Subscribe for N1000/month for downloading access and an ad-free site. Contact WhatsApp +2348140419490 if you can't pay / subscribe. SUBSCRIBE

24 yin

A JININSA YA KE Book 1 Complete Hausa Novel Document by A JININSA YA KE Book 1


A JININSA YA KE Book 1

Cover Design Copyright and attribute to Marus Graphics

Uploaded by @Taskar

Total Words: 48749



A JININSA YA KE Book 1

Reading Time: 4 Hours

Added On: 06, Feb 2025

Author: Zulaihat Sani Kagara ,

Ebook Compiler : Admin

Author Group : Unknown group

Author Phone : Not Inserted

Book License : Free

Category: Love Novels

File Size: 242.17 kb

File Type: txt

Views: 180+

Download: 272+

Last download: 4 hours ago

Description/Story: Ajininsa yake 1-01
Posted by ANaM Dorayi on 07:24 AM, 03-Nov-15
Under: Ajininsa yake
__________________ NA ZULAIHAT SANI KAGARA_______
________
Rabe jikin daya daga cikin bishiyon da suka yi wa
filin sukuwar kawanya. Jikinsa kayan mkrntar
firamare ne. Farar riga da koren wando. Gaba-
daya hankalinsa tattare ya dora bisa dawakan da
ke zuba tsere kamar za su tashi sama. Babu
abinda yake tunani, illa ina ma shine bisan dokin
da yayi wa saura fintankau?"
Jama'a suka hau ihu, don taya mai dokin daya zo
na farko murna. Shi ma ya kwasa a guje.
Yana isowa bai ma san ya jefar da jakar
littattafan sa ba. Ana ture shi, yana turawa, sai
da ya kutsa ya ta6a jikin saurayin daya zo na
farko.
Kamar an sanya shi al-janna, haka yake ji cikin
ran sa.
Wasu rukunin dawakan ne za su taso yanzu, shi
yasa duk jama'a suka koma inda suke.
Haka shima ya nemi wata bishiyar ya kuma
ra6ewa jikin sa na tsuma, tamkar na 'yan dambe.
Caraf!
Ya ji an cafke kunnunwan sa 2, a firgice ya juyo,
su kai ido 4 da mahaifinsa. Ido warwaje ya daga
hannayen sa sama, amma ya kasa cewa komai.
"Ba za ka daina bata min rai ba Naseer?
Makarantar kenan?
Ya 6ata rai kwarai, manyan idanuwan sa suka
kada jajir!
Haka ya tsurawa Baban sa ido.
"Zo mu je mkrntr, jikinka ne zai gaya maka,
tunda kai kunnan kashi gare ka, ni ma ba zan
fasa ba!
Ina jakar ka?
Ya shiga dube-dube,"Au jakar ma ba kasan inda
take ba?"
Ya maka masa duka a keya,"Wuce mu je ka nemo
jakar, dan banzan yaro marasa jin magana!"
Yaja kunna sa suna tafiya har suka yi karo da
jakar,"Duka ka dauko ta!"
Ya sa hannu ya dauko, a haka suka shiga. Cikin
mota, kunci kamar Naseer zai yi bindiga sabo da
kunburi."(L.E.A Primary School) da ke kusa da
ofishin "Yan-sanda na Tudun Wada Zaria nan
suka shiga shugaban makaranta.
Ya tsura masa ido ya-ce,"Ba za ka bar Babanka
ya huta bane Naseer! Kai wane irin yaro ne?" Ya
juya gefe ya tura hannunwan san a aljihu.
Hedimasta ya dankwafar kan sa ya ce,"Rage
tsawonka, ka kuma cire hannayen ka daga
aljihu!"
Ya durqusa yana huci, saboda tsabar zuciya,
kirjinsa na bugawa muraran kowa na gani."
Malam Balarabe ya ce,"Zane min shi za ka yi a
gaba na in gani.
Idan kuma ba za ka iya ba, ni zan dauki bulalar
in hukunta shi bar ni da shi.
Ya ce,"nan da nan ban zuwa Hedimasta, sai na
ga jikin Naseer yayi rudu-rudu.
Ina bulalar take? Miko min ita nan!"
Hedimasta ya jawo dorina, Baban sa ya cire masa
riga da karfin tsiya yana kallo aka rinka tsala
masa dorina dai-dai har goma sha biyu.
Amma Naseer ko gezau bai yi ba, balle ya fidda
hawaye.Takaici kamar ya kashe Malam Balarabe,
ya ja kujera ya zauna, ya ce,"Ban san yadda zan
yi da wannan yaron ba, shi kadai gare ni, amma
gaba d'aya ya buwayeni."
Hedimasta ya ce,"Sai addu'a, yaran yanzu addu'a
ce ke ladabtar da su, don haka ka yi tayi masa
ita.
Babu komai, ka na iya komawa ka bar ni da shi
kawai.
Ya karkada kai cike da damuwa, yasa aljihu ya
labubo Naira 2 ya dora bisa tebur ya ce,"Ga
kudin tarar sa nan don na san da wadancan ya
shiga mota ya je filin sukuwar."
Ya ce,"To shi ke nan.
Allah ya shirya mana."
Ya mike yana fadin,"Amin.
Ya mika masa hannu suka yi Musabaha.
Ko ta kan Naseer bai sake bi ba, ya sa kai ya
bar ofis din.
Hedimasta ya duba shi ya ce,"
"Naseer!"
Ya sunkuyar da kai kasa, ban tanka ba."
Haba Naseer, ka na da kokarinka, kaf ajinku
babu mai kwakwalwar ka, amma ka zauna cikin
aji, sai ya gagare ka?
Kai kullum hankalinka na filin Sukuwa.
Idan ba kayi karatu yanzu ba, sai yaushe za ka
yi?"
Ko alama kai ba ka koyi da abokanka, ba ka
tausayin mahaifinka.
Kodayaushe shine zarya filin sukuwa yana kamo
ka.
Ka yi wa kanka fada Naseer, ka ga yanzu aji 6
ka ke, a gantale, a gantala dai ka kusa zana
jarabawar shiga sakandire, idan ba ka maida
hankali ba, ka na ji ka na gani abokanka za su
wuce su bar ka anan.Yanzu abinda na ke son ka
da shi, shine ka maida rigan ka, ka wuce aji, ka
ga sauran minti 10 a fito (Break), sai ka zo ka
amshi kud'in ka.
Ga su nan aje su waje na. Idan ba ka zo ba,
wannan zai tabbatar min cewa ka gudu ne.
Tashi ka wuce."
Ya mike ya maida rigarsa, bayan sa rudu-rudu
da zanan bulala.
Kai tsaye ya wuce ajinsu.
Malamin da ke cikin ajin yace , "Sai yanzu ka ke
zuwa?" Yayi shiru yana hura hanci.
Ya ba shi rankwashi 2 masu kyau, sannan ya-ce
ya je ya zauna.
Ya taho a kunbure ya tsaya gaban bencin baya,
inda ya saba zama.
Kallon sauran yaran kawai yayi, suka hau
matsawa ya sami wuri ya zauna. Ya ci gaba da
kunci, bai ko sauranon Malamin turancin da ke
ajin har aka kada Break tara. Malam ya fita,
kowa yayi waje, sai Naseer kadai ke zaune yana
tunanin yaya za'a kare wasan da ya baro ana
yi? Wani yaro dai-dai tsawon sa wankan tarwada
ya shigo, ya zauna kusa da shi.
"Naseer, ashe ka zo?
Ya dube shi ido jazur!"
"Eh,
Ya kura masa ido ya-ce,"Yau ma dukan ka aka
yi?"
"Ban sani ba!"
Ya fada cikin fushi.
Ya-ce,"Ai na gaya maka, kar ka je, amma ka ki
ki, don na san dole ne Babanka zai zo nan ya
bincika."
Ya nuna shi," Kar fa ka dame ni Sageer, meye
ruwan ka!
To!"
Ya mikie ya-ce,"Allah ya ba ka hkr. Ni zan je
wajen masu abinci, in sayo maka gyada ne?"
Ban ci!"
Ya amsa, bai kalle shi ba.
Sageer ya wuce abin sa.
Tsaki yayi, ya jawo jakarsa ya fidda littafin sa da
biro yayi ta zana dawaki suna tsere, ko alama
bai yi tunanin ya je ya amso kudin sa ba. Duk
da cewar Hedmasta ya-ce idan bai zo ba, to ya
san ya gudu ne.
Kuka yake ta ji, ta bayan tagar ajin da yake
zaune. Kwarai kukan ya dauki hankalinsa, don
haka ya mike ya leka.
Wata 'yar yarinya-ce rabe take ta gurshashan
kuka ba ji, ba gani.
Akalla za ta kai shekaru 8 ko fin haka.
Ya sanya mata ido, duk tayi zufa, majina sharaf-
sharaf, nan take tausayin yarinya ya lullube shi.
Ta tagar yayi tsalle, ya diro gaban ta, don haka
ta dube shi a firgice.
"Ke da wanene?
Ta kasa magana, saboda kuka da ya ci karfinta.
Ya kamo kafadun ta, ya-ce,"An ce wa ya duke
ki?"
Cikin muryar kuka ta amsa,"Kudi na ne suka
fad."
Kudinki?"
Ta amsa da ka.
"To ina yan-uwanki?
Ko ba ki da su?"
Da ka tasa ke amsawa.
Yayi dan shiru, ka-fin ya-ce,"Ki yi shiru, zo nan
ki zauna ki jira ni.
Ya jawo hannun ta, suka zagayo barandar ajinsu
ya zaunar da ita," Zauna nan ki jira ni."
Ta zauna tana share hawaye.
Wasu na sake zubowa.
Kai tsaye ofishin Hedimasta ya nufa.
A kofa suka yi kicibi6.
Hedimasta ya-ce,"Ai na dauka ka yi halin naka
ne.
A jinku da za ni yanzu, shigo ka amsa."
Suka shige tare, ya jawo dirowa ya dauko, ya
mika masa." Ana tashi kuma, ka zo nan kafin ka
wuce gida."Can kasan makoshinsa ya amsa da
"To."
Ya fice.
Malama Abu da ke zaune ta ce ,"Ina son yaron
nan, amma bai son karatu, ga shi da kokori.
Hedimasta ya ce,"Ke ko ni wallahi akan dole na
ke dukan sa, saboda baban sa tausayi yake ba
ni, koma yana son yayi karatun."
Ta ce,"Yara ai sai hkr, Allah dai ya shirya mana."
Ya ce,"Amin."
Shi kuwa wajen yarinyar nan ya koma, har
yanzu tsiyayar hawaye take yi.
Ya kamo hannu ta yana fad'i,"Har yanzu kukan
ki ke yi?
Ta so mu je ki zabi abinda ki ke so ki ci."
Ya ja ta zuwa wajen masu abinci.
Can ya hadu da Sageer."
Ina ka samo wannan?"
Ya ce,"Kudin ta ne ya suka fadi, shine take
kuka, kuma bata da kowa anan.
Zo ki zaba, me ki ke so?"
Kankara kawai ta nuna.
Ya siya mata, sannan ya kara mata da aya mai
siga da gyada mai gishiri.
Ta ce,"Na gode.
Ya kamo ta suka dawo da Sageer.
Nan bisa baranda suka zauna su 3 tana ta shan
kankara ta."
Ya sunan ki?"
Ya tambaya ta.
Ta-ce,
"Zahra Umar.Ya ce,"Wane aji ki ke? Ta amsa,
"Aji uku." Ya ce,"To maza ki cinye, ki koma aji.
Ya juya suka ci gaba da hira da abokan sa.
Labarin wasan da ya baro ana yi, shi yake ba
Sageer.
"Abinda ke hana ka karatu kenan Naseer, kai
kullum hankalinka ka akan polo yake.
Ya gyara fuska, don shi Naseer akwai iya tsare
gida tamkar wani babba, ya ce,"Kowa ya dame
ni akan Polo, ni kuma ina so, burina in ganni ina
sukuwa, kamar Yakubu Jah-Jah. Yau ba karamin
burgeni yayi ba, sai da na kukkutsa na ta6o
shi."
Ya ce,"To ai komai dan lkc ne Naseer. Ina
amfanin kullum sai an yi maka bulala? Dubi jikin
ka, ko'ina ta6on bulala ne, sam ba ka jin
magana Naseer." Ya ce,"Ban ji din idan ka yi
min iskanci yanzun nan, zan kwashe ma hakori
wallahi, ka kuma sake magana, ka gani."bai ce
kala ba, ya juya ya ci gaba da murza gyad'ar sa,
yana afawa baki. Naseer ya juyo kan Zarah, sai
ya ga wayam!
Tuni ta kama gaban ta. Yayi dan shiru, kome
yake tunani? Oho.
Ya dubi Sageer, ya ce,"Yaushe Zarah ta gudu?"
Yayi banza da shi, yana ta jan gyadarsa.
Tsaki yayi shi ma, ya mike ya haura aji ta taga.
Yara cike da ajin ga littattafin sa da biro, amma
babu wanda yayi gigin ta6awa, don sun san
kayan Naseer ne.Yana zama ana kada
kararrawa. Muryar Sageer ya ji ta taga yana
cewa,"Dama ana tashi ka yi tafiyar ka, kar ka
sake ka neme ni!"
Ya ce,"Kai din banza,
Domin cigaba da karantawa sai ku downloading.
Yadda ake downloading na littafin: ku tabbata kunyi register da shafinmu sanna kunyi login, idan bakuyi register a kasa zakuga maballai guda biyu daya an rubuta LOGIN dayan kuma an rubuta REGISTER sai ku taba su kuyi register, daga nan sai ku yi subscription koda na naira 1000 ne, domin sai kunyi subs dinann ne kadai zaku iya dauko littatafanmu.

Ya ya akeyin Subscription namu : Bayan kun yi Login ko register daga kasa zaku ga wani jan maballi (button) an rubuta SUBSCRIBE sai ku taba shi zai kaiku inda zaku zabi package wato tsarin subs na ku da mu. akwai na wata guda, watanni biyar da shekara guda. da zarar kun zaba zai kaiku inda zaku biya kudin, wanda daga nan sai ku cigaba da downloading kawai abunku

ABUN LURA : duk wani littafi da kuka gani a shafinnan kyauta ne, wannan tsari mun zo da shine don mu samu hanyar da zamu iya rike shafin muna managing na shi, izan ku kayi subs na mu tamkar DONATION ne ku ka yi mana, ku ka bamu kwarin guiwa don mu ciagaba da kawo muku sabbin littatafai, amma duk wanda ya ga bazai iya ba toh zai iya karanta littafin kyauta a cikin shafinnan namu batare da ya downloading ba, kawai ya yi kasa zai ga Koren maballi (button an rubuta) START READING sai ya taba zai kaishi inda zai karanta littafin.

Sannan duk wanda yaga kamn wannan process din zai bashi wahala kai tsaye zai iya min magana ta whatssApp +2348140419490, ya tura min kudin ni kuma zan dora mai subs din akan account na shi

NB: iya ta haka ne zaku iya karanta wannan littafi a shafinmu babu wata hanyar. DAN ALLAH KU DAINA MANA MAGANA AKAN MU TURA MUKU LITTAFI TA WHATSAPP, BAMA TURAWA HANYA GUDA MUKE TURA LITTATAFANMU SHINE WEBSITE NA MU https://taskarnovels.com.ng DUK MAI BUKATAR LITTAFINMU YA JE CAN YA KYAUTA NE, AMMA DOWNLOADING KUWA BA KYAUTA BANE SAI YAYI SUBSCRIPTION NA WEBSITE NAM
This is not the real Download Button


Read / Download A JININSA YA KE Book 1

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .

START READING

OR

Login Register

This is not the real Download Button
Please Login or Register in order to submit comment

Releted Novels

Releted Album