Join Our WhatsApp Group

A LOKACIN NE Complete Hausa Novel Document by A LOKACIN NE


A LOKACIN NE

Cover Design Copyright and attribute to Marus Graphics

Uploaded by @Taskar

Total Words: 77503



A LOKACIN NE

Reading Time: 6 Hours

Added On: 16, Sep 2023

Author: Zainab Idris Makawa ,

Ebook Compiler : Admin

Author Group : Unknown group

Author Phone : Not Inserted

Book License : Free

Category: Love Novels

File Size: 391.41 kb

File Type: txt

Views: 1049+

Download: 615+

Last download: 7 hours ago

Description/Story: 8/8/19, 10:30 PM - Messages to this chat and calls are now secured with end-to-end encryption. Tap for more info.
9/6/19, 10:31 PM - ~: A LOKACIN NE
1⃣

BISSIMILLAHI RAHAMANIN RAHIM DA SUNAN ALLAH MAI RAHAMA MAIJIN KAI,
ALLAH NAGODE MA DAKA BANI WANAN DAMA NA RUBUTA WANAN LABARIN DA KE DAUKE DA YADDA RAYUWAN ZAMANIN NAN NAMU MATSALOLI DA ILLOLIN DAKE CIKIN WANAN RAYUWAN NA WANAN LOKACIN DA MUKE CIKI ALLAH KA BAMU IKON AMFANI DA FADAKARWAN DA ZAMU TSUNTA A CIKIN WANAN GUNTUN LABARIN,,,

IDDAN BAKI BIYABA DAN GIRMAN ALLAH KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE BADA YARDANA BA,,,,,,

Zaune take saman sallaya a gurin da ta idar da sallah hannun ta ya na dauke da farar tasbaha tana ja a hankali sai dai a zahiri ne hakan a can cikin kasan zuciyar ta tunane fam a ranta tana tunanen ko a halin yanzu ina dan ta Umar ya shiga,
Kadan kadan tana daga kanta tana kallon agogon dake manne a,bangon dakin ta a hankali,
Karfe goma,sha daya na,dare saura agogon ya nuna mata a lokacin hankane ya kara sa hankalin ta, tashi sosai don tana tsoron kada ya shigo mata kamar yadda take zargin ganin shi
Tarasa gane wani haline dan nata yake kokarin jefa kan shi a ciki, ga yawan surutun kishiyoyi dake damun ta a a kullun,
Maimakon ace sun taimaka mata gurin kara bashi tarbiyan da suke ganin baida shi issashe sai kawai suka buge da gulma da kara mugun zance a kan dan nata wanan al,amarin ne ya ke kara sa jefa Maji a cikin tashin hankali, da damuwa a rayuwan ta gashi dai ita a nata fannin bata kasa da nasu yaran ba, gurin daukan su har a cikin zuciyar ta a,tsakani da Allah take masu komai,
Kara daga ido tayi takai duban ta ga agogon bangon dake manne a bangon dakin nata,
Karfe sha biyu saura yan mintina na dare ta gani haka ya kara tayar mata da hankalin ta,
Bata kai karshen tunanen taba taji an turo kofan dakin ta, da karfe inda sabo da hakan tasaba tasan ba mai mata wanan halin sai maigidan su,
Ba sallama sai cewan da yayi a hasale wai ina danki ya tafine ?
Shiru Maji tayi don ta saba da wanan kalman na danki a bakin maigidan nasu,
Kefa nake tambaya yakara fadi daga inda yake tsaye daga kofan daki rike da labulen dakin nata,
A hankali Maji ta dago kanta zuwa kalkon shi tace cikin yar murya siririya ban san ina ya shiga ba ba nima tun dazun nake zaman jiran shigowan shi don yaci abinci,
Wani wawan kallo ya watsa mata daga inda yake tsaye yace ai dama nasan da yardan ki yake wanan mugun rayuwan da take don ke ce kike daure mai gidin yake kara lalace wa ai kowa yasan hakan,
Hmmm kawai tace tare da fadin Allah ya kyauta malam amma ta yaya zan goyawa Sadauki baya ya dinga abinda yake alhalin nasan ba alheri yake koyawaba a rayuwan shi,
Wanan kuma ke kika sani don ke ce da hasara saboda ni ba shi kadai ke gareni ba ai,
Yana fadan haka ya gaura kofan dakin da karfi yafita daga dakin nata rai a bace,
A hankali maji ta sauke ajiyan zuciya, zuciyan ta yai mata wani tauri saboda kalamin da mijin ta ya fada akan dan tilon danta namiji guda da Allah ya bata a gidan sai yan kannen shi mata da ke bayan shi su uku rak Allah ya bata a gidan mijin nata,
Yayin da sauran kishiyoyin ta suke da yara fiye da nata a gidan
Maji itace mace ta uku a gidan malam habu dan kasuwa ne shi, sai uwar gidan su mama hauwa mai yara bakwai a gidan,tana aikin a women center,
Sai mummyn Asiya, wace itace Maji ke biwa, tana da yara biyar a gidan, tana aikin koyarwa sai amaryan su Anty Kubura da ke da yara hudu ita ma aikaciyar jinyace a wani asibitin gwaunati,
Daga cikin su maji ce bata wani aiki kwakwara don ita batai boko mai zurfi ba tana aji hudu secondary malam habu ya auro ta don haka bata da aiki sai yan buga bugan kasuwanci irin na mata da take a gida kawai,,
Da farko malam Habu yana matukar son Maji da kuma tausaya mata don bata da ilimi mai zurfi, sosai,
Amma yanzu matsalar dan ta, Umar ya wanda takewa lakani da sadauki don kasancewar shi sunan shi Umar faruk, kuma a matsayin shi na dan farin ta yasa take kiran shi da haka,
Rayuwan da Umar yake ciki a yanzu yafara kawo matsalar a tsakanin malam habu da matar shi Maji mai suna maimuna,,
Matsalar farko dai daga irin yanayin shigar shi na tufafin shi, don sam baya iya saka irin tufafin diyan hausawa na al,ada a jikin shi,
Sai kuma gashi ya bullo da dabi,ar son wasan kwallo a rayuwan shi don duk abinda yake da zaran time din zuwan shi filin wasan kwallo yayi dole yabar koma maynene zuwa gurin wanan wasan a duk safiya da marance, na kulli yaumin,
Malam habu yayi iya kokarin shi gurin ganin Umar yabar wanan wasan kwallon kafan da yake yawan fita tun yana dan karamishi,
Amma abin ya faskara duka zagi da bakar magana ga mahaifiyan shi bai sa Umar ya daina wanan wasan kwallon kafan ba da yakeyi
Yan uwan Umar duk yan kasuwa ne sai masu aikin gwaunati daga cikin su amma shi ba ruwan shi da shiga harkan kowan su
Iyakar shi yai wanka yafuta gurin abokai sai kuma zuwa wasan ball, da yake a gaban shi,
Maji tai nasihan rana taina dare amma bai sa Umar ya daina wanan halaiyar nashi ba

Fitan malam Habu daga part din Maji suka hade da Umar wanda ke shigowa gidan a lokacin wani wawan kallon da tsana ya watsawa Umar din,
Sannu Baba ina wuni yakai har kasa yana gaida mahaifin nashi a cikin ladabi da biyayya wanan gaisuwan yaran dakin maji ke da wanan tarbiyan a gidan kawai,
Uwaka na ce uwaka tare da kara mika mai dakuwa da hannun shi na dama yace yaron banza yaron wofi kawai mai ladabin shegu,
Da ban wuni ba zaka gan ni haka ina ka shige haka tun safe sai yanzu zaka shigo min gida, kana wani ladabin shegu haka dakai,
Baba bafa ko ina naje ba ina gurin training tun dazu yanzun kuma da zan dawo na tsaya gurin dantani mai shago muna hira a majalisasr su,
Training din uwar ka na ce training din tsiya jeka ai tunda rayuwan da kazaba wa kanka ke nan ni ba ruwana inka samo wahalanka kada ma kace ni Ubankane,
Umar dai yana duke a gurin da yake baidaga ba yana sauraren kalaman mahaufin nashi,
Malam habu ya wuce ciki fuuu yaba ta faman sababi da bambami akan umar din,
Daga kai yayi ya kai kallon shi ga kofan dakin mahaifiyan shi wace yasan daga gurin ta mahaifinshi yake yagama zazzaga mata tsiya ke nan a kan shi don haka yasa tafasa shigan da yai niyar yi gurin ta a lokacin,
Don yasan yanzu tana can ranta a bace akan rashin ganin shi da batayi ba yini guda zur ga kuma baba ya je yanzu ya zazaga mata balain shi da ya saba,,
Yashige part din shi ya fara dan rage kayan jikin shi, daga shi boxe din shi irin ta maza ya rage a jikin shi,
Dukawa yayi kasan gadon shi ya jawo wasu kwalabe cikin wani leda mai karfi daga karkashin gadin inda ya balli wasu kwaya dake cikin ledan ya bude wani kwalban syrup ya hade su tare ya shanye, a lokaci guda, ya fada saman kujeran shi tilo daya dake dakin,
A hankali ya fara zukan syrup din har sai da ya shanye duk ruwan maganin dake cikin kwalban gaba daya, ya wurga kwalban a kasan carpet din dakin,
Nan saman kujeran ya dan fara lumshe idanuwan shi a hankali yana rufe su ko may ya tuna sai kuma ya mike daga inda yake zaune zubur ya dauke kwalban daga inda ya aje su ya mayar gurin da ya dauko su,
Nan yaja jiki zuwa saman kujeran da ya fara zama ya kara zubewa sama da karfi har saida kujerar yai, dan kara don fada mashi da karfi da yayi,
Nan barci ya kwashe shi babu bata lokaci a gurin baifi mintuna ba sai ga Maji wacce ta kasa barci ta shigo dakin ganin ko ya dawo daga yawon da mahaifin shi yace ya tafi,
Maji ta dade tsaye a kan shi tana kare mashi kallo cikin mamaki tayi tayar dashi amma bai tashi ba dole tafita daga dakin tabarshi a hakana,
Zuciyar ta fam da kunci sai kuna dan zargi da ya fara darsuwa a zuciyar ta a hankali,
A haka ta kwana ranta babu dadi a cikin sa sai faman tunanen da takeyi har dare ya raba sosai a lokacin,

****** ********* ******
Zaune take a f
gaban mahaifin ta a cikin natsuwa take sauraren shi, yana mata zance akan zuwa birnin da zatayi gur8n kaunan shi dake can tana aure don ta matsa a kan Bintu tazo mata hutu ta dan kwana biyu a gurin ta,
Sam Bintu bata,son wanan tafiyan don dai babu yadda zatayi ne da umurnin mahaifinta da gaskiya bataje ba,
Don tafi son ta,zauna a kauyen su tare da mahaifinta don koda take mace ce itace kamar jagoran gidan nasu duk da kasancewar Bintu karamar yarinya ,
Haka take yawan aikin wahala a kan su samu dan abinda zasuci a gidan su kasancewar mahaifin nata ba,wani mai abin hannun shi bane,
Itace zuwa icce itace suyan awara da rana da safe kuma tana koko da kosai kafin ta dawo zuwa makarantan bokon da yake a ranta,
Yanzu gashi gwagonta ta birni ta matsa sai tazo gurin ta wai hutu wanda ita bata san dalilin da ya sa,duk tazo sai tai zancen zuwan Bintu gurin ta hutu ba,
Yan kayan ta,already ta,shirya su a dan jakar ledan ghana most go karama duk jakar ta tsufa sosai don har ledan jikin jakar ta dan tashi ya,wani dan takure daga jikin shi,
Kudi mahaifinta ya ciro daga aljihun shi dubu daya ya mika mata tayi kudin mota dashi,
Kallon kudin take tana mamaki inda ya samo har dubu daya yabata wai tai kudin mota dashi,
Hannu biyu Bintu ta mika ta karbi kudin cikin ladabi tare da fadin na gode Baba,
Bayan ta karba ne yake cewa tau Bintu ki saurareni kiji abinda zan fada maki da kyau,
Ki sani dai rayuwar birni daban yake da,tamu irin na kauye don haka kiyi taka tsatsan da duniya ki kama kanki ,
Ki kawar da idon ki ga duk abinda,bai shafeki ba a rayuwan ki ki tsaya inda gwagon ki ta tsayar dake duk da yake ke yarinyar ce nnatsatsiya amma nasan zakiga abin mamaki da zai iya canza maki rayuwan ki a can,
Don haka kiyi taka tsatsan da duniya baki dayan ta a yanzu babu gaskiya ki tsaya a matsayin ki na yar talkawa kamar yadda kika samu rayuwar mu, aciki tun farko,
A hankali Bintu tace insha Allahu baba zan tsare kamar yadda kace zaka kuma samayni da kiyayyewa insha Allahu,
Yace Allah yai maki albarka Bintu Allah ya tsare min ke da tsarewar shi ta karba da amin Baba idanuwan ta sun kawo hawaye kamar zasu digo dag idanuwan ta,
Shi da kan shi ya rakata har tasha inda zata samu motar da zai kaita, garin Sokoto,
Tana zuwa motar ta cika suka kama hanya sai Sokoto zuciyar ta fam da kunci a cikin sa,
Sai karfe biyu suka shigo gatin na sokoto a lokacin mutane suna ta haramar yin sallah azahar a garin,
Mai yar mashin ta dauka kamar yadda akai mata kwatance tace a kaita Sama road, a bakin shagon dantani mai yar mashin ya tsaya da ita,
Shi ta tambaya gidan Gwago Asmau mai masa ya nuna mata da kwatance tabiya mai mashin kudi ya tafi ta dauki yar jakar kayan ta zuwa gidan da akai mata kwatance, dashi,
Da sallama a bakin Bintu ta shiga gidan ta samu gwago zaune a tsakar gida tana gyara kayan yin masan ta,
Tana ganin Bintu ta fara fara,a tana cewa a,a,a wanake gani yau garin namu kamar Bintu,
Maraba da yar gwago sannu da zuwa sannu da zuwa tana mata maraba cikin jin dadi da ganin ta,
Daki ta nunawa Bintu ta,shiga da kayan ta daga cikin dakin tare da,samun guri ta dan zauna a takure daga gefe guda,
Gwago ta,shigo, dakin dauke da kwanon abinci a hannun ta a rufe ta aje a gaban Bintu, tana fadin zauna ki ci abinci sai mu gaisa,
Cikin yar muryan ta take cewa gwago sallah nake son nafara yi tace tau Bintu ga bayi can jeki ki kewaya,
Sai bayan ta idar da,sallah ne ta fito inda gwagon ta take zaune tana gyaran alaihu tana kokarin karba daga hannun ta,
A,a haba Bintu jeki ki ci abinci mana daga zuwanki zaki buge ga aiki haka jeki kawai ki ci abinci kinji Bintuna,
Kamar yadda gwago tace haka din Bintu tayi ta koma daki ta zauna tare da lankwashe kafafuwanta a hankali ta bude kulan dake gaban ta shimkafane da,wake da mai da yaji a cikin kulan abincin da gwago ta aje mata,sai salad da tumatir da aka yanka daga saman shi,
A hankali take ci a cikin natsuwa har ta kare cin abincin nata wanda ko rabi batayi ba ta mayar da kulan ta rufe wai ta koshi,
Bata zauna ba a,tare sukai aikin masa da gwago ranan ba bata lokaci suka kammala komai da wuri,
Nan suka samu guri suka zauna,suka,fara hiran mutanen gida gwadabawa,

****** ******** ******
Hasken ranan da ya haska dakin ne ya haska dakin...


Read / Download A LOKACIN NE

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .

START READING

OR

Login Register

2 Comments On A LOKACIN NE
avatar
usama-6

6 months ago

Reply

Alhamdulilah

avatar
taskar

6 months ago

Reply

Replying to usama-6

Masha Allah

Please Login or Register in order to submit comment

Releted Novels

Releted Album