Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD



Ahmad yace shekaru talatin muna tare fa dan uwa taya za ayi barangane matsalarka ba


Hakeem yayi murmushi yace hakane amma bazan fada ba sai na musu

Jarabawa daya kaga daga tabbatar gidan danaje Neman iri


Next page
Your comments is needed fansd'd'd'd'd'


Anfara wasa fa fansd'd'd'd'

Sainaji ku
[05/05, 11:08 AM] UMMU AFAN <Ø9ß: <Ø—ß<Ø—ß<Ø—ß<Ø—ß<Ø—ß<Ø—ß<Ø—ß<Ø—ß<Ø—ß<Ø—ß<Ø—ß<Ø—ß<Ø—ß<Ø—ß<Ø—ß<Ø—ß<Ø—ß<Ø—ß<Ø—ß<Ø—ß<Ø—ß<Ø—ß<Ø—ß<Ø—ß<Ø—ß<Ø—ß<Ø—ß<Ø—ß<Ø—ß<Ø—ß<Ø—ß<Ø—ß

BISSIMILLAHIR RAHMANIR RAHIM


<Ø—ßHAKKIN MALLAKA NA UMMU AFAN <Ø—ß


<Ø9ß<Ø9ßFIRST CLASS TECHNOLOGIES WRITERS ASSOCIATION<Ø9ß<Ø9ß

<Ø9ßF.C.T.W.A<Ø9ß



<Ø9ßHOME OF QUALITIES AND TRUSTED WRITERS OF THE NATION<Ø9ß



<Ø—ßDEDICATE THIS PAGE TO sis JIDDER (BAEWAR ALLAH)
WANNAN PAGE IN NAKI
SABODA KAUNA DA KIKE NUNA WA WANNAN
NOVEL NAWA NA
<Ø—ßAKWAI LOKACI<Ø—ß
Allah yabar zumunci keep it up =ØÞ=ØÞd'd'



Masu comment ina sane da Ku kafin na kamla littafin nan duk sai kunji sunanku daya bayan daya so kucigaba da bin ummu afan takuce d'






<Ø—ßAKWAI LOKACI<Ø—ß





<Ø—ßPAGE 66 to 70<Ø—ß





PROF HAKEEM zaune kan resting chair dinsa a bakin sweeming fool yana shan iska dan yanzu yafito daga cikin ruwan

Wayarshi ta daukara yana dubawa yaga dalibata wato mummynshi kenan dan sunan dayasa mata kenan

Bayan sungaisa Hakeem yace mummyna albishirinki mummy hafsat tace goro

Yace naga matar aure a kano fa

Cikin tsananin farin ciki mummy hafsat tace alhamdulilla naji dadin wannan albishir

Yaushe zakazo katura mahaifinka gidansu yarinyar


Hakeem yayi murmushi yace daliba kenan ai ban ma taba fada wa yarinyar ba nikadai nake kida kuma nake rawa na

Mummy tace shirme ni harkasani ina murna to idan bazaka iya fada mata nika nuna min gidansu yarin sai naje

Ayau saina zo kano wallahi akanka my son

Hakeem yayi murmushi yace nasani mummy na

Nasan zakifi kowa farinciki shiyasa nafada miki tunkafin na fada wa yarinyar

Sai mummy Kinsan masu soyayyar Allah kadan suke aduniyar nan

Kuma dadin da dawa ma yarinyar danagani din ba masu karfi bane

Kinga idan naje kaitsaye Kuma akayi rashin sa a saikiga sun soni don kudina badan Allah


Mummy taja numfashi tace hakane son sai dai zuciyata tana bani bazataba son abinda baidace dakaiba


Hakeem yayi murmushi yace Kinsan menakesonyi mummy tace a a son sai kafada

Yace zan jarabasu nagani zanje amatsayin talaka banida komai

Ingani zasu karbeni kokuwa


Mummy tace hakan ma tayi son dina
Kuma ina maka fatan alkairi

Insha Allah zasuci duk wani jarabawar da zakayi musu

Wasunan surukartawa Hakeem yayi murmushi mummy ta sosa mishi inda yake mai kaikayi

Yace ai harma tazama surukarki
Mummy tace aiba surukaba ma 'yata zama son

Hakeem yayi murmushi yace asmau amma anakiranta da HUSNA


kai masha Allah ashema babban suna ne da ita

Insha Allah asmau zata Mata agareka tun kafin naganta naji inasonta


Hakeem yace shiyasa nakeson Ku iyayena kuna matukar daraja abinda nakeso

Allah yabani matar da zata bauta muku da zuciya daya badan kudinku ba ko kudin danku


Mummy hafsat tace aikasamu son zantayaka da addua




****

Washagari Hakeem Bayan sungama komai ya shamsu yazo musu sallama zai wuce gida dan karfe hudu yake tashi a lectures


Ahmad yace wa ya shamsu yaufa kafanmu kafarka zamuje mugaida Abba da umma

Dan idan muka biye maka bazaka gayyace zuwa samun ladan nan ba


Ya shamsu yayi dariya yace shikenan idan kun shirya muna iya tafiya

Hakeem yace na dauka zaka kawo wani excuse ne ince ai ba umma kai kadaibane muma namune


Ahmad da ya shamsu sukayi dariya

a motar Hakeem akatafi ya shamsu agaba Ahmad yabaya

Ya shamsu yana nuna wa PROF HAKEEM hanya




******

HUSNAH ce zaune tsakar gida tagama aikin gidan kenan tas ko ina yadau kamshi

Ita kuma anty kubra tana kitchen tana hada abincin dare Wanda sudama kafin biyar sungama komai sun zuba a kula

Kuma aikin sukayi Husnah da kubra yau idan kece da aikin gida to dayar kuma saitayi abinci

Yau Husnah ce da aikin gida

Tagama komai da wuri tana wa anty kubra dariya tana kitchen dan yau ya shamsu yace ayi tuwon semovita miyar kubewa danya
Har kudin danyar kifi yabayar



Anty kubra tace zanrama ai Allah yasa ran girkinki Abba yace sakwara yakeso

Husnah tayi murmushi tace kai ai danagane kuskurena kuwa


Umma datake jinsu tace tun tuni kinjuye ruwa Yakama kishiga kiyi kisamu kifito kije min aika ko


Husnah tace to umma
Umma ta kalli kubra tace sannu kinji kubra Allah dai yamaku albarka yabaku masu yimuku kuma

Kubra acikin zuciyarta ta amsa da amin dan tana jin kunyar umma idan tace Allah yabasu masuyi musu



Husnah tafito daga wanka tayi dakinsu tashafa mai tadauko powder tashafa sai kwalli sai tasa lips glow alebenta


Tabude akwatin kayan ta tafara zaban wadda zata saka

aikuwa idon ta yakai kan wani material pink da kuma ratsin baki ajiki Wanda ya shamsu yamata a bikin shi

Tunda tasa a biki batasake sawaba

Sai tadauko shi tasaka dinki duguwa Riga ce
Daga sama ya dameta sosai dan Husnah fa akwai kayan aiki

Shiyasa umma bata cika barinta fita da gyaleba saidai hijabi dan Allah yamata kira

Husnah takalli kanta a madubi itakanta tasan tayi kyau sosai

Sai kuma tasan dakyar umma zata bari tasaka gyalen material din

Itakuma yau mayafi takeson yafawa

tace barin gwada dai tagyara gashinta tadaure da ribbon fari
Kafin tayafa gyalenta dan bata saka dankwaliba
Kota saka dankwalima abanza
Dan bayazama akanta sabonda tsantsin gashinta


Tadauko turarenta tafesa kafin tadauki Jakarta na suwaga pink da takalminshi duk pink tasaka
Kai masha Allah da wannan kyakkyawar hallita


Tafito tace umma nafito
Umma ta kalli 'yartata tace au da wannan gyalen zakifita

Husnah tace Allah sarki umma na gyalen kayan nefa

Kuma kinga kayan ai yana da fadi sosai
Kafin umma tayi magana anty kubra taleko tace umma dan Allah kibarta wallahi tayi kyau kuma kinga ai kayan yana da fadi

Umma ta ce wato bakinku daya ko to shikenan kije Allah yakiyaye hanya

Husnah tace to umma baki min bayaninba umma tace kinci gidanku yau kika saba karbomin zuman ne

Husnah tayi murmushi dimple dinta tsuka lotsa sosai
Tace to ummana afuwan nadauka bakaman na kullum bane


Tayi waje sukace mata adawo Lafiya




adai dai kofar gidansu ya shamsu yanuna wa Hakeem yayi parking

Suka fito atare Ahmad yace kashiga saikamana iso

Ya shamsu yace to shikenan yaya cikin gidan alokacin umma ce kadai a tsakar gida kubra ta fito mata da taburma
Dan anna suke hirar Daren su gadaya

Ya shamsu yayi sallama umma tace a a ubana har andawo yace a umma yagidan nan dai yagaida umma kafin yace umma daman su ogana na office ne sukazo gaisheku

Umma ta ce shine kabarsu a waje kuma sushigo ciki dan Allah haba waje

Ya shamsu yaje ya musu iso zuwa cikin gidan

Umma ta ce kashiga dasu daki Ahmad yace a umma mu kusa da ummanmu zamu zauna basai munshiga dakiba

Umma taji dadin har ranta tace to shikenan 'ya'yan ummu kuzauna nan suka kwashi gaisuwa agurin umma ta amsa cike da farin ciki
Nan kuma ta musu godiyar hidimar dasukeyi da su

Hakeem yace haba umma ai mu da shamsu Yanzu munzama 'yankuma bagodiya tsakaninmu ai yiwa Kaine

Umma ta ce hakane kam Allah yake mutum da mutum
Kodai Allah yasaka muku da aljanna

Umma ta ce wa shamsu ubana aisai kayi maza kaje nan shagon mati ka karbo musu lemu mai sanyi da ruwa

Hakeem yace haba dai umma mufa ba bakibane

Komai ummanmu tabamu cizamuyi
Ba umma ba harta ya shamsu yaji dadin wannan kara da Hakeem da Ahmed suke musu

Sallmar HUSNAH ce yasa Hakeem daga ido yakalli hanyar waje aikuwa suka hada ido cikin ido Husnah tayi saurin dauke idonta dan dama akasi aka samu ta kalleshi

HAKEEM yasamu Kansa cikin wani yanayi Wanda yakasa fassarashi ba Ashe ganin da yayi mata a school ma tafi haka


Husnah ta durkusa har kasa tagaishe da su Hakeem Ahmad ne karfin amsawa shikam ogan ba baki
Yakasa komai ne

Ba Wanda ya kula da canzawarshi sai Ahmad

Ahmad murmushi yayi shikadai

Kubra tafito tagaishesu

Ahmad yace ai kawarki basan zamuzo ba dakinganta

Kubra tace dan allah yakawo mata Aisha Dan zaman da sukayi a gurin graduate dinsu Husnah sun saba sosai


Ahmad yace ya mata alkawari ran sabar zai kawo Aisha tamata wuni daga nan tagaida umma

Umma ta ce Allah yakawo ta Lafiya umma na maraba da ita

Husnah da kubra suka kawo musu abinci a kula da biyu suka ajiye
Husnah tadauko plate guda biyu da serving spoon duk ta ajiye musu

Sai ta dauki jug ta kawo musu ruwa maisanyi na randar umma ta kawo musu da cups biyu


Umma ta ce maza hada musu zobo Husnah
Husnah tace to umma ai na dafa tunda dazu hadawa kawai zanyi saidai ba kankara


Ya shamsu yace hada barin karbo kankara

Ya shamsu yafita jimawa kadan sai ga shida kankara yakawo yaba wa husnah

Hadaddan zobo ta hada Wanda yasha kayam kamshi da cocumba

Tasa musu a jug shima takai musu kafin ta wuce dakin anty kubra umma tace bara nashiga kuci abincin Ku

Ya shamsu yace bissimillarku kuci abinci

Hakeem yayi murmushi yace aiko baka fada ba

Ahmad yayi murmushi dan yasan dalilinsa na fadar hakan

Hakeem yayi serving kanshi

Tuwo daya yasaka sai sai yasa miyar baiga ruwan wanke hanuba sai

Yace yaya shamsu ruwan wanke hanu dan bana cin tuwo da cokali

Ya shamsu yayi dariya yace amma yallabai kaso barkwanci ninekuma yayan
Hakeem yayi murmushi baice komai ba

Ya shamsu yakira Husnah takawo ruwan wanke hanun

Takawo ta ajiye gaban ya shamsu shikuma ya mikawa Hakeem gabansa


Hakeem sosai yaci tuwon dai Bayan ya cinye Leda daya sai ya kara Ahmad nema yarage kadan

Ya shamsu yace haba yallabai dan Allah kacinye wallahi umma zataji dadi

Hakeem yace rabudashi ya shamsu tsoron madam Aisha yakeyi kartatsareshi sai ya cinye abinta yakasa Bayan yacinye na gidan umma

Duk suka kwashe da dariya
Hakeem yatsiyayi zobon da Husnah ta hada musu yasha

Aikuwa yaji kunnenshi kaman zai yanke dan dadi
Kodan ya hadu da soyayyane oho


Kafin yayi magana Abba yashigo dattijon arziki

Duk suka mike tsaye sai da Abba yazauna suka zauna suka kwashi gaisuwa

Ya shamsu yagabatar dasu

Abba yace a manya baki ne damu agidan Ashe
Nan shima yashiga musu godiyar hidimansu akansu



Sun dan taba hira kafin Abba yashiga daki yabarsu nan da ya shamsu


Hakeem yace Gaskiya ya shamsu wannan zobon asamin awani Abu natafi dashi zansha zuwa dare


Ahmad yace narigaka azuci karigani a baki dan kasan duk inda nasha abinda yamin dadi sai narage wa madam

Hakeem yayi murmushi yace kai man kafadi gaskiya

Ya shamsu dai dariya yakira Husnah yace tasamo jugs guda biyu ta zubo zobo tace to

Hakeem tabita da kallo komai na yarinyar yamishi Dari bisa Dari
Tana da duk wasu qualities din dayake bukata ga mace


Husnah ta zuba takawo ta ajiye
Ta yigaba abinta

Sai da akakira magrib suka yi sallama da su umma da Abba da anty kubra

Husnah tana kan sallaya idan tayi magrib bata ta shi sai tayi isha


Hakeem yaso yasake ganin Husnah

Amma taki fitowa

Ahmad ya ajiye bandir din kudi 'yan dubu dubu yace a ba wa kanwarsu tasai kayan kwalliya

Ya shamsu yace dan Allah karmuyi haka kudauki kudinku

Ahmad yace ai nariga na ajiye kuma ma aibakai muka ba ba kanwarmu muka ma kyauta


Da kyar ya shamsu yabar kudin nan

Suna cikin mota Hakeem ya karya kwana zuwa baibi hanyar gida ba

Ahmad yace man yana zaka kaimu kuma Hakeem yayi murmushi yace sa ido kawai kayi kallo man

Ahmad yace OK baringa ikon Allah to

Hakeem yayi parking adai dai gurin wani malamin almajirai suka sauka

Malam na ganin HAKEEM yataso yazo sannu da Zuwa professor Hakeem yayi murmushi suka gaisa da malam Garba

Malam Garba yace mukarasa daga taburma nan suka karasa

Hakeem yace malam bawani Abu yakawoni ba illa Neman wata alfarma

Malam Garba yace alfarma kuma alhaji da kanka
Hakeem yace a malam

Aure nake nema malam

Amma kasan rayuwa ta baci yanzu sai aureka badan anasonkaba sai dai don abinda kakedashi


Malam yace hakane

Hakeem yaja dogon numfashi
Ya kalli Ahmed da ya kagu yaji dalilin abokin nashi nazuwa nan


Hakeem yace malam zanje Neman aure da sunan talaka talakan ma futuk Mara iyaye

Koda anzo Neman tarihina guringa za azo dan
Kai zanfada a matsayin malamin danayi karatu agurin shi

Kai kuma inason kanuna tun ina karami aka kawo maka ni


Wannan kadai nakeson kamin malam

Malam Garba yayi murmushi yace gaskiya alhaji kana da tunani mai kyau Allah ya tabbatar da alkairi

Hakeem da Ahmad suka ce amin malam


Nan suka wa malam sallama Hakeem yadauko bandir din kudi yaba malam yace gashi a rabawa yara sadaka

Ya ba malam wani kuma yace Gashi wannan nashine

Malam Garba yayi ta musu addua


Acikin mota Ahmad yace amma meyasa makayi wannan tunanin haka Hakeem

Ahmad yace kana nufin bazasu ganeka ba wai kome

Hakeem yayi murmushi yace duk zan shirya wa hakan

Ahmad yace Allah yasa amma dai yakamata duk wani abinda zakayi wallahi kayi sauri kafin wani yariga ka


Hakeem yayi murmushi yace inaji ajikina wannan yarinyar rabonace

Ahmad yace to tunda kana da tabbacin haka
Meye na gwada ta kuma

Hakeem yace inason nasan mena aura ne kuma rayuwata zanbata kaga kuwa ina bukatar bincike sosai


Ahmad yace sai prof komai naka daban ne wallahi gaskiya bazan boye maka ba I like your life style Bros
Keep it up

Hakeem yayi dariya yace baka jiya abokina

Ahmad yace ai bazangaji

Komai naka is so special


****
Bayan sati uku Hakeem yayi order na fuska daga India

Yau yakesaran za akawo mishi

Hakeem ya zaune wani abokin
Wayar shi tadau kara yana sai yaga number din Wanda yaba sautun siyo mishi fuska

Yadaga wayar yace badai har kun isoba
Doctor isah yace gani ma acikin school dinku

Hakeem yace what's a surprise
Ganin zuwa

Hakeem yafita yaje yashigo da doctor isah

Nan Bayan sungaisa doctor isah

Yafito mishi da sakonsa

Hakeem yakarba yace masha Allah kuma gaskiya kayi yadda nace

Doctor isha yace to ai kasan aikan manya irinku ba kasafai akacika muku shirme ba

Hakeem yace zakafara kaima ko

Doctor isha yayi murmushi yace ansamu ragi sosai yallbai dan Rabin yakai dubu Dari da hamsin

Hakeem yace OK zaka iya barinshi a wajenka yazama naka doctor

Doctor yace a yi haka yallabai
Hakeem yace karka damu ai kamin komai



***

Da daddare Hakeem ya fesa wanka yadauki jallabiyya yasaka yadauko fuskarsa yasaka kafin yadauki carbi yarike a hanu

Yadauko wayar Nokia da yasa akasayo mishi second hand wacce duk tasha dauri da roba

Ya kalli kanshi a madubi shida kanshi yaba kanshi dariya

Yadauki kudi yan hamsin da kuma 'yan goma yasaka a aljihunshi


Ya kulle gidanshi yafita zuwa gidan Ahmad yayi sallama
Maigadin yace sannu malam daga ina haka kuma gurin wakazo

Yace inason kamin sallama da maigidan ne

Bayan Ahmad yafito ne yaga mutum ustaz har da gemunshi

Yace assalmu alaikum

Hakeem ya amsa mishi cikin canjawar murya


Hakeem dai yakasa danne dariyar shi yacire fuskan

Ahmad wazaigani Hakeem ne

Cike da mamaki Ahmad yace amma ka shammaceni

A ina kasamu masks nasan dakyar akesamu a Nigeria

Hakeem yace daga India aka kawo min
Kaga kai ma danake tunanin zaka ganeni baka ganeniba

Bana tunanin shamsu da mutan gidansu zasu ganeni

Dan haka ni wuce daga yau zafara basu exam's din su

Hakeem ya mayar da fuskarshi yagyara da kyau yadda baza a ganeba
Yayi bakin titi yatari kekenapep zuwa anguwar su Husnah


Next page

Tofa fans za afara wasa fa

Your comments is needed

Ina alfahari da masoya novel na<Ø—ß AKWAI LOKACI<Ø—ß



=ØÖÜ=ØÖÜ=ØÖÜ=ØÝÜ=ØÝÜ
[05/05, 11:08 AM] UMMU AFAN <Ø9ß: <Ø—ß<Ø—ß<Ø—ß<Ø—ß<Ø—ß<Ø—ß<Ø—ß<Ø—ß<Ø—ß<Ø—ß<Ø—ß<Ø—ß<Ø—ß<Ø—ß<Ø—ß
<Ø—ß<Ø—ß<Ø—ß<Ø—ß<Ø—ß<Ø—ß
<Ø—ß<Ø—ß<Ø—ß<Ø—ß<Ø—ß
<Ø—ß<Ø—ß<Ø—ß<Ø—ß
<Ø—ß<Ø—ß<Ø—ß
<Ø—ß<Ø—ß
<Ø—ß
BISSIMILLAHIR RAHMANIR RAHIM

Story & written
By
The special writer


UMMU AFAN

=ØŠÝ=ØŠÝ=ØŠÝ=ØŠÝ=ØŠÝ=ØŠÝ=ØÚÜ



<Ø9ßFIRST CLASS TECHNOLOGIES WRITERS ASSOCIATION<Ø9ß


<Ø9ß<Ø9ß (F.C.T.W.A)<Ø9ß<Ø9ß



<Ø9ßHOME OF QUALITIES AND TRUSTED WRITER'S OF THE NATION<Ø9ß




<Ø—ßI DEDICATE THIS PAGE TO YOU sister surayya auwal ina matukar jin dadin comments din ki amma Dan Allah sister kikara yawan comments din ki ina alfahari da Ku da da comments din ku<Ø—ßd'd'd'd'd'





<Ø—ßAKWAI LOKACI <Ø—ß





<Ø—ßPAGE 86 to 90<Ø—ß





HUSNAH zaune tana gyaran farcenta Umma tace auta nikam ya kukayi da Alhaji ne naga jiya yazo


Husnah ta bata fuska tace wallahi Umma guduwa nayi dakin anty kubra na buya Dan wallahi Umma nibana sonshi


Umma tayi salati tasanar da ubangiji
Tace aidaman zaran hijabin dakikayi kaman kinje
Bazuwa kikayi ba


To ma wai meyasa bakya sonshi meyamiki husnah karki zamo me saka alkairi da sharri mana


Tunda Allah baiyi aurenki da shi abdullahinba sai ki ba
Wannan dama kodan halinsa na kirki badan abin hanun shiba



Anty kubra tace wallahi Umma kullum sai namata wannan nasihar amma kamar anshuka dusa



Husnah tace wallahi ni kwatata bana jin zan iya son wani bayan ustaz ne

Kuma bana son na aureshi nakasa yimashi biyayya Umma na Dan Allah kufahimceni


Umma tace ai shi so ahankali yake shiga
Kyawawan halaiyar wannan yaro kadai zaisa kifara sonshi azuciyarki

Dan yana da duk wani nagarta atare dashi



Kafin Husnah ta yi magana ya shamsu yayi sallama yashigo yazauna

Yana gaida umma kubra ta tashi tace sannu dazuwa tayi hanyar fridge tadauko mishi ruwa maisanyi

Takawo mishi

Ya dauka yasha kafin yakalli umma yace mekuke ta tattaunawa ne ummana

Umma tayi murmushi tace wallahi wannan shasharce muke taba baki saikace wata uwarmu
Sai waina mu takeyi


Ya shamsu ya kalli Husnah yace wai meyake damun kine husnah

Ustaz yariga yatafi bazai dawoba
Wallahi husnah da ace zaidawo lokacin da akeshirin daurin auranki da Abdul Hakeem za afasa a daura dashi

Sai dai kash ba a mutuwa adawo

Sai dai ina miki albishir dacewan Allah yamiki sakayya da mafificin alkairi


Mun dade muna Neman hanyar da zamu sakawa wadan nan mutane

Sai gashi Allah yakawo tunda yasawa yallbai kaunar ki aransa

Maizai hana kitayamu maida alkairi da alkairi husnah


Abdul Hakeem yamana komai a rayuwa kuma duk abubawan da yayi mana na tabbatar Dan Allah yayisu


Kaman yadda kema zamu bashi dan Allah badan abin hanun shiba



Husnah tace shikenan yayana
Namaka alkwarin bazan baka kunya ba
Na amince da shi
Amma wallahi danku Dan wallahi yaya bana sonshi



Ya shamsu yayi murmushi yace Abu mafi mahim manci dai shine ki amince



Husnah ta turo bakin shagwabar tace wato bakadamu dani bako yaya na



Ya shamsu yayi dariya yace caf waya fada miki yar kanwata
Yace ai nafi jidake

Dan idan kikayi aure ma fa tare zamu tafi


Husnah tayi murmushi tace ai wallahi yaya da dagaske kake da naji dadi sosai


Amma nasan kana fada be kawai
Amma nifa kullum sai nazo gidan nan



Umma tace kwarai kuwa daga ke har yayan naki zan ga me hankali acikin Ku


Anty kubra tace gaskiya kam umma
Nima naga alama tana dariya

Ya shamsu yace dawa kikeyi yadauki pillow na gefensa ya wurga mata ta tashi
Tagudu yabita shima


Umma tayi murmushi Dan yadda Dan ta guda yake zaune lafiya da matarshi bata taba ganin wani abun ki agurin kubra



Husnah tace umma Dan Allah yau kimana danbun tsaki da kanki
Kinga yau nice da girki


Umma tayi murmushi tace naki wayon sai girkin 'yata azo zanyi


aikuwa husnah tayi murmushi duk kugama badaini ba wato sai ran girkin anty kubra zakiyi ko
Shikenan nasan mezanyi muku a gidan kuma dole kuci


Umma tayi dariya tace kinga kuwa kyayi aiki har dare kenan



Husnah tayi murmushi ta tashi tace Abba yakusan da wowa

Barin yi kitchen

Tana shiga kitchen din tafara tunanin abinda zata daura

Taduba store dinsu taga suna da doya

Tadauki guda biyu tafere shi tas ta wanke
Ta rarraba shi kanana
Tazuba tunkuya takawo gishiri tasa dai dai misali



Kafin tadebo albasa attaruhu da tattasai dakuma tomatoes amma kwaya hudu tasa tomatoes din bata bukatar tumatir dayawa

Nan ta wanke komai tas
Tafara greating dinsu a greater ba a blender ba

Dan bata bukatar suyi laushi

Nan tasoya su da mangyada saidataga tayi soyu sannan tadauko yankakkakun kayan namanta kanana dake cikin fridge tafashashshe
Tazuba tadauko gyararran kifinta Wanda tariga tacire kayar tas shima tazuba tacigaba da juyawa

Kafin tadauko maggi tazuba dai su curry da thyme da dai sauransu


Tahada tacigaba da soyawa haba ai nan da nan gida ya hau kamshin girkin husnah

Sai da ta tabbatar ya soyu kafin tarage gas din kadan

Tadebo kwai (eggs) guda biyar
Tafasa su a kwano daban tasaka magi guda daya takada

Kafin tadauko tana zubawa kadan kadan tana gaurawa har tagama tacigaba da juyawa

Gaskiya ko itada datayi miyar yakayatar da ita balantana Wanda saidai yagani kawai saici

Nan ta sauke tasama Abba a kulansa kafin tasa ma umma ma anata kulan

Ta ajiye a gefe
Tadauko nasu ya shamsu da anty kubra tasamusu dama tumsafe tayi kunun ayarta Wanda yasha madara tasaka a fridge yayi balin sanyi kuwa


Ta dauka nasu yaya shamsu tayi da shi part dinsu
Taje tana ta sallama taji shiru

Can saiga anty kubra tafito da gudu daga bedroom dinsu kanta ba Dan kwali ga gashinta duk an hargitsa

Ga rigarta zif din agaba yake kana ganin kasan akwai magana Dan anfara Jan zif din amma baikai kasaba



Kubra bata San ma da mutum a falonba ganin husnah kawai tayi tasake baki tana kallonta


Kubra ganin kallon yayi tace ke malama lafiya kuwa


Husnah tayi murmushi tace a a bakomai gani nayi kinfi to kamar wacce tayi dambe da zaki

Takarasa maganar tana dariya


Kubra tasan metake nufi
Itama tayi murmushi tace kema kwana nawane zakije fada da zakin


aikuwa husnah tabarai ta turo bakin tace zakifara ko anty kubra
Ta ajiye musu abincin tace gashi idan kungama soyayyar kwaci

aikuwa tana fadar haka tagudu


Kubra tayi murmushi kawai kafin ta koma ciki




Husnah wanka tafada tana fitowa tayi sallar La asar dinta kafin taje gaban dressing mirro dinta tafara shafa mai abinta tanagama shafa maidin tadauko body spray tafesa kafin dauko wani doguwar rigar English wear tasaka


Ta dauki gashinta daure da ribom baki kasancewar kayanta marun colour ne

Yana da bakin dankwali tadaura tayi daurin tauban
Tasaka jambaki shima marun colour gaskiya ba karya duk Wanda ya kalli husnah sai yaso yasake kallo


Kayan dama dayane daga cikin kayan da mummy hafsat takawo mata ne

Ta fito tasami Abba da umma sungama cin abincinsu

Abba yayi murmushi yace autar Abba gaskiya abincin yayi dadi wallahi
Waya koya miki ne autar ummanta


Umma tayi murmushi aini wani girkin ma fa kirkiran abinta takeyi kuma saikaga yayi dadi


Husnah tayi murmushi tace aini a school dinmu Abba food &nutrition naza ba akan agriculture

Abba yace kai amma auta ta kinyi dabara

Umma ce takatse musu zancen nasu

Tace anya kuwa kinci abinci Dan nasan halinki sarai idan ba aganki ba saiki kai har goma na dare bakici komai ba



Abba yace wai har yanzu rashin cin abincinta yanan
Umma tace sai abin da yakaru

Idan tagadama wataran dakanta zata dafa indomie

Ya shamsu ne yashigo falon yagaida iyayen nasa

Ganin fitowar ya shamsu yasa husnah zuwa gurin kubra


Wayar ya Shamsu yayi kara yana yaga yallabai kamar yadda ya saving wayar


Yadauka bayan sungaisa prof yakecewa gani acikin gidanku

Ya shamsu yace haba yallabai kaman wani bako kashigo mana

Hakeem yayi murmushi yace ai gurin matata nazo katurota Dan Allah yakashe wayar yana dariya

Ya shamsu yafada wasu Abba Hakeem ne yazo

Abba yace ya zai tsaya a waje kuma kaje kashiga da shi falonku tunda yau surkunta yakeji damu

Umma tayi murmushi tace ina ruwan Abdul Hakeem yaron kirki wallahi


Ya shamsu yaje suka shigo tare da Hakeem harkasa Prof yatsuguna yagaida su umma

Kafin ya shamsu yace mune daga ciki tana can ma
DOWNLOAD
DOWNLOAD

2 Comments On AKWAI LOKACI
avatar
musa-6-3-2

7 months ago

Reply

Akwai lokaci

avatar
oumara-wassai

4 months ago

Reply

Replying to musa-6-3-2

17866

Please Login or Register in order to submit comment