Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

idanunta daga kallonsu,suka qaraso kusa da afra,kusan a tare suka ce da maimunatu

"Sannu New roommate" murmushi tayi musu

"Sannunku"

"Sunana fatima baqo" sai dayar ma ta kama

"Ni kuma ummu ayman buhari" ta qarashe maganar tana miqa mata hannu

"Maimunatu Abubakar muhammad" ta amsa musu tana miqa musu nata hannun itama

"Nice meeting you" suka amsa fuska sake kaman sun saba da ita dama can.

To hausawa sukace juma'ar da zatayi kyau tun daga laraba ake ganeta,dukkan alamu sun nunawa maimunatu zataji dadin zama da abokan karatun nata ainun tun a waninsu na farko,wasu irin mutane ne masu sauqin kai da kuma dadin zama ainun,yadda suke nan nan da ita da kuma haba haba sai ka zaci an jima da haduwa tare.

Takeaway mai yawan gaske suka zube musu sukaci,sunayi suna duba jikin afrah,duk da cewa da sauqi saboda maganin data sha,har sukayi sallar la'asar,sannan suka fara shirin tafiya islamiyyar cikin makarantar,wadda suke shiga hudu na yammaci

"Inaga tunda ku kun saba zuwa,kuje kada ku rasa karatunku na yau,ni zan zauna da sister afra(ta fadi kamar yadda taji suna kiran juna),idan yaso ko zuwa gobe sai na fara zuwa"abunda ya yiwa afran dadi qwarai,ta kuma sake jin maimunatun cikin ranta fiye da daxun farkon zuwanta,bayan fitarsun kuwa hira suka dinga yi sosai da afran,a nan ta fahimci dukkansu 'ya'yan manya ne,sai maimunatun taji a ranta ya kamata ta kama kanta,tunda ita din ba 'yar kowan kowa bace,amma duk da hakan sai ta saki jikinta,ta dinga dan tambayar afran game da wasu abubuwa na makarantar,ta samu haske kuwa sosai,don su tun daga js one suka fara,ba kamar ita ba data datsi ss one.

Ta fahimci team ne na masu son karatu aka hada daki guda,afra ayman da fatima,wannan yasa itama ta sake jaddada niyyarta na zage damtse tare da yin karatu tuquru haiqan,son karatunsu ne ya sanya a aji suka raba set,don kada suje kasa maida hankali,kowacce a cikinsu akwai babban alqawarin da aka yi mata daga gida na idan ta gama ta fita da sakamako me kyau a dukka record nata,to zata zabi duk abinda takeso kuma shi za'a bata,wannan yasa a tsakaninsu duk term ake samun first second and third position,saidai sukanyi exchange a tsakaninsu wata ta karbe position din wata.

Fadan me uwa inji hausawa sukace,idan ana masa mara uwa labewa yakeyi ya saurara ya kuma yi aiki dashi,dama da niyyar karatun ta shigo,haduwarta dasu afra yasa ta sake ninka qudurinta.

Kusan abinda ya tashi hirar qarar wayar afran dake daman katifarta,ayman ce ta miqo mata,tana duba number ta miqe ta haye gadonta basu sake jin motsinta ba,maimunatu dai na jinsu suna mata tsiya amma bata fahimta akan meye ba,don tayi nisa a tunanin yadda zata tafi da tata rayuwar,qarar wayar ya sanyata tunowa da tata wayar da yaa hisham ya bata,ta miqe ta haura,ta dauko tata jakar ta bude ta ciro wayar ta bude kwalin.

Ido da baki ta saka tana kallon kyan wayar,sai takega wayar tafi qarfinta,ko ba's gaya mata ba tasan mai tsada ce ainun,don haka ta bude cikin locker dinta ta turata ciki ta mayar ta rufe.

********Cikin kwanaki qalilan sabo mai qarfi ya shiga tsakaninsu,musamman tsakaninta da afra,irin sabon da ita kanta maimunatu tayi mamaki,saboda sabo ne da tun zuwanta duniya batayishi da kowacce halitta ba idan ba mahaifiyarta ba,tunda kusan a tsangwame ta tashi,batasan dangin mahaifinta ba,dangin mahaifiya kuwa babu wannan fuskar,wajen inna furera ma kam ba'a wannan maganar,bata jima sosai tare dasu anni ba bare ta gama tantance wannan,duk da dai alhmdlh,ta samu sakewa sosai dasu,don ma ta gaza sakin jiki dasu,wala'alla don tana musu kallon iyaye,su laila kuwa sun dan girme mata kadan,fa'iza da khadija ne kusan sa'anninta.

Yadda suke rayuwa basa boyewa junansu komai,infact tama lura kusan kowa yasan family din kowa,don ko waya daya tayi da gida zatace wance tana gaidaku,kusan tasan labarin kowa a cikinsu,har da na mahaifin afra da bashi da lafiya,wannan yasa itama bata boye musu ko wacece ita ba,ta shaida musu,saidai bata gaya musu tana da aure ba.

Zamansu tare ta fara koyon abubuwa daga garesu,kowacce nada tarbiyya gwagwadon iko,hakanan itama sun fara koyon nata dabi'un,ada basu wani damu da islamiyya ba,bata dadasu da qasa ba,suna zuwa,amma suna mata asha ruwan tuntsaye,zuwan maimunatu da yadda sukaga ta maida hankalinta ga zuwan,shine yaja hankalinsu,ita da kanta data fuskanci yadda malamin yake da sauqin kai fahimta da kuma iya koyarwa ya sanya ta roqeshi da kanta ya sanya musu wasu litattafan,hakan yayi masa dadi shima,saboda kusan itace daliba ta farko data fara mai da hankali kan karatun,harta nema a sanya musu wasu litattafan bayan qur'ani da ake musu,ba bata lokaci kuwa ya laluba litattafan da suka shafi fiqhu hadis da sira ya saka musu,tun dalibai da dama basu wani damu da karatun ba,sai gashi sannu sannu abun yana jan hankalinsu,ba'a wani bata lokaci ba islamiyya ta cika da dalibai,abun da ya fara tambara sunan maimunatu a makarantar,haziqa ce sosai musamman ta fannin islamiyya,bangaren boko ne yake dan bata kashi,saboda kusan jumping tayi,a sannan taga amfanin lesson din da anni tasa aka dinga yi mata lokacin da tana gida,ya taimaka mata matuqa da gaske,da batasan yadda zatayi da karatun makarantar ba.
*GURBIN IDO*
37

*AREWABOOKS:HUGUMA*
https://arewabooks.com/chapter?id=6364b8542730d61e0981706d
______________

Sanda sukai jarabawar first semester ta goma sha biyar tazo cikin su arba'in,ko kadan hakan bai mata dadi ba,saboda ta saba,har ta gama rayuwar primary dinta bata wuce ta biyar,bata nunama kowa ba sai aminanta kuma roommates dinta,afra ce tace

"Naga qoqarinki ma maimoon(sunan da suka koma ce mata kenan),a wata uku kacal kin doke mutum ashirin da biyar?" Kai ya girgiza sanda take hada kayanta,don a gobe kowa zai wuce gida hutu

"Ina qoqari a nan afreen(sunan da ita dinma take kiranta dashi),bazan iya nunawa kowa result dina ba"

"Zaki iya maimoon,i trust you,duk wanda ya iya arabic,boko bazai bashi wahala ba sam sam sam,boko minor abune akan arabic"

"Next time I will try my best in sha Allah" ta amsa mata tana sakar mata murmushi,tare da jin dadin irin qwarin gwiwar da ko yaushe afra take bata.

Washegari tana ta zuba idanun ganin wanda zayazo daukarta saiga yaa hisham,ya fito suka gaisa dasu afra,ya kuma gabatar musu da kansa da kansa a matsayin yayan maimunatu,sosai abun ya mata dadi,ya girmamasu ya kuma mutuntasu a mazauninsu na aminanta,su kansu sun nuna jin dadin hakan,afra taso su gaisa da 'yan gidansu,suga kuma sabuwar aminiyarta,to amma ya hisham din ya bada uzurin yana da patient da zai gani,dole sukayi sallama suka shiga mota.

Yana qoqarin tada motar ya lura da envelope din hannunta,wadda ke dauke da tambarin makarantar,sai ya miqa hannu

"Duk da ba'ayimin tayin ganin result din ba,nayi shishshigi,a bani na gani" idanu tadan zaro,ta yima kanta alqawarin babu wanda zai gani,har sai tayi abun arziqi,amma tana jin nauyin hisham din

"Ya hisham,don Allah.....ka bari sai next term saina hada maka da wannan din duka ka gani gaba daya" ta fada tana marairaice masa,wanda har ga Allah ita din batasan tayi ba,kamar yadda batasan mugun kyan da hakan ya qara mata ba,har sai daya janye idanunsa da sauri daga fuskarta yana fadin

"Subhanallah" cikin ransa ya furtata a hankali

"Ba matsala,Allah ya nuna mana" yadda taga yayi maganar yana tada motar ba tare da ya sake waiwayowa ba yasa taji babu dadi cikin ranta,sai taji kamar bata kyauta masa ba,don haka ta zaro ta miqa masa,sannan tayi qas da kanta tana jiran jin maganar da zai fada mata

"Kinyi qoqari sosai,ma sha Allah,wannan ne karonki na farko fa?" Ya fada cikin nuna qwarin gwiwa da kuma qarfafata,maganar tazo mata a ba zata,ta kuma bata mamaki,sannan kuma taji dadi gaki da sake samun qwarin gwiwa.

Ta zaci gidan abbi zai kaita,sai taga ya wuce da ita gidanta,bata tambayi dalili ba,bayan ya aje ta tayi masa godiya,ta kuma bashi saqon gaisuwa wajensu anni,tare da roqonsa a kawo mata amna.

Gyare gyare ta shiga yi,irin na mutumin da ya kwan biyu baya waje,sai data gama komai sannan ta sake wanka,ta kuma wuce kitchen ganin azahar har ta gota don ta samawa kanta abinda zataci.

Har zata shiga ta tuna da unaisa,sai taga bai dace tana cikin gida ba amma batasan da dawowarta ba,ko banza ta girme meta a shekaru,wannan tunanin yasa ta karkata akalarta zuwa sashen unaisan.

Knocking biyu aka tambayi waye,kai tsaye ta amsa da itace maimunatu,sai da aka dauki mintuna sannan ta bata izinin shigowa.

Zaune take saman doguwar kujerar falon nata,ta miqe qafafunta akai tana shan lemon fata,da alama tun dazun a hakan take a zaune,kawai dai batayi niyyar bata izinin shigowar bane,kallo daya tayi mata ta canza fuska ta kuma kau da kanta taci gaba da kallonta ga tv.

Koda ta gaisheta sama sama ta amsa

"Na dawo,nace bari na shigo na sanar miki" wata dariya ce ta zowa unaisa,ya tabbata ja'afar din mugun dan rainin hankali ne,hakazalika da biyu ya dauki yarinyar ya kaita makarantar kwana saboda ya raina ajinta da kwanyarta,to amma hakan yayi mata ita din,tunda ko banza kawo yanzun tana dan samun wasu sauye sauyen,duk da cewa ko sau daya bau taba hada dakin kwana da ita ba

"To yayi" tace mata kawai taci gaba da shan lemonta tana kada qafa gami da ci gaba da kallonta,ganin babu wani magana data sake hadasu sai maimunatun ta miqe zata fita

"Agwai" ta kirayeta da sunan da maimunatun tafita sanin me sunan yake nufi,sunan yadan sosa ranta,amma bata nuna ba ta waiwayo tana dubanta

"Am please idan kin tashi girkinki,ki dinga yi iya cikinki,wanda naci a baya ma shahada nayi,don ba abinci kowanne irin mutum nake ci ba,so ina da masu aiki,zasu dinga yin komai" kai ta gyada sannan tayo gaba tana bar mata dakinta.

Ga mamakinta sai taji maganganun unaisa sun dan sosa ranta kadan,abinda tun tasowarta da irin cin zarafin data gamu dashi a rayuwa bata taba jinsa akan kowa ba,ko hakan yana da nasaba da zama dasu afra?,hakan na nufin ta fara sanin kanta da kuma sanin mene ne rayuwa?. Muje zuwa dai.

Tunda ta dawo gidan bataga koda gilmawar J ba,abinda ko sau daya bai ɗaɗata da ƙasa ba,sau tari mancewa take dashi kwata kwata cikin rayuwarta,tasa litattafanta a gaba tana ta haddar hadisan data daukarwa malamin islamiyyarsu alqawarin zata kawo masa su kafin a koma hutu,da kuma izifin data diba shima zata daw da haddarsa,don hatta haddar qur'aninta bata bari ta tsaya ba,tana ganin wannan damar ta roqa alfarma,yake mata qari kuma tana kawo masa.

Ta fannin boko ma litattafan da zasu sake inganta mata koyo da gane turancinta ta karba aro masu yawa daga library din makaranta ta taho dasu,wadan nan abubuwa sune abokan hirarta,kewar da tayi fama da ita zamanta na baya a gidan yanzu duka babu,mantawa ma take da inda take,wani lokaci ma idan tayi breakfast bata sake neman abinci saina dare,batajin yunwa sam idan ta duqufa karatunta,bare kuma ba wani motsi zatayi me yawa ba bare ya zazzage mata cikinta ya jawo mata yunwar ba,tana daki kwance,saman gado idan ta gaji ta dawo falo saman kujera,ba kasafai take shiga kitchen din ba,dalilin da yasa har zuwa sannan batasan ma kalar 'yan aikin da unaisa ke maganar ta kawo ba,don sanda zata shiga da safe basu soma nasu aikin ba,lokacin da zata sake komawa kuma dare yayi sun gama nasu aikin sun bar kitchen din.

To da wannan damar data samu yasa tayi karatu me yawan gaske,wanda ita kanta batasan ta yishi ba,hutun da akazo gida don yinsa nata hutun kadanne.



Randa tayi sati a gidan,tana daga bakin window dinta ne taji cewa ja'afar din tafiya yayi ashe,ta bakin unaisan sanda tayi baqi take rakasu zuwa parking lot na gidan xasu shiga motarsu,saita janye zuwa ciki,ta bude shafin gaba na littafinta taci gaba da karatunta.

Sai da tayi kwana takwas da dawowa sannan su fa'iza suka zo mata,harda amnanta,ranar kamar sallah haka ta jita,sun sameta anata sana'ar wato karatu,amna na jikinta ta dauketa zuwa kitchen don ta sama musu abun sha,kafin tayi tunanin me zata girka musu.

Sanda suka shiga amnan nata mata tambayoyi da zuba mata surutu,tabbacin yarinyar tayi kewarta matuqa,bata lura da unaisa dake tsaye riqe da cup da yoghurt a hannunta ba har sai data kirayi sunan yarinyar,tare suka waiwaya zuwa gareta ita da maimunatun,maimunatun ta dubi yarinyar data zubawa unaisa idanu tana kallonta,duba na rashin sani da kuma rashin sabo

"come-on baby,new mom dinki ce" unaisa ta fada tana murmushi gami da miqawa yarinyar hannu,karon farko da yaro ya burgeta,kasancewarta ba ma'abociyar son yara ba,tsantsar kamanninta da silly mahaifinta din nan ya bayyana,tana fatan batayo miskilanci irin nasa ba.

Kamar kuwa yarinyar tasan me take rayawa a zuciyarta,sai ta noqe kafada tana ci gaba da kallonta

"Zo mu gaisa mana,haba amna,nace miki new mon dinki ce" ta sake maimaitawa dai,sai ta sake maqale mata kafada,wannan karon kallon fuskar maimunatu dake duba lemon da zata dauko musu tayi

"Wannan ce new mom dina,ke ban sanki ba" ba unaisa da yarinyar ta fadawa maganar ba,ita kanta maimunatu taji mamakin maganar,ta dago kanta tana duban fuskarta,waye ya gaya mata itace new mom dinta?,ya akayi ta fahimci haka?,duk da dai yarinyar nada wata muguwar kwanya da kaifin basira,wanda maimunatu tafi tsammanin daga wajen mahaifinta ta gajeta.

Sauke amnan tayi qasa tana dubanta

"Itama new momma ce,kije ki gaisheta kinji" saita gyada kai,duk da bata sake jikinta ba amma haka ta nufi unaisan,abun ya yuma unaisan ciwo sosai,yarinyar ma ba zata zo wajenta ba sai wannan agwai din ta yarje mata,ta kuma yi mata umarni?,ta zabgawa maimunatu harara sanda ta riqe hannun amna,hararar da maimunatun bata ma san tana yinta ba,da hilata ta samu ta janye amnan zuwa part dinta,saidai suna tsaka da hira sai ga daya daga cikin masu aikin unaisan sun dawo da amnan,idanu fici fici da alama rigima ko ma kuka tayi musu.

To hutun kwata kwata na sati hudu ne,suna gama satittikansu suka sake diba suka koma makaranta,maimunatu ta sake dasa yaqin neman karatu,babu ji babu gani,bakin rai bakin fama,su kansu su afrah sunyi mamakin yadda qwaqwalwar maimunatun ta sake budewa daga zuwanta hutu zuwa dawowarta,ta dings musu dariya ganin yadda dukka suke mata duban mamaki,a wani yammaci suna hanyar zuwa islamiyya,bayan ta bada amsar wata tambaya cikin subject din math,shi kansa malamin sai data burgeshi yadda ta amsa question din a gaban allo.

To bata qarasa basu mamaki ba sai da sukaje islamiyyan,duka ta zubewa malaminsu haddar hadisan data yo,a washegari kuma zai karba na qur'ani,wannan yana daya daga cikin abinda ya sake zaburar dasu suma,sannan kuma farat daya sunan maimunatun ya fara tambari cikin makarantar,tun daga juniors dinsu zuwa seniors,cikin watanni shida kacal ta fara zama sananniya,duk wanda kacewa maimunatu abubakar muhammad zaiyi wuya yace maka bai santa ba,dalibai maza da kuma mata,saboda zuwan da tayi da tarin baiwarwarki a lokaci qalilan,kyakkyawar bafulatar usul,wadda ke dauke da wani irin kyau mejan hankali,musamman da a yanzun take zaman makarata,daga dakunan kwanansu sai ajujuwansu na boko sai kuma masallacin makarantar inda a nan suke gudanar da islamiyyarsu,fatarta ta sake wani irin haske,kamar zata tabata jini ya fito,jajayen labbanta da bata sanya musu komai sun sake ja,hakanan idanunta masu wani irin kyau da suke dauke da golden din qwayar idanu,ita kanta takan jima gaban mudubi tana kallon kanta,tare da tambayar kanta ita dince kuwa?,itace maimunatun rugar ummaru?,itace maimunatun inna furera?tabbas ta canza,canji me nisan tazara kuwa.

Duk da cewa gayu da wasu dabi'u nasu afrah sun ratsata,har sun zame mata jiki itama ba tare data sani ba,amma hakan bai hanata yin takatsantsan da kanta ba,qwarai ta sani cewa ba daya suke dasu ba,ita din akwai auren wani a kanta,zuwa yanxu ta sake samun ilimi sani da kuma wayewa kan muhimmancin aure da girman matsayinsa saman kan kowacce diya mace,duk da cewa takan manta sosai da cewa ita din matar wani ce,don shi kansa wanda aka daura mata igiyar ta sanadinsa ba ganinsa take ba,wani lokaci sai taje hutunta har ta dawo baifi su hadu sau daya cikinn gidan ba,idan an samu akasi ne suke haduwa biyu,gaisuwa kusan itace maganar da take gilmawa tsakaninsu,har yau har gobe basu taba wata magana data gota babin gaisuwa da amsa ba.

Tana qoqarin tunawa kanta cewa ita din me aure ce,bawai don damuwa ko soyayya ba,haka kawai cikin ranta takeji bai kwanta mata ba ko kadan,me yasa bai dauko halin hisham ba?,hisham din mutum ne da take matuqar ganin kima mutunci da kuma martabarsa,bata ga alama koda ta kuskure da zata nuna maka yana mu'amala da wani abun maye ko shaye shaye ba,sabanin shi da tun ranar data fara ganinsa tasan cewa mazuqin taba sigari ne,sauran abinda kuma yake sha wannann Allah ne kadai ya barwa kansa sani,tunda ita a nata hasashen,duk wanda yake shan sigari to yana shan komai ma na kayan maye.

Abu na biyu hisham din mutum ne me kimanta dan adam da darajtashi,koda yaushe yana faran faran da ita dama sauran qannansa,a gu daya take ganin kamewarshi da nashi salon miskilancin shima,idan ya fita cikin mutanen da suke ba ahali a garesa ba,ko kuma baqin fuska,a duk sanda zai dawo da ita makaranta ko kuma zai maidata,hira ce me tsafta take wanzuwa a tsakaninsu,yakan bata shawarwari da qarin haske akan karatunta,labarai da suke da nasaba da karatu,kamar labarin lokacin da yake dalibin secondary kamar ta,takan iya sakin jiki dashi kadan yanxu,wannan baquntar da take masa a da yanzu ta ragu sosai,yayin da shi kuma yake girmamata kamar yadda zai girmama dan uwansa,har wani lokaci yakan bata kunya ainun,ganin cewa ya girme mata nesa ba kusa ba,ita yafi cancanta ta bashi wannan girman.





An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya

Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,

Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan
Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490

A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,

Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu

Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC

Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng
You can download more hausa novels there
Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online
It is free we do not charge for uploading novel
Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services

Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us

Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it

Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT

This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng
For feedback and support
Facebook : https://facebook.com/taskarnovels
Twitter : https://twitter.com/taskarnovels
Telegram : https://t.me/taskarnovels




DOWNLOAD
DOWNLOAD

2 Comments On GURBIN IDO
avatar
salima

12 months ago

Reply

Nice story

avatar
ibrahim-6-8

9 months ago

Reply

That's so amazing

Please Login or Register in order to submit comment