Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

bacci akan sallahya gakuma plet d'inda taci kaza ga ragowar kazar a gefe,zama yayi shima ya cika cikinshi sosai sanan yashiga toilet d'inta yayi alwalah yazo ya tada sallah ,yana idarwa ya kwnta ta bayanta ,khadija jin mutum a kusada ita yasata kurma uban ihu tana salati ,lokacin dare yayi sosai dan 11pm na dare ,dady ne yafito shida momy cikin razana ,kai tsaye d'akin khadijan suka nufa ,humaid najin alamun zasu shigo ya shige toilet yana rawar jiki ,ganin harta koma bacci yasasu komawa bayan momy tayi mata 'adu'a ta fice .....


humaid ganin khadija zata iya tona masa 'asiri yasashi komawa d'akinshi babu shiri ...


Dady ne yata humaid da khadija akan maganar komawarta hhh jiyafa humaid kwana yayi yana sallah akan Allah yasa khadija ta yarda ,dady ne yace ”to gareki khadija zaki koma gidan humaid 'd'inne kokuwa ,dogon 'nazari tayi akan hallacin da su momy sukayi mata ko d'an cikinsu albarka gaskiya koda batason humaid bazata iya duban idanunsu tace ”bazata komaba ,sunkuyar da kai k'asa tayi tace ”na 'amince wow kuzofa kuga rawar jiki ko kunyar dady baiyi ba ,ba humaid ba har dady 'yaji dad'i sosai ,albarka yadinga samusu dakuma fatan alkairi da zuri'a d'aiyyiba ,momy ce tafito itama tana tsaye tanajin duk abinda 'ake cewa ba k'aramin murna tayi ba.....



Washe gari wani gyara momy tafara yiwa khadija su dilka ne su tsumi ne dasu garin sha magani dai kala_kala gasu humra da ta jiki data kaya gakuma kayayyakin d'aki da dady 'yasa 'akawo daga kamfani a fitar da na gidan......✍️.




Kwanaki k'alilan khadija ta sauya tayi kyau sosai ,humaid kuwa jira yakeyi ace yatafi da ita 'amma shiru ,hhh yadai fara shawarar ya gudu da ita , saida 'kayi one month da magar sanan momy ta amince yake zuwa gurin khadija washe gari kuwa dady 'yace ”ya tattara matarshi su wuce ,aikuwa kamar yana jira yace ”tafito ,momy ce tace ”ya kara mata one week 'komawa d'aki yayi yana kuka hhh manya, washe gari kuwa ko sallama baiyi musu ba Yakoma can gidan ganin Sabin gyaran da dady 'yasa 'ayi yasashi farinciki....


Yana 'alfahari da iyayenshi sosai da sosai adu'oi yadiga kwararo musu ,yana cikin hakanne yaji ana nocking zuwa yayi bud'e k'ofar yana budewa yaga khairat ce ,tsaki yaja ,cikin k'ufula yace ”mekuma kikazoyi gidana ?"tsaki taja tace ”naje na zubar da cikin kuma yanzu takarda ta nake jira ,cikin sauri yayo kanta ,kome ya tuna ya fasa ,cikin azama tace ”wallahi daka doka hmm kabani takaddata in ficema daga gida ,domin wanan ai bak'inciki ne ace mutane na sonka insunji da igiyar aure a tsakani saisu gudu mtsw ,humaid ne yaje ya d'auko takadda ya rubuta mata 'abinda ta buk'ata ,godiya tayiwa 'Allah daganan ta fice ,shikam ko damuwa baiyi ba tunda Khadijanshi zata haifamai y'ay'a ...


Sati ya cika yaune ake shirye shiryen komawar khadija ,humaid ne yakoma gun doctor Umar akan ak'ara dubashi ,congrat yayimai yana dariya yace ”aci amarci lafiya yanzu kazama normal fa ,dariya humaid yayi yace ”nikam tun yau na d'auki hutu sai wata biyar dariya sukasa ,daganan yawuce gida zuwa d'auko gimbiya khadija ,tana kukan rabuwa da momy ,yashigo momy ce tace ”ka kula min da yarinya dan Allah ,insha humaid yace ”daganan momy ta rakata zuwa mota ,tuk'i yakeyi a hankali ,har Allah ya kawosu gida lafiya tana sauka zata fito ya ,sunkuceta ya goyata ya direta 'a k'ayataccen d'akinta ,ammafa d'akin yayi kyau ,tafad'a cikin zuciyarta ,humaid ne yace ”lovely dan zaki biyoni shine harda kuka ?"murmishi tayi ta nemi gefen gado ta zauna ,soyayya 'kuwa humaid ba bayaba dan jin k hadija yakeyi inta k'ara guduwa bazata dawoba*LADIDIN KAUYE*


Funny & love story


45 _46

Zai iya rasa rayuwar shi lalla6ata yakeyi akan taci kaza 'amma sai wani sharewa takeyi murmishi ne ya su6ucewa Humaid cikin zuciyar shi yace ”kamar ba ita bace kwad'a yayyar kaza ba ,haka yadinga bata 'a baki tana ci tana yanga suna gama ci yace ”taso muje muyi sallah dan nuna godiya ga Allah ,a gajiye take amma batada za6i dole ta mik'e sukaje yin alwalah ,suna idarwa ne yazo yaja musu sallah raka'a biyu sukayi yai sallama bayan sunyi adu'oi masu yawa , ya d'ora hannu a kanta yana yimata 'adu'a ,suna kammalawa ya mik'e ya nufi bedroom d'inshi sleeping dress yaje ya sako ita kuma lokacin tsabar gajiya kwanciya tayi da kayan jikinta ,Humaid bai kulata ba yaja filo ya kwanta 'acan gefe ."

Washe gari bayan tayi sallah ta duba bataga Humaid ba ,jin alamun shigowarshi yasata durk'usawa har k'asa tace ”barka da safiya yaya ,yww barka dai amaryar yaya ,da 'alamu baki damu da yayan naki ba ko ¿sunkuyar da kai k'asa tayi tana wasa da fingers d'inta surarta yai yace ”zomuje mu kwanta bacci nakeji please ya marai raice kamar yaro ,dariya yaso bata tace ”gaskiya not ni yanzu bazan kwanta ba buh wlh wanka zanyi tana magana kamar zatayi kuka Humaid ne ya shige ya barta 'a gurin ,juyi yakeyi baccin ma yak'i d'aukarshi tunani ya fara ,ina murna farinciki na ta dawo ashe akwai problems a gaba oh god Allah kadawo min da Khady kan hanya ."

Breakfast ta had'a musu mai rai da lafiya chips ne na dankalin turawa sau wainar k'wai dakuma tea mai kauri wanda yaji kayan kamshi ,dining room ta wuce dashi kasancewar ankuma gyara gidan ,tana fitowa ta koma kitchen kayan data 6ata ta wanke ta rufo kitchen d'in ,tsintsiya ta d'auko tafara share parlorn tanayi tana hutawa 'a haka ta gama mopping d'in tayi daganan ta kuna turaren wuta ,wani sihirtaccen k'amshi ke tashi a gidan ,bedroom d'inta ta shige ta cire kaya ta d'aura towel ta shiga wanka ,ta dad'e tana wanka da sabulun da momy ta bata mai kamshi tana fitowa ta ciro kayanta , gaban dressing mirror ta zauna simple makeup tayi ammafa ta had'u atamfar ta d'auko mai ratsin wait and black tayi d'auri mai kyau ,kin shiga bedroom d'in Humaid tayi can kuma ta shige da sallama tana cewa yaya Humaid katashi breakfast is ready ohk yace ”dagan ya mirgino yana yimata wani kallo cikin sigar wasa yace ”ke bakisan inda ake tashin miji daga bacci bane ¿" am sorry tace "daganan ta fice, brush yaje yayi daganan yai wanka ya shafa manshi man kamshi ya fito sanye da shadda pink sai d'aukar ido takeyi ,murmishi ya sakarwa Khadyja yace ”lovely mai yasa baki kirani nazo na tayaki ba ¿cikin sanyi murya tace ”nagama ai ,janyo gwangwanin madara da ragowar kayan tea yayi saida ya k'ara komai bacin wanda tasa dagan yace ”to bud'e baki naga 'alamun bakison cin abinci sosai ko ¿shiru tayi daganan tafara cin abincin ,kad'an taci tace ta k'oshi."


Kallonta Humaid yakeyi yarasa mai yasa yarinyar nan yanz bata sakewa dashi ,duk rashin kunyarta da neman tsokana yanz duk sunyi sanyi ,tunani ya shigayi to aure babu hira ina labari ,duk inda naso naga ta fahimceni amma lamarin ya citura ,mik'ewa yai yace ”lovely biyoni ki kar6i wani abu ,cikin sanyin murya tace ”ya Humaid banajin dad'i ynz kaina nayimin ciwo ,subhanallah to zomuje hospital a'a kabarshi inada maganin a d'aki please zani in kwanta ohk yace ”yarasa mai yaiwa khady take wanan slow d'in ,kodai har yanzun bata sonshi ne kwai tabi umarnin Momy da dady ne ,iska ya fesar mai zafi ya bugi bango yana dogon nazari itako tun tuni ta shige part d'inta."



Kwance take tana kallon sama tana tunanin rayuwarta tada 'a cikin gidan hmm da yace ”baya sona yanz kuma yace ”yana sona kai da 'ayar tambaya wlh but naji masoya na cewa in mutum ya k'ika daga frko to karshe koyace yana sonka yai karya , haka ta dinga juyi a bed d'inta tarasa maiyake damunta .


Washe gari ai yuka ta gabatar inda tasaba ko ina ta gyareshi gidan sai zuba k'amshi yakeyi ,yau 7 days da auransu ,nocking taji batayi azamar tashi ba saboda Humaid na nan ,ganin gimbiyar bata tashiba yasashi mik'ewa ya bud'e k'ofar ,su inna Hauwa ya gani ita da wata yarinya zatakai 13yrs a duniya sanye take da rigar banba lasta rigada wando sai hijab da yaji jiki ,inna ce tace ”munsha hanya fa khadija najin muryar inna ta mik'e da gudu tana oyoyo ,Humaid ne ya kar6i kayansu ya shige dashi d'akin bak'i yadawo suka gaisa ya fice sbda ana kiran sallah ,khadija ce tace ”inna kunsha hanya ya su baba ,lafiya Lou inna tace ”tana kalle² khadija ce ta dubi wanan yarinya tace ”inna naso in ganeta amma ta 6acemin ,yarinyar ce tace ”uhm ai wanan daular haka dole bazaki ganeni ba to inkin manta nice sahura waro ido khadija tayi tana duban sahura tace ”wai kece kika girma haka ? Sahura ce ta dubi khadija tace ”to ke kinga inda kika koma ne walahi kamar matan turawannan da muke gani a shagon mai shayi na anguwarmu ,dariya sukasa dukansu ,khadija ce ta shige kitchen sbda yimusu girkin lokacin 11am shinkafa jollof mai kifi da carrot dakuma green bean's dataji alaiyahu lokaci k'alilan gidan ya kaure da kamshi sosai ,Sahura ce tayo kitchen d'in da sauri tana cewa kufa y'an gayu inzakuyi girki bakwa gayya dariya khadija tasa tace ”to a wanan girkin menene abin wahala ?Sahura ce tace ”walhi ku kula saboda ance yawan ciye _ciyen kayan dad'i nasa ka mance da lahira Khadija dai bata kulata ba sai aikinta takeyi ,Sahura ce taga bread a saman fridge tsalle tayi ta d'auko ta yaga tace ”oh sai natuna lokacin da kike cutar mutane ki gudu amma yanzu ana yimiki magana ma sai kinyi ra'ayi ,hmm kawai khadija tace ”sbda hankalinta na kan girkinta."



Khadija ce ta dubi sahura tace ”to muje muyi sallah sai muci abinci ko ?Sahura ce ta yago bread tace ”tabb inma zaki zubo abinci ki zubo dan ni wata shegiyar yunwa nakeji yasin khadija ce tace ”zan zuba miki naki nikam zanyi sallah , tunda khadija ta zubo abinci Sahura ke had'iyar yawu tana lashe baki ,khadija ce ta mik'a mata tare da wani soyayyan nama a kai Sahura ce tace ”ke bakida wayo nikam kawo naman injishi a hannuna kar azo ba'a sawa inna ba tace saitaci ,khadija kam wucewa tayi tabarta a gurin tana tura nama cikin aljihun wando, bayan sun kammalah cin abincin khadija ta kwashe takai kitchen saida ta wanke sanan ta fito ,inna ce ta mik'o wa khadija wani k'ullin buhu tace ”lalle ne da barkono da kuma citta godiya khadija tayi sosai daganan inna tace ”zasu wuce Sahura da ido yai ja tace ”nifa inna kitafi walahi bazan koma k'auye ba kicewa babanmu sai yazo aurena ,dariya suka sa khadija ce tace ”to kizaune in kikayi sati biyu ko uku saiki koma ,tsalle sahura ta doka ta cakumi khadija tana murna ,inna ce tace ”to anta6a yanke hukunci babu mai gida khadija ce tace ai ya Humaid bashida matsala, haka inna ta tafi tabar Sahura ."


Washe gari Sahura ce gaban TV tana kallo a MBC action wani film suke yi mai fad'a suna cikin fadanne wani ya kaiwa dan uwansa naushi Sahura ce ta doka tsalle ta kaiwa khadija naushi har tana neman k'ara mata ,a razane khadija ta dago tana kallon Sahura da hankalinta ya tafi ga TV nuno gurin kuka 'akayi aifa ta zauna tadinga kuka harda gumi ,khadija ce ta tashi ta kashe TV n sallamar humaid sukaji Sahura ce ta dubi humaid tace ”barka mijin ta jikin t b juyiwa yai yace ”to waye ta jikin t b ?kallon khadija data had'e rai tayi tace ”to ai naga yan gayu idan mijinsu ya dawo fara'a sukeyi kekuwa kin wani had'e rai kamar dillaliya anzo cin bahi lolz ,wani mugun kallo khadija ta jefeta dashi shikuma humaid na kallonta baice komai ba ya *LADIDIN KAUYE*


funny & love story

47_48

Ganin abin zuba sharar gidan ya cika mai zuwa kwashewa bai zoba yasata d'auka ta nufi wani guri tafiya takeyi tana dube dube a uban kwandon zuba shara a kanta ,hango wani k'aton kare tayi yana shirin dosota jikinshi duk gashi cikin tsoro tafara gudu aikuwa kare yadinga binta duk inda ta shiga saiya bita gudu takeyi da kwandon shara a kanta ,tama manta layin dazata dosa gashi gidajen duk kusan kala d'aya wani mutumi ta hango yana gyra parking din motarshi k'arawa tayi da gudu tace ”dan Allah ka temakeni karya halakani ,mutumin ne ya kalli karen yace ”mai tayi ma kake binta ?itako Sahura ganin yana neman raina mata hankali tace ”shi mutumne dazaka tsaya tuhumarshi ko kaima mugune irin karen ,mutumin ne ya rike baki tana salati cewa karen yayi duk inda tashiga kabita karka raga mata."



Aikuwa kare yafara bin Sahura gudu take ci babu mai temakon ta ,humaid ne tafe a cikin mota hango ta yai tana gudu ashe harta zo anguwar takuma juyawa yanzukuma ta dawo duk bata sani ba ,fitowa yai daga cikin motar yana cewa keee!!da k'arfi ziwa tayi ta cakumeshi tana ihu ,karen humaid yabawa hak'uri daganan yace ”to ga gidan nan amma ina zaki da kwandon shara cewa tayi naje zubar muku da shara shine kare ya biyoni wata shu'umar dariya humaid yasa yace to jeki gida maganin mai yawo kenan ,murgud'a mai baki tayi ta shige ciki , tana shiga tafara cewa Ladidi ki fito yau nakusa mutuwa ,da sauri Khadija ta fito tana cemata na k'arshe karki sake cemin ladidi ,to natuba dan kunga ku yan gayu ne shine kikeso kisa a maidani gida to ta Allah ba takiba ta shige d'akin da yake mazaunin nata."



Washe gari salamar momy ce ta karad'e harabar gidan da gudu khadija ta fice tana oyoyo momy a tare suka shigo parlor rik'e da hannun juna ,Sahura na zaune tana kallo tace ”hajiya barka da zuwa momy ce tace ”yww daughter yar aiki kika samu ne ¿khadija ce tasa dariya tace ”tare sukazo da inna hauwa ,oh momy tace ”na tuna ai ta fad'a min amma bbu wani matsala kho eh momy komai normal , nan momy ta jata zuwa bedroom d'inta tanata bugar cikinta 'akan ko tana cikin wata damuwa ,juyin duniya khadija tak'i fad'awa momy komai,momy ce ta fiddo da wani turare tace ”yau d'inan 'nakeso kiyi using dashi ,to Khadija tace ba tare data musa ba ,nasihoyi momy tayi mata akan ladabi dakuma hak'urin zaman aure,momy ce ta d'au jakarta tana shirin tafiya narai _narai Khadija tayi da fuska zatayi kuka momy tace ”nazo kuma dan inganki inji dad'i shine zakiyi kuka kull kiyi hak'uri zaman aure ba wasa ba ,raka momy tayi har gurin motar da tazo sukayi sallama ,magrib nayi tayi wanka tasa riga da wando rigar dai _dai cinya wandon kuma dai _dai gwuaiwar k'afarta ,turaren da momy ta bata ta fito dashi shafawa tayi a fuska tana mai jin k'amshin yayi mata dad'i ,,jin sallamar Humaid yasata fitowa a kunyace tace ”barka da dawowa yaya uhm barka yace yana k'are mata kallo ,wani lamari yakeji mai wuyar fasarawa sabda inya kalli fuskarta ,cewa yai kaimin bag d'innan ciki ohk tace ”ta wuce taje kaiwa ,tana shirin fitowa taga an kashe light d'in d'akin anbar kadan zaro ido tayi lokaci guda kuma tsoro ya baiyana a fuskarta ,cikin zuciyar shi yana cewa da nace sai lokacin da kika amince to yau na soke wlhi ,nufota yakeyi tana ja da baya ,a haka har tasamu tayi d'akinta da gudu ,6acin rai ne ya dirarwa Humaid sabda yafara wani tunani daban akan Khadija yafara zarginta sosai sabda had'in kan datak'i bashi tana nufin Allah bazai kamata da laifi ba kenan?takoma kamar jahila wacce batayi karatun islama ba ,yau dai 6acin rai yasa Humaid maganganu marasa kan gado juyi yakeyi yana tunanin anya wani bai rigashi ba hmm ."


Yaune Sahura zata koma gida sai kuka takeci kamar an aikota wai zatayi kewar burodi da shayi ga kayan dad'i harda bubuga k'afa ,a haka suka had'a mata goma ta arziki akwati sabo Humaid ya siya mata hardasu atamfofi driver akasa ya kaita.


Khadija batada wal walah kwata ²komai cikin sanyin jiki takeyi gashi ta koma very silent abin haushi ma dariya tsada takeyi mata ,washe gari da safe kira ya shigo wa Humaid cewar wanan doctorn yanason suyi wani aiki tare urgent yaje ya sanar dasu momy fatan alkairi sukayimai sanan sukace to matarka fa ?"sosa kai Humaid yai yace ”tace batason yawo lolz tunkafin ka tambaya hh,a tunanin su momy cikine da ita dan yau bikinsu 1 month kenan ,ficewa yai sunata sanya mai albarka komawa gidansa yai yasami gimbiyar na goge TV k'arasawa yai ya rungumeta yana cewa lovely munsami cigaba fa kitayani murna ,murmishinta tayi mai tsada tace ”Allah ya tabbatar da alkairi ,wanan adu'ar tasa yaji dad'i sosai ,yace to kishirya muje tare a'a tace ”a tak'aice shiru yai bai sake magana ba ,yanason cewa ki shiryamin kayana a jaka yakasa ,hakadai ya shirya da sauri sauri ,Jalal ya kira akan yazo ya kaishi airport sai ya dawo da motar ,yayi yayi Khadija ta rakashi koda airport d'inne amma ttak'i."



Haka tayimai Allah ya tsare ,yana tafiya ta fashe da wani matsanancin kuka ,ring d'in wayarta taji mik'ewa tayi ta d'auko wayar ganin number babu suna yasata kallon number, dauka tayi had'e da sallama dagacan 6angaren akace ya kike kwalli lpy Lou Khadija tace ”dan bata gane mai maganar ba Fati ce kokin manta da mukayi school tare oh na tuna yakk hope kina lpy eh ya amarci dariya Khadija tasa tace ”amarci nan sai wanda ya k'aru daganan sukayi sallama ,zaman shirunne ya isheta ta zari hijab ta shiga mak'otan su gidane tangameme kuma tsararre da yafi nasu komai ma nocking takeyi amma shiru , can mai gadi ya bud'e yana kallon Khadija yace ”daga ina ne ?cewa tayi ga gidnmu nan wanan na jikin nakun ,Allah sarki yace dagan an yabata hanya ta shige ,da isaera k'ofar parlorn wata k'ofa ce ta glass tana haske kala kala sallama tayi jitayi an amsa ,matar dai batasan Khadija ba amma dayake batada girman kai yasa tace toshigo mana sister."



Shiga tayi matar da a shekaru zatayi 27 tace ”saidai ban ganeki ba wlhi tana murmishi ,Khadija ce tace ”ga gidanmu nan jikin naku ,oh ko kece amryar da aka kawo kwanaki 8 months da suka wuce ,jinjina maganar Khadija tayi tace ”wata takwas kina nufin Humaid yayi aure kenan ?matar ce ta dubi Khadija tace ”oh su6utar baki please karki tada hankalinki ita wacan ba zaman aure ya kawo ta ba ,kinga ni sunan na Rahma yarana biyu kin gansu nan a photo yarane kyawawa masu kamada uwarsu sunsha kyau sosai Khadija ce ta dubi Rahma tace ”ni kuma sunana Khadija danan hira ta 6arke kamar sun dad'e da sanin juna horn sukaji Rhma ce ta mik'e tana lek'awa ta window ,oh kinga sweety ya dawo please ina zuwa , Khadija ce ta mik'e window da Rahma ta lek'a nanta fara lek'awa wani kya kyawan magidanci ta gani fari sol kamar bature ,hango Rahma tayi ta bud'e masa mota ta kar6i jakar ta rataya ta kuma ruk'o masa hannu shikuma ya rungumota suna tafiya suna dariya ,Khadija ce tace ”danasan iskancin da zan gani kenan da banzo gidannan ba wlhi ni nazo domin d'ebe kewa amma naga abinda yafi k'arfina nifa bazan iya k'arewa a yiwa namiji bauta ba hmm ,ita kad'ai taketa maganarta ,can kuma taji gabanta na fad'uwa sosai ,yarinya tagani wacce zatayi shakara hud'u a duniya tace ”jeki cewa momynki bakuwar ta tafi ,da gudu ta shige tana cewa momy bakuwa zata wuce ,OK kice ganinan Rahma ce tace ”sweety zani yiwa bakuwata sai gobe ,janyota yai yace ”daga ina tazo a mak'otanmu take ,Rahma ta fice tana dariya ,samun Khadija tayi a bakin get a tsaye ,Khadija ce tace ”to aunty Rahma sai wani lokaci godiya Rahma tayi mata ,Khadija ta fice.shige ciki....✍️.*LADIDIN KAUYE*



funny & love story



49_50


Jin fad'uwar gaban ya tsananta sosai yasata k'ara saurin tafiyar ta ,tana dosowa bakin get abinda taganine yasata kurma uban ihu ta fad'i sumammiya .


Sahura ce zaune tana cin tuwo tana turo baki ,inna Hauwa ce tace ”nifa banasan kinibibi garama abincin gidanmu naku da ko kafi zabo babu ,kuka Sahura ta fashe dashi tace ”ni walahi sonakeyi in koma jos gurin Ladidi ,zaro ido inna tayi tace ”to ga hanya nan kitafi k'wad'ayayya sunmayi namijin k'ok'ari da har kikayi musu sati biyu batare da sun koroki ba ,wani kallo tayiwa inna harda murgud'a baki tace ”to dan kiji ma yasin ni bazanyi aure a nanba saboda talauci yayi muku kanta ,salati inna keta jerowa ita ko sahura surutunta take jerowa ,jin salamar yaro yana tallar alele hhh fans means allale ,tace ” kai d'an hanse kawo dan uwarka ,inna ce tace ”walhi ki kiyayi zagi saikace baki zuwa islamiya ,mugud'a inna baki tayi hakan yabawa inna damar yin shiru ,Sahura ce tace ”wa yaron biyar biyar ko¿" a'a yaron yace wake ya k'ara tsada goma goma ne , cewa tayi to sako na wazobiya inna mik'omin kwanon kusa dake ,mik'o mata inna tayi duban yaron tayi tace ”kasamin manja da yaji sosai ,bayan yasa ne tace ”inna bismillah kawo kwanonki ,inna da bata wuce tayi ta mik'a kwano aka samata guda d'aya ,Sahura ce taga yaronna kallonta cewa tayi d'an hanse zakaci alelen ne eh yace aikuwa tace to ci d'aya da rabi ninikuma inci biyu inna ga wanan rabin ki kara ,inna na rawar jiki ta kar6i alale tanaci tana lashe rroba."




Saida suka gama ci yaron yace ”Sahura bani kud'in ?" cewa tayi kai na nawa kaci ?" yace ”to ai kece kika bani kyauta ,juyawa tayi gurin inna tace inna kinci na sha biyar ko ? eh inna tace tana zaro ido to talatin kenan ungo murtala sauran kuma sai kubiya ,yaronne yafara kuka yana ihu ,shigowar malam Adamu yasa Sahura zamewa ba tare da kowa ya ankare ba ."


6angaren su Jalal kuwa soyayya suke zubawa wacce babu algus kowa bayason yaji 6acin ran d'an uwansa shiri takeyi zatace hospital gaishe da Khadija da ake yimata k'arin ruwa Jalal ne yace ”Honey inkin gama kizo mutafi ,shagwa6e fuska tayi tace ”anya babyn ma zaibari na fita kuwa ,k'arasowa Jalal yai dai _dai saitin cikin nata da zaiyi wata hudu ya kasa kunenshi yana dariya ,girgiza kai yayi yace ”to baby's sunce ko America zaki saikin dawo ,dukan wasa ta kaimai tana cewa tabb barinzodai mu tafi dan naji ance jikinata yayi tsanani ."


Emergency room aka kwantar da ita saboda lokacin da ta yanke jiki ta fad'i Allah yasa da mutane a gefe ,kwance take ansa mata oxygen wato abin nunfashi ,nunfashinta baya fita sosai kowa ya cire rai da khadija momy kuwa sarkin kuka kullum cikinsa take tanacewa kukuma jarabawarku kenan wayo rayuwa, Saudat ce tayi sallama ita da Jalal amsawa su momy sukayi itada k'anwarta durk'usawa har kasa sukayi suka gaidasu momy dagan an ya ajiye food folks a gefe yace "ya jikin Khadijan da sauki momy tace ”had'a baki sukayi gurin cewa Allah yabata lafiya amen momy tace ”bayan Jalal ya zauna ne yace ”momy number ya Humaid bata shiga yau 3 days kenan ina gwadawa amma a kashe ,momy ce ta share hawayen da suka zubo mata tace ”shima dajin wanan lamarin da yafaru a gidannasu ya kwanta rashin lpy dan naji ance jikin ya tsananta sosai ,Jalal ne ya tausayawa yayan nashi yace ” momy insha Allah jibi zantafi dubo shi to Allah ya kaimu tace ”daganan shiru ya biyo baya."


Momy ce ta shiga room d'inda aka kwantar da Khadija samunta tayi ido a kakkafe tana kuka momy tsabar firgici tayi gurin doctor tana kuka ,da sauri doctor Umar ya shigo yafara gawaje gwaje ,cikin sa'a nunfashin ta ya dawo normal can tafara bud'e ido ruk'o hanunta momy tayi tace ”alhamdulilh daughter Allah yakara miki lafiya ,Khadija babu bakin magana sai kalle kalle takeyi..


Tabarmai nagani da mutane a k'ofar gidansu dady kowa kaganin fuskarsa bbu dad'i zaman makoki akeyi dakuma adu'oi , dady ne keta kar6ar gaisuwa gurin jama'a suna yimasa ya karin hakuri ,washe gari jikin Khadija yayi kyau sosai dan har tana cin abinci sosai ,sallama
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment