Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

kuma nan nad'ashi a kanta .


Duk wanda yaga Ladidi to ze d'auka aljana ce saboda ba lallai ka gane taba .

YADIKKO ce keta k'wala mata kira amma tana ji taki kulata .

Kuma lek'awa kofar gidan nasu ta yi hango su baban ta da malam adamu suna tsaye da alamu baban nata gida ze shigo shikuma malam adamu zashi masallaci ya kwana .


Wurga sandar ta tayi kana ta dura ta katanga .


Tunda tafara tafiya bata had'u da kowa ba ta kusa isa gidan malam adamu ta had'u da wani mutumi me tallan tsire yana ganin ta .



Ze ruga da gudu kenan Ladidi ta nunashi da sanda tace "wlh ko ka tsaya ko kuma yanzu inkaika gurin baba ifiritu me tsire yaji za,a kaishi gurin aljani ya dur k'usa har kasa ya ce ku kuke ganin mu ba mu muke ganin kuba dan girman Allah kuyi hakuri LADIDI ce ta zaro jajayen idanuwan ta kana tace

"Zamu kyaleka amma da sharad'i me tsire ne yace "kome kukeso zan Baku indai zaku barni da raina da lpy .



LADIDI jin hakan ta dubeshi kana tace "tashi ka bud'emin wannan kwanon .


Me tsire na rawar jiki yaje ya bude kwanon ya mik'owa LADIDI tsire ne aciki tsinke biyar .


Kwashewa ta yi duka ta had'esu guri guda tana tafiya tana ci shikuwa me tsire tunda yaga tayi nisa ya ruga da gudu yabar kwanon a gurin.


Kafin ta k'arasa gidan su malam adamu k'arfe 9 tayi kowa ya kwanta suma su jalal sun gaji saboda gudun da suka kwasa d'azu.

Taci sa,ar gidan a bud'e yake tunawa tayi da malam adamu a masallaci ze kwana kai tsaye d'akin nashi ta nufa lek'awa tayi ta windown d'akin suna kwnce suna danna waya.

Basu ankara ba sukaji durowar mutum da farko hankalinsu be tashi ba seda suka hango farar fuska kamarta aljanu .

Dakin nasu babu haske sosai .

LADIDI ce taje bakin k'ofar d'akin tasa sak'ata tanata zaro jajayen idanuwan ta .


Humaid tunda ya firgita ya koma kusada jakar kayan su ya 6uya shiko jalal dur k'usawa yayi yana bata hakuri .


LADIDI ce ta dubi Humaid kana tace "kai bakan manya bako to yau karyarku ta kare .


Rik'e hanun juna sukayi suna matsawa da baya da baya Humaid ganin abin yakeyi kamar a mafarki d'ago kan daza suyi suka hango nama a hanunta kurma ihu suka dingayi .

Humaid tsabar tsorata fitsari yayi a wando shi kuma jalal yaje yin tusa ya had'o da kashi .


Ladidi ce ta lura da abinda sukayi tace "kowannen ku ze kar6i wanan naman yaci Humaid ne yace


"Ai Allah yayi kune dan Ku temaki mutane amma kunzo zaku cutar damu .


LADIDI ce ta daka musu tsawa kana tace "tunda bazakuci naman ba to Ku cire wandunan Ku kai da kayi fitsari ka tsotse kai kuma me k'aton kai dakayi kashi kaci kad'an .


Zaro ido sukayi kana suka fara "dan Allah kuyi hak'uri tsawa takuma daka musu tace Ku za6a yaji ta hango a gefen ta a kulle a leda ajiye musu a gaban su tayi ta finciko nama a tsinken tsiren tace to sekun shanye yajin nan duka .

Humaid yana kuka yace Jalal gara musha yajin.


Dukufa shan yajin da da d'an guntun naman sukayi idanunsu yayi jajur ga kuka ga shan yaji .


Suna tsayawa zata daka musu tsawa inna hauwa ce tajiyo tsawar.

Fitowa tsakar gidan tayi bata gane ta ina akeyin tsawar ba seda ta jiyo k'arar bud'e k'ofar d'akin malam adamu wanda su Humaid suke ciki .


Kafin ta ankara taji an turo ta d'akin su Humaid juyowar da zatayi suka had'a ido da LADIDI .


Inna hauwa ce ta kurma ihu tana salati tana fad'in dama ashe aljana ce tashigo mana gida shine bata k'arasa maganar ba taji LADIDI na rawa .

LADIDI ce ta zaro musu ido kana tace rawa zakuyi ina hauwa ce ta zaro ido kana tace "kuyi hakuri kusan mu bil adama bamu da k'arfi .

LADIDI ce ta d'aga sandar ta zata buga musu sukasa ihu rawa sukeyi kamar mahaukata inna hauwa ta dage se rawa take kwasa.


LADIDI ce tace "jibeku dame k'aton kai dame k'aton hanci.

Kekuma yar tsohuwa me k'aton goshi ki k'ara shiga abinda babu ruwanki .

Inna hauwa ce ta had'a hanuwan ta biyu tace "kiyi hakuri bazan sake ba .


LADIDI ce tace musu "kowa ya rife idanu kuma karku bud'e har senace inkuma ba haka ba to zaku tsinceku a duniyar aljanu .

Kafin ta gama ,magana har sun rife ido .

Ficewa tayi a d'akin ta nufi d'akin inna hauwa ......✍🏽✍🏽✍🏽.



*Mom Islam✍🏽.*

*LADIDIN K'AUYE*


_Funny & love story._


*_Labari mai ban dariya had'i da fad'a karwa_*


*NA*


*MOM ISLAM*

*ZAINAB HABIB*.


*MARUBUCIYR :*

*ZAINABU ABU*


*AND*

*LADIDIN K'AUYE*




*BISMILLAHIR RAHMANIR _RAHIM*


*Episode: 7_8*

_____kwanuka tagani wanda akaci abinci wani kwano ta hango a rufe bud'ewa tayi abinda idanunta suka hango ya bata mamaki sosai.


K'ara bude ido tayi nama ne soyayye cike a kwanon leda ta hango ta d'ibi iya san ranta ta fice a gidan .

Tana fita suka bude ido sunata mamakin aljanar da suka gani .

Inna hauwa ce tace "jalal zoka rakani d'aki jalal ne ya zaro ido ya dubi inna hauwa yace "walh inma zaki tafi ki tafi babu inda zani.

Inna Hauwa ce tayi a uzubillahi ta ruga d'akinta da gudu .

LADIDI ce ta koma gida duk mutanen gidan sunyi bacci lalla6awa tayi ta shige d'akinta ta kwanta babu maganar sallah .

Washe gari bayan sallar asbah Humaid ya fito da jakar kayan su ko wanka basu yi ba malam Adamu ne ya dube su kana yace "badai tafiya zakuyi ba da wanan duku dukun safiyar gari be gama haske ba.

Jalal ne yace "wlh mun shirya inna hauwa ce ta fito da carbi a hannun ta ,tana lazimi ta ce "malam ai dole suce zasu tafi, malam Adamu ne ya nemi guri ya zauna kana yace "meke faruwa.¿

Humaid ne ya nisa kana yace "wlh malam aljana ce tashigo gidannan jiya da daddare tadin ga yimana mugunta.
malam Adamu ne ya jinjina lamarin ya ce to shine dalilin tafiyar Ku da wanan safiyar .

Jalal yana gyara takal minshi yace "insha Allah yanzu zamu wuce jos .

Ina hauwa ce taje d'auko kwanon da ta zuba soyayyen nama ganin naman ciki befi biyar ba yasa ta rafka salati har su jalal suna rugawa da gudu .

Malam Adamu ne ya lek'a d'akin kana yace "meke faruwa ne¿
inna hauwa ce ta dubi malam da alamun damuwa tace "kaga naman da kasiyo wlh ragowarshi kenan malam be nuna dumuwar komai ba yace "karki damu kawo a kai musu .

Barinje in siyo musu lemon kwalba ficewa yai .

Ba dad'e ba se gashi ya dawo da lemon kwalba guda hud'u .

Inna Hauwa ce ta kai musu d'aki suna zaune suna jiran lokacin tafiyar su yayi .

Inna Hauwa ce ta mik'a musu had'e " da nama kar6a sukayi ci sukeyi da sauri sauri nan danan suka gama .

Fitowa sukayi rataye da jaka a kafad'ar su inna Hauwa ce tayi musu Allah ya tsare.

Humaid tsabar ya matsu su tafi harya shige mota Mallam Adamu ne ya fito d'auke da tsaraba a hannun shi bud'e bayan motar Jalal yayi ya shige motar suka d'auki hanya se jos.

Washe gari Malam musa ya tashi babu lpy duk iya gigiwar LADIDI seda tayi sanyi ganin jikin mahaifin nata kwance yake se nishi yakeyi kamar me ciwon zuciya YADIKKO da jikinta yagama yin sanyi .

Tanaji kamar Malam musa baze tashi ba tari ne ya sark'e mai wuya .

Yafara k'ok'arin magana sunan YADIKKO ya kirawo wato Aisha amsawa tayi da na,am Malam yunk'urawa yayi .

Kana yace dan Allah ki kula da LADIDI kinga y'a mace ce tunda Malam musa yafara magana YADIKKO ta fara hawaye .

Tari ne yakuma sark'eshi YADIKKO ce ta umarci LADIDI ta kawowa mahaifin ta ruwa bayan ta kawo yasha .

Yak'ara da cewa na bawa Malam Adamu LADIDI YADIKKO ce ta rushe da kuka ta aika LADIDI ta kirawo Malam Adamu ba,a jima ba se gashi sun dawo tare da gudu Malam Adamu ya k'araso ya rik'e hannun Malam musa jiki a sanyaye yace "sannu Malam .

Amsawa yayi da yauwa ga amanar LADIDI nan nabaka jikin Malam Adamu yakuma yin sanyi sosai ya daure yace "insha Allah zakaji sauki .

Murmushin yak'e Malam musa yayi daga nan ya kirawo LADIDI matsowa tayi kusa dashi ya kamo hannunta ya rik'e gam daganan yafara shak'uwa .

Kulli nafsin za,ikatul mauti ..

Allah yayiwa Malam musa rasuwa kowa ya jimama mutuwar Malam musa .

YADIKKO inta kalli k'ofar Malam musa setaji hawaye ya zubo mata .

LADIDI kuwa takoma kamar mutuniyar kirki bata fad'a bare neman tsokana duk wanda ya tsokaneta bata kulashi.

Bayan anyi sadakar bakwai kowa ya watse YADIKKO ta kwanta rashin lafiya har asibiti Malam Adamu ya kaita amma an rasa gane ciwon dake damun YADIKKO .

Kulum cikin ciwo take LADIDI kuwa tunda taga YADIKKO na ciwo shikenan ta karaya tana ganin kamar itama zatabi mahaifinta ne a kulum YADIKKO in suka zauna da LADIDI basayin wata magana kamar tadinga cemata ki rik'e mutuncinki a matsayinki na y'a mace, LADIDI na kuka tana jin YADIKKO.


Ciwon YADIKKO ne yatashi sosai da gudu Ladidi ta tafi domin kiran Malam Adamu YADIKKO na d'agawa LADIDI hannu akan tadawo ina LADIDI ta kid'ime bata ankara ba tafice da gudu Malam Adamu tasamu a zaune shida inna Hauwa suna hira ganin ta cikin wanan yanayin yasa su mik'ewa a zabure LADIDI tana kuka tana cewa su Malam Adamu YADIKKO na zata mutu kuzo duk wanda yaga LADIDI a lokacin komi rashin imanin shi seya tausaya mata .

Kafin inna Hauwa ta d'auko gyale ta fito har Malam Adamu ya isa gidan su LADIDI salati yahau yi ganin YADIKKO rai yayi halinsa .

Inna Hauwa ce suka k'araso itada LADIDI Malam Adamu na ganin su ya juya fuska yana sharar kwallah .

Tunda LADIDI taga haka itama ta zauna ta rafka uban ihu tareda birgima a k'asa babu wanda yayi yunk'urin hanata kukan mutane ne suka fara shigowa masu kuka nayi masu salati nayi masu adu,a nayi hak'ik'a mutuwar YADIKKO ta girgiza mutane sosai .

Tsakaninsu da mijinta Malam musa wata d'aya bayan anyi sadakar uku inna Hauwa tasa LADIDI ta kwaso kayanta ta dawo gidanta da zama duniya tayiwa LADIDI kunci kwata,kwata batajin dad'in zaman duniyar.

Bayan sadakar bakwai aka rufo gidan da kwad'o tunda LADIDI ta dawo gidan inna Hauwa takoma shiru shiru ko abinci takeso bata magana sedai in and'auko anbata.


JOS tunda su Humaid da Jalal suka koma garinsu kowa ya koma bakin aikin shi Humaid aiki yakeyi a hospital d'in dadynshi daya bud'e mai , shikuma Jalal aiki yakeyi a ma,aikatar mahai finshi.

Wato saida kayayyakin mata na sawa dana maza da sauransu sun maida hankali akan sana,ar sosai .

Dady ne zaune a dining suna breakfast shida su momy da Humaid da Jalal kirane ya shigo wayar dady d'auka yayi kana ya kara a kunnenshi jinayi yace innalilahi yaushe ¿"dady ne ya ajiye wayar yana jimama rasuwar Malam musa da Aisha wato YADIKKO.

Jalal ne yakalli dadyn nashi kana yace "badai iyayen LADIDI bane suka rasu¿ daday ne ya amsa da cewa dama sunada y'a LADIDI ne ?

Jalal ne yace inadai kauyen da muka jene to tabbas iyayenta ne abokin Malam ne dadyne yace tabbas sune momy ce ta fara tambayar dady kwatance yayi mata inda zata gane adu,a sukayi musu daganan kowa ya wuce gurin aikin shi.


★ ★★ ★ ★ ★

Bayan shekara uku LADIDI tana da shekara 14 years tayi tsayi tayi k'iba farinta ya k'ara fitowa ga k'irjinta yafara cika tafiya takeyi tana waka ta hango me tallar k'uli,k'ulli tana zaune a gindin bishiyar kukar dake k'ofar gidan Malam Adamu da tazamo gurin zamanta tun ana hanata har anzo ana barinta.

Me k'uli _k'uli ne ya kawowa Ladidi ,'d'agawa tahauyi tana cewa nawa nawa yaro me tallan k'uli yace "ashirin,ne Ladidi ce tace "za6omin d'auri d'aya kuma k'atoto mik'o mata yaron yayi kunce ledar tayi tanaci tana jefa k'afa yaro ne yagaji da zama yace ba bani kud'in kafin ya k'arasa Ladidi ta buge bakin yaron tace tunda har katambayeni wlh bazan bada kud'in ba kuka ya hauyi yaron tasowa tayi ta kama kunnenshi ta murd'a seda ya kwala k'ara ta sakeshi kana tace daga yau ka karayimin rashin kunya kagani.....✍🏽✍🏽✍🏽








*MOM ISLAM✍🏽✍🏽✍🏽.*

*LADIDIN K'AUYE*


Funny & love story.

*Labari mai ban dariya had'i da fad'a karwa*



*NA*

*MOM ISLAM*

*ZAINAB HABIB*

*MARUBUCIYAR:*

*ZAINABU ABU*



*AND NOW*

*LADIDIN K'AUYE*



*BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM*


*Episode:* 9_10


______malam Adamu ne yakira dadyn su Humaid a waya akan cewar Ladidi zata dawo gurinshi saboda tasami ,ilimi sosai"beyi musuba yace ranar lahadi se su Humaid suzo su d'auketa malam adamu ne yace da muna shirin kawota gobe nida Hauwa dady ne yace to ai babu damuwa duk d'aya ne sekun so Allah yakawoku lpy daganan sukayi sallama".

Inna hauwa ce ta ,tattaro wa Ladidi kayanta had'i da bata kud'in sabulu akan tayi wanki gobe zasu wuce birni aikuwa Ladidi jin haka ta fara murna tana tsalle ta kar6i kudin tafice siyo sabulu tana cikin tafiya ,ta had'u da k'awarta tana siyarda d'anwake gashi Ladidi najin yunwa k'awar ce tace Ladidi barin zuba miki d'an waken saboda tasan inta wuce Ladidi zata iya 6aro da robar d'an waken".

Fara zubawa tayi Ladidi tace ke barshi haka yarinya gobe zamu tafi birni mushi kayan d'ad'i kawar Ladidi ce ,tace nima inason zuwa birni sedai bamuda y'an uwa a birni .


Bayan ta siyo sabulun tafara wanki seda tagama duka sannan ta zauna tana jira su bushe ta ninke ".

Washe gari bayan sunyi sallahr asbh malam adamu yashigo yace su shirya da wuri saboda wuyar mota.

K'arfe goma suka tafi tasha sunyi sa,a wata mota bata cikaba suka shige malam adamu yabiya kud'in motar suka d'auki hanya zuwa jos".

Tunda suka shiga mota Ladidi ta hango wani k'aton arne yana cin Apple lek'enshi takeyi tana lashe baki had'a ido sukayi ta sunkuyar da kai a karo na biyu takuma d'ago kai tayi sa,a shima yad'go suka had'a ido ita kuma Ladidi ganin yanata kallon ta mugud'a mai baki shikuwa yana ganin haka ya bige bakin inna Hauwa ce ta ce kaikuma metayi maka dazaka bigi yar marainiyar Allah .

Da hausar da bata game bakinshi ba yace wanna yariya batada hakali Ladidi ce ta ,tuntsire da ,dariya shikuwa yaji haushin wanan dariya ana zuwa gurin sojoji ya bawa Ladidi 6awon gyad'a yace tazubar mai Ladidi bata ta6a shiga motar da zatayi tafiya me nisaba aikuwa ta watsa 6awon gyd'ar kusada wani k'aton soja suna ganin haka suka tare motar su Ladidi suka ce kowa ya fito da kuma wacce ta watso 6awon gyad'a ".

Ladidi ce tahau zaro ido saboda tana tsoron masu bakin kaya malam Adamu ne yace mekuma mukayi arnen ne yace daughtern kuce ta zubo bawon gyada malam Adamu ya bud'e baki yace ba ita bace".

Koda zamu fito bataci gyad'a ba kuma babu komai a hannun ta Ladidi ce ta nuna arnen tace wlh shine yabani yace in wurgar sukuwa sojoji sun rasa wazasu kama sukace Ladidi itada Arnen su fito suyi tsalen kwad'o .

Sojanne ya k'araso kusada su kana yace ku za6a ko tsallen kwad'o ko ayi muku bulala Ladidi ce ,tace wlh gara ayimin bulala tunda wanan k'aton arnen yajamin bulala biyar sukayi mata lafiyayyu malam Adamu bashida ta cewa kar a had'a dashi yaja baki yayi shiru direban motar sune yaketa masifa .

Ladidi ce tashige mota tanata kuka shikuwa arnen yak'i zuwa ayimai d'ayan sojan ne ya nuno arnen da bindiga da gudu yazo ganin sun saita kanshi.

Tunda aka fara bulalar yafara kuka yana basu hakuri ,ita kuwa Ladidi se dariya takeyi.

Malam Adamu ne yace wlh da tuni mun isa bayan an gama bulalar suka shige mota kowane fasinja yana fad'ar albarkacin bakinci har suka iso well come to plateau .


Kowa ya sauka a mota Ladidi tak'i fitowa seda ta ciro wata allura a kanta lokacin su malam Adamu sun tari adaidaita sahu zasu shiga ta sokawa arnen ta shige da gudu ".

Sun isa 6ukur park G.R.A anan ne anguwar su dadyn Humaid take wato alhaji abdullahi tsaya sukayi a bakin get d'in megadi ne ya lek'o kana yace daga ina kuke malam Adamu ne yace daga kano muke ni yayan mai gidannan ne seda megadi yakira a waya tukun yabarsu suka shige".

Tun daga k'ofar gidan Ladidi ke kallon tsarin gidan tunda tazo duniya bata ta6a kallon kyau da tsarin gida irin wanan ba sekace baza,a mutu ba inna Hauwa ce ta janyo mata hannu suka shige domin malam Adamu yarigasu shigewa.

Da sallama suka shigo itada inna Hauwa k'asa Ladidi ta zauna ina Hauwa a kujera malam Adamu shima yana kujera suna jiran mutanen gidan wata wata mata ce fara sol da ak'alla zatakai shekara arba,in a duniya sanye take da wani dakakken leshi me duwatsu tafiya takeyi kamar wata sarauniya ta iso gurin su inna Hauwa ta nemi kujera ta zauna .

Inna Hauwa ce ta fara gaida hajiya amina hajiya amina batasan inna Hauwa ba amma ganin malam Adamu yasa tagane matar shice bayan sun gaisa hajiya amina ta gaida malam Adamu Ladidi kuwa ta ,tafi a kallon palon dan batasan me akeyi ba seda inna Hauwa tace Ladidi baki iya gaisuwa bane ¿".

Ladidi ce,tace ina wuni hajiya amina tace lpy daughter ya kike shiru Ladidi tayi taci gaba da kalle kallen ta .

Hajiya amina ce ta k'walawa yar aikinta me suna ummi kira dagudu ummi ta k'araso ta durk'usa a gaban hajiya amina.

Cewa tayi kikawowa su malam abinci amsawa tayi da to hajiya ta mik'e ta nufi kitchen jollof d'in taliya ce wace taji kayan lambu sai k'amshi take zubawa da hollondia yogurt me sanyi ta d'oro akan turai ta kawo musu mik'awa malam Adamu tayi takuma mik'awa inna Hauwa nata ta d'auko wani ta mik'awa Ladidi nata da rawar jiki Ladidi ta k'ar6e abincin ta cire cokalin hajiya amina ce ,tace daughter kisa cokalin mana Ladidi ce tace a a wlh da hannu ma ya nak'are bare nasa cokalin.

Bayan dare yayi suyi sallah hajiya amina ta nunawa inna Hauwa d'akin da zasu kwanta suna shiga d'akin Ladidi ta d'are gado tanata tsalle tana cewa wanan aba kamar burodi mu agarinmu babu wanan aba me laushi haka inna Hauwa tana jinta bata kulataba.

Inna Hauwa ce takira sunan Ladidi tsayawa tayi da tsallen tace na,am inna kinsan me nakeso dake Ladidi tace a a".

Kinga kindawo birni da zama tsalle Ladidi tayi tana murna inna Hauwa ce ,tace kirik'e mutuncin ki dan Allah kinga ke marainiya ce kar ,rud'in duniya yasa ki zubda tarbiyarki to Ladidi tace".

Washe gari su Humaid sun shigo part d'in momy take gaya musu suje su gaida matar malam Adamu jalal ne yace ai tun jiya muka gaisa da malam Adamu sedai ,inna bari muje momy ce tace musu amma zaku shigo kafin kutafi ko Humaid ne yace eh insha Allah momy.

Direct dakin da momy tace musu inna Hauwa na can suka nufa sallama sukayi ,inna tana kan sallahya tana lazimi suka shigo gyaran murya tayi musu ,bayan ta shafa adu,ar ne suka fara gaisawa inna tace jiya tunda mukazo bamu had'u dakuba Humaid ne yace wlh inna aiyuka ne sukayimana yawa shiyasa inna ce ta sanya musu albarka suna cikin hira sega Ladidi nan tafito daga toilet da gudu batama lura dasu Jalal ba tahau jikin inna tana ihu Humaid ne yace inna a ina kika samo wanan yarinyar Jalal ne ya zaro ido ganin kamar yarinyar da tabige k'afar Humaid ce ,a zabure Jalal ya mik'e yadubi Humaid kana yace wlh brother wanan yarinyar ce da ta addabi mutanen k'auyen su d'ago kai Ladidi tayi suka had'a ido da Humaid .

Humaid ne yazaro ido yace yaushe zaku tafi ne inna¿" inna Hauwa ce ta washe baki ,kana tace ni da malam yau zamu wuce ita kuma Ladidi anan zamu barta .

Kwata ,kwata Ladidi batasan gidan su Humaid suka zoba sai yanzu ,

Humaid ne ce munshiga uku "inna Hauwa ce ta dubi Jalal da yakasa cewa komai se Humaid ne da keta salati duban su tayi kana tace wanan yarinyar yar uwar kuce dan Allah ku, kula da ita sosai duk cikin su babu me magana suka mik'e suka wuce d'akinsu .

Dayake d'akinnasu a had'e yake Jalal ne yadubi Humaid yace wlh brother ankawo mana bala,i cikin gidan mu.....✍️✍️✍️






Mom Islam ce ✍️✍️✍️

*LADIDIN K'AUYE*


Funny & love story.

*Labari mai ban dariya had'i da fad'a karwa*



*NA*

*MOM ISLAM*
*ZAINAB HABIB*


*MARUBUCIYAR:*

*ZAINABU ABU*



*AND NOW*

*LADIDIN K'AUYE*



*BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM*


*Episode:* 11_12


_____washe gari ,inna Hauwa ta shirya malam Adamu ya aiko jalal ya kirawo ta dan bayason suyi tafiyar dare shigowa inna Hauwa tayi ta sami guri ta zauna dady ne shida malam Adamu suna hira dady ne yace ina Ladidin inna Hauwa ce ta kwalawa Ladidi kira segatanan da gudu ta k'araso dady ne yace sannu baiwar Allah ina kwana tace bayan ya amsa ne malam Adamu yadubi Ladidi kana yace yanzu ,zamu tafi amma inna tagaya miki anan zaki sauna ko ¿"Ladidi tana murna tace eh ta gayamin malam Adamu ne yafara yimata nasiha da fad'a akan tarbiya dakuma tayiwa su dady biyayya to tace musu daganan suka mik'e Humaid ne da Jalal suka shigo suka durk'usa suka gaida malam Adamu shida dadyn su ".

Mik'ewa sukayi sega momy nan d'auke da wata leda mekyau ta mik'awa inna Hauwa godiya inna Hauwa tayi mata daganan suka fito waje" Ladidi ce ,tace inna yaushe zaku dawo"ina Hauwa ce tadube ta da alamun tausayawa tace karki damu zamuzo dubaki Ladidi bata nuna 6acin raiba saboda tana son zaman birni "Humaid ne yatada mota suka shiga dady ,yaciro dubu goma yabawa malam Adamu godiya malam Adamu yadinga yiwa dady daga nan suka fice daga gidan suka zarce tasha suna zuwa suka shige mota se kano.


Ladidi ganin babu wanda tasani acikin gidan yasata yin sanyi gashi yunwa takeji tarasa inda zatasa kanta tagumi tayi seta fara tuno inna Hauwa da acan k'auyen,nne da ko tuwo ne taci sau biyu su nan idan aka bawa mutum shayi da burodi abincin rana se k'arfe d'aya na rana" dady ne yazo wucewa yaga Ladidi a kan dakalin wucewa palon tazuba uban tagumi "dadyne yadube ta kana yace Ladidi meke faruwa ne Ladidi da tarasa abinda satace seta k'ak'alo karya tace dama narasa d'akin dazan shiga ne dady ne yarik'e hannunta ya nuna mata d'akin da suka kwana jiya yace nanne d'akin ki ,kinji to tace mai shikuma yafice daga part d'in ,nata.


Tunda tashiga taji kamar an karo yunwar ne juyi tadingayi a katifa yar aikin gidan ce wato ummi tashigo da tiren abinci doya ce da miyar k'awai se lemon gora fanta da sauri Ladidi ta diro daga kan gadon ta kar6i abincin ita ko ummi mamakin ci ,irinna Ladidi takeyi " ko wanke hannu batayi ba tadinga tura doyar tana kur6ar ruwa seda taciye duka sanan takoma kan miyar kwan tana ta lasa tarasa miyar menene amma dai koba komai tayi dad'i tak'yar ta mik'e tanufi bayi kashine ya matseta seda tashiga ta tuna tunda suka zo batayi kashi ba seyau lek'a bayan gidan tadingayi kozataga masai "ina sewata kwalba fara mekamada kujera sekuma baho a gefe shima na kwalba .

Ihu ta kurma saboda kashi na neman zubo mata da gudu momy tashigo d'akinnanta taduba bata ganta ba k'wala mata kira tayi momy ce taji Ladidi takuma kurma ihu k'ofar toilet d'in ta ,tura ganin Ladidi a zaune tana ihu tayi" k'arasawa kusada ita tayi kana tace Ladidi meke faruwa tundaga room d'ina najiyo ihunki Ladidi batasan room ba sedai cewa tayi kashine ya matseni wlh na kusa yi a wando momy ce ta rik'o mata hannu ta mik'e nuna mata inda zata zauna tayi Ladidi gani takeyi kamar
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment