Subscribe for N1000/month for downloading access and an ad-free site. Contact WhatsApp +2348140419490 if you can't pay / subscribe. SUBSCRIBE

24 yin

MUSABBABI Part 2 Complete Hausa Novel Document by MUSABBABI Part 2


MUSABBABI Part 2

Cover Design Copyright and attribute to Marus Graphics

Uploaded by @Taskar

Total Words: 82748



MUSABBABI Part 2

Reading Time: 6 Hours

Added On: 20, Jun 2024

Author: Habiba Abubakar Imam ,

Ebook Compiler : Admin

Author Group : Unknown group

Author Phone : Not Inserted

Book License : Free

Category: Love Novels

File Size: 426.15 kb

File Type: txt

Views: 466+

Download: 1048+

Last download: 1 day ago

Description/Story: MUSABBABI BOOK 2

NA

HABIBA ABUBAKAR IMAM

Page 1

Jin muryar Haj kilishi cikin kuka yasa Haj Rakiya ta yi saurin gyara zamanta tace, “Haj lafiya me ke faruwa?, na jiki cikin wani irin yanayi, kamar fa kuka ki ke yi”.

Haj kilishi ta saki wata katuwar ajiyar zuciya tace tana kokarin tsaida hawayen da ke cigaba da sauka a kuncinta, “Kuka na ke yi Haj, domin ina son na sami sauki da sassaucin matsananciyar damuwar da nake ciki, shin yaushe zan samu nutsuwa da kwanciyar hankali?, yaushe zan samu cikar duka burikana akan musaddik?”. Jin hakan yasa Haj Rakiya ta fahimci inda Haj kilishi tasa gaba, don haka ta tabe baki, ta kara janyo kwanon abincinta ta jefa wayar a speaker out ta aje ta cigaba da cin cinyar kazarta hankali kwance, sannan tace,

“Subhanallahi yanzu kuma meya faru me ake ciki?”,
Ta goge hawayenta tace “Anya kina ganin shi ma Tsiduhu aikinsa yana yi kuwa?”, da sauri tace “kai ai bana tababa aikinsa yana yi sai dai ko jinkiri, me kika gani kika ce haka kuma?”.
A hankali cikin sanyin guiwa haj kilishi ta kwashe abinda idanunta suka gani ta gayama Haj Rakiya.
Ta kara da cewa “jin zuciyata nake kamar zata fashe, wani irin zafi jikina yake min, na rasa abinda ke min dadi, kinga annurin dake kwance akan fuskar musaddik kuwa, kinga yadda yake wasa da dariya da maigadi, baida wata damuwa, ni ke da kudi amma shine yake da farinciki, shi yasa nake tunanin anya aikin Tsiduhu ya ci kuwa”.
Haj Rakiya ta tsotse kashin kazar ta watsar gefe, sannan tace “Bana jin a jikina aikin nan baiyi ba amma me zai hana mu kara komawa mu yi masa bayani kila ko akwai inda aka sami matsala idan kuma hakane muna zuwa zai warware mana komai”, Haj Kilishi tace “Eh gara mu koma din zanfi samun nutsuwa, sannan kuma mu je wajen mai Rakwacam shima ina bukatar yasan komai fa ya canja, yakamata ya kara bamu tabbaci akan ajiyar mu ta karkashin bishoyar kuka, domin ina fargabar ko an samu matsala”.

Haj Rakiya tace “Bana jin haka kawai dai kina wannan fargabar da gangane , domin ko dazu naje na duba wajen amma dai mu je din don hannu da yawa maganin kazamar miya”. Haj kilishi tace “Hakane haj”, Haj Rakiya ta dan muskuta tace “To wai Haj ya maganar maganin da Tsiduhu yace ki sama Afrah a abinci, kin sa mata kuwa?”,Haj kilishi ta kara cika da damuwa tace “Har yanzu ban sami dama ba domin yarinyar tamkar ta gane ni ,nafa gaya miki ko shigowa ta daina yi yanzu, to ta yaya zan sa mata a abinci ta ci”, Haj Rakiya tace “Haba sai kace ba ke ba, tsakani da Allah, ai kwantar da kanki zaki yi ki bi duk hanyar da zaki bi domin ganin ta ci abincin”, tace “To ta yaya?”. Tace “ki gayyatota da kanki cikin gidan ai ba zata ki zuwa ba daganan sai kisan yadda zaki yi ta ci abincin”, Haj kilishi cikin gamsuwa da maganarta tace “zan gwada yin hakan, domin yarinyar nan itace bala’i a gare ni yanzu, the n dai da ita a tsakani to bana jin zan sami sukunin rayuwa”.Daganan suka cigaba da tattaunawa sun tsaida maganar cewa zasu fara zuwa wajen mai Rakwacam gobe, jibi kuma su wuce wajen Tsiduhu, kai wannan wahala da yawa take,
Haj Rakiya ta mika hannu ta kashe wayar tana buga tsaki, ta mike ta je ta wanke hannunta, ta dawo ta zauna tana murmushi, gaskiya babu wahalalle sai mai bin malamai da bokaye, yanzu wannan rashin nutsuwar ta haj Kilishi ai katuwar masifa ce, ita dai kam ta dawo daga rakiyarta, yanzu neman kudi ke gabanta, idan so samu ne duk ragowar kudin haj kilishi su dawo hannunta, gashi nan kullum kaji take ci, har wani ja ta fara yi sabida cin nama.
Tayi dariya sosai ta janyo waya ta kira Tsiduhu ta sanar da shi komai, ta kuma gaya masa ya shirya suna tafe jibi, ya kuma tabbatar mata babu wata matsala a shirye yake.

Shigo da kayan da akayi yasa Afrah ta shi cike da farinciki, sannu ta dinga yi ma Baba maigadi har ya gama shigo da komai, sannan musaddik ya shigo rike da ledar atamfofi, ta mika hannu zata karba da sauri tana yi masa sannu da zuwa, maikan ya sakar mata ledar sai kawai ya janyo hannunta ya matseta sosai a kirjinsa, yana jin kamshin jikinta, itama lafewa tayi a kirjin nasa tana jin wani irin dadi yana ratsa zuciyarta, gaskiya ne mahakurci mawadaci, a haka suka karasa cikin falon sai da suka zauna sannan tabar jikinsa cike da fara’a tace tana kallonsa “ yaya wadannan kayan fa”, ya yi murmushi yau jinsa yake cikakken magidanci, har wani girma yaji yana ba kansa .

“Albashina ne, naje nayo mana siyayyar kayan abinci, ki duba ki gani ina jin ai ban manta komai ba ko?” Tace cikin nuna godiya, “ Bana jin ka manta wani abu, Allah ya saka da alheri Allah ya kara budi ya kara wadata, nagode”yace “kin fi haka Afrah, duk abinda zan nema saboda ke ne, don ta ni na rantse miki ko nera bazan fita na nema ba, amma ina son ganin farincikin ki shi yasa zanyi komai domin na dauwamar da wannan murmushin a fuskarki,” ta gyada kai tace “Nagode da wannan kulawar”.
Ya mika mata ledar hannunsa yace “Ga wannan ki dauki guda biyu , idan zaki tafi islamiyya ki tafima da inna Halima daya”, bata gama wannan mamakin ba taga yasa hannu a cikin aljihunsa ya fito da kudi ya mika mata dubu biyar yace “wannan kuma ki kaima kawu Mahmud ya yi cafane”.
Kawai saita rungume shi sosai, harda kwallar farinciki, ya dagota yana share mata hawayen, “ meyasa kike kuka?”, ta lumshe ido hawaye ya kara fito mata tace “Kukan farinciki kawai nake yaya, Allah ya yi min dukkan gata na hadani da kai a matsayin abokin rayuwata”, ya girgiza kai yace “Ni zanyi ma Allah godiya da ya bani mata irinki, amma ni sai dai kawai ki yi maleji da ni”, ta bugama mai duka a cinyarsa tace cikin dariya “ kafi karfin maneji haba yaya , mijin nawa zaka kira maneji”, yayi dariya yace “Gaskiya ne fa”, ta fito da da atamfofin tana kallo, ta dago ta dube shi sosai tace “kai tsaya yaya, wadannan kayan da irin wannan siyayyar da kayi sun fi karfin albashinka, ya akayi haka?”.

Ya yi ajiyar zuciya yace “madalla da mata irinki me kokarin ganin ta san halinda mijinta yake ciki”. Ya kara matsantarta sosai yace “Haj tayi min karin wasu kudin bayan albashina”. Ta zuba masa ido tace “ Allah ya saka mata da alheri, lalle tasan martaba tare da darajar ma’aikatanta”.sun dade suna cigaba da maganganunsu, daga bisani musaddik shine ya tayata gyara cikin store suka jera kayan abincinsu a ciki lemo kuma suka shirya a cikin frij ragowar suka maida store komai ya yi kyau.
Saida suka gama komai yamma likis, sannan musaddik ya tashi zai fita .
Afrah ta zuba masa ido ta ji wani iri a cikin jikinta, domin ranta ya bata cewa wajen shaye shayensu zai tafi, a sanyaye tace “ yaya musaddik, don Allah ka daure kada ka yi almubazzaranci da abinda ya rage maka ma’ana kada ka fita kaje ka sha wani abu da zai sa ka wulakanta , kada ka je ka sha abinda zai maida min farincikina bakinciki”.
Jikinsa ya yi sanyi a hankali ya koma ya zauna ya kama kansa ya rike tam, kawai sai yaji hawaye yana fita masa, ta dawo kusa da shi ta zauna tana kallonsa cike da damuwa da kulawa tace “ka daina kuka don Allah “.
Ya kara yin kasa da kansa domin baya son taga hawayensa, nan da nan itama taji na ta hawayen yena sauka a saman kuncinta, yace kai a kasa “ki yi hakuri Afrah ki barni na fita, na rantse miki ji nake kamar zan mutu idan ban sha ba, ki barni na je nayi miki alkawarin bazan sha da yawa ba”, ta ji wani abu a ranta, a hankali ta goge hawayenta tace “Tashi ka tafi Allah ya shiryeka”.
Sai da ya dauki wasu mintoci sannan ya iya tashi amma ya kasa hada ido da ita har ya fice.
Ta koma ta zauna sosai akasan dakin tana tunanin akwai wani abu a boye a cikin lalacewar rayuwar musaddik, amma yau ta tabbatar musaddik ba dai dai yake ba,
Domin cigaba da karantawa sai ku downloading.
Yadda ake downloading na littafin: ku tabbata kunyi register da shafinmu sanna kunyi login, idan bakuyi register a kasa zakuga maballai guda biyu daya an rubuta LOGIN dayan kuma an rubuta REGISTER sai ku taba su kuyi register, daga nan sai ku yi subscription koda na naira 1000 ne, domin sai kunyi subs dinann ne kadai zaku iya dauko littatafanmu.

Ya ya akeyin Subscription namu : Bayan kun yi Login ko register daga kasa zaku ga wani jan maballi (button) an rubuta SUBSCRIBE sai ku taba shi zai kaiku inda zaku zabi package wato tsarin subs na ku da mu. akwai na wata guda, watanni biyar da shekara guda. da zarar kun zaba zai kaiku inda zaku biya kudin, wanda daga nan sai ku cigaba da downloading kawai abunku

ABUN LURA : duk wani littafi da kuka gani a shafinnan kyauta ne, wannan tsari mun zo da shine don mu samu hanyar da zamu iya rike shafin muna managing na shi, izan ku kayi subs na mu tamkar DONATION ne ku ka yi mana, ku ka bamu kwarin guiwa don mu ciagaba da kawo muku sabbin littatafai, amma duk wanda ya ga bazai iya ba toh zai iya karanta littafin kyauta a cikin shafinnan namu batare da ya downloading ba, kawai ya yi kasa zai ga Koren maballi (button an rubuta) START READING sai ya taba zai kaishi inda zai karanta littafin.

Sannan duk wanda yaga kamn wannan process din zai bashi wahala kai tsaye zai iya min magana ta whatssApp +2348140419490, ya tura min kudin ni kuma zan dora mai subs din akan account na shi

NB: iya ta haka ne zaku iya karanta wannan littafi a shafinmu babu wata hanyar. DAN ALLAH KU DAINA MANA MAGANA AKAN MU TURA MUKU LITTAFI TA WHATSAPP, BAMA TURAWA HANYA GUDA MUKE TURA LITTATAFANMU SHINE WEBSITE NA MU https://taskarnovels.com.ng DUK MAI BUKATAR LITTAFINMU YA JE CAN YA KYAUTA NE, AMMA DOWNLOADING KUWA BA KYAUTA BANE SAI YAYI SUBSCRIPTION NA WEBSITE NAM
This is not the real Download Button


Read / Download MUSABBABI Part 2

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .

START READING

OR

Login Register

This is not the real Download Button
Please Login or Register in order to submit comment

Releted Novels

Releted Album