Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD




Suna sallama dai dai lokacin husnah take gwadawa kubra rawan ittiki

aikuwa Hakeem idonsa kyam akanta ya shamsu yace to dancer of the year

Anty kubra tayi dariya tace sannu dazuwa tana wa Hakeem cike da kulawa ya amsa tareda tambayarta gida


Nan ta tashi tayi falon su umma Husnah zata bita ya shamsu ke dawo nan baki iya gaisuwa bako


Cike da jinkuyar Prof tun ranar daya ganta half nacked bata kaunar su hada ido

Tadawo tazauna gefen ya shamsu kai a kasa


Ya shamsu yace to yallabai saika fito


professor Hakeem yace Weldon ya shamsu
Ya shamsu yayi murmushi yafita


Hakeem yamaida kallonshi kan husnah wacce take ta wasada da yatsunta daya sha Jan lalle


Batayi tsam Mani ba kawai taganshi agabanta


Zama yayi kasan shima yana fuskantarta

kasa dagowa tayi saboda kunyarshi gashi itadai bawani sonshi take ba


Yace tunda nibaza a gaisheniba nibarin gaisheda my wife


Dafatan kin wuni lafiya kasa amsawa tayi

Yace koki amsa gaisuwata konasa hanu na dago da fuskarki



aikuwa bashiri tadago tace cikin shagwabbiyar murya tace kayi hakuri karka tabani ina wuni


Professor Hakeem yayi matukar kaduwa jin wanann murya na husnah

Gawani masifaffan kyau tamishi

Kayan data sa ajikinta kaman Dan ita akayisu

Prof jiyayi kaman ya rungumeta a kirjinsa kozai zamu saukin sha'awar data taso mishi lokaci daya


Husnah ganin hanun Prof kawai tayi yadanki hanunta

Cikin tashin hankali husnah tabi hanunshi da kallo

Yace baby kinsan damuwata wallahi kece ina matukar son kasacewa dake amatsayin mata

amma haryanzu bansan matsayina ba agurinki
Husnah tace zanfada maka amman saika sake min hanu

Hakeem yayi murmushi yace shike nan inajinki


Husnah tafara magana tace na'amince zan aurekà amma bana jin zaka sàmi soyayyata Dan nariga nagama soyayya a rayuwatà Dan ni kwata kwatà soyayya bai karbeniba


Kar sàinafara sonka kaima narasàka

Takarasa maganar da kuka mecin rai


Hakeem jiyayi kukan har cikin ranshi yadauko hand kacif a aljihunsa fari Sol yasha kamshi yamika mata

aikuwa ganin hankacif din nan saiyada ta girgiza

Ta karba dasauri tace Dan Allah yaya a ina kasamu wannan hand kacif din

Hakeem yace nawane kokina sone cikin sauri tadaga kai tace Dan Allah kabarmin wallahi irin Wanda ya muallim yake amfani dashine

Koranar da zamu rabuma shine a hanunshi

Takarasa maganar hawaye mai tsanani Hakeem yace banason kukan nan kigoge fuska kimin magana Wanda yamutu ai yamutu


Husnah tayi murmushin data kumatunta lotsawa sosai

Tace aikuwa sai dai kayi hakuri Dan har abada bazan daina tunaninshi ba saboda yatafi da zuciyata gabadaya


Hakeem yaji matukar jintausayinta kaman yarungumeta ya rarrasheta


Husnah tacigaba da bashi labarin soyayyarta
Akan bashir da abinda yayi mata bayan tadauki zuciyarta tabashi lokaci kawai akejira ayi biki amma yafasa
Kuma yakoma suna soyayya da babbar kawarta


Sannan takarabashi labarin masoyin asali ya muallim


Hakeem yace nikuma na godewa Allah nakuma godewa saurayinki dayace yafasa

Dan da befasaba danayi asarar zukekiyar yarinya kamarki

Kinga kuwa nidan gatan Allah
Akaro nabiyu yasake kama hanun Husnah yace please baby kiyarda dani

Yakura mata ido tace naji amince amma kasake min hanu Dan Allah bakyau fa

Hakeem yace nasani baby shiyasa nakeson abanike a matsayin mata saboda banason nacigaba da sabawa Allah taba jikinki batareda aure ba
Because I can't control my self in front of baby


Husnah ta tabbatar dagaske yakeyi
Tayi murmushi bara maka ruwa da lemu

Yaji dadi har ranshi data nuna kulawar ta agareshi

Murmushi kawai yayi tare da 'daga mata gira ta tashi zata je sai kuma taga idonshi akanta

Ta juyo a shagwabe please yaya kajuya kadaina kallona inbasokake nafadiba


Maganar yaba Hakeem dariya yace jeki na rufe idon


Da gudu kuwa tafita yabi bayanta da kallo

Sai yatuna da ranar dayazo amatsayin ustaz

Zataje dauko masa kudi wai sai yarufe idonsa


Murmushi kawai yayi shikadai
Tare da zaro wayarsa daga aljihunsa


Sallama tayi da tire a hanunta dauke da abinci ta ajiye gabansa


Hakeem yaganta cikin wata jibgegen hijabi abin yaso bashi dariya ma
Kar dai ace tagane abinda yake kallo
Sai yayi murmushi kawai


Husnah tace ga abinci yaya
Hakeem yace nakoshi

Husnah takalleshi tace saboda me


Hakeem yace saikin fada dalilin ki nasaka min hijabi daga shiganki dauko min ruwa


Husnah tayi murmushi kawai
Tace sanyi nakeji tafada tareda boye kanta cikin hibinta


Hakeem yace baby
husnah tadago batareda ta amsa ba


Yace cire hijabin nan kizo ki serving dina


Husnah ta marairai ce kaman zatayi kuka tace Dan Allah kayi hakuri yaya wallahi kunyarka nakeji


Prof ya tsareta da maya tattun idonshi masu kwarjini

Yace OK kinfison acire miki da kauna ko


Husnah tayi saurin girgiza kai

Yace OK do as I said cikin sanyin jiki husnah tacire hijabin ta ajiye kan kujera tasauko kasa ta
Samishi abinci


Prof ya gyara zama yafara cin abincin tareda tsareta da ido

Duk kallonshi yasa ta takura

Yace batayi tsanmani ba taka spoon din a hanyar bakinta
Tadago ido takalleshi ya daga mata gira

Tace azumi nake yi

Yau Wednesday dama ana azumin nafila

Husnah tace wallahi Nina koshi cikina ma kaman zafashe

Yace tunda yayi niyar bata tabude baki kawai yasamata


Bata da zabi haka tabude Dan karamin bakinta yasaka mata


Yanayin yadda take cin abincin nata ma kawai abin kallone

Yatsaya kawai yana kallon ikon Allah

Yace bude bakin nagani
Tayi saurin cewa na am da karfi

Tace inazuwa umma nakirana ta tashi tagudu abinta


Hakeem murmushi yayi kawai yagama cin abincinsa yafita yashamsu yace har zaka gudu

Hakeem yace a nayi bakine
Shine zanje nagansu

Ya shamsu yarakashi har gurin mota

Prof yakira megadi yabashi manyan lodoji yashiga dasu gida


Ya shamsu yace yallabai Dan Allah karage kashe mata kudi haka sunyi yawa karka manta fa yarinyace Husnah har yanzu bata gama sanin kantaba



Prof yayi murmushi yace karkadamu itama ai hakkinace so konawa zankashe mata basuyi yawaba

Karka damu ya shamsu
Nagode da kulawarka
Yashige mota yayi gaba
Yabar ya shamsu da tunanin irin karamcin na PROFESSOR HAKEEM



****
Meenat sun wuce honey moon itada agonta bashir a inda zasu zaga kasashe sama da biyar

Shiyasa ma suke saran sai nan da 5 months zasu dawo Nigeria




Dadddyn Hakeem da shi dawasu amin tattun abokansa sukaje nemawa ABDUL HAKEEM ABUBAKAR SHUAIB

Auran ASMAU SULAIMAN SHAMSU



Sun bada sadakin husnah da zinare Wanda akalla zai kai million daya da rabi


Abba da ya shamsu suka suka kikarba

Daddyn Hakeem yanuna rashin jindadin shi

Sai su Abba suka karba tare da wa abin albarka


Nan daddyn Hakeem yace yana Neman alfarmar asaka auran nan da two Weeks


Next page

Your comments is needed Fan's



Ina alfahari daku masoyana d'd'd'd'd'd'


=ØÝÜ=ØÝÜ=ØÝÜ=ØÝÜ=ØÝÜ=ØÝÜ=ØÝÜ=ØÝÜ=ØÖÜ=ØÖÜ=ØÖÜ=ØÖÜ=ØÖÜ=ØÖÜ=ØÖÜ=ØÖÜ
[05/05, 11:08 AM] UMMU AFAN <Ø9ß: <Ø—ß<Ø—ß<Ø—ß<Ø—ß<Ø—ß<Ø—ß<Ø—ß<Ø—ß<Ø—ß<Ø—ß<Ø—ß<Ø—ß<Ø—ß<Ø—ß<Ø—ß
<Ø—ß<Ø—ß<Ø—ß<Ø—ß<Ø—ß<Ø—ß
<Ø—ß<Ø—ß<Ø—ß<Ø—ß<Ø—ß
<Ø—ß<Ø—ß<Ø—ß<Ø—ß
<Ø—ß<Ø—ß<Ø—ß
<Ø—ß<Ø—ß
<Ø—ß
BISSIMILLAHIR RAHMANIR RAHIM

Story & written
By
The special writer


UMMU AFAN

=ØŠÝ=ØŠÝ=ØŠÝ=ØŠÝ=ØŠÝ=ØŠÝ=ØÚÜ



<Ø9ßFIRST CLASS TECHNOLOGIES WRITERS ASSOCIATION<Ø9ß


<Ø9ß<Ø9ß (F.C.T.W.A)<Ø9ß<Ø9ß



<Ø9ßHOME OF QUALITIES AND TRUSTED WRITER'S OF THE NATION<Ø9ß




<Ø—ßI DEDICATE THIS PAGE TO YOU SIS NERFEESERT A MUSA

INA MATUKAR JIN DADIN YADDA KIKE COMMENTS DINKI DAFATAN ZAKI CI GABA DA SUBURBUDO COMMENTS
KEEP IT UP =ØÞ=ØÞ=ØÞ<Ø—ß





<Ø—ßAKWAI LOKACI <Ø—ß





<Ø—ßPAGE 91 to 95<Ø—ß





PROF zaune cikin falonshi na gidansu yanawa da Ahmad madam Laila tazo tazauna kusa da shi fuska a kode


Tace ina da magana fa baban meenat


Hakeem yakalleta da nutsuwa yace ina sauraronki maman meenat


Laila tadago kanta ta kalleshi Dan taga kaman yau akwai abin arziki

Sai tadauko ko kwalliyar da tayi ne ta burgeshi


aikuwa sai tasake wani shagwabe fuska wai ita zatayi shagwaba


Abin yaso ba Prof dariya amma sai ya make

Tace daman inason wasu kudine Dan Allah


Hakeem yayi murmushi tare da kurban copee dinshi


Yace kaman nawa kike bukata uwargida rangida idan bake bagida


aikuwa kanta yasake fashewa

Tayi dariya tace kuma daga ni bawata nice amarya nice uwargida


Saboda dariya Hakeem har kwarewa yayi
Ya ajiye coffee din yana murmushi Wanda yake karawa kyakkyawar fuskarshi kyau

Yace Allah ko tace sosai

Yace nawa kike bukata kenan

Tace million biyu Hakeem ya kalleta yace sun isheki

Laila tankalleshi da mamaki

Sai dai kuma tabasar tace a idan zansamu kari ma aizankarba

Yace OK yatashi yaje dakinsa yadauko cheque yarubuta naira million biyar

Yabata aikuwa madam laila data karba taga abinda keciki

Kusan suman zaune tayi agun


Sosai takasa control din kanta

A take ta dau waya takira hajiya rukayya tafada mata kudin da hakeem yabata

Tsaban batan basira irin nasu daga uwa har 'yar suka hau murna


Ta ma mance agaban Prof take da mamaki Hakeem yake kallonta


Kuma godiya haka ta tashi zata fita


Hakeem yace baki jiba zokizauna

Baki tambayeni kudin menene ba

Laila tace aina sani tunda Nina tambayeka kuma ka nunka min fin abinda na tambayeka


Hakeem yace OK wannan kudi kiyi amfani dasu ne naki

Dan nan da two weeks za a daura min aure

Kinga saiki sai abinda kike bukata ko

wani wawan ihu tafashe dashi
Tacire Dan kwali ta yar tace cikin tsananin tashin hankali tace wallahi Abdul baka isa ka cimin mutunci ba kayi kadan

Kuma wallahi banga 'yar iskar data isa nayi kishi da ita

Wani wawan kallo Hakeem wa watsa mata

Yadawo PROFESSOR ABDUL HAKEEM dinsa data sani yace karkisake kiran matata da 'yar iska if not zan baki mamaki

aikuwa Laila ta tafa hanu tace auwa harma tazama matar taka to wallahi Baku isaba

Kodayake kaima ba yinkanka bane duk abinda kakeyi saka akeyi

aikuwa tawuce fuuuuuuuuuuu tayi hanyar part din mummy hafsat


Hakeem daya kai cup din coffee baki ganin tafita ya ajiye coffee din

Yace tashin hankali badai matar nan gurin mummy na zata ba

aikuwa yatashi yazare belt din jikinsa yayi part din mummy hafsat


Mummy tana zaune tana waya da hajiyar Ahmad suna shirya yadda zasu tsara komai kafin bikin ganin Laila tashigo a fusace yasa mummy hafsat tace zankiraki hajiya



Laila ta tsaya agaban mummy hafsat tana girgiza jiki

Mummy hafsat tace ke lafiyar ki kuwa zakizo kitsaya kina girgiza


Laila tace burin ki yacika sai dai ina son kisani wallahi ba aisa akawo min wata 'yar iska gidaba


Nidaman nadade dasanin bakya kaunata kuma wallahi ba yadda kika iya dani


Mummy sake baki kawai tayi tana kallonta

Zata sake wata maganar taji belt ta kota ina ajikinta

Hakeem ne sosai yake sauke mata belt din nan ajiki

Mummy hafsat tashiga tsakani tace barta haka son
Yace mummy kibarni na babballata hartana da gost dazata sameki tana miki rashin kunya Who is she by the way

To bari kiji bazan dauki raini ba ballanta na ki ma mummy na wacce bani da kaman su aduniya

Kekinsan zamana dake ma ai darajarsu kike ci Dan ubanki

To kije nasakeki kuma yanzu zaki bar gidan nan nonsense '""



Ya kalli mummyn shi yace mummy Dan Allah kiyafemin wallahi nayi da nasanin hada zuria da hajiya rukayya


Bantaba tunanin zan ajiye matar da zata iya miki abinda Laila tamiki yanzu ba


Mummy tace kayya son kayi sauri da baka saketa ba
aiko wace mata da irin nata kishin idan mijinta yazo mata da zancen Karin aure


amma ni baka min komai ba hasali ma kanuna min kai d'ane Allah yamaka albarka

Tajuya ta kalli Laila dake kurma ihu tana kuka kaman ranta zai fita


Mummy tace kekuma tunda rayuwa da kika zaba wa kanki kenan aishikenan

Mummy ta wuce abinta Hakeem shima komawa sashinsa yayi nan da Laila ta dauko waya tafashe da kuka hajiya rukayya ta rude tace ke lafiya kike kuka waya mutu


Laila tafada mata abinda kefaruwa
aikuwa itama hajiya rukayyar kusan haukar tayi

Tace ba inda zakije ganin nan zuwa kadunan shidin banza share hawayanki
Kekadaice a gidan mijinki


Kwantar da hankalinki ganin ta howa




Alhaji abubakar daddyn Hakeem yana hanyar dawowa daga office
Hajiya rukayya takira wayarshi tana kuka

Daddyn Hakeem yayi tafada mishi abinda abinda kefaruwa

Daddyn Hakeem yace Abu baiyi kyau ba ammanshima yanzu zaikoma gidan


Tace itama gatanan a hanyar zuwa yace Allah yakawoki lafiya


Ya kashe wayar yacigaba da tukinsa

Hajiya rukayya nazuwa sai da tabi tacan gidansu ta taho da uwarta itama wato hajiya suwaiba sukazo tare


Laila na zaune tana jiran hajiya rukayya suby kanwarta tuntuni tazo suke zaman jimami tare


Karasowar kowa da kowa aka hadu a falon daddyn Hakeem

Tunda daga kan hajiya suwaiba mummy hafsat hajiya rukayya Laila suby da kuma uban gayya ABDUL HAKEEM suna zaune gaba dayansu

Daddyn Hakeem yafara gaida hajiya suwaiba tunda itace uwa agaresu bakidaya

Kafin yagaida yayarsa hajiya rukayya

Daga nan kuma yabukaci yasan abinda kefaruwa

Hajiya rukayya tafara magana cike da zafin zuciya

Tace bantaba tunanin abinda wannan yaro zaimana bakenan ya suna zamansu lafiya da matarsa
Za azuga shi yayi aure wannan ma ai Neman tashin hankali ne

Kuma abin batsaya nan ba sai su hadu shida uwarshi sun mata duka

Sannan kuma tabashi umarnin ya saketa saboda bakin hali da akasha a nono


Ran Hakeem tafarfasa yake saboda bakaken maganganun da akejifar uwarsa dasu


Hajiya suwaiba tayi salati tasanar da ubangiji tace yanzu duk wannan abubuwan dake faruwa shine ba asanar daniba

Ta kalli Hakeem tace yanzu kai Ashe har yanzu baka daukemu da mutunciba
Kokana ganin Dan bani na haifi ubanka ba


To bari kaji idan bani da iko da kai inadashi da ubanka kuma ai ubanka yana da iko dakai ko

To wannan aure bazakayi shiba
Kuma maganar saki babushi dole yarinya ta zauna gidan ka


Daddyn Hakeem da tun da hajiya suwaiba tafara magana baice komaiba

Yayi gyaran murya yace to hajiya naji duk hukuncin dakika yanke


Maganar Saki tabbas zai maida matarsa kobakomai saboda darajar 'yar da ke tsakaninsu

Maganar fasa aure kuma babushi

Ba fashi

Idan bazaki matanba alokacin dakika zo da bukatar hada su aure sai da Abba na Allah yajikan rai yafada cewan duk lokacin dayazo da bukatar kara aure bawanda ya isa ya hanashi


Sannan kuma koda SON bashida sha awar kara wallahi sai namishi da kaina
Saboda kugirbi abinda kuka shuka

Hajiya rukayya da Hajiya suwaiba suka kalli juna


Daddyn Hakeem yaciga dacewa
Narayu cikin maraici tunda natashi bansan dadin uwaba sai na uba ga kuma gallazar matar uba wato ke Hajiya suwaiba narayu a hanunki cikin kunci da gallazawa


Kuma.abinda bakisaniba shine kice silar mutuwar mahaifiyata amina bayan ta haifeni kukamata jifa da ciwo da haka har Allah yadau abinsa

Kinsan a ina naji kamaku nayi kuna zancen keda Hajiya larai kishiyar ki

Nayi kuka kaman raina zaifita
Dana ji wannan magana daga bakinki


Kunsani maraicin dole kuma kuka kasa rikeni tsakaninku da Allah

Ba irin abinda bakuyiba ganin namutu amma Allah yace saina rayu a duniya

Alokacin da Allah yabani haihuwar ABDUL HAKEEM nadade ina mishi adduar Allah yarabashi da sharrinku

Dan nasan yanzu hankalinku zai komo kan 'Dana
Kullum cikin mishi addua a ruwa nake inabashi yasha
Wanda nasan ko mahaifiyarshi batasan niyya na ba



Saikuma kwatsam kukazo da gudirin aurawa Hakeem Laila alokacin shekarunsa basu wuce ashirinba kuka dage sai anyi na amince ne saboda wani dalili


Dan koda din ma abbana bai aminceba inzaku iya tunawa


Saboda haka babu Wanda ya isa ya hanshi aure

Idan kunga 'yarku bazata zauna da kishiya you are free to live with her

Hajiya rukayya da jike sharkaf da zufa
Zatayi magana daddyn Hakeem yadaga mata hanu ba abinda zakice yaya rukayya


Hajiya suwaiba ta sauka har kasa tace Dan Allah abubakar kayafe min wallahi duk sharrin shaidan ne hakan bazai kara faruwaba

Daddyn Hakeem yace haba Hajiya ai duk da abinda kika min bazaisa nadaina ganin ki a matsayin uwaba
Dan haka kitashi daga tsuguna min


Hajiya suwaiba tace nagode Allah yamaka albarka kaida zuriarka

Hajiya rukayya ma tana kuka taba wa daddyn Hakeem hakuri daddy dayake shiba meruko bane ya yafemata


Hakeem ya kalli mahaifin nasa yaga daddy na goge kwalla
Bakomai yasa daddy kukaba sai rashin imani irin nasu

Idan ya tuna sune sillar rabashida mahaifiyarshi da ko kamannin ta baisaniba saiyaji wani kunci
Daddy kasa jurewa yayi yatashi yashige bedroom dinsa

Abdul Hakeem yabi bayansa mummy hafsat ma tashi tayi tabisu


Hajiya rukayya tabuga tsaki aikin banza wallahi wannan kukan danayi bazai tagi banzaba

Hajiya suwaiba tace towayafada miki dama tubar gaskiyace

ai kawai ganinayi asirinmu yatonu shiyasa na bullo musu tanan


Laila cikin kuka tace yanzu dai kuna gani Hakeem zaikawo wata dasunan mata


Suby kanwar Laila ta ce ai wallahi duk wacce tayi gigin shigowa gidan ki anty Laila wallahi taja wakanta balain duniya Dan wallahi sai mun nakasa rayuwarta


Hajiya rukayya tace ai zama bai kamamuba

Ke Hajiya bari musa driver yamaidake gida

Gobe zamuyi nijar saboda ke Laila yau kije kibashi hakuri

Kinuna kinyi ladamar abinda kika aikata har dai yasamu yabarki gobe mutafi


Laila tace shikenan hajiyarmu Allah yabar mana.ke kina kokari ganin farin cikinmu


Nan sukatashi kowa yakama gabansa


Laila ta koma part dinsu tazauna tana tunanin abubuwan da suka faru

Wanda sana diyarshi allura ta tono garma



****

Laila sundawo daga nijar yanzu tana zaune ne zaman jiran amarya Dan tafara aiwatar da niyarta

Hakeem kuwa sake tsarin gidannasu yabayar akeyi badare ba rana
aiki ake zabgawa


Zama yayi yaga gaskiya a yanzu yakamata dadinsa yadaina fita office
Shiyakamata yayi komai su su huta

Kuma bashida da sha'awar raba gida da mahaifansa

Yayi shawarar dawowa A B U Zaria sunfi kusa da nan

Zaisamu daman da dazaije ya kula da harkokin kasuwancin daddynsa

Ahmad ma yace shima kawai kadunan zaidawo yacigaba da rike company daddynsa
Shiya sama yasa ma aikata gyaran gidanshi na Kaduna

Sunyi parking gabadaya zuwa Kaduna Aisha matar Ahmad ta tare a sabon gidanta dake Kaduna



Hakeem ankam mala komai ainda aka fitar wa da kowa dinshi

Part din Hakeem yana tsakiyarsu

A babban folon PROF zai iya shiga part din kowacce falon nashi guda biyu akwai a sama Wanda idan ka haura sama falon PROF shima daga gefe kuma wasu maka makan bedroom dinshi guda biyune


Kai gaskiya dai naira tayi kuka a gidan Prof

Gabakidayansu yasakewa was furniture's har daiyayensa

Komai yazuba wa Husnah Wanda uba yake wa 'yarsa Prof ya dau nauyin komai

Bakin ciki kamar zai kashe Laila amma ba yadda ta iya dole tanuna bakomai saboda tasamu ta cimma burin ta akan amaryarsa



Mummy hafsat gobe zasu daga zuwa Dubai itada mummyn Ahmad

Hado kayan lefe


*******

Biki ya rage saura kwana hudu Hakeem ne cikin motarshi yana zaune agefen mai zaman banza

Yayinda Ahmad kuma yake driving zasu kano gidan su husnah


Ahmad yace kai prof gaskiya kacanja wallahi gaskiya Allah yawa husnah albarka data saita mana kai


Dafa magana wahala yakebaka
amman yanzu sai a zauna dakai asha hira musam man ma na husnah


Hakeem yayi murmushi yace kaikuma dadina dakai sa ido wallahi

Ahmad yace aidole ne asamaka ido yadda yarinya karama tacanja ka


Hakeem dai murmushi yayi yace bazaka kanebane abokina bakasan yadda nakejin babyn a raina bane ko



Ana kiran la asar suna shiga gidansu husnah ya shamsu yataresuda murna yace kaga manyan kannena

Ahmad yayi murmushi yace fada dakyau ya shamsu girma fa Allah yabaka


Hakeem yace kana mamakine yaya shamsu

Ya shamsu yayi dariya yace waneni da mamaki Dan na zama yayan manyan maza

Daga shiya shamsun dayayi maganar harsu Ahmad da Hakeem sai da sukadara

Ya shamsu yace bissimilla mushiga daga ciki

Hakeem yace mudai fara gabatar da sallah tukun

Nan suka wuce masallacin unguwar




Husnah zaune itada anty kubra

Anty kubra tace Dan Allah husnah kisanar da kawayenki
Maganar bikinki


Husnah ta yatsina fuska tace nifa bazanyi taroba ma
Nibana mason hayaniya wallahi

Kuma da kika damu bagakiba dake da anty Aisha kusai kuzama kawayena


Kubra tarike baki tace lalle husnah wuyanki ya isa yanka
Nice ma zan zama kawarki ko


Husnah tace to Baku kuka dage saina aureshi ba


Anty kubra tayi murmushi tace aini dadina da gobe saurin zuwa
Kaman yaune zakizo kinacemin anty kubra
Wallahi inason mijina


Husnah tayi murmushi tace humm anty kenan nifa nafada miki auren biyayya kawai zanyi amma ba wai danso ba

ai nagama soyayya


Anty kubra tace shikenan tunda haka kikace akwai ranar maida martani


Anty jumai wacce aka dauko tunda Sudan saboda gyaran amarya tunda akasa bikin washagari ummu tayi Sudan dama can ita mutuniyar cance


Anty jumai tadubi husnah tace tashi muje kishiga wankar tunda
Hadin yayi awa biyu da shafawa

Husnah tace anty wai Dan Allah yaushe za adaina min wannan shafe shafen nan da shaye shayen nan


Anty jumai tayi dariya tace sai randa kikabar gidan

Kuma kuji dakyau dawasu zaki taki tafi

aikuwa Husnah ta turo baki ta tashi taje ta shiga wanka


Tana kansaka kaya taji muryar su yayanta da PROF suna gaisawa da umma a falo


Tayi niyar kwalliya tafasa Dan mutumin nan yabata tsoro ranar


Riga da skirt tasaka nawani tsadaddan net tayi kyau bakadanba

Powda kawai tashafa sai man baki

Tana kan maida kayanta cikin durowa anty kubra tashigo tace amarya ango nakira yana falonmu husnah ta turo baki tace anty kinfara ko


Zanrama wallahi nasan abinda zanmiki kema

Kubra tace ya hakuri 'yar kanwata nadaina

Dan nasan ki sarai wallahi


Husnah tayi murmushi tace a to dole abani hakuri dai

Tadauki mayafin kayan tayafa

Kubra tace kai husnah kedai komai baki baiwane

Wallahi kinwani canja ne fa gabadaya
Kinciko tako ta ina

Jin abinda anty kubra tace yasa husnah tunani tabbas ko itakanta tasan komai nata yacanja

Kuma acikin sati biyun nan da akafara mata gyaran jiki ne


To gaskiya bazata tasa gyaleba

Ta ajiye gyalen tadauki jibgegen jijabinta

Anty kubra tace haba Dan Allah mijinkine fa yazo zakije masa da wannan katon hijabin


ai gwamma dai kidau ki mayafin dakikayi niyar sawa

Kinga zaisake shiga hanu kafin nan da kwana hudun nan


Husnah tace aikuwa kinja ma wallahi rayuwar hijabin zanyi agidansa


Ta wuce anty kubra tayi falon


Tashiga da sallama ya amsa mata tamkar wani balarabe

Kamshin sa yacika falon

Husnah tanemi kasa tazauna


PROF yakureta da kallo wani kyau yaga tamishi
Kaman yau yafara ganinta


Husnah tagaisheshi bai amsa ba jin bai amsa ba yasa tadago suka hada ido yakafeta da idonshi

Kasan yasauko yazauna yana fuskantarta yace haka ake tarbar miji baby

Tayi shiru batace komaiba yace babay magana nake fa


Husnah cikin shagwabarta Wanda ita bada niyya tayi shiba tace menama kuma

Yace nafarko nace kidaina samin hijabi idan zakizo gurina bakida mayafaine

Tace tokai meyasa bakason insa hijabin

Hakeem very good question
Nafarko inason hijabi amma a muhallin daya dace asaka kaman kiganni da wani ko abokaina da kuma sauransu


amma banda dagani saike kisaka
Bakisan nazo naganki Dan nasamu nutsuwabane ?


Husnah tayi shiru tana wasada da zobenta

Murmushi Prof yayi Yakama hanunta tana kokarin janye hanunta prof yacire zoben hanunta
Kafin yasaketa


aikuwa Husnah ta kalleshi a tsorace tace Dan Allah kayi hakuri kabani zobenan

Yace meyasa zan baki tace nima bani akayi

Yace wakenan tayi rau da ido kaman zatayi kuka

Tace masoyina ya muallim


Yace zan baki amman saikinbi maganana kicire wannan jijabin
Dan ba anan yakamata kisaba

Husnah tace Dan Allah yaya kayi hakuri kabarni da hijabina nariga nasaba

Hakeem yace OK yasaka zoben a aljihunsa

Yace nawa kike bukata game da events din ki

Husnah takalleshi tace nima bana bukatar komai

Ya kalleta da mamaki yace saboda me tace bakomai wallahi ni duk wani Abu dayashafi bidia bana kaunarsa


Dan Allah yaya daman inason na roki alfarmar events din dakukasa akatin nan wallahi banaso
Dan Allah kabarshi kawai



Hakeem yace duk abindakikace haka za ayi amma bashi ne
Duk randa kika haifamin baby zan
DOWNLOAD
DOWNLOAD

2 Comments On AKWAI LOKACI
avatar
musa-6-3-2

7 months ago

Reply

Akwai lokaci

avatar
oumara-wassai

4 months ago

Reply

Replying to musa-6-3-2

17866

Please Login or Register in order to submit comment