Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

zata fad'a ciki se zaro ido takeyi kamar an tare kwarto.

Yau watan Ladidi daya a yaune dady ,ya samowa Ladidi makarantar primary a class 5 aka sata kasancewar sunje anyi mata interview tanada basira bazatayi wuyar d'aukar karatu ba "tunda tafara zuwa makarantar bata shiga sabgar kowa ,wata rana suna zaune a class teacher yashigo yace a fad'a mai masu ,surutu kowa a class d'in Ladidi yanuna kasancewar tunda tashigo school d'in ba,a ta6a kawo k'ararta ba ai kuwa malamin ya kamata yayimata duka sosai seda yafasa mata farcen baban dan yatsa" kuma tasha alwashi seta rama tunda yanaso tadawo Ladidin k'auye .


K'arfe hud'u na yamma dady ,yakirawo Humaid yana gurin aiki akan yaje ya d'auko Ladidi a school ranshi ba k'aramin 6aci yayi ba amma babu inda ya iya dole ya ajiye abinda yakeyi yaje d'aukarta babu kowa a school d'in kowa yatafi gida se teachers dasuke office suna ta ttaunawa tana hango motar Humaid gabata yashiga bugawa shigewa baya tayi seda yatada motar ya daka mata tsawa yace ubanwaye drivernki fitowa tayi saboda yunwa takeji dukda anbata kudin break amma ,a banza.

Tun kafin takoma gida take ciwon ciki sosai tarasa inda zatasa rayuwarta Humaid ,da yalura da halin da take ciki seya rud'e ko magana bata iya yi hospital d'inshi ya wuce da ita wani d'aki ya kaita da babu kowa aciki se karar Ac daketa bada iska yaje siyo mata abincin turo k'ofa yayi yaga jini yana zuba zaro,ido yayi yadubi Ladidi da ko motsi batayi seda ya,yayyafa mata ruwa kana ya murd'e bakin ,nata ko kulashi batayi ba dan ita kad'ai tasan wahalar da takesha alura yayi mata daganan yafice d'auko mata magani wayarshi ce take ringing dady yagani d'agawa yayi dadyne yace ina Ladidi Humaid cikin jin nauyin maganar da zegayawa dady yace gatanan a hospital zaro ido dady ,yayi kana yace meke faruwa da ita Humaid ne yakasa yiwa dady bayani yace am dady in momy na kusa please kabata wayar dady ne yahau banbamin fad'a kana yace ubanme kayi mata dabazaka fad'amin ba itako Ladidi hatta jinin da yazuba a jikinta duk bata sani ba tunda tana farfad'owa daga suman datayi yayi mata allurar bacci .

Dadyne rai a 6ace yamik'awa momy Humaid ne yace momy zakizo hospital d'innne¿" eh momy tace gamunan nida dadynka"hijab momy ta d'auko zuka nufi hospital d'in Humaid itada dady da isarsu direct office d'inshi suka wuce dady ne ya nannad'e malun malun din'shi yace to gamu maunzo nace uban me kayiwa yar mutane momy ce ,tace katsaya a tambayeshi mana kanata fad'a Humaid dai yakasa magana dan yana ganin kamar inya cewa iyayenshi Ladidi tafara period zasuce bashida kunya" sunkuyar da kai k'asa yayi kana yace 6atan wata tafara kuma yau d'inan momy ce tadubi Humaid tace to wanan shine abin 6oyewa dady ne yanemi guri ya zauna yace to yanzu tana ina Humaid ne ya mik'e yace kuzo muje d'akin "suna zuwa suka samu haryanzu tana bacci momy ce takalli fuskarta hak'ik'a tayi rama sosai Allah sarki.


Momy ce ta ,tambayi Humaid kasiyo mata pad kuwa eh yace kana yabawa momy ledar harda sababin pants yasiyo mata dady bece komai ba yana tsaye yazuba hannu cikin aljihu.

Farkawa tayi taga su momy a kanta tuno ciwon cikin datayi ne a mota sekuma taga jini a zaninta zaro ido tayi tafara kuka dady ne suka fice shida Humaid momy ta k'arasa gurinta tayi mata bayani dakuma inda zatayi ta gyara kanta momy tayi mata fad'an sallah akan lokaci " bayan ta gama shiryawa ne momy takira Humaid a waya tace yasiyowa ladidi riga ko doguwa ce "be jima ba segashi da rigar "dayake basuda nisa da masu saida kayayyaki".

Ruwan zafi yasa akawomata bayan tafito daga wankan ta kintsa kanta suka nufi gida momy a motar dady suka tafi shikuma Humaid da Ladidi suka tafi tunda suka fara tafiya talura da kallon da humaid yake yimata amma seta basar".



*BAYAN SHEKARA DAYA*

Ladidi na hango takuma kyau tayi haske tayi k'iba sosai gashi tafara jin turanci kuma tadena wauta irinta yan k'auye " samarine da ita sunkai biyar amma Humaid na ganinsu seyace anyi mata miji "itadai Ladidi batasan hujjar yin hakanba " tagama primary yanzu tana jss 2 komai nata yak'ara baiyana ".

Batada abokin shawara inba jalal ba duk wata damuwa tata yasani basa shiri da jalal " wata rana tana cikin tafiya zataje gidan wata k'awarta ta had'u da wani saurayi kya kyawa yana cikin mota ita kuma tana tafiya a k'afa"baya yayi da motarshi yace ya ,yammata ina magana kink'i kulani cigaba tayi da tafiya jitayi ya rik'o hannunta a zabure ta juye dan tunda take babu namijin da yata6a gigin rik'e koda gefen mayafinta ne........✍️✍️✍



✍️Mom Islam ce

*LADIDIN K'AUYE*


Funny & love story.

*Labari mai ban dariya had'i da fad'a karwa*



*NA*

*MOM ISLAM*
*ZAINAB HABIB*


*MARUBUCIYAR:*

*ZAINABU ABU*



*AND NOW*

*LADIDIN K'AUYE*



*BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM*


*Episode:* 13_14

___durk'usawa yayi a gabanta yace please beautiful ki saurareni wlh tunda naganki naji nasami matar aure ko banyi miki bane Ladidi ce ta yamutsa fuska kana tace bancema haka ba"mik'ewa yayi yace sunanan Amar jitayi sunan yayi mata d'adi sosai Ladidi ce ta fad'amai asalin sunanta wato khadija wow Amar yace daganan yace kozan iya d'aukar ki a mota ,ta eh tace babu damuwa daganan ya maidata gida sunyi musayar number tashige gida mom ce take tambayarta daga ina take cewa tayi daga gidansu yar ajinmu ne naje dubota babu lpy momy ce ,tace to kiyi sallah kici abinci semu shiga kitchen ".

Bayan tayi sallah taci abinci ta d'auko wayarta tana duba massage number Amar tagani ya rubuto mata sak'on" kin budewa tayi saboda batason seta fara karantawa momy ta kirata kuma taga sak'on da yawa tana shirin tashi tajiyo kiran momy amsawa tayi ta jona wayar tata a charge ta,tafi kiran direct kitchen tawuce tasami momy tana had'a kayan buk'ata na girki saboda yanzu tare sukeyin girki ummi tayi aure kuma bata nemi yar, aiki ba".

Bayan sun gama girkin ta nufi d'akinta ta gyara dan sam batason k'azanta shiyasa komai nata tsaf ,tsaf bayan sallahr isha,I tana shirin karanta massage d'in Ammar sega kiranshi nan yashigo muryarshi me sanyi ce tadaki dodon kunnenta kirari yafara yimata yana wasata godiya tayi mai daganan suka gaisa "rungume fillow yayi ,yace kinsan me khadija ¿a,a tace yaci gaba dacewa wlh jinakeyi ,inama kena rungume ba fillow ba murmushi tayi kana tace to mekakeci naba na zuba ".


Dambu yace suka suka sa dariya" tambayarta yayi kinayin whtsapp ne ¿"a,a tace mai Amar ne yace to meyasa¿Ladidi ce ,tace ra,ayina ne hakan shiru yayi kana yace inason zuwa hira yaushe kikeso inzo shiru tayi nad'an wani lokaci kana tace zanyi shawara"Amar ,ranshi ya 6aci amma be nuna mata ba sukayi sallama "bacci ya gagara d'aukar shi se tunanin Khadija yakeyi wato Ladidi yarasa wane irin so yake yimata sona sha,awa ne kokuma so na zuciya se juyi yakeyi "jiyayi mararshi tashiga ciwo yarasa ina zesa kansa yaji dad'i wata babyn shi yakirawo da sukeyin masha,arsu ".


*WAYE AMAR*
Amar d'a ne ga Alhaji atiku dollars yataso cikin gata da kulawa sam bashida tarbiyar kuma baya tare da iyayenshi a London suke da zama tun mahaifan Alhaji Atiku suna London har aka haifi Alhaji Atiku shikad''ai Allah yabasu shiyasa basa,son lefin Alhajin shiyasa gatan da iyayen Alhaji Atiku suka bashi,shi yabawa d'anshi a ganinshi ,shine birgewa" Amar yaza6i yayi karatu a Nigeria shiyasa yabar iyayenshi yazo Nigeria yana karatu bashida kowa a Nigeria shiyasa yake abinda yaga dama y'an matanshi sunfi a k'irga "yanzu gashi Allah ya had'ashi da Ladidi kuma indai yaso abu to seya mallakeshi yake samun nutsuwa" gashi Allah yad'ora mai yawan sha,awa baya sati beyi sex da mata ba' gashi kya kyawa "wanan kenan.


Washe gari bayan Amar yaji sauk'i yakira Ladidi a waya ringin d'aya ta d'aga wayar jin muryarshi tayi wata " iri"cewa tayi lpy Amar najika haka¿lpy yace mata ya nisa,yace beauty kin hanani barci"zaro ido Ladidi tayi 'kamar yana ganinta".

Tace nikuma "eh yace kinsani wanka zeci gaba tace momy na kira na bari,inje in dawo katse wayar tayi'ta dafe k'irjinta tunda take Allah beta,6a had'ata da mara kunyar saurayi kamar Amar ba".

Yau kwanansu hud'u da had'uwa ,yaune Amar yakira Ladidi a waya ,yake gaya mata, bashi,da lpy " hankalin,ta yayi mutuk'ar tashi tarasa yanda zatayi ta fad'awa momy saboda tanason zuwa gaishe,shi".ganin shiru,shiru "bata zoba yasa,shi neman number ta" wayar nata ringin amma tak'i d'agawa saboda yau Humaid na gida shikuma Jalal yatafi gurin sana,arsa.


Ranshi ya 6aci sosai"amma ya,d'au alwashin,shirin dayakeyi a kanta , momy ce ta,k'awala mata, kira amsawa tayi "da,sauri ta'amsa' bayan ta gyara fuskar,ta " tana ganin kamar momy zata gano damuwa shimfid'e a fuskar ta,da sallama tashigo palon momy,samun guri tayi ta zauna"kana tace momy gani .

Momy ce ta dubeta ,tace khadija meyasa bakyason fad'amin damuwar,ki "murmushin yak'e tayi kana tace momy wlh bani'da wata damuwa kawai tunanin karatu nakeyi" momy badan ta yarda'ba tace to shikenan kinci abinci kuwa eh tace suna cikin magana tajiyo wayar momy na ruri"tashi tayi taje ta'd'aukowa momy wayar,ta momy ce tace waye yake kira¿"Humaid ne Ladidi taba momy amsa to ki d'aga mana jiki na rawa ta d'aga wayar da sallama jin muryar mai maganar yasa'shi daka mata tsawa ,cewa yayi ubanwa yabaki ,ikon d'aga waya momy na "nakira ba keba rau'rau tayi da idanu momy taga yanayin'ta amma bata ce komai ba yak'ara da kicewa Ummi ta,kawomin abinci to 'tace ta ajiye wayar momy ce tadubi ladidi tace meya,ce miki ¿"Ladidi ce tace wai Ummi ta kaimai abinci momy ce tayi murmushi kana tace to meyasa baki cemai Ummi takoma garin su Ladidi da idan ta yakawo k'awllah tace bakomai momy barin je in kaimai ,momy ce tayi'mata Allah ya shi albarka Ladidi tanajin dad'in wanan kalmar sosai shiyasa takeson momy bata'son 6acin ran'ta .


Kitchen ta wuce tazubo mai abincin ta had'o da juice me sanyi ta nufi hanyar da zata sadata da ,d'akinsu Humaid kasancewar da nisa a tsakanin'su da isar'ta " tayi nocking batayi magana ba" k'ara buga k'ofar tayi Humaid ne yace ubanwaye'yake damuna "shiru tayi bata'ce komai tura k'ofar tayi da sallama tashiga d'akin ganin halin da,yake ciki'ne ya sata sake kular abincin da kofin da'ta d'auko juice d'in zata gudu ya kamo ta ya k'ulle k'ofar.


Munafuka waya baki,izinin shigo'min d'aki " tayi mamakin sosai amma tasan ba acikin hayya'cinsa yaje ba "kwalbar giya ce 'a gaban shi se kwalin taba ya birki'ta d'akin " Ladidi ce takuma rugawa da ,gudu k'ofar d'akin tanufa"amma ina taji a kulle duban ta "takai ga Humaid da idanuwan shi sukayi ja kamar gauta tace please brother kabud'e,min k'ofa wlh nomy zata neme,ni shiru yayi yakuma duban 'ta mik'ewa yayi jiki na rawa yace baby kinzo a lokacin da nakeda buk'atar ki Ladidi ce ta mai'maita sunan da yakira ta wai baby tafiya yakeyi yana layi alamun yasha ya bugu ya matso kusada ita sunajin 'numfashin juna matsawa tadingayi shikuma yana binta kamar k'aramin yaro saida ya kaita bango tukun ya rungume'ta runtse idanun tayi wasu hawaye masu zafi na zubo mata jin alamun tudun breast d'inta yasa,shi rud'ewa " je'fata kan makeken gadon,shi yayi yafara had'e fuskar su guri d'aya"Ladidi kuka takeyi kamar,ranta ze fita tuno nasihar Yadikon,ta "tayi tashiga ture Humaid daga jikinta amma ko turuwa bayayi dake ingar'man ,namiji ne k'arfin ta ,ta had'a da cizo ta yak'ushi ta tureshi tana mikewa ta hango key, tabud'e k'ofar zata fice ya kamo'ta baya tayi da k'afarta ,ta tokare,shi ya fad'i a bakin k'ofar " ta fito da hawaye sha6e,sha6e a fuskar ta duk wanda yaganta yasan tana cikin damuwa Allah yatema keta tunda ta fito daga part d'in Humaid babu wanda ya ganta .


{K'ALU BALE GAREKU Y'AN MATA BA WAYON'KIBA BA DABARAR,KIBA ADU,A ITACE TAKI ALLAH YABAKU MIJI NAGARI DUK MACEN DA TABI DUNIYA TO TABBAS DANA SANI SHINE KARATUNTA ,KAR SOYAYYA TA RUFE MUKU IDO KUCE AI ZE AUREKI INA WLH BA AURANKI ZEYI BA .}..✍️✍️✍️



Mom Islam ce ✍️✍️


*LADIDIN K'AUYE*


Funny & love story.

*Labari mai ban dariya had'i da fad'a karwa*



*NA*

*MOM ISLAM*
*ZAINAB HABIB*


*MARUBUCIYAR:*

*ZAINABU ABU*



*AND NOW*

*LADIDIN K'AUYE*



*BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM*


*Episode:* 15_16

_____gado tafad'a taci gaba da rera kukanta a yanzu ko san taga Humaid batayi "misalin k'arfe shida na yamma tafito zuwa ,kitchen tasamu momy tagama komai sedai jera abinci a dining, temaka mata Ladidi tayi suka k'arasa.

"Washe gari ammar yakirata a waya, yake gaya mata tazo tarakashi gidan su k'anwar momyn'shi " cewa tayi zatazo amma seta tambayi momyn ta ,cikin farinciki ammar ya sa aka ,gyara gidanshi aka feshe gidan da turaruka masu tsada.

Washe gari Ladidi takira Ammar a waya tacemai yazo ,misalin k'arfe sha biyu na rana yazo ya d'auketa ,jin haka ya buga tsalle yana murna" suna cikin haka ne yake tambayar ta ,wane colorn abinci tafiso?dariya tayi kana tace indomie "cikin jin dad'i yace to karki damu drinks fa ?kowanne tace ,sukayi sallama .

Washe gari misalin k'arfe sha d'aya na rana Ladidi tagama komai tasami momy take gaya mata zataje gurin wankin kai " momy ce tace kije ki tambayo dadynki tunda yana gida.

Da sallama tashiga parlour n dady ,samunshi tayi yana waya bayan yagama ne ta gaishe'shi cikin ladabi ya amsa "sekuma ta sunkuyar da kanta k'asa dady ne yace Khadija meyafaru?cikin jin nauyi tace dama inason zuwa gurin kitso ne" dady ne yace to gashi su Humaid basanan ,amma kisa driver ya kaiki" to tacewa kana tamik'e zata fita.
Kiranta yayi ,yabata kud'i ,godiya tayimai ta fice ."

Zuwa tayi parlourn momy tagaya mata dady 'ya barta kuma yabata kud'in kitson"nasiha momy tayi mata daganan ta d'auko hijab d'inta ta fice, taje tayiwa driver magana tafad'a mai 'inda ze kaita "

Bayan sunje suna hanyar dawowa suka ,hango motoci bak'ak'e sun zagaye su ,babu hanyar da zasu ,wuce "

Bude murfin motar tayi ,
baba driver ne yace"wallahi Khadija karki fita, Ladidi 'da hankalin ta ya tashi tace karka damu yanzu zan dawo ficewa tayi a motar, ta nufi gurin masu bak'ak'en motocin'nan bata hango kowaba acikin motar ,zata juya ta koma ,tasu motar "taji an janyota an turata mota,baba driver ne ya fito yana salati kafin yakai gurin masu motocin ,tuni suka wuce da gudu ,Baba megadi yara yazeyi ,mezeje ya fad'awa su Alhaji " driving yakeyi amma hankalin shi baya jikin shi ,haka ya iso gidan .
Momy ce dake shirin fita anguwa taji Horn d'in baba driver ,bayan yafito daga motar ne ya durk'usa kana yagaida momy'mom daketa lek'en ta ina Ladidi zata fito "baba driver ne yace hajiya wlh tsau'tsayine yafaru da Khadijan " momy da bata,gane inda yadosa ba tace mekake nufi "koba tare kuka fita da khadija ba ¿" shiru yayi cankuma yace wlhi Allah hajiya muna cikin tafiya mukaga wasu a wata bak'ar mota ,yabata labarin inda akayi har cemata da yayi karta fita.

"Cikin tashin hankali momy ta ,kalli baba driver tace kuma ka iya dawowa saboda ragon azanci baka bisu ba ko"

"Kana ganin kai rayuwar ka tafi ta kowa muhummanci .
Shiru drivern yayi kana yafara da ayi hak'uri hajiya ,momy cikin fushi tace ai wlh zakayi dana sani bari alhaji yadawo .
Waya sani ma koda sa hannunka a tafiyar da 'akayi da ita".

" cikin rud'ani driver yace ,wlhi hajiya babu sa hannun' na momy ce cikin fusata da 6acin rai tace shot up your mouth .

"Tace wlh idan kasake magana senayi report d'inka gurin police "zaro ido driver yayi kana yabar gurin ,momy da hankalin ta yagama tashi tarasa wace kalama zata ,fad'awa dady idan yadawo".


Shigewa part d'inta 'tayi ganin Humaid a ,zaune yasata ware ido tace" wato kai bakaji tashin' hankalin dake faruwa ba"Humaid da hankalin shi yatafi gurin TV a tsorace ya d'auki remote ya ,kashe kallon kana yamaida hankalinshi,gurin momy 'yace momy meke faruwa?"

Momy da idanuwan'ta suka ciko da hawaye ,tashare tadubi Humaid tace "tunda Khadija ta fita wlh ba,a gantaba a tsorace Humaid yace" bangane ba momy .
Momy na kuka tabashi labarin da 'driver yabata, a zabure Humaid ya mik'e ya'yi hanyar fita waje ,momy da keta kiranshi yak'i juyowa bare ya saurareta.

Kai tsaye gurin baba driver yanufa ,tunda baban ya hango shi ya fara salati,saboda dama basa shiri da Humaid ."

Cikin azama Humaid ya ,nufi gurinshi yana zuwa ya cakumo wuyar 'rigar baba driver yace gidan uban wa kakai marainiyar Allah "baba driver daya gama tsorata yace yaro " karka manta shekarata goma ina aiki a gidannan kuma ba,a ta6a samun matsala ba, seyanzu ne zance zan cutar da wani".
Humaid da bayajin ko mai da baba driver yake cewa yadinga ball dashi ,har seda momy tajiyo hayaniyar su tazo tana yiwa Humaid fad'a"

"Hak'uri tabawa drivern,ta ruk'o hannun Humaid suka shige ciki , tana cikin yimai fad'a sega Jalal nan ya k'araso ,ganin fuskar momy da Humaid babu fara'a yasashi k'arasowa da sauri yana momy meys faru " Humaid cikin k'unar zuciya yace Khadija cefa driver ya 6atar da ita "a zabure Jalal ya mik'e yace shine bro ka barshi? "Momy ce tadubi Jalal tabashi labarin da driver yabata Jalal yace wlh k'arya yakeyi" momy cikin d'aga murya tace zan sa6a muku "kubari dadynku yadawo ."


"Da daddare dady 'yashigo da fara,arsa ,rungumo momy ,yayi seyaga tak'i yin dariya alhalin ba haka tasaba yimai ba" duba fuskarta yayi kana yace hajiya meke faruwa naga kin sauya cikin tashin hankali da muryar da taci kuka ,tace Khadija .
Dady ne yace meyafaru da Khadijan¿ momy tace barin kirayo maka driver "mik'ewa tayi ,dady ganin momy tayi waje yasa'shi mik'ewa tare suka fita .

Tunda suka isa parking space d'in momy take ta k'awalawa driver kira ".
A hanzarce ya fito cikin ladabi ya gaida dady ' dady ne yace meyafaru ne da Khadija ?"
Cikin fad'uwar gaba driver yabawa dady labarin abinda yafaru dasu .
Kid'imewa dady 'yayi yahau fad'a ,yana cewa wlh baku kyauta minba meyasa ba'a kirani a wayaba "momy da kuka ya ku6uce mata ,takasa magana ,dady ne ya d'auki motarshi ya nufi police station yayi musu bayani ".

Tare dakawo photon Ladidin dakuma kalar kayan da tasa .

Bayan su momy sun dawo gida,suna zaune da safe ,suna kallo a TV sukaji ana cigiyr Ladidi momy jitayi hawaye sun zubo mata,dady kuwa hak'uri yake bata amma shima yanajin cikin zuciyarshi babu dad'i".

Tunda Ladidi ta 6ata momy tadena jin dad'in aiki sosai ,seda tasa aka d'auko mata yar aiki .


*WAYE YA SACE LADIDI*

Tunda suka sata a mota suka rufe mata fuska da bak'in wani abu, ihu takeyi 'iya k'arfinta amma babu wanda ya kulata, jitayi an d'auketa ana tafiya da ita ,daganan taji an sauketa an zaunar da ita an wurgo mata Jakarta .
Takai minti talatin a haka can kuma taji an bude mata ido,ganin ta a wani k'ayataccen parlor yasata sakin kuka tana, kiran momy " Ammar ne yafito d'auke da plate na abinci a wani farin trai me adon flowers masu kyau.
Ajiye mata yayi a gabanta ,nunashi tashiga yi da 'dasha shiyar muryar ta 'tace Ammar wanan ce soyayya ? ta k'ara dacewa wlh ka cuci kanka kuma tayarwa da iyayena hankali da kayi se Allah, yayimin sakayya .✍️✍️✍️


Mom Islam ce✍️✍️✍️

*LADIDIN K'AUYE*


Funny & love story.

*Labari mai ban dariya had'i da fad'a karwa*



*NA*

*MOM ISLAM*
*ZAINAB HABIB*


*MARUBUCIYAR:*

*ZAINABU ABU*



*AND NOW*

*LADIDIN K'AUYE*



*BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM*


*Episode:* 17_18

_____Dariya ma tabashi ,seda yayi mai 'isarshi kana yace "kin mance da masoyinki ko ?kin kulashi tayi,sekuma taji hawaye na zubo mata .
Ammar ne yaturo mata abincin kana yace kici abinci " dama kince kinfison indomie ,kuma ita na dafa miki .
Kici kiji girkin Ammar d'inki "cikin masifa tace tirr !da hali 'irin 'naka ,tuno halinta na da lokacin da take k'auye tayi ,shirin mugunta take yimai .

" Tace to yanzu ka maidani gida" wani 'irin kallo yayi mata, ina wanan brother naki mara mutunci "cikin fusata tace bangane ba ¿" dariya yayi mata irin 'na y'an duniya yace manta.
Jiyo k'arar wayarta tayi dake hand bag d'inta ,zata d'auka Ammar ya kwace wayar ,cikin masifa tace wlh koka bani wayata kokuma kayi nadama"yayi receive din kiran kenan , zeyi magana da alamu han,kalinshi na kan wayar yana shirya iskancin daze fad'a musu .
Ficewa yayi a parlor yana tunanin ai bazata fice ba".

Bud'e k'ofar tayi a hankali tayi waje babu hijab a jikinta babu takalmi, lek'awa tayi taga babu megadi ,ta bud'e k'ofar da gudu ta ruga tanata gudu ,tarasa inda zata nufa .
A wata anguwa mesuna rikos ta tsaya tana jiran mutane ,hango wani yaro tayi ze shiga wani gida."


Azama tayi ta isa gurin yaron kana tafara tambayar shi ,dan Allah yaro daga nan zuwa 6ukur park G.R.A dan Allah nawa ne ? yaron yace" masu napep zasu kaiki a d'ari biyu ,godiya tayi mai tacigaba da tafiya.
Tana cikin tafiya ne ta hango wani me adai,daita yace hajiya ina zuwa "anguwar ta fad'amai, yace " tashiga su tafi ."


Sunyi tafiya me nisa sanan suka iso anguwar ,a lokacinne tafara gane anguwar tasu,nuni tayi mai da ga'gidan can "barinje in kar6o maka kud'inka ."

Me napep ne yashiga yimata masifa yana cewa dama kinsan bakida kud'i kika shiga to wlh inan a nan kishiga ki fito ".
Tana shiga taci karo da Jalal ,yana ganinta yahau tuhumarta" Ladidi cikin jin tsoron abinda ze biyo baya tace dan Allah brother dari biyu zaka bani 'inbawa me napep "Jalal ne yace gashi mik'a mai ".
Fita tayi tabashi ya tafi,tadawo cikin gidan.
Bata sami Jalal din waje ba ,tashige cikin gidan ,tana shiga tayi sallama ta hango momy da Humaid da Jalal da ,dady saboda baije aiki ba.
Tunda dady'ya hangota yafara yimata wani kallo tana shigowa ,Humaid ya mik'e ya wanka mata tagwayen maruka har biyu,babu wanda yayi 'yink'urin hanashi .
Cikin 6acin rai Humaid yace gidan ubanwa kikaje" banza mara tunani" Ladidi da tarasa mai zatace tadubi dady da tun shigowar'ta yake kallon ta 'taje har gabanshi tana kuka tace wlh dady ba wani guri naje ba "ya d'aga hannu zekai mata mari momy ta rik'e hannun tace katsaya muji abinda zatace" ai alamun mai gaskiya ya fita da ban .
Dady ne ya saurara,yana jiran mezatace cikin murya mai ban tausayi Ladidi tace wlh dady dama cemaka nayi zani gurin kitso ,to bayan an yimin muna cikin dawowa da driver mukaga wasu ,bak'ak'en motoci sun zagayemu "shine na fita inyi musu magana ,naji anturani cikin mota an rufemin fuskata ,an kawoni wani gida kuma bansan inda jakata take ba " momy ce tadubi Ladidi tace to d'azu da Jalal yakira a wayarki waye ya d'auka? cikin she' shek'ar kuka Ladidi tace lokacin da aka shigo dani cikin wani gidan shine naga babu kowa a gidan ,cankuma naji motsin,fitowar mutum.
Bayan mutumin ya fito shine , naji alamun ana kira a wayata ,ashe wayar na gefena "nazo d'auka naji an kwace wayar" da mutumin yashige ciki nikuma na gudo ".

Dady ne ya jinjina lamarin yace " amma kinsman shine ?atsorace tace wlh dady bansan shiba ,su Jalal da Hunaid 'da suka zuba mata ido suna kallon ta ,momy tace Allah sarki daughter Allah yadad'a tsareki "kowa ya amsa da amin.

Washe gari dady 'yakira nalam Adamu ,suna cikin wayar ne naji dady yace" yaya so, nakeyi muhad'a Khadija da Humaid aure ,cikin farinciki malam Adamu yace" wanan ai abin murna ne, amma naji dad'i sosai .
Dady ne yace"abinda yasa nakawo wanan shawarar saboda muk'ara k'arfafa zumunci ,malam Adamu yace"karfa kadamu ,sukayi sallama.

"Bayan dady 'yakoma gida yasamu momy da maganar ,itama tayi farinciki sosai sedai tana ganin ,anya Humaid baze wulak'anta Khadija ba ? ".

Saurin kawarda tunanin tayi ,dady da yalura momy tunani takeyi yace" tunanin mekuma kikeyi ,fara'ar dole momy ta k'ir' k'iro tace" duk acikin farinciki ne ".

Yau
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment