Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

na rana ta mik'e had'e da salati a bakin ta ,wata masifaffiyar yunwa takeji mik'ewa tayi ta nufi kitchen tana shiga taji k'amshin indomie jollof ,bud'e murfin tukunyar tayi ganin kayan k'wad'ayin da 'aka samata yasata zaro ido k'wai ne dafaffe sai karas ,abinka da gidan kwad'ayi ai dandanan taji ranta ya biya tuno mai girkin tayi wato Humaid tsaki tayi kana ta sunkuci tukunyar tayi d'aki ,bathroom ta shiga seda tayi wanka tayi brush sanan ta fito ta zauna 'a gaban dressing mirror tana shafa mai tana wak'a tunowa tayi ai bata kulle k'ofa ba ,dagudu ta mik'e taje tasa key tadawo taci gabada Kwaliya bayan ta d'au makeup mai kyau ta ciro shadda bugaggiya mai ruwan coffee tasa takuma ciro bra da pant da warwaro da sark'a wow ba k'aramin kyau tayi ba ,zama tayi gurin tukunyar indomie tafara baiwa cikinta rabonsa saida taci ta k'oshi tayi gyatsa sanan ta mik'e tayi gurin madai daicin fridge d'inta taciro hollondia mai sanyi ta kkora."


Daganan ta 6oye tukunyar .




Yana fita direct kitchen yanufa ganin baiga tukunyar daya d'ora ba yasashi zaro ido had'e da dogon tunani ,komawa parlor yayi ya murd'a handle d'in k'ofar jin a kulle yafara tunanin kodai Khadija ce ta d'aukemai hanyar d'akinta ya nufa jin k'ofar ansa key 'yasashi cewa "wallahi koki bud'emin kokuma duk lokacin da kika fito sainayi maganinki , tanaji yana sababi amma fur tak'i fitowa ,gajiya yayi da tsayuwa , komawa d'akinshi yayi ya watsa ruwa daganan ya fito yayi shirin tafiya gurin cin abinci .

Tanajin k'arar motarshi ta fito rik'e da gyale a hannunta dakuma takalmi mai tsini yiwa drivern gidan "magana tayi da saurinshi ya taho ya durk'usa 'a gabanta yace " hajiya Mota zakishiga ?"eh tace"daganan ta shige mota suka nufi 6ukur park wato anguwarsu momy ,murna take sosai kamar mai shirin tafiya hajji ,suna isowa kusada gate d'in drivern ta yafara horn mai gadi ne yaje ya bud'e mai daganan suka kutsa ciki ,suna sauka ta ruga ciki da gudu,turuss tayi ganin Humaid zaune yanacin farfesu ,zaro ido tayi tana jujuyasu shikwa yiyayi kamar bai ganta ,fakar shi tayi ta shige bedroom d'in momy da gudu ....✍️✍️✍️.



~MOM ISLAM CE~✍️.

*LADIDIN K'AUYE*


Funny & love story.

*Labari mai ban dariya had'i da fad'a karwa*



*NA*

*MOM ISLAM*
*ZAINAB HABIB*


*MARUBUCIYAR:*

*ZAINABU ABU*



*AND NOW*

*LADIDIN K'AUYE*



*BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM*


*Episode:* 25_26



_____Samun momy tayi ta fito daga wanka ,dagudu taje ta rungume momy saikuma ta fara kuka Momy datake murna saikuma 'annurin fuskarta ya disashe kasancewar taga Khadija na kuka ,janyota momy tayi zuwa bakin gado bayan sun zauna ne "momy take tambayarta tare sukazo da Humaid ne ?" saboda taga Humaid 'din bai dad'e da zuwa ba ,Khadija ce ta share hawayen ta tace"momy babu komai kawai farincikin ganinki ne ,badan momy ta yarda ba tace"to nima nayi farinciki da ganinki my daughter ,saidai naga kin rame sosai kodai da wata matsalar ne? a'a tace" Momy ce tace"to gyramin gaban mirror d'innan ,to Khadija tace" tafara 'abinda momy ta sata momy tayi hakane domin tasami damar zuwa gurin Humaid saboda shid'in ma ya rame sosai,bayan momy ta fita ne Khadija tace" na shiga uku gara da ban fad'awa momy komai ba da walhi zata iya fushi da Humaid.


"Momy nazuwa parlor tasamu Humaid na danne _danne a waya yana ganin momy 'ya d'ago kai yace" barka da fitowa momyna dafatan kin fito lafiya ? Lafiya lau momy tace"Allah yayi albarka cike da kulawa yace amen momy _momy ce takai dubanta ga Humaid tace"amma dai kuna zaune k'alau ko?"cikin rawar baki yace"eeh eeh lafiya Lou ,momy ce tayi murmushin su na manya tace"bakwa zaune lafiya Humaid a zabure Humaid ya kalli momy 'yace ita Khadijan ce tagaya miki haka ? ko d'aya momy tace"daganan kuma duban Humaid a karo na biyu saboda 'akwai abinda take karanta "cewa tayi karka manta yarinyar nan marainiya ce bamu baka ita dan ka cutar da ita ba kuma na fuskanci ko a lokacin auran kayi farinciki amma metayima dahar zaku dinga cutar da rayuwar ku?" sunkuyar dakai yayi kana yace nikam 'momy saidai kiyi hak'uri dani dan wallahi bazan ta6a son Khadija ba kuma wlhi ko meye ya wanketa zaro ido momy tayi had'e da d'an gutun hawaye tace"ni Humaid kake gayawa wanan kalmar ni ko kukane ya kufcewa momy cikin k'araji tace tunda kazo.duniya bamu ta6a musu dakai ba 'amma zuwa yanzu ne zakace zamudinga musayar yawu dakai ,hak'uri ya shiga bata ganin bata kulashi ba yasa ya durk'usa kan guwaiwar shi yana bata hak'uri,ko kallon shi momy batayi ba ta mik'e cike da matsanancin 6acin rai tace "wallahi wallahi inhar ka cuci Khadija 'Allah ya isa tsakanina dakai!!!."


Cikin firgici ya d'ago kanshi da yayimai nauyi yace "ni momy kike yiwa mugun baki " nafad'a nace nafad'a kozaka mareni ne tunda yanzu ka isa yiwa kanka komai "momy tace" cike da takaicin halin da takeciki, komawa tayi cikin bedroom ta sami Khadija ta zuba uban tagumi girgiza kai momy tayi daganan tace"kitashi kibi mijinki ,Kadija ce ta dubi fuskar momy tace"momy maiya faru naga kamar kuka kikayi ?cikin sasanyar murya momy tace "ba kuka nayi ba kwai raina ne ya 6aci ,adu'a Khadija tayiwa momy daganan ta d'auko mayafinta ta fice, bata sami kowa 'a parlorn ba hakan yabata damar wucewa parking spice da sauri jin anata kiraye _kirayen sallah magrib yasa ta k'walawa drivern daya kawota kira jin shiru bai zoba yasa fara jin haushi tafara cewa kodai'in kar6o keyn mota ta ne?komawa tayi tace" momy bani mukullin motar da dady 'yasiyamin 'nabaki ajiya ,momy ce tace"ina mijinnaki yayi ?"cewa tayi ya tafi wlh kuma driver ba banganshi ba ,d'auko mata momy tayi daganan tayiwa momy sallama ta wuce mota .



Ganin motar a lulu6e yasata yayewa ta shige da bismillah ta fita daga cikin gidan tahau titi ,tafiya takeyi cike da kulawa har Allah yakawota gida lpy, da saukarta ne taga Humaid bai dawo ba hamdala tayi daganan ta wuce kitchen ta d'ebo kayan shayi duka har indomie kwali biyu ta d'ibo kwai kuma ciko kwali tayi kasancewar yafi k'arfin abin d'ora k'wan a cewarta tadena fita mancewa tayi bata d'auko abin girki ba zuwa tayi tana tunanin da gas da electri wane zata d'auka ,kinkimo gas tayi tana cikin tafiya ne taji alamun dawowar Humaid ,cikin azama ta ruga dashi d'aki tana nishi ,ta rufe k'ofar da key.



Yana shigowa da sallama 'a bakinshi ya doshi k'ofar d'akin Khadija jin ta rufe k'ofar ne yasashi k'wafa yace"wallahi tunda kikaje kika had'ani da momy na wallahi saina miki jina jina ,tana daga d'aki tana yimai gwalo haka yagama sababin shi ya fice ,yayi d'akinshi".






Bayan Khadija tayi sallah taji wata fitinanniyar yunwa na mata sallama mik'ewa tayi ta kuna gas duba tukunyar dazata d'ora ruwan zafi tayi bata gani ba zaro ido tayi tana salati tace yanzu ni mezanci d'anyan k'wai kokuma d'anyar indomie kokuma lifton zanci? babu madara babu sugar ?wayo Allah na nashiga uku ni LADIDI!!.tasa indomie a gaba tayi ta farke leda d'aya tanaci tanashan ruwa kasancewar lemu ya k'are a d'akinta bayan tagama cine tayi ,isha 'I daganan ta haye gado bayan tayi addu'oin dasuka zamemata wajibi ta kwanta badan ta k'oshi ba , asbha ta gari.
Washe gari bayan tayi sallahi ta mik'e tanason fita tanajin tsoro ,shiko gogan tunda yadawo daga masallaci ya zauna ' a parlor ya kunna TV kuma yaune komawar shi gurin aiki wato hospital d'inshi dan tun dare ake ta yimai waya'akan anason ganinshi ,shi burin shi bai wuce yaga ya illata Khadija ba ,ita kuma Khadija tak'i fitowa saboda tsoron Humaid ,gajiya yayi da zama duba 'agogon dake d'aure a tsintsiyar hannunshi yayi ,k'arfe goma da rabi 10:30 bai fita ba duk akan wanan shegiyar yarinyar?"yake tambayar kanshi tsaki yaja ya fice zuwa bedroom d'inshi wanka yayi yana fitowa yaga har sha d'aya tayi 11:am zaro ido yayi ,kamar maijin kashi ,shiri yakeyi jikin gaggawa kamar mai tashi sama da sauri yayi waje gurin motar shi , ya tayar ya mik'i hanya".


Tanajin fitarshi ta fito da gudu tayi d'akin shi ganin kayayyakin daya siyo tayi zaro ido tayi tace"shiyasa ko ya nemi abubuwan dana d'ebo tabb aikuwa saina kwashe wa in an ma ,fara jidowa tayi tana haki ta kwashe kayan abincin dukka harda su carton d'in maltina dana madara dakuma k'wai duka ta kwashe tana dawowa taga wani kayan ganin jikin kwalin anrubuta golden ai kawai ta loda takai d'aki a ranta ko tana cewa shikenan 'na huta da girki ko lemon kwalba ma ya isheni, kitchen taje ta d'auko tukunya da wuk'a dakuma mangyad'a da kayan miya tadawo d'aki tasa key .


Misalin k'arfe biyar na yamma yadawo a gajiye ya shige toilet ya watsa ruwa yana fitowa kwai yaji yana sha'awar shan golden beer zuwa inda ya 'ajijiye kayan yayi ganin baiga komai ba yasashi zaro ido ,cikin kunar 'rai yace "wato wanan tsinanniyar bacin zina har giya takesha?" zama yayi a bakin gado yadinga girgiza k'afa yana bala'i arayuwa bayason a d'auki abinshi ba'a tambayeshi ba ,cikin masifa yafice daga d'akin 'nasa yana zage zage kuma ya kudurta 'a ranshi ko k'ofar zata 6alle yau saiya ci uban Ladidi ,yana zuwa yaji kamar kullum k'ofar a rufe take da key dukan k'ofar yakeyi kamar mahaukaci amma tak'i bud'ewa itako tana tsoron karfa ya 6allah k'ofar nan yazo yakusa kasheta dan yau kamar yasha ya bugu,shigewa cikin drower tayi tanata zaro ido kasancewar akwai gurin sa sak'ata ta ciki kuma tanada zurfi ba lallai mutum ya bud'eta da garaje ba....✍️✍️✍️.



Mom Islam ce


*LADIDIN K'AUYE*


Funny & love story.

*Labari mai ban dariya had'i da fad'a karwa*



*NA*

*MOM ISLAM*
*ZAINAB HABIB*


*MARUBUCIYAR:*

*ZAINABU ABU*



*AND NOW*

*LADIDIN K'AUYE*



*BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM*


*Episode:* 27_28



_____Cikin k'arfi ya bigi k'ofar har saida ta bud'e tsayuwa yayi yana maida nunfashi kasancewar k'ofar bata ra'go bace ,kutsa kai yayi cikin d'akin yana haki yana cewa inakike dan ubanki yau saina karyaki ,dube dube yakeyi amma ina baiganta ba bud'e toilet yayi nanma bata nan rik'e k'ugu yayi kamar mace yanason yaga ta inda zata bullo amma inna ko alamun ta baigani ba, wata muguwar tsawa ya daka, Khadija dake cikin kaya saida ta firgita 'amma dayake tasan tayi lefi ko k'ok'arin guduwa batayi ba , ficewa yayi da gudu yaje ya d'auko wani key a d'akinshi yazo ya kulle k'ofar a tunaninshi ta fice yawo ne, yana fita ta fito.daga ma6oyar ta sai gumi take sharewa ,zuwa gurin kwalayen data d'ibo tayi ganin golden beer dama tasa biyu a fridge ta bud'e ko karantawa batayi ba ta hau sha jin zak'i zak'i yasata lumshe ido ,tanagama sha ta wurgar da gwangwanin ."



Luuu tafara gani wata zabura tayi tafara maganganu tanacewa wai naga kamar duniyar tak'ara haskene tabb naga ta kaina yaukuma gashi goma na dare amma basai ankunna fitillah ba tafara layi tana surutai ,gyatsa tayi tace"sweet lemu kamar nasha zuma kai firig zonan kabud'e in k'ara ,ganin dai fridge bashida niyar zuwa yasata mik'ewa tana layi ta bud'e zata d'auka tafad'i k'asa tana cewa to wane mugunne kuma yake k'ok'arin ganin bayana?"can kuma tasa dariya tace"ni wallahi nagaji da wannan duniyar kuzo ku kaini duniyar ku.

Jin alamun bud'e k'ofa yasata zubawa da gudu yana bud'e k'ofar yad'n matsa yana so ya kamota aikuwa ta fice da gudu tayi kitchen tasa sak'ata lokacin tafara dawowa hayyacin ta ,baibi takan d'akin 'nataba bare yaga 'abinda tasha hannu ya buga'a bango yanacewa kokuma 'ajanun k'auye sun shafeta ne shiyasa take 6acewa?"can kuma ya mik'e yayi d'akinshi jin ana kiran sallahr mgrib , bayan yayi alwala ne ya kulle gidan ta baya ya wuce masallaci ,Khadija najin fitarshi taja jiki tana tafiya tana layi tayi d'aki ,ganin gwangwanin madara yasata bud'ewa ta saida ta shanyeta tass tukun ta kuma kwanta 'a gurin bacci mai nauyi ya d'auketa ...

Jin wani sanyi mai kamada ruwan k'an k'ara ya tashe daga baccin da takeyi duka taji ko ta ina tarasa waye mai dukan 'nata ihu takeyi 'iya k'arfinta 'amma innaa bbu halin tashi bud'e idanuwanta dasukayi mata nauyi tayi ganin Humaid a tsaye kamar wani soja yasata cewa to Allah ya isarmin mugu kawai buge bakin yayi ya cire bell d'in wandinshi yana dukanta ta ko ina ganin babu mai ceton ta yasata juye juye tananeman abinda zata buga mai ,ganin babu komai yasata dai daitar saitin wandonshi ta murd'e gabanshi ta zura da gudu wani wahallalen k'ara yasa mai wuyar fassara wa yarasa maiyakeji ,jiyayi kanshi na juyawa rike da mararshi ya fad'i k'asa sumamme, Khadija ko kitchen tanufa ta fere doya ta wanke ta dafata daganan ta soya da mai tanayi tanacewa kafin ya tashi naci nak'oshi mugu kawai ,tana gamawa ta soya miyar k'wai kasancewar akwai kayan miya batasha wuyaba seda taci ta k'oshi dak'yar take iya tafiya da ruwan gora 'a hannunta ta k'arasa d'akin ,ganinshi kwance yarik'e gurinda ta murd'e kumfar yawu na zuba 'a bakinshi yasata rugawa d'akinshi da gudu cikin tashin hankali wayarshi tagani a kan gado duba number tahauyi ,ganin doctor Umar yasata danna kira ring d'aya ya d'auka 'a zatonshi Humaid ne ,jin muryar mace yasashi cewa madam barka dai, cikin firgici Khadija tace "Umar dan Allah kazo ka duba Humaid dan Allah kayi sauri ko motsi bayayi ,a tsorace Umar yace " karki damu ganinan zuwa to tace"kawai domin hankalinta yafi na 6arawo tashi.


Ba'a d'au wasu mintuna ba saiga horn d'in motar doctor Umar yana zuwa ya nocking d'aga murya tayi tace"shigo doctor ,da y'ar jakarshi a rataye ya k'araso yana haki'i tsabar kukan daya ku6ce mata bata iya magana ba nunamai d'akin da Humaid yake kwance tayi , shigewa yayi da sallama Doctor Umar ganin halinda Humaid yake ciki yasashi rik'e kai yana cewa innalilahi wa innailahirraji'un ya Allah help me,idonshi cike da hawaye ya kinkimi Humaid kamar gawa yasa 'a mota cewa Khadija ta kulle gidan ta biyoshi yayi to kawai ta iya cewa kasancewar gani takeyi kamar Humaid ya mutu ne."


Rufawa doctor Umar baya tayi dole ta shige gidan gaba saboda 'an kwantar da Humaid a back side ,tun doctor Umar na hanya yake waya akan a tanadar musu d'akin saboda Humaid babu lafiya kuma yana buk'atar temakon gaggawa kasancewar hospital d'in akwai nisa saida sukayi tayi maid'an 'nisa sannan suka iso a keken tura marar lafiya 'aka turashi direct d'akin da 'aka tanadar musu suka tafi likitoci biyar ne akanshi amma kowa sai share gumi yakeyi ,itako Khadija sai safa da marwa takeyi a harabar asibitin ,likitoci sun shafe wajen awa 1 hour suna bincike akan suma samu nunfashin ya tsaya 'abin ya citura sai da suka kuma shafe mintuna talatin sanan sukayi sa'a ceto rayuwar shi ,ba'amayi batun gurinda 'akayiwa illa ba tukun ganin ya bud'e ido yasa likitocin cewa Alhamdulilh Allah mun gode maka ,jin ana hamdalah yasa Khadija saurin k'arasowa tana kuka tana ganin Humaid ya bud'e ido takama dariya tana yiwa Allah godiya.



Likitocin'ne sukace to yanzu saimu koma kan inda yaketa nunawa tun d'azu a kunyace Khadija ta fice daga d'akin ganin ana k'ok'arin duba gurin bayan sunyi y'an bincike ne suka gano cewar yasami matsala 'agurin kuma indai ba fita dashi k'asar waje akayi ba to kafin yayi sex da matarshi zai iya kaiwa shekarar biyar kokuma k'asa da hakan kasancewar Nigeria basuda cikkakun kayan aiki,kwanansu hud'u a hospital d'in Doctor Umar shike jigila 'akan kayan abinci asibiti dai babu bataun biyan kud'in domin mai asibitinne a kwance babu lafiya.



Yaune aka sallamesu Khadija na tsoron gayawa momy halin da 'ake ciki saboda hukuncin dazai biyo baya ,amma babu inda ta iya dole ta sanar dasu ,tanashirin d'aukar wayane Humaid yace "karki kira su momy dan wallah natashi saina kusa karyaki ,Khadija ce taja baya ta murgud'a mai baki tace a hakanne zaka karyani tabb wlh gara kayi a hankali karka famo gurin da 'akayima bandeji hhh, harararta yayi sanin bazai iya tashi ba yasata fad'ar hakan, rugawa tayi da gudu ta d'auki wayar ta danna number momy ring biyu ta d'auka momy ce tace" my daughter yakike lafiya tace"cankuma tace momy Humaid babu lafiya fa momy ce tace"maiya sameshi ? Shiru tayi can kuma tace" fad'uwa yayi a toilet momy ce tace"to yaji ciwo ne?eh Khadija tace"dan yanzuma 'a kawance yake kwananmu hud'u a asibiti shine yace"wai karna fad'a muku,momy ce tace"to gamunan zuwa 'Allah yakawoku lafiya Khadija tace"daganan ta shige bedroom d'inta ta kwaso kayan abincin datakai can tana cikin kwasowa ne hankalinta yakai kan kwalin golden beer d'inda tasha tana karantawa tahau salati ,can kuma tayi gumm da bakinta mayar da kwalin golden beer d'akin Humaid tayi ta tura 'a k'ark'ashin gado sauran kuma takai kitchen ,wanka tashiga tayi kwaliya kamar maishirin fita anguwa ,shidai Humaid na parlor magana ma ta isheshi ....✍️✍️✍️.



Mom Islam ce

*LADIDIN K'AUYE*


Funny & love story.

*Labari mai ban dariya had'i da fad'a karwa*



*NA*

*MOM ISLAM*
*ZAINAB HABIB*


*MARUBUCIYAR:*

*ZAINABU ABU*



*AND NOW*

*LADIDIN K'AUYE*



*BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM*


*Episode:* 29_30



_____Momy ce ita da dady suketa sallama cikin sassanyar murya Humaid yace"wa'alaikumussalam shifowa sukayi ,ganin Humaid ya mugun ramewa yasa momy k'araswa kusada shi da sauri tace"my son maiya faru dakai naga ka koma haka ?"cewa yayi momy babu komai kwai banida lafiya ne dady daya saki baki yace"to ai Khadija tace "mana zamewa kayi ?" shiru yayi yana tunanin k'arya irinta Khadija cewa yayi eh hakane kasancewar inya fad'a musu halinda suke ciki zai 'iya fuskantar matsala dukda ciwon dayake damunshi , Allah yabada lafiya sukace daganan saiga Khadija ta fito sake baki momy tayi ganin wata uwar 'rama da Khadija tayi amma taja bakinta tayi shiru ,rungume momy Khadija tayi tana murmushi tace "momy na kinzo lafiya ?dady ne yace" to gani a gefe tunda 'an manta dani rufe fuska tayi tace"dady afuwan kunzo lafiya cikin farinciki dady 'yace"lafiya yamai jikin ? dasauk'i tace "cankuma ta shiga damuwa momy ce taga 'alamun fuskarta tace" lafiya Khadija??" fashewa da kuka tayi shidai Humaid na gefe ido ne nashi ,tsagaita kukan tayi kana tace "momy matsala Yaya Humaid yasamu momy ta bud'e baki tace" a ina?shiru tayi can kuma tace"kuma doctors sunce sai an fitar dashi waje!!! jin wanan kalmar ta k'arshe ya girgiza su momy sukace to matsala yasamu a brain d'inshi?a'a tace" tashi tayi taje ta d'auko file d'in asibitin mik'awa momy tayi ,momy na kar6a ta mik'awa dady Humaid ko dariyace taso kufcemasa wai takasa fad'ar abinda yasameshi hhh,dady na dubawa yace"innalilahi oh Allah momy ce tace"maiya faru ne ?dady daya had'a zufa ba kud'in fita k'asar wajenne damuwar shi ba larurar Humaid d'ince damuwar shi ,dady ne yagawa momy komai dagan suka fara jinjina lamarin.




Dady ne yace ”Allah yakaimu gobe ,dady ne yakira waya airport saboda 'ayimusu tanadin jirgi , yayi sa'a zasu samu na k'arfe 4pm zasubi , dady ne yace ”maganar hospital d'in babu matsala wuyarshi Allah ya kaiku lafiya ,Khadija ce tace ”dady nidai bazanje ba momy ce tamaida dubanta ga Khadija tace ”to ko maiyasa bazaki ba Khadija? "shiru tayi ta sunkuyar dakai ,tana wasada fingers d'inta ,momy ce tace ”aikuwa tafiya dake dole kece matarsa mukuma daga baya zamu biyoku anjima zan sa driver yakawo miki waya saboda gaisawa ,to kawai tace” saboda musu ba halinta bane mik'ewa sukayi suna yiwa Humaid Allah yak'ara lafiya 'amen kawai yace”daganan suka fice ,mita tashiga yi tana cewa mutum bai damu dakaiba baidamu da damuwarka ba baisan darajar kaba 'amma kaje kayimai jinya daga baya 'yazo ya wulak'antaka,shidai Humaid na jinta bashida lokacin bata 'amsa kasancewar shi ta ciwon jikinshi yakeyi ,wurgamai harara tayi daganan takuma cewa wallahi mukaje ka walak'antani saina k'ara janyo wani jan aikin tunda mutum cin zali yayimai yawa ,zaro ido yayi kuma yana mamakin wai yatsaya wanan shegiyar yarinyar tana gayamai maganganu baid'au mataki ba ,tunawa yayi sai an temakamai zai 'iya tashi k'wafa yayi ya maida kai ya kwanta 'akan kujerar bud'e baki Khadija tayi tace ”da dukana zakayi ahayye ni Dije wallahi kama sameni ne da lokacin da nake garinmu ne tabb dakadinga yimin ladabi dan bana d'aukar 'raini, Humaid maganganun Khadija sun 6atamai rai sosai amma da yanada lafiya babu abinda zaihana ya hukuntata, amma 'akwai lokaci ."




Komawa d'aki tayi tafara had'a kayanta dakuma 'abubuwan dazata buk'ata kitchen ta wuce ta d'ebo naman kaza 'a fridge ta sa kayan k'amshi dasu atta ruhu ta tafasa naman yana dahuwa ta d'auko turmi tafara dakawa da 'alamu dambun 'nama zatayi bayan tagama ne tahau suya rana gama suya ta d'ibo dakkaken yaji ta zuba 'a roba takai jakar tafiya , d'akin Humaid ta nufa tana duba kaya tana dariya gajerun wanduna ta d'ibar mai sunkai guda ishirin sai t sheet guda goma ,nikwa nace to ina manyan kayan ?" golden beer d'inshi ta d'iba har guda biyar tasa 'a jakarshi ,saikuma man shafawa dakuma takalmanshi tana gamawa ta fice ta nufi d'akinta .

Washe gari misalin k'arfe 9am saiga driver da abincin karyawa dakuma kwalin waya ,tana rawar jiki suka gaisa mik'a mata sak'on yayi godiya tayimai tashige ciki da gudu ,ganin babu Humaid yasata rik'e baki tace ”toshi harya sami sauk'i ne?"batada mai amsa mata tambayarta yasata yin shiru ,tafara duba wayar spark 2 ce maikayau sosai bud'e abincin tayi ganin soyayyen dankali dakuma wainar k'wai a gefe yasata kwashe k'wan tabar dankalin a dining, komawa d'aki tayi tacigaba da shiri wnka tayi ta fifito da kayan data d'ibar musu komawa tayi hanyar d'akin Humaid tana shiga ta hangoshi rik'e da waya 'a hannu da 'alamu charting yakeyi ,girgixa kai tayi tafara cewa lallai to ai basai anje Indian ba tunda kaji sauk'i barin cewa su momy wai abarshi ,da mamaki yake kallonta dubanta yayi 'irin kallon kinrainani d'inan yace”wallah zan 6a66allaki wucemin anan dan ke bata yimiki amfani shine zakimin mugunta ko muguwa kawai dariya tasa tace”kai kadamu da iskanci nikam Allah ya sitiri buk'wai ,shiru yayi ganin raini zai shiga tsakani ,k'arawa gaba tayi tace ”daya d'auka ni yar iska ce ,hmm to ma wai da dayakecemin mazinaciya menene amsar hakan?tana yiwa kanta tambayoyi can kuma tace ”ok natuna lokacin da Ammar ya saceni shine yake zargin 'nice naje d'akinshi?rasa maibata 'amsa tayi hakan yasa takoma d'akinta tana saka sim card a wayar ta memo ta d'auko wanda tayi seven number k'awayenta dakuma ta momy saka numbobin tashiga yi tana murna."




Da misalin k'arfe 3:dai dai dady 'yakira Khadija kasancewar sund'au number tata tana d'agawa dady yace”to inkun kammalah gamu nan a hanyar zuwa airport ku hanzarto angama komai tun jiya to tace”gamunan zuwa dady ,zuwa d'akin Humaid tayi tace ”kafito gasu dady can a hanyar airport mik'ewa yayi jiki babu k'wari yace ina kayana?cewa tayi gasunan a jaka bud'e gurin kayan 'nashi yayi yakuma lodar 'rigada wando kamar yasan bata d'ibarmai ba ,cemata yayi bar 'rawar jiki dan kona sami lafiya 'aure zan k'ara ,Khadija ce tace ”a hakan da babu k'arfin jikin kana tafiya kamar mace,zaro ido yayi yace"wlh zanci ubanki shigewa tayi tarabu dashi tasandai koba komai ta gasamai magana.



Shigewa mota sukayi sun d'anyi tafiya sanan suka iso airport d'in samunsu momy sukayi a zaune suna jiransu k'arasawa gurinsu sukayi suka durk'usa suna gaisuwa Humaid dak'yar ya mik'e itako Khadija dariya takeyi k'asa k'asa jin lokacin tafiyarsu yayi yasa momy yimusu fatan 'nasara ta mik'awa Khadija wani babban jaka mai zurfi ,dady ne yace ”nayima transfer na kud'i bakada matsalar su godiya yayiwa dady daganan suka shige jirgi ,hawaye Khadija tafara shareware saboda tasan momy ma dauriya kwai takeyi ,jin tashin jirgin yasata rik'o Humaid ta matseshi tsaki yaja yace ”dalla ni karki sakamin k'azamin jikinki banza kawai ko kulashi batayi ba tacigaba da rik'eshi ,shikuwa bashida k'arfin kokawa
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment