Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

yasashi ficewa da gudu yana haki, misalin k'arfe goma sha biyu 12pm zaune suke shida Khairat suna kallo ganin abinda take gari yasashi had'e fuska yace ”kewai saikace ba mutum ba kullum abu d'aya ?"k'ara matsoshi tayi ,can kuma sukaji ana nocking ,humaid ne yace ”jeki sako hijab ,mik'ewa tayi ta shige ciki ,shi kuma humaid yaje domin bud'e k'ofa ,yana bud'ewa yaga doctor umar ne dakuma doctor sufiyan ,da fara'a ya tarbesu yana yimusu sannu da zuwa zama sukayi ,aka fara yiwa humaid tsiya, akan ango ya 6uya ko office yak'i zuwa murmishi yayi musu yace ”insha Allah yanan lek'owa ,Khairat ce tafito da hijab hark'asa ta zauna suna cemata 'amarya kinsha k'amshi dariya takeyi amma idanunta nakan humaid saboda tsananin buk'atarshi takeyi ,drinks ta mik'e takawo musu da cincin dakuma dubulan sunci babu laifi daganan suka ce zasu wuce , humaid ne ya fice rakasu ,daganan yadawo domin kwanciya yake buk'ata saboda gurin da 'akayimai aiki yanayimai zafi ."





Khairat ce tashigo da wasu mahaukatan kaya rigace ko cinyarta bata k'arasa ba ta fad'a jikin humaid ,juyawa yayi yana rik'e da gabanshi yana wani ihu ,khairat na ganin abin kamar wasa kuma dai taga yafi k'arfin k'wa_k'wal warta, mik'o mata waya yayi yace ”ki kiramin doctor Umar please ,jiki na rawa ta dubo number ,ring d'aya doctor Umar ya d'auka gamida yin sallama ,Khairat ce tace ”Umar humaid babu lafiya wallahi ,a tsorace doctor Umar yace ”to kicewa drivern gidanku ya kawoku hospital d'inmu , to kawai tace ”daganan ta kamawa humaid ya mik'e ,parlor takaishi ,itakuma takoma bedroom d'inta ta sauya kaya ta d'au hijab da takalmi marar tudu suka wuce, driver takirawo dagudu yazo ya tsuguna yace ”hajiya gani "cemai tayi maza_maza fitoda mota asibiti zamuje ,angama hajiya yace ”yana fitoda mota ta rik'e humaid tasashi a mota ,mintuna kad'an saigashi sun iso ,cikin gaggawa doctor Umar ya taresu yashige da humaid room d'in da 'aka kwantar dashi kwanaki....




Dubashi yashigayi da na urori , ganin lamarin yakusa dawowa nada yasashi share ,wahalalen gumin daya tsa tsatsafo mai ya dubi humaid daketa maida nunfashi yace ”humaid kana wuce gona da iri fa ,humaid cikin wahalaliyar murya yace Umar babu inda na iya naje na 'auro wacce k'arfin halittarmu batazo d'ayaba ,Umar ne yace ”to wallahi 'inkacigaba da sex kullum kokuma sau hud'u a rana wallahi saidai wataran ka hak'ura da mace ,kana kallonta amma bazaka iya ta6uka komai ba .....



Humaid ne yace ”Umar please help me yanzu ya za'ayi ,iska Umar ya fitar ta bakinshi cankuma yace ”umm....



Yanzu shawarata bazatai amfani ba cox kuna cin amarcin Ku yanzu ,humaid ne yace ”yanzufa ba maganar wasa mukeyi ba dan Allah kaduba please, Umar ne yace ”karka damu amma ka kiyaye fa kar asami matsala ,insha Allah humaid yace ”daganan ya basu magani kasancewar Khairat na waje suka wuce gida, tunda suka koma khairat keta tattalin humaid, kwana uku a tsakani saiga humaid yaji sauk'i ,alkacinne tazomai da buk'atarta ,humaid bayason tasan halin dayake ciki shi yasa yakeson 6oyemata ...



Yaukam zama tayi tafara kuka kamar wacce akayiwa duka humaid na bacci yajiyo kukanta 'a zabure ya mik'e yayi gurinda tazuba uban tagumi ,tambayarta yashigayi ,ko kallonshi batayi ba tafara magana ,tana cewa wallahi nayi nadamar auranka 'ashe dama kaida mace banbancin Ku kad'anne to wallahi ni bana auranka kaje ka nemi dai_dai kai walhi bazaka d'auki hakki naba kokuma kasani bin mazan banza "ka d'an d'anamin Zuma 'a baki yanzu kuma kace bazaka iya daniba ,humaid jiki a sanyaye yace ”dan Allah Khairat kiyi hak'uri bazan iya rabuwa dake ba karki gujeni ,tashi tayi kamar wacce aka zabura tayi cikin bedroom d'inta ,firfito da kaya tafarayi ta lodasu a 'akwati tana kuka....✍️✍️✍️.



Mom Islam ce...🤙

*LADIDIN K'AUYE*


Funny & love story.

*Labari mai ban dariya had'i da fad'a karwa*



*NA*

*MOM ISLAM*
*ZAINAB HABIB*


*MARUBUCIYAR:*

*ZAINABU ABU*



*AND NOW*

*LADIDIN K'AUYE*



*BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM*


*Episode:* 39_40




_____Tsugunawa yayi a gabanta yana bata hak'uri ,ko kallo ma bai 'isheta ba tacigaba da kwasar kayanta ,tana gamawa tace ”saura takadda ta ,humaid da yad'auki lamarin k'arami saiyaga 'abin ya zarce gona da iri ,yana rok'arta itako tana tafiya ,ficewa tayi daga gidan da k'atoton akwati tayi bakin titi ,napep ta tara ya kaita har k'ofar gidansu , tana sauka ta mik'a mai kud'inshi tayi nocking mai gadi ya bud'e mata da sauri ta shige cikin gidan ,samun momynta tayi a parlor tana kallo a tashar MBC 2 ,kwanciya tayi tafara rera kuka ,momyn ce tace ”kiyimin bayani mana maiyafaru daga biki yau kwananki biyar amma kice kin taho da k'aton akwati ?"ko wata matsalar ce kinfi k'arfin ki kiarani a waya? Momy tadinga jero mata tambayoyi a jere, Khairat ce ta dubi momy tana hawaye tace ”momy ki fahimceni please karkiyimin mumunanr fahimta ,momy ce tace” tashi mu shiga ciki kinsan gidan baya rabo da mutane, rufawa momy baya tayi tare da 'akwatinta ,suna shiga momy tace ”ina jinki daughter ya 'akayi wani sabon kukan tafara tace ”momy wallahi mutuminnan bashida lafiya , momy bazan iya zama dashiba wallahi ,momy da bata fuskanci 'inda y'ar tata _ta dosa ba yasata cewa rashin lpy kuma ?eh Khairat tace”daganan ta bata labarin hirar dasu humaid sukayi a hospital dakuma 'yanayin zamansu ....





Momy cikin jinjina, lamarin tace ”gaskiya zama bazaiyyi ba za'a cuci d'aya dama yasan bashida lafiya ya auro ki tabb, amma bari yau dadynki yana hanya sai muyi maganar aji inda lamarin zai kaya, to tace” daganan ta kwanta momy kuma tayi waje..




Gidan su Humaid momy ce tacewa”dady anya baka zargin wanan yaron Ammar shine ya sace Khadija?",dady shiru yayi nad'an wani lokaci cankuma yace ”eh to gaskiya ban zargesa ba kasancewar baya gari ,kinsan iyayensa ba Nigeria suke ba ,amma zansa 'a bincika min ko da wata mak'ark'ashiyar ,momy ce tashare wasu zafafan hawayen dasuka kwaranyo mata ,dady cikin tausayawa yace ”dole sai hak'uri uhm 'momy tace ”Jalal ne yashigo cikin sallama , bayan su momy sun amsa ne Jalal yace ”dady kunji abinda yafaru ?" Momy ce ta dubi Jalal tace ”menene yafaru ”gyara zama Jalal yayi yace ”momy wlh matar yaya Humaid ce tace ”wai saidai ya saketa ,cikin ko inkula dady 'yace ”to saime ni banga dalilin da kowa zai tada hankali ba ,inace aurene ?to tinda yariga yayi shikenan yaje yaci aure ,momy uffan batace ba, ta mik'e tayi cikin bedroom d'inta....



*AFTER 1 MONTH*

Kwance yake a parlour ,kallo ya kunna 'amma hankalinshi baya gurin ,tunani ne suka taru sukayimai yawa yarasa tudun dafawa ,jin nocking yasashi mik'ewa ,handle d'in k'ofar ya murd'a ganin Khairat yasashi mamaki ,cikin fushi tace ”karkayi zaton ko nazo ne ,dama nazo in gayamaka ciki ne dani kuma kuma three3 weeks kenan ,hamdala Humaid yayi yace ”kinga munada rabon samun baby's ko ,murmishin da baikai zuci tayi ,tace ”a cikin wa? cemaka 'akayi zanyi shayarwa tabb, to kasani aihuwar ma bazanyi ba dan yaron daba 'a gidan ubanshi nake ba mezan haifa? Humaid jiyayi damuwar tashi takuma nunkuwa over ,cewa yayi please khairat ki fahimceni mana ,nifa bani na koreki ba cox kekika tafi da kanki bansan lefin danayimiki ba, bud'e baki tayi tace ”au bakamasan lefin dakayimin ba to bari 'in tuna maka koka manta dakaida mace banbancin ku kad'anne?."




Dafa kai Humaid yayi yace ”kibar ganin ina lalla6aki wallahi zanyi miki dukan tsiya kuma inga mai tsaya miki, kallon up and down tayimai kana tace” turr tayi gaba ,tana fita Humaid yamaida k'ofa ya rufe yafara kuka kamar k'aramin yaro ,yana tambayar kanshi wai shi meyayine a rayuwa bashida sa'a yanzu yayi aure dan yaji dad'i amma sai tozarci dayaketa biyo baya ,ga wanan shegiyar yarinyar tayi sanadiyar had'ashi da iyayenshi ,wayoo Allah na yafad'a cikin k'unar'rai dazanga Khadija saina kusa kasheta ,domin ita masiface.....


Momy ce zane rik'e da carbi tana lazimi jin sallama yasata d'ago kai ,ganin Khadija ce take shirin shigowa parlor yasa wani matsanancin kuka ya ku6cewa momy ,tana cewa daughter ashe zanganki ? three months kenan bakya gida ,itama Khadijan wani kukane ya su6uce mata tana momy kiyi hak'uri nasan nayimuku lefi ,amma kafin in zauna kuyafemin ,ta had'a hannuwanta biyu ,tana rok'arsu momy ,rungumeta momy tayi tace ”bakiyi mana komai ba daughter amma kinsamu fargaba ,rik'o hannunta momy tayi tace ”zonan kije kiyi wanka sai kizo kici abinci ,babu musu tabi momy ,bayan momy ta rakata d'akinta nada kafin tayi aure ta fice , wanka tashiga tayi alwalah ta tada sallah tana idarwa ta zauna gaban dressing mirror tafara tsara kwaliya ,wata doguwar 'riga tagani bak'a mai adon stone ajiki dakuma flawoyi masu kyau ,farinciki ne ya lulu6eta tafara magana cikin zuciyar ta tanacewa 'anya nayiwa momy hallacci dahar natafi nabarta ? gashi duk da haka bata ganin lefina kuma bata fifita y'ay'anta 'a kaina ,share guntun hawayen daya kwaranyo mata tayi tasa rigar dakuma bra da pants tasanya rigar ,rolling d'in d'ankwalinta tayi tafito ,ganin bataga momy a parlor ba yasata wucewa bedroom d'inta ,canma batanan ,k'ara fitowa tayi ta zuwa kitchen....


Rungume momy tayi ta baya tace”momy da kanki kike girkin ?"ina ummi fa ?momy ce tace ”ah ai yau dole nayi miki girki daughter na guda tadawo ,daganan suka shiga hirar duniya ,amma momy batace ina taje ba , itama bata ce komai ba ,bayan sungama girkin 'ne suka wuce dining ,cikin so da k'auna suke cin abinci momy nata janta da hira,Jalal ne yayi sallama 'amsawa sukayi da Khadija da momy Jalal jin muryar Khadija yace ”tabb yaushe a gari ?kodai Makkah kikaje ne ?bud'e baki Khadija tayi tana dariya tace ”yaya Jalal nasiyoma kalo kalo ,bashiba har momy saida tayi dariya ,zama yayi shima yace ”to momy ina 'abinci na ?Khadija ce tace”kaga zomuci anan inbamu k'oshi ba ma k'aro ,zaro ido Jalal yayi yace ”tabb kinaso yaya Humaid yazo ya ganni 'inacin abinci da matarsa kenan ko ?"d'aure fuska tayi tace"barin zuboma naka to ,momy na kallon yanayinta 'amma bata nuna mataba ,tana fita Jalal yace ”ina tajene wai” cikin rad'a ,momy ce tace”wlhi bata gayamin ba nikuma ban tambayeta ba......




Tana dawowa rik'e da plet na 'abinci Jalal yace ”to sannu a yawo ,dariya tasa tace” yaya nifa ba yawo naje ba ,to ina kikaje inji Jalal ?to garinmu naje ,momy ce ta 'ajiye cokalinta ta tsaya kallon Khadija wacce magana takeyi ko a jikinta kuma babu alamun damuwa 'a fuskarta ,wallahi yaya Jalal ina gidanmu ganin babu wanda yake shiga gidan ,yasani yin saukar dare na bud'e gidan na zauna 'aciki kuma ko inna da malam Adamu basusan inanan ba dan babu Wanda na gayawa.....✍️✍️✍️.




Mom Islam ce🤙
*LADIDIN K'AUYE*


Funny & love story.

*Labari mai ban dariya had'i da fad'a karwa*



*NA*

*MOM ISLAM*
*ZAINAB HABIB*


*MARUBUCIYAR:*

*ZAINABU ABU*



*AND NOW*

*LADIDIN K'AUYE*



*BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM*


*Episode:* 41_42




_____Shiyasa ba'asan inanan ba ,kuma koda na koma banida matsalar abinci kasancewar komai na d'iba ,momy sai lokacin tayi magana tace ”to me ya had'aku da Humaid?? "nisawa tayi tace ”tunda mukaje India yake wulak'antani nikuma yasa na gudo kawai nakoma can gidan ,kuka momy tasa tana cewa dama,cin mutunci da tozarcin da Humaid zaiyi mana kenan hamm ya kyauta , Jalal ne yace ”to momy ai tunda tadawo farinciki zamuyi ,shikuma yaya Humaid d'in ku yafemai ,momy batace komai ba ta share hayenta tace ” daughter Allah yayimiki albarka mu mun had'aku ke baki bijire mana ba 'amma shi ya bijire mana ,hak'uri Khadija tashiga bawa momy ....




Washe gari dady 'yadawo daga tafiyar dayayi ,ganin Khadija 'a parlour yasashi dad'a wara iadanu tace” Khadija saukar yaushe?cikin ladabi ta gaida dady tace ”jiya kanta 'a sunkuye masha Allah dady 'yace daganan ya wuce ciki ,Jalal ne yashigo da y'ar dariyarsa yace ”albishirinki ?goro Khadija tace fari ko ja Khadija ce tace ”fari k'al ma ,zama yayi kujera mai kallon tata yace” nakusa yin aure ,tsalle ta buga saida su momy suka fito suna cewa ,maiyafaru ne hayaniya tayi over ¿" Khadija ce tace ”yaya Jalal ne zaiyi aure zaro ido momy tayi tace ”to yaushene mukam bamu sani ba?Khadija ce tayi shiru cankuma tace ”yaya Jalal gayamin in sanar dasu ,dukkansu tabasu dariya har dady sanda ya dara ,shiyasa tafiyarta kokwa yai missing d'in dariya.....




Dady ne tace ”ai bikin da saura tunda saura 3 weeks ,Khadija cikin murna tace ”tabb nikam wazaiyimin anko?tazuba tagumi momy ce tace ”da kinada saurayi da saiya yimiki ,dariya tasa tace ”tabb aikuwa momy ke zakiyimin atamfa da material dakuma gwagwaro tunda naji d'azu yaya Jalal suna waya da 'antyn tamu ,momy ce tazaro ido tace ”to wanan kayan da kika kirawo sunkai 50k Khadija ce tace ”hh momy karki damu inbasu isaba zan k'ara miki dady dayaketa dariya yace ”momy and daughter anfansu a rana,dariya Jalal yayi ,momy ce tace ”to naji karsujimu , juyawa Khadija tayi tace ”ywa dady kai kuma gyale da takalmi da jaka da sark'a da d'an kunne ,dady shima ganin abin yazo kanshi yasashi cewa kekuwa bakida samari ne ?dariya tasa tace ”dady nadena samari ,kowa yazo yagansu zaiyi sha'awarsu kasancewar dady da momy suna wasa da y'a y'ansu ...


Dady ne yace ”to naji shikuma Jalal mai zai siya miki ,shima juyawa tayi tana kallonshi tace ”yaya ango turare da kayan makeup ,dariya yayi yace ”karki damu autar momy ,daganan suka mik'e kowa ya shige nasa dakin , dare nayi tazo yiwa momy sallama saiga wani yaro nan ya shigo wai ana sallama da Khadija ,zaro ido tayi tace ”to koma waye ya makaro ,momy da take jinta tace ”kaje kace yayi hak'uri gobe yadawo ,to yace ”yaron ...




Washe gari momy da dady da Jalal da Khadija sun taru a palory ,dady ne ya dubo number Humaid ya danna kira ,Ring daya kamar mai jira ya d'auka yace ”aslamu alaikum dady ,dady cikin kakkausar murya yace ” ba doguwar sallama mukeso ba kazo yanzu kuma banason 6ata lokaci ,insha 'Allah ganin zuwa , gaban Khadija ne fara fad'uwa tana zaro ido ,had'a ido da Jalal sukayi yayi mata gwalo ...


Cikin mintuna kad'an saiga Humaid nan ya rame sosai yayi bak' ,duk tsanar da momy tayimai saida ta tausaya mai sosai saboda ko shima dady bai nuna'a fuska ba ,sallama yai yashigo ,ganin Khadija takuma k'iba da kyau yasashi tsayawa kallonta ,wani mugun kallo ta watsamai ,saida yasami guri ya zauna ,yana zama dady 'yace ”dama ba komai yasa na kirawoka ba saidan inason kabawa Khadija takardar saki kuma ba saki biyu ba saki uku nakeso ,cikin bada umarni dady 'yayi maganar ,kid'emiwa gamida k'arewa Khadija kallo yakuma duban momy kozatace wani abu ,ko kallon inda 'akeyin magana batayi ba , wasu zafafan hawaye ne suke fitowa daga fuskarshi ,ya durk'usa gaban su momy 'yace ”mom da dady dan darajar fiyayyen halitta dan darajar al qur ani ku yafemin wlh na gane kuskurena ,dan Allah ,kuka Jalal yafara 'abinka da d'an uwa yace ”momy da dady maizai hana ku yafewa yaya Humaid tunda har yagane kurensa kutuna fa 'Allah munayimai laifi a kullum kuma mu rok'eshi ya yafe mana wasuma bazasu rok'eshi ba kuma baya fushi dasu to dan hasken annabi Muhammad kowa yace”sallalahu alaihi wa sallam ,mun yafe maka, momy tace ”idanunta na tsiyayar k'wallah dady ma cire farin gilass d'insa yayi yace ”mun yafe maka Humaid ....




Wani farinciki da nishad'i suka ziyarci zuciyarshi d'a hannu yayi samma yana godewa 'Allah ,dady ne yace ”to saura maganar takardar saki ,Humaid ne yaji k'irjinsa na dukan uku uku yace”dady ai na d'auka shikenan ,momy ce tace”yanzu dai za6i yarage ga mai zaman gidan ,Khadija dai an d'aure mata kai dan tarasa yazatayi kawai tafara kuka tana cewa walhi bazan komaba ,
Ran momy yad'an 6aci kad'an to kunsan tsakanin d'a da uwa sai Allah haka 'aka tashi taro abin babu dad'i .


Washe gari har k'arfe goma bata ko lek'o parlor ba ,momy da bata iya daure rashin ganinta yasata nufar d'akin Khadija , zaune tasameta tanata gurshek'en kuka ,momy ce ta dafata tace ”au akan maganar Humaid ne kike wanan kukan ?to sha kuruminki saikin yarda zaki koma, amma inason baki shawara inhar kina sinsa to walhi karki zurfafa jamasa rai 'inkuwa bakya sansa kiyi magana tun wuri ,shiru ne yabiyo baya ,momy jin Khadija tak'i magana yasata mik'ewa ta fice, kukane ya kuma ku6cewa Khadija jitakeyi dama mutuwa tayi ta huta da duniyar nan saboda k'uncin da take ciki...


Gobe juma'a gobe ne d'aurin auran Humaid duk da bak'in cikin da Khadija take ciki bai hanata murna ba ,kar6o kayanta tayi a gurin momy tanata yimata godiya dady ko tun kafin bikin agama tashi siyayyar haka ma Jalal...



*WEEDING*💍🥰.

Kowa na gidan shirin zuwa d'aurin aure yakeyi Humaid kuwa shine kan gaba ,misalin k'arfe biyu dubban jama'a suka shaida d'aurin auran JALAL ADAM DA AMARYARSA SAUDAT KABIR akan sadaki dubu d'ari ,kowa kagani yana cikin farinciki ango kuwa inkaga bakinan kamar gonar auduga sai gaggaisawa yakeyi da mutane sunata yimasa Allah ya sanya 'albarka ,shirin komawa gida sukayi ,saboda zasuyi shirin zuwa reception gurin rawa ...


Humaid na shigowa da fara'arsa kamar shine angon yacewa momy an d'aura fa ,cikin farinciki momy ta kwararo adu'oi tana murna cikin zuciyarta kuwa saitaji tausayin Humaid sosai ,amma 'a kullum tana adu'ar Allah yasa Khadija tasoshi, motoci ne zasu wuce itako Khadija batasan lokacin tafiya ba domin tatafi gurin kwaliya ,basu jima da wucewa ba saigatanan ta dawo ,momy na ganinta tace”kai kai kai ko amarya albarka dariya Khadija tasa tana cewa momy barinje in shirya kar masu moto suzo ,rik'e baki momy tayi tace ”tabb aikuwa sun wuce ,ida nunta sunyi rau rau alamun zatayi kuka tace ” nashiga uku nikam wazai kaini ,momy ce tace ”barin kira Humaid ina tunanin k'ila basu fara d'aukar y'an matan ba ,wani kishi ne yataso mata amma bata nuna inda momy zata gani ba ,ring d'aya biyu akayi sa'a ya d'auka Aslamu alaikum yace ”momy ce tace ” walaikumusalam kazo ka d'auki matarka tarasa mota ,cikin zumud'i yace ”ganinan zuwa momy ,Khadija ko harta shige gida sa kaya saboda kafin ta tafi tayi wanka , wow tana sanya kayan suka fito da ainihin kyawun ta inka ganta zaka rantse itace amaryar dukda nima banga amaryar ba ,da k'yar tasa skirt d'in domin ya matseta sosai gakuma takalmi mai tsini sosai ga nad'in gwagwaro da 'akayi mata ,d'ankunne da sark'a tasa ta d'ibi kud'ad'en datakai akayimata canji aka bata sababi ,mayafin kayan ta yafa a kafad'a ....✍️🤙.



Mom Islam ce

*LADIDIN K'AUYE*


Funny & love story.

*Labari mai ban dariya had'i da fad'a karwa*



*NA*

*MOM ISLAM*
*ZAINAB HABIB*


*MARUBUCIYAR:*

*ZAINABU ABU*



*AND NOW*

*LADIDIN K'AUYE*



*BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM*


*Episode:* 43_44




_____D'akin momy ta nufa ,momy na ganinta ta rangad'a gud'a mutane sai kallonta sukeyi wasu na gulma wasuna cewa tabasu sha'awa ,momy ce tajata gefe tace ”please daughter karkiyiwa mijinki rashin kunya kinga can jama'a suna kallonku dan Allah badan niba ,sunkuyar da kai Khadija tayi tace ”momy wallahi bazan yimai rashin kunyaba ,cikin jin dad'i momy ta mik'o mata dubu biyar sabbi tace ”tayi manni ,godiya tayiwa momy ,suna cikin magana saiga Humaid nan yashigo cikin shadda mai ruwan coffee shimafa ba k'aramin kyau yayi ba kai kace shine angon ,durk'usawa yayi har k'asa ya gaida momy ,bayan ta 'amasa ne yashiga ya gaida jama 'ar dasuka taru ,daganan yafito ,ya yiwa Khadija magana ,cikin yanga tace ”inzo mutafi ? wani kalo yake yimata mai kamada na so hhh masoya kenan 😘,momy ko ganin hakan yasata shigewa ciki ,Humaid cikin wani salo maijan hankali yace”muje lokaci na tafiya ,ohk tace ”daganan suka wuce ,gidan gaba ya bud'e mata ,shigewa tayi shima yashiga hmm riders duk wanan ladabin da khady take yiwa humaid duk a cikin umarnin momy ne hhh🤣 driving yafarayi cikin k'warewa rik'o hannunta yayi da d'ayan hannunshi d'ayan kuma yana driving dashi ,ko k'ala batace ba ....



Da isarsu yayi parking gurinda kowa ya parka motarshi ,fitowa yayi yana jiran Khadija tafito ,hhh abinku da gimbiyar mata saida ta jima yana tsaye sanan tafito ,a yangace take tafiya ,Humaid ne ya hango wasu samari suna k'arewa shigar Khadija kallo, cikin zafin nama ya rik'o mata hannu suka wuce ,da shigarsu Hall din kalo yakoma gunsu ,sai tafi ake yimusu ,kusada ,amarya Khadija ta zauna shikuma Humaid friends d'insu nacemai ga guri yana cemusu shifa kusada gimbiyar zai zauna ,dole aka mik'o wata ha d'ad'iyar chair ya zauna ,kammo hannunta yayi yana mata rad'a 'a kunne ,nimafa banji meyace ba nadaiga suna dariya ,duk abinda sukeyi doctor Umar yana yimusu photo ...




Kiran Amarya akayi dakuma k'awayenta ,mik'ewa amaryar tayi Jalal kuwa yana rik'e da 'amarya dan haka suka mik'e a tare yana cemata wananfa matar yayana ce ,cikin fara'a 'amaryar ta rik'o hannun Khadija tace" kitaso muyi rawa dayake Saudat tasan rigimar Humaid ko kallonshi batayi ba 'amma tana jan hannun Khadija ,saboda daga ganinta saudat taji tashiga ranta sosai da sosai ,humaid kuma damk'e hannun Khadija yayi wai adole bazatayi rawa ba ,fakar idonshi Khadija tayi ta mik'e aka fara cashe rawa ,ganin bai hangota ba yasashi tashi yana lek'e ,hangota yayi kusada mai d'aukar photo ,zuwa yayi ya janyota yana mata kallon soo💖 ammafa 'akwai kishi over, ahaka dai akayi abubuwa kamarsu yanka cake dakuma bada tarihin amarya da sauransu ,ana shirin tashi ne aka sake kid'a mata da maza suna rawa ,Humaid na waya Khadija ta mik'e taje tafara rawa ,cikin zafin nama ya figota yana cewa kinada hankali kuwa ?ko kulashi batayi ba ya rik'e mata hannu suka fice.....





Direct wani katafaren hotel sukaje kayan dad'i yasa 'aka kawo musu ,sunci sun k'oshi daganan ya wuce gurin mai saida kaza tofa🤦‍♀️,


Guda biyu yasiya saboda yasan mutuniyar akwai son cin dad'i ,daganan ya wuce da ita wani katafaren shago kayane na Makkah su dogayen riguna da etc.. cemata yayi kiza6i wanda ranki yakeso cikin zumid'i ta hango wata riga da tun tana budurwa take burin sata 'amma saboda tsananin tsadar 'rigar yasata hak'ura ,yaukam zata gwada d'auka ko zai siya mata ,nuna rigar tayi tace ”nidai wanan rigar nakeso ,Humaid ne yace ”to ita kad'ai ta isheki ?eh tace ” saboda tana tunanin inyaji kud'in rigar cewa zeyi ya fasa ,mik'a rigar yayi ,mai lissafin kud'in kayanne yace”50k take ,cikin ko d'ar yace ”ok yabada ATM aka cire suka wuce,mamaki ne yacikata ,amma babu bakin mgna tayi shiru ,hanyar gidanshi ya nufa da ita ,zaro ido tayi tana kallon ikon Allah ,momy ce take kiranshi a waya ,ganin kiran yasashi cewa osh momyyy ,d'auka yayi ,yace ”momy mundawo fa momy bata yardaba tace ”to yanzu kuna ina? Munje kasuwa yace”a tak'aice hmm momy tace ”to maza _maza kudawo gida ,farinciki ne ya lulu6e khadija ta fara murkishi tana cewa hhh kaza zanciki ina komawa gida ,shiko humaid haushine ya cikashi ganin yaufa momy ta takura masa ,yanzu yasiyo kajin a bati kenan ya tambayi kanshi ,juya kan motar yayi zuwa unguwar su momy ....





Suna isa yayi Horn mai gadi ya bud'e mai ya shige da motar ,khadija ce ta juya ta hango ledar kazar a back side ,saida tafara bud'e k'ofa tukun ta janyo ledar ta ,arce da gudu tana dariya ,wata muguwar yaunwa humaid yakeji gashi Khadija ta d'auke kajin ,kaii yace yana mai d'ora kanshi a booth d'in motar ,





Cikin sanyin jiki ya shige parlor yana mai sallama wucewa part d'inshi yayi ya kwanta idanunshi a rufe amma ba baccin yakeyi ba,yanason su zauna da khadija yaji ko tana sonsa kokuma zata sauya ra'ayi ,amma yana tsoron yimata magana ta taso da 'abinda yariga ya wuce , bacci ne ya d'aukeshi yana cikin tunanin khadija ,wani mumunan mafarki yayi wai ga khadija nan wani mutumi ya rik'e mata hannu sunata gudu, a tsorace ya farka yana salati ,çikin azama yayi part d'in khadija ,samunta yayi tayi
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment