Subscribe for N1000/month for downloading access and an ad-free site. Contact WhatsApp +2348140419490 if you can't pay / subscribe. SUBSCRIBE

24 yin

BINTU DIYAR BAYI CE Book 2 Complete Hausa Novel Document by BINTU DIYAR BAYI CE Book 2


BINTU DIYAR BAYI CE Book 2

Cover Design Copyright and attribute to Marus Graphics

Uploaded by @Taskar

Total Words: 19772



BINTU DIYAR BAYI CE Book 2

Reading Time: 1 Hours

Added On: 20, Jan 2025

Author: Khadija Sidi ,

Ebook Compiler : Admin

Author Group : Unknown group

Author Phone : Not Inserted

Book License : Free

Category: Love Novels

File Size: 98.31 kb

File Type: txt

Views: 375+

Download: 211+

Last download: 11 hours ago

Description/Story: Bintu ɗiyar bayi ce (book 2) Chapter 1
Admin 001 Mukhtar Adam Nation
Tareda Naja'atu Lawal Rijau
@Whatsapp 08083232323 09060202323

WAIWAYE
Daga cikin Masallaci aka fara abinda ya had’a jama’a a
wannan masarauta, wato d’aurin aure, in da aka umarci
waliyin Ango da Amarya su matso kusa. Waziri ne ya fito daga
6angaran Sa’ayrasa, Fabarusa kuma Sarki Abdulrahaman ne
ya nuna kan sa a matsayin waliyi.
Daga waje Khalil ne ke ta yiwa Yarima Barde hira, amma shi
ina hankalinsa na ga Gimbiya K'amariyya, Allah Allah ya ke a
shafa fatiha ya tafi garera don jin soyayyar ta ya ke har ransa,
bare kuma yau gabar da ke tsakanin Masarautasu za ta kau, za
su yi soyayyarsu a zahirance ba tare da wani shakku ba. Jin an
shafa fatiha Yarima Barde ya tashi ya na mai fad’in.
‘’Alhamdulillah tunda an amra sai ku tashi mu tafi ko?’’
Har Khalil da Jafar sun tashi, tuni su ka tsaya cak jin marok’a
na fad’in
‘’An d’aura auren *Yarima Abubakar BARDE* tare da *Gimbiya
Fatima* akan sadaki (50000 CFA)"
Yarima Barde da sam bai lura da abinda su ka ji ba tsabagen
hankalinsa ba ya wajan, a hasale ya kai kallonsa ga
abokannasa ya na mai fad’in
‘’Me ku ke jira ne? Mu tafi, Allah Allah na ke na gana da
Gimbiyata.’’
Su kuwa marok’a ba su fasa shela ba. Khalil ne yayi k’arfin hali
ya ce
‘’Da ma kai ne Barde?’’
Cikin rashin fahimta Barde ya ce
‘’Ni ne wa?’’
‘’Angon da aka amrawa amren.’’
Jafar ya bashi amsa a tak’aice. Kai Yarima Barde ya girgiza
cike da murmushin irin ban son rainin hankali fa. Khalil ya ce
‘’Saurara ka ji Barde’’
Nan kuwa muryar wani marok’i da ya zo giftawa ta dafda su ya
doki kunnan Barde, fad’i ya ke
‘’An amra auren Yarima Abubakar Barde da Gimbiya Fatima....’’
Nan ya ya tsaya cak tamkar wanda aka zarewa rai, su kansu
abokannasa sun girgiza kwaran gaske.
Daga cikin masallaci, ana gama d'aurin auren, inda kowa ya ke
mamakin sauyin al’amura da aka samu, musammam jama’ar
Sa'ayrasa, shi kuwa Aisar tunanin hanyar fita daga cikin jama’a
yake, domin zuwa neman Bintu ba tare da Junaidu ya ankare
ba. Bayin Sa'ayrasa ne d’auke da farantin goro da alawa, su ke
bin kusirwa kusirwa in da suke mik’a farin tin jama’a na d'iba
san ran su.
Bawan da ya zo kusurwar da su Aisar su ke, Aisar ya fara
mik’awa, in da ya girgiza masa kai alamar ba ya buk'ata, har
bawan zai wuce, nan idanun Aisar su ka sauka bisa yatsun
bawan, me zai gani? Zobensa da ya bawa Bintu ne cikin
yatsun na shi, bai ankara ba sai ji yayi Aisar ya damk’o
hannunshi, a tsorace bawa ya saki farantin hannun sa dan ko
shakka babu ya san tawagar shugaban k’asa ne
gabansa.Hakan ya dawo da hankalinsu Junaidu da sauran ‘yan
tawagar garesu. Aisar na mai duban idanun bawan ya furta
‘’Ina ka sami wagga zo6en? Menene dangantakarka da mai
zo6en? Ina Bintu d’iyar bayi?’’
Babban gida kuwa 6angaran Jakadiya, Bintu na zaune tare da
su Jakadiya sai ga Gimbiya K’amariyya ta shigo, ta yi kyau
kwarai cikin jajayen kaya, ta d’aura alkyabba ruwan zuma bisa
kayan, ga bayi nan biye da ita. Ta zo kar6ar mabudin wajan aje
baki na musammam domin kar6ar Yarima Barde.
Ta na zaune ta na jiran Jakadiya ta shiga ciki dan d’auko mata
mabud'in, su ka ji an shigo 6angaren Jakadiya an gud’a. Tuni
hanjin cikin Bintu ya kad’a don kuwa ta san ta faru ta k’are an
yiwa mai dami d’aya sata, aure dai an aura. Tuni ta fashe da
kukan da dama ya tsaya k’asan mak’ogaran ta.
Jakadiya ta fito d’auke da mabud’i, yayinda Ladiyo ta shigo jiki
na rawa, sai tafa hannu ta ke cikin salati da sallallami.
Jakadiya ce ta tambaya ko lafiya, yayin da hankalin kowa ya
koma gareta.
Cike da ladabi Ladiyo ta durk’usa gaban Jakadiya ta na mai
fad’in
‘’Yau na ga lafiyar Allah Maigari gauro talaka da mata hud’u.’’
Cikin k’aguwa Gimbiya K’amariyya ta ce
‘’Me ya faru ne Ladiyo?’’
‘’Wato Allah shi taimaki Gimbiya, ji da gani dai ba ya k’arewa
sai randa kurman bebe ya makance, Sarki Abdulraman na
Fabarusa cike ya ke da abin mamaki, wani lamari sai shi.....’’
‘’Yo to wani abin mamaki? Ya ce ya fasa ne?’’
Jakadiya ta tambaya cikin rashin fahimta. Kana Ladiyo ta ce
‘’Eh to ya fa fasa be kuma fasa ba, da ya tashi yin bazata, sai
ya amrawa d'ansa Barde Bintu.....’’
Hakan yayi daidai da ihun da Gimbiya K’amariyya ta kurma ta
na mai zubewa k’asa sumammiya. Nan da nan aka yi kanta.
Bintu kuwa yanda maganar ya doki kunnenta ta tabbatar ta
zama kurma, don kuwa ba ta jin hayaniyar da ake gabanta
‘’Ya amra ma d’an sa Barde Bintu....’’
Maganar da ke ihu jikin kunnenta kenan.
1⃣
Tuni waje ya kaure da salati da salallamin bayi, Jakadiya ce ta
sa aka yi maza aka shigar da K’amariyya daga cikin d’aki
gudun gulman da ta san tabbas sai ta yad’u daga bakin bayin
da ke wajan. Bintu kuwa ta ma kasa gane komai, kukan ta
kawai ta ke, aure dai an d’aura mata, ko ta na so ko ba ta so
tafiya ne dole a tafi da ita. Gashi a rasa wanda za a d’aura
mata sai saurayin Gimbiya K’amariyya, Yerima Barde na
Fabarusa! Hannu biyu Bintu ta d’aura bisa kan ta ta na mai
fad’in
‘’Wayyo ni Bintu alk’iyama ta ta zo’’
Daga cik’in uwar d’aka, bayan an kori duka bayin da ke
b’angaran Jakadiya, Hajja Kilishi da Inna Salti wanda Jakadiya
ta aika Ladiyo da Kyallu su sheda ma su abun da ke faruwa ne
su ka shigo d’aya na bin bayan d’aya, biye da su Gimbiya Binta
ce, wacce ita ma labari tuni ya je mata.
Jakadiya ta umarci bayin da su ka taka mata baya su yi jiran
ta waje. Bayan an watsa ma Gimbiya K’amariyya ruwa, da
rokan Allah ta farfad’o ta na mai bin su da kallo kamar lokacin
ta fara ganin fuskokinsu. Kanta bisa kan cinyar Inna Salti,
Jakadiya zaune gaban ta sai kuma Gimbiya Binta wacce ta
dad’e da gigicewa da jin lamarin da ya faru, in ban da kuka
babu abinda ta ke don gani ta ke duk laifin Bintu ne ko shakka
babu ita da uwarta ne su ka sa musu hannu wannan balk'in ya
fad’a kan ‘yar uwarta.
Ko da idanun Gimbiya K’amariyya ya sauka kan Gimbiya Binta,
ita ma d’in ta fashe da kuka don sai a sannan ne ta dawo cikin
hayyacinta sosai. Cike da damuwa Hajja Kilishi ke tambayar
‘’Menene ne? Gide menene ke faruwa? Tun dazu fa nake
tambayar ki Binta amma amsa ta gagara daga gareki, yanzu
kuma mun samu ta farfad’o maimakon a sami sauki ina, kun
maishe da gida kamar wajan makoki! Shin ba kwa gudun
abinda zai je ya dawo? Kun fa san gidan ga cike yake da baki
da kyar na sami hitowa daga cikin jama’a, ko rufa mana asiri
ku sheda mana abun da ke faruwa.’’
Cikin kuka muryarta dak’yar ya ke fita, Gimbiya K’amariyya ta
amsawa Hajja Kilishi, ta na mai fad’in
‘’Na shiga uku Hajja, Inna Salti na shiga uku, na d’au wuk’a na
dab’a ma kaina, Allah Ya nuna min ikonSa, Barde…..Yarima
Barde na Fabarusa……’’
Kuka ya ci k’arfinta, ta kasa k’arasawa sai shasshek’a ta ke.
Cikin rashin fahimta Inna Salti ta ce
‘’Barde? Me ya faru da Barde na Fabarusa?’’
‘’Ni kam ta dad’a sa kai na cikin duhu, jakadiya wagga yarinya
ba gamo ta yi ba kuwa?’’
Cewar Hajja Kilishi cike da damuwa.
‘’Yarima Barde da Didi masoya ne, shi ne dalilin ta na k’in
amincewa ta auri sarkin Fabarusa wanda yake mahaifi a
gareshi.’’
Gimbiya Binta ce ta amsa ma su.
‘’Kayya! Kai wagga lamari da me yayi kama! Kun ga irin ta ko?
Gashi dai an cuci d’iyar mutane kin kuma cuci kanki
K’amariyya, anyi gudun gara an tadda zago! Jakadiya dai ga
irinta nan dai kin gani don kuwa wagga kulli ke da wagga d’iya
ku ka kulla.’’
Fad’in Inna Salti ta na mai nuna matuk’ar b’acin rai.
Jakadiya da tunda aka fara maganar ta sha jinin jikin ta, jikinta
ya yi sanyi kamar wacca aka tsunduma cikin ruwan sanyi
cewa ta yi
‘’Uhum Allah shi ja da ran ki, yo to ni me zance? Ni ina naga ta
ce wa? ‘’
Cikin kuka don kuwa idanunta sun rufe K’amariyya ta furta
‘’Don Allah ku taimaka a warware wanga lamari, don Mai
Sama, kwarankwatsa zan iya rasa rayuwata, dan Allah ayi
maza a shedawa takawa kafin na rasa raina, Ammu ki taimaka
min…..’’
Kai Hajja Kilishi ta jinjina kafin ta ce
‘’Gide Takawa zai saurari wanga azzance kuwa Jakadiya?
Yanzun ga ya na can wajan liyafar d’aurin amren nan......’’
Kafin Jakadiya ta amsa Gimbiya Binta ta yi saurin taran
numfashin ta ta hanyar fad’in
‘’Ku taimaka tun kafin a makara, dan kuwa ba Sidi ba ko ni ma
ina tara muddin ba a warware wanga
amre ba, ya d’iyar bayi za ta amri mutum kamar Barde, dan
Allah Jakadiya ki sama mana mafita tun kan na had’iyi zuciya
na mutu dan kuwa ciwon da na ke ji ya ma fi na Didi’’
‘’Makara kam an riga an makara, saidai fa a jira bayan komai
ya lafa a yiwa Takawa magana watakil shi bai zai rasa dabara
ba.’’
Cewar Hajja Kilishi yayin da tashi tsaye jiki sanyaye, tak’ara da
fadin.
‘’Kunsan mu na da baki, duk abinda za ku yi kada ku manta da
martabar Takawa, ku kula ku kame kanku kada ku jawo mana
abun da zai halaka yankin ga gaba d'aya’’
Ta na gama Magana
Domin cigaba da karantawa sai ku downloading.
Yadda ake downloading na littafin: ku tabbata kunyi register da shafinmu sanna kunyi login, idan bakuyi register a kasa zakuga maballai guda biyu daya an rubuta LOGIN dayan kuma an rubuta REGISTER sai ku taba su kuyi register, daga nan sai ku yi subscription koda na naira 1000 ne, domin sai kunyi subs dinann ne kadai zaku iya dauko littatafanmu.

Ya ya akeyin Subscription namu : Bayan kun yi Login ko register daga kasa zaku ga wani jan maballi (button) an rubuta SUBSCRIBE sai ku taba shi zai kaiku inda zaku zabi package wato tsarin subs na ku da mu. akwai na wata guda, watanni biyar da shekara guda. da zarar kun zaba zai kaiku inda zaku biya kudin, wanda daga nan sai ku cigaba da downloading kawai abunku

ABUN LURA : duk wani littafi da kuka gani a shafinnan kyauta ne, wannan tsari mun zo da shine don mu samu hanyar da zamu iya rike shafin muna managing na shi, izan ku kayi subs na mu tamkar DONATION ne ku ka yi mana, ku ka bamu kwarin guiwa don mu ciagaba da kawo muku sabbin littatafai, amma duk wanda ya ga bazai iya ba toh zai iya karanta littafin kyauta a cikin shafinnan namu batare da ya downloading ba, kawai ya yi kasa zai ga Koren maballi (button an rubuta) START READING sai ya taba zai kaishi inda zai karanta littafin.

Sannan duk wanda yaga kamn wannan process din zai bashi wahala kai tsaye zai iya min magana ta whatssApp +2348140419490, ya tura min kudin ni kuma zan dora mai subs din akan account na shi

NB: iya ta haka ne zaku iya karanta wannan littafi a shafinmu babu wata hanyar. DAN ALLAH KU DAINA MANA MAGANA AKAN MU TURA MUKU LITTAFI TA WHATSAPP, BAMA TURAWA HANYA GUDA MUKE TURA LITTATAFANMU SHINE WEBSITE NA MU https://taskarnovels.com.ng DUK MAI BUKATAR LITTAFINMU YA JE CAN YA KYAUTA NE, AMMA DOWNLOADING KUWA BA KYAUTA BANE SAI YAYI SUBSCRIPTION NA WEBSITE NAM
This is not the real Download Button


Read / Download BINTU DIYAR BAYI CE Book 2

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .

START READING

OR

Login Register

This is not the real Download Button
Please Login or Register in order to submit comment

Releted Novels

Releted Album