yiwa aiki d wani gold zare mai kauri,idanunsa suka sauka a kanta,tana lafe a wani lungu dake daura da gadon,sai ya sake jan tsaki can qasan ransa,yana jin takaici na sake kamashi,baisan me anni ma ta dauki aure totally ba data hadashi da wannan.

Bai tsawaita magana da ita ba,cikin taqaitattun mintuna ya gama tsara mata dukkan wasu qa'idoji da dokoki da yakeso tabi da kuma zauna akai,ya riga daya sani a yanzun bai isa yace ya rabu da daya daga cikinsu ba ko ta yaya kuwa sukazo masa indai bada wani qwaqwaran dalili ba,sai ya sauke boyayyar ajiyar zuciya,yana jin yayi maganin rabin matsalarsa,ya tabbatar a yanzun bashi da wani sauran case da ita wannan yarinyar,saura dayar,ya fuskanci itakam waccar kanta yana rawa sosai,zai kuma shata mata layi tsakaninta da rayuwarsa.

Fita yayi ya barta a dakin,bai dawo ba sai da bacci suka kama idanunsa,duvet din ya yayima ya koma saman kujera yayi kwanciyarsa,bayan ya kashe hasken dakin,bai wani jima sosai ba bacci ya daukeshi,don tunani da damuwar dake kansa a yanzun ta ragu sosai.

Kasa sakewa tayi cikin dakin,motsi kadan saita tuna abinda yayi mata dazun,abinda ke sake bata tsoro kenan,duk da maganganun da yayi mata dazun sun sake nuni da girman tazarar dake tsakaninsu,wanda zuciyarta tafi raya mata cewa gargadine ya sanya ya aikata mata hakan,bawai don ta isa ko tana da wani abu ba,babban shinge da layin daya gindaya tsakaninsu kawai ya sake tabbatar mata da cewa da gasken gangancin aka aikata na hadata aure dashi kamar yadda ya gaya matan,ita kanta daga dazu zuwa yanzu da kuma sanin data yi masa a baya ta sake tabbatarwa kanta tako ina yafi qarfinta,ya kuma yi mata fintikau,tun tana takure har gajiya tasa gabbanta suka saki,ta kuma zame da jikinta a nan qasa daura gadon,bacci mai nauyi ya fara fusgarta,zuciyarta cike fal da tsoronsa daya dasa mata a wannan rana.



31

Ya samu nasarar dasa tsoronsa sosai cikin zuciyar maimunatu har ma fiye da yadda yakeso,washegari da suka fito tafiya kasa hada idanu tayi da anty maama,wani irin kunya da nauyinta ta dinga ji,cikin motar kuwa tana cure waje daya,kamar xaka ce ket! Ta zura da gudu,wannan karon a bayan ya zauna,ya kame owners corner abinsa,duk wani motsinsa tana ankare dashi,saidai da kunnuwanta don tuni ta saye idanuwanta cikin mayafi.

Duk tsahon awannin da suka diba suna tafiya aiki yake da na'ura,daga system zuwa wayar hannunsa,tsahon wadan nan awannin ko daya baiji tayi wani qwaqqwaran motsi ba,abinda ya sanyashi daga kai suna dab da shiga garin gombe ya dubeta.

Ko ta cikin yalwatacce mayafin data lulluba har saman kanta yana iya hangen zallar quruciua da kuma qanqantar data yi masa,wani takaici na sake kamashi kan anni,sam ita babu ruwanta da duba da cancanta ne ko kuma dacewa?,gwara unaisa ta cika shekarun da zai kirata da mace,saidai ko ita din ma bata burgeshi ba ballantana wannan rabin macen,ta yaya ma idanuwansa zasuji wata diya mace ta burgeshi?,baya zaton zuwan wannan ranar,wannan duka shaheeda ta tafi dashi,tabar masa fankon zuciyar,ta yaya fankon zuciya kuwa zata san dai dai daba dai dai ba?,sai yaja dan qaramin tsaki acan ciki,yana maida dubansa ga allon computer,yana karanta saqon rubutun da ya mamayr fuskarta.

Katafaren wuni ake cikin gidan dr marwan,don sanda duka isa gidan a cike yake maqil,abinda ya sanya ammi ta bada maqullin wani kebantaccen waje dake gidan aka sauki maimunatu da danginta,aka kuma cikasu da cimaka kala kala,kafin yammaci inda suka hau shirya maimunatun bisa jagorancin anty maama,don Allah ya sanya mata matuqar qaunar maimunatu,tana burgeta ainun.

Sanda suka kammala sunso su kaita cikin gidan wajensu anni da amma,amma sai annin tace a wuce da ita gidanta kawai,maimunatu tasu ce,babu wani abu sabo da zasu gaya mata,don haka direct aka fito da ita zuwa jerin gwanon motocin da aka aje domin miqata gidan captain ja'afar marwan khalid akko.

Duk abin nan da ake tana jin komai ne tamkar a mafarki,wasu hawaye masu dumi suka zubo mata sanda taji.motocin sun fara motsawa zasu bar gidan dr marwan,babu abinda ya fado mata a sannan sai

"Allah ya nunan ranar aurenki,ya baki miji na gari" sai gata yau a bigiren zuwa gidan mijin da batasan yadda zasu rayu dashi ba,a lokacin da qasa ta jima da rufe idanun mahaifiyar tata

"Allah ya jiqanki daada"ta fada cikin ranta,wannan din addu'a ce da kullum rana batasan sau nawa take yinta a ranta da kuma sarari ba.

Tana jin sanda 'yan uwanta da sauran 'yan rakiya ke yaba kyau da kuma tsarin gidan,kowanne bakinsa na furta addu'o'i a kanta,abinda ita ta rasa gane kansa har yanxu,Allah ya zaunar da ita yakuma dawwamar da ita a gidan mutumin nan?.

A hankali yake takawa zuwa sassan ammansa,sanye da wani irin sassalkan yadi ruwan hanta,wani irin dinki aka masa me kyau wanda yake nuni da zallar zamani da kuma wayewa,takalmin fata ne a qafarsa budadde wanda ya dace da kayan jikinsa,kamar yadda saman kansa yake sanye da hular da itama ta dace da kalar takalmin qafarsa.

Wata irin tafiya yake,sam jikinsa babu kuzari hakanan Babu karsashi a tattare dashi,ya tura qofar falon amman,akwai sauran baqi da suka rage cikin gidan,umma ce qanwa ga ammansa ita da wasu mutum uku,su suka gaya masa amman tana bedroom dinta,sai ya wuce kansa tsaye.

Sai da yayi knocking ta bashi izini sannan ya tura ya shiga bakinsa dauke da sallama,luf luf dakin yake a tsaftace gana fidda wani irin qamshi me dadi,kai baka ce ba biki akeyi cikin gidan ba,tana saman gado tana gyarawa amna kwanciya,sai ya matsa ya rusuna gabanta yana gaidata,ta amsa kana shuru na sakanni ya biyo baya,ta gama gyarawa amnan ta saka mata pillow sannan ta waiwayo ga ja'afar

"Zaku wuce kenan?" Kai ya jinjina mata,yana zare hular dake kansa,can qasan zuciyarsa kuwa wata nannauyan ajiyar zuciya ya sauke,yana jin komai har yanzu kamar a mafarki

"Ma sha Allah,Allah ya tsare,ubangiji yasa a shiga a sa'a,Allah ya kauda dukkana abunqi,ya albarkaci tarayyarku,kayi qoqari ka riqe amanar yaran mutane,ka kuma ji tsoron Allah a zamantakewarku,ka sauke nauyin da duka Allah ya dora a kanka,na horeka ka zama adali,ka kiyaye haqqin kowacce akan 'yar uwarta,karka yi zalunci,kada kuma ka bari a zalunci kowa,Allah ya shige muku gaba"

"Ameen ya rahman,na gode amma" ya fadi yana jin jikinsa yana yin sanyi,wannan daren yana tuna masa da daren aurensa na fari ne da shaheeda,wanda akwai tarin bambance bambance masu yawa.

Matsawa yayi gaban gadon ya dora hannunsa saman kan amna ya shafa,sannan ya duqa yayi kissing kuncinta,ya maida mata abun rufar ya miqe tsaye yana zuba hannayensa cikin aljihunsa

"Sai da safe" yace da amma yana takawa zai fice

"Allah ya bamu alkhairi" ta fada tana bin.bayansa da kallo,duk yadda yake qoqarin boye damuwar dake saman fuskarsa ita ta karanci hakan,saita rakashi da addu'a

"Wannan hadin ubangiji kasa ya zama silar waraka a rayuwarka".

Motarsa ya wuce kai tsaye kamar yadda ya zaba tafiya shi kadai babu dan rakiya ko daya,don zuwa yanzun ma yasan abokansu sun tsufa gidan jabir koma suna shirin juyowa,yace baya buqata,shi din ai ba auren fari xaiyi ba.

Yana shirin bude motar yaji sallamar khadim a bayansa,sai ya waiwaya yana amsawa,cikin girmamawa ya miqa masa wasu ledoji dake hannunsa

"Gashi inji ammi" jim yayi na sakanni yana bin ledar da kallo,sai kuma ya bude masa back seat bau tare da yace komai ba,khadim din ya fahimta abinda yake nufi,don haka ya qarasa ya saka musu su a baya,har ya juya zai tafi yace masa

"Kace mata na gode" yayi maganar ne sanda yake shigewa cikin motar,ya maida.murfin ya rufe ba tare daya jira cewar khadim ba.

A hankali yake tuqin kamar wanda baison isa gidan,tafiyar data daukeshi mintuna masu tsaho fiye da mintunan da zasu isheshi a al'adance,horn daya mai gadin gidan ga dage masa gate din,sai a sannan yadan ja motar da gudu ya shige da ita farfajiyar gidan,sannan ya faka ta a parking lot idanunsa na sauka kan wata qaramar sabuwar mota ruwan zuma,ya dauke kansa yana kashe tasa motar.

Har ya fito ya tuna da ledojin da ya bari cikin motar,sai ya koma ya debosu,tun kafin ya bude ma ya fuskanci meye a ciki,sai ya riqesu a hanauyensa,dai dai sanda me gadin gidan ya iso cikin rusunawa ya fara gaidashi,amsa masa yayi cikin kulawa,saboda yana daga cikin dabi'arsa girmama duk wanda yake aiki a qasansa,barshi dai da zafinsa miskilanci rashin daukan raini da rashin son wasa da aiki,hannunsa ya sanya cikin aljihunsa ya fiddo 'yan dari biyar biyar sababbi guda shida ya miqa masa,hannu biyu ya sanya ya karba yana ta zabga godiya,yayin da shi kuma yayi gaba abinsa ba tare da yace tak ba.

Sai da yayi addu'ar shiga gida sannan ya kutsa kai cikin babban falo,shuru yake babu alamun motsin me rai cikin gidan,cikin nutsuwa ya fara takawa zuwa stairs,sai kuma ya tsaya cak saboda maganar da abbi da kuma amma suka gaya masa a daren jiya da yau,ledojin hannunsa ya kalla,a hankali sai yayo baya,ya kuma nufi qofar dake hannun dama na falon.

A hankali ya tura qofar,falo ya bayyana,wanda aka qawata da kalolin kujeru da curtains masu azabar kyau,royal blue da golden,komai na falon,a tsaftace yake cikin qamshi da sanyi daya gauraye da sabunta,ci gaba yayi da tafiya har ya isa qofar bedroom din,itama ya turata ya shige.

Dai dai lokacin da take zaune saman abun sallah,saboda ganin yadda lokaci yaketa tafiya,an doshi sha biyu na dare,kuma ana binta sallar isha'i da kuma shafa'i da wuturin da batayi ba.

Can qasan maqoshinsa yayi sallama idanuwansa suna sauka a kanta,gabanta ya buga fat,don bata tsammaci shogowarsa din ba,saboda dukkan wata magana daya gaya mata a jalingo ta haddacesu tsaf a kanta, janye kansa daga wajen da take yayi,ya isa gaban madubi ya ajjiye ledar a kai,sai ya tsaya yana goye da hannayensa a qirjinsa.

Raka'ar qarshe take amma kawai sai ta miqe taci gaba da kawo wasu raka'o'in,abinda ya sanyashi sakin hannayensa kenan,ya kuma juya a hankali ya fice a dakin bayan yaja qofar kamar yadda ya ganta.

Sallamewar sallarta ta fito ne hade da ajiyar zuciya,ta danyi shuru tana karanta la'ilaha illa anta subhanaka inni kuntu minazzalimin,tana kuma jin yadda zuciyarta take bugawa,lumshe idanunta ta sakeyi,ba shakka tana tsananin tsoronsa,tana tsoronsa bilhaqqi da gaske,hoton sanda ya zuba mata lafiyayyen marin nan ya gilma a idanunta,sai kuma sanda yake zuqar hayaqin taba yana bulbular da ita daga bakinsa zuwa hancinsa,sai ta girgiza kai,tana jin wani bala'in haushinsa yana ratsata.

Yaya akayi ya kasance mashayin taba?,bayan shi din ya fito ne daga gidan tarbiyya kamar haka?,mutane masu karamci dattako da sanin darajar dan adam?,bata tunanin akwai wanda yasan yana sha din cikin gidan,don ko da wasa bata tabs jin anyi magana makamanciyar wannan ba.

Tunanin ta ture gefe,ta fara karanto azkar dinta da bata samu tayi ba a yau din,gefe na zuciyarta kuma cike taf da kewar amna,tana jin cewa zaiyi wuya bata nemi su anni su bata yarinyar ba,don ko a yau ma sai da akayi wayon janyeta sannan suka tahi,wanda ita bata kawo hakan ba,ta tsammaci zasu taho ne da ita,amma sai taga akasin hakan,to me zata zauna ne tayi a gidan?,gwara gwara ma ace da amnan,zata taimaka mata wajen debe kewa.

Kamar yadda ya shiga sasssan maimunatu haka ya shiga na unaisa,saidai ita ya sameta tsaye ne a gaban mudubi tana kallon kanta bayan ta gama sake feshe jikinta da turare tana gyara zaman rigar jikinta.

Sallamarsa hade da turo qofar ya sanyata saurin maida mayafinta saman kanta, ta rufe ruf,saidai tana iya hangensa ta cikin mudubin,wani
DOWNLOAD
DOWNLOAD

2 Comments On GURBIN IDO
avatar
salima

12 months ago

Reply

Nice story

avatar
ibrahim-6-8

9 months ago

Reply

That's so amazing

Please Login or Register in order to submit comment