Join Our WhatsApp Group

DEEN Complete Hausa Novel Document by DEEN


DEEN

Cover Design Copyright and attribute to Marus Graphics

Uploaded by @Taskar

Total Words: 333984



DEEN

Reading Time: 27 Hours

Added On: 26, Aug 2023

Author: Aisha Ashanty ,

Ebook Compiler : Admin

Author Group : Unknown group

Author Phone : Not Inserted

Book License : Free

Category: Love Novels

File Size: 1.94 mb

File Type: txt

Views: 3274+

Download: 3360+

Last download: 6 days ago

Description/Story: *DEEN*


(The heartbreak💔)

An amazing love story💘



Story written by Ashaanty love💖

Marubuciyar
_AUREN KWANGILA_



_Am back again! Alhamdullilah!🧚🏻‍♀️_




*001*




_"So let me know, if you no wan do again, I no go disturb you, I no go hold you!... Let me know uwo uwo if you no wan do again, I no go disturb you, I no go hold you... But no call me back oo, no call me backkk! When you see sey I dey with another person, baby no call me back oo, no call me baaaack when you see sey I dey with another gele..."_

Kpaaam! Kpaaam!! Kpaaam!!! Aka sake bubbuga kofar toilet din kamar za'a 6allata

Inaa? Batama San anayi ba saima qara volume din muryarta datayi tana bin waqar dake tashi a earphones din kunnenta
_"Even if you call e no go connect, cos I no go dey, I no go dey make you forget, come another day..."_ tafada tana lallauye jikinta kamar wata macijiya tana shashafa jikinta dake lullu6e da kumfa cikin wani irin salo

Qara bubbugo kofar akayi da wani mahaukacin qarfi wanda saida taji qarar dukda earphones din kanta

Saurin waigawa tayi ta kalli kofar tana zame earphones din kanta a lokaci daya

"Wai don ubanki bazaki fitoba!!" Aka fada daga waje ana qara bubbugo qofar

Wara manyan idanuwanta tayi kamar zasu fado daga raminsu sannan tashiga dauraye jikinta cikin rawar jiki

*"ZAINAB!"* aka sake kwala kira daga waje, daga ji kasan mammalakin muryar amatuqar fusace yake

"Na... Na'am mummy, wlh yanzu zan...fito" tafada cikin rawar murya tana jawo towel dake rataye a hanger ta daura ba don ta ida dauraye jikinta ba ta sauko daga bathtub din ta nufi kofar cikin 6arin jiki

Kallon kofar take a tsorace tama kasa kai hannu ta bude saboda tsoro

"Wai bazaki fitoba?!" Aka sake fadi cikin tsawa wanda har saida ta zabura

Hannu na rawa ta zare sakatar kofar tana yin saitin gudu

Banko kofar tayi da karfi itama tayo waje aguje tana callara ihu cikin zazzaqar muryarta

Mummy datayi baya baya saboda bangajeta da Zainab tayi tayi saurin dafa wani qarfe dake gefe wanda ba don shi ba da tuni tajita qasa

Zainab kau tana fitowa, waje tayi ido rufe tana sake fasa qara tana kiran sunan Daddy

Bata damu da abinda ke jikinta ba ta sauka qasa da gudu hannu dafe da guntun towel din jikinta ta ratsa yan aikin dake falo suna karakaina

Duk dakatawa da abinda suke sukayi suka juyo atsorace suka bi *MADAM* da kallo cike da alhinin meya biyota

Basu qarasa tunanin zucinsu ba suka samu amsa don *HAJIYA* ce sukaga itama tayo qasa cikin gudu gudu sauri sauri, cable din chaza a hannunta tana kwala kiran Zainab ganin haka zata fita waje

Saurin sunsukuya kai sukayi hartazo ta ratsasu itama tafice sannan suka dago suna girgiza kai na takaicin halin *ZAINAB*

Zainab kau haka ta ratsa ma'aikata dake harabar gidan cikin gudunta wanda hakan yasa duk cinyoyinta suka fito waje, ma'aikatan sai binta da kallo suke amma ita ko ajikinta, itadai burinta ta cinma part din daddy kafin mummy ta kamata don tana jinta abayanta

Ganin mummy ta fito yasa dukkan ma'aikatan dasuka bi Zainab da kallo saurin kame Kansu suna gaidata cikin girmamawa

Babu wanda ta ko kalla sai nufar part din daddy datayi kamar zata tashi sama


Zaune yake yayi balancing a kan wata lumtsetsiyar kujera yayi bake bake yana kallon abinda managern shi ke nuna mashi a laptop

"Daddy! Wayyo Allah nashiga uku!" Suka tsinkayi muryar Zainab hakan yasa duk suka dago alokaci daya suna kallon kofar shigowa

Banko kofar akayi, sai gata ta dirko kamar wacce aka tillo

Kafin kiftawar ido harta qaraso gaban Daddy ta danneshi tana qara cikwikwiyeshi

Iya rudewa Daddy ya rude don sosai take kurma ihu gashi taqi bari ma yatashi zaune bare ya tambayi abinda ke faruwa, tawani qanqameshi tana ihu kamar wacce ake yankawa


Manager kau tsaye yayi agefe yana Kare mata kallo qasa qasa yana lasar le6e ganin yadda duk rabin fresh boobs dinta ke waje ga santala santalan jajjayen cinyoyi mallam

Shigowar mummy yasashi saurin shiga taitayinshi yayi qasa da kai

Ganin shigowar mummy yaqara volume din ihun Zainab tana qara maqalqaleshi cikin 6arin jiki

Sai a sannan shima Daddy yasan meke faruwa hakan yasashi dagowa ya zubamata idanu cikin fushi

Kallon da mummy tayiwa manager yasashi saurin daukar laptop din gaban Daddy ya rufe ya kwashe tarkacenshi yayi musu bankwana cikin girmamawa yayi waje

Fitarshi keda wuya mummy tayo kansu Daddy gadan gadan wanda hakan yasa Zainab sakin wata mahaukaciyar qara ta cusa kanta a qirjin Daddy jikinta na rawa

Ganin hakan yasa Daddy maidata bayanshi yayimata tsakani da mummy yana kallon mummy cikin huci

Mummy kau mazuranshi da siracinshi be hanata qoqarin jawo Zainab dake la6e a bayanshi ba

Qara kareta yayi yana riqo hannun mummy yafara magana cikin 6acin rai
"Wai Maimuna meke damun kwalwarki ne?!"

"Hauka ke damunta! Nace hauka nake, wlh yau babu mai hanani illata wannan shashashar anan!" Tafada tana qara yunkurin kamo Zainab dake bayan Daddy tana kuka sosai

"Saiki illata ta din! Nace ki illatata! Wai Maimuna kanki daya kau? Kibiyo Yar qaramar yarinya da gudu da wannan lafcecciyar wayar a hannu, nufinki me to? Badai nufinki akanta zaki dora wannan tsinnaniyar wayar ba?" Yafada rai 6ace

"Qaramar yarinya? Did you just called Zainab yarinya? Macen dake cikin shekara ta ashirin da daya? 21 ba 12 ba! Ace batasan daidai da rashin daidai ba? Bata iya ware fari da baqi? Kaikuma bakada aiki sai kareta? Bakada aiki sai lallata yarka da kanka!" Tafada cikin tsananin 6acin rai hawaye na kawomata

"Yanzu me tayi kuma dazaki biyota dagudu kamar wata qaramar yarinya riqe da wannan uwar bulaliyar kamar ta bugun jakki? Anya kinada tausayi? Yanzu da kin samu riqeta da zubamata ita zakiyi ko? Don rashin imani irin naki, wlh ba don agida kika haihu ba kuma kuna kama da jewel da wlh nace ke ba uwarta bace, 'ya guda tilo da Allah yabamu duniya da lahira shine zaki kashemana ita? Inbanda abinki duka nawa take dazaki dinga addabar rayuwarta haka? To wlh baniso, banaso! Karki sake min haka don ban hada diyata da kowaba kuma zan iya yin komai akanta, idan ke baki sonta to ni inason abuna" ya qarashe yana huci sosai

Mummy da tun lokacin daya fara zuba ta kafeshi da idanunta dake digar hawaye ta sa bayan hannunta ta share hawayenta ta saki wayar chazar dake hannunta ta juya tanufi hanyar fita afusace ta fita tana rufo qofar da qarfi

Wata wawiyar Ajiyar zuciya suka sauke mai nauyi bayan sun rakata da kallo

Komawa da baya Zainab tayi tafada kan kujera tana maida numfashi ahankali tareda furzo wata zazzafar iska daga baki

Daddy da duk jikinshi yayi sanyi ganin yanayin da mummy ta fita ya nemi guri kusada Zainab ya zauna ya miqa hannu ya jawota jikinshi

"Baby na, hope dai kina lfy?" Yafada cikin tsantsar kulawa

Fizge jikinta tayi daga riqonshi sannan tafara magana cikeda tsiwa
"Inafa lfy Dad? Ni wlh Allah yasani wannan Matar ba qaramin takurawa rayuwata tayi ba, can you imagine wai dukana zatayi? Yanzu data samu damar kamani fa dukana zatayi, am almost 21 amma ban girmi dukaba a gidanmu, imagine" taqarashe tana girgiza Kai fuska a yatsine

Qara rungumota Daddy yayi cikin sigar rarrashi yace
"Shiiii... Ya Isa haka, nayi maki alqawari zanyiwa tufkar hanci"

Cikeda rashin kunya da tsantsar sangarta tace
"Yaushe? Tun yaushe kake cewa haka amma abu ya gagara? Ni wlh haryanzu ban yarda wannan matar uwata ce ba, matarda kwata kwata bata qaunata? Ta tsani ta ganni cikin walwala da annushuwa, duk hanyar datasan zatabi domin daqile farincikina tasanshi, komai na duniyar nan idan nayi to ba daidai bane, tasamin ido tasamin hanci da baki, kai wlh nagaji, ace agidanku bakada freedom? A matsayina na diyar *Alh. Farouq Dan faranshi* diyarshi daya tilo ace banida freedom? Gasu kucakan friends dina wanda ko kwatan arziqinmu basu dashi suna life dinsu yadda sukaga dama, suna living free live babu takura, saini daddy? Saini the whole *ZAINAB FAROUQ DAN FARANSHI?*" ta qarashe zancen tana sakin kukan ta6ara

Qara rungumeta yayi sosai yanajin kukanta na ta6a Mashi zuciya sosai

"It ok Darling, Dan Allah ki daina kukan nan kar yajamaki wani ciwon, insha Allah zanyiwa tufkar hanci ok?"

"Till when Dad? Nace ka kaini abroad na qarashe karatuna ka qiya, ka biye mata kun Sani a wannan Yar iskar makarantar da duk tarin yan jagaliya ke ciki, kai shikenan duk abinda mummy tace saika biyemata, da farko ka yarda zaka kaini UK karatu amma daga ta janyeka daki tayimaka karatu saika chanza magana, wai Umaru Musa Yar adu'a, wai kamar ni a UMYAU, mtcheew!" Taja tsaki cikeda rashin kunya

Ajiyar zuciya Daddy ya sauke cikin rashin sanin tacewa saikuma can yace
"Yanzu dai it ok, banason ganinki a 6acin rai wlh, hankalina tashi yake, and batun karatu abroad bawai don mummynki ta nuna batasoba yasa nafasa turaki canba, kawai baxan iya jurar zama na tsawon wasu lokutaba batareda na sanyaki a ido ba, Zainab kema kinsan ina qaunarki sosai banason ko quda ya ta6a min ke, kece rayuwata kece fitilata, ke kadai zan Kalla naji sanyi a zuciyata, be kamata kina tadamin hankali da fushinki ba, am sorry uhm? Insha Allah zan tabbatar kinsamu freedom dakike buqata, uhm?" Yafada yana qara tausa murya

Zainab da tunda yafara magana tayo gaba da baki cikin sangarta tace
"To daddy, yawuce amma please kayi warning dinta ta sakarmin mara nayi fitsari"

Dariyar jindadi Daddy yayi yace
"Ki kwantar da hankalin ki ok? Insha Allah zanwa tufkar hanci... Yanzu kije kisaka kaya kinga towel kawai ke jikinki, ga gashin ki ajiqe halan baki dade da fitowa daga wanka ba?"

"To Ai daddy fitowar kenan, kawai ina cikin wanka naji ana bubbuga kofa kamar za'a 6alla, wai _Don ubanki bazaki fitaba_ inajin hakan nasan muguntar ta motso kenan shiyasa ina samu na bude na arto aguje" taqarashe tana kyalkyala dariya


Shima daddy biyemata yayi shima yana kyakyata dariyar sannan yace
"Maimuna? Ai halinta sai ita, yanzu dai rabu daita Babyna ki tashi kije kisa kaya kar sanyi ya kamamin ke"

Kwalalo idanu tayi tana cewa
"Inje ina insa kaya? Ca6! Sokake nakai kaina da kaina taji dadin farfesuna bare dama ka qara kunnata? Ca6!" Ta qarashe tana rungume hannayenta a qirji ta koma ta jingina da kujera tana karkada kaffafu

"To yanzu ya za'ayi?"

"Kawai kaimin shopping din kayan dazansa online don daga nanma school nayi don babu tsotsan dazai zaunar dani"

Murmushi Daddy yayi yana girgiza kai sannan ya dauki daya daga cikin wayoyinshi dake kan stool din gefen kujerar dayake kai zaiyi yadda tace

Fitt... Ta fige wayar daga hannunshi tana cewa
"Ni zanyi, kana iya yimin wanda bemun ba" tafada hankalinta nakan wayar

Maimakon yaji haushi saima murmushi daya saki yana girgiza kai

Saida tagama danne dannenta sannan ta cilla wayar a dayar kujerar dake gefenta ta miqe daga ita sai guntun towel din tana miqa mai tafe da hamma babu ko kare baki🤦‍♀?

"Daddy yunwa" tafada kamar zatayi kuka

Tashi shima yayi yana cewa
"Muje ga abinci can dining ba'ama dade da kawowaba ko budewa banyiba"

Binshi tayi tana so6are baki

Shi da kanshi yayi serving dinta ya dinga bata sai zubamashi shagwa6a da ta6ara take shikuma yana biyemata

Koda suka kammala har an kawo kayan datayi shopping

Ledar kayan daddy ya bata ta fizge tanufi sama da gudu gudu tsalle tsalle

Binta da kallo yayi sannan ya girgiza kai yana murmushi, yarintar diyarshi na qara burgeshi😒

Saida yaga hayewarta saman sannan shima yajuya yafita don zuwa lalla6o Yar matarshi don yasan haryanzu tana can tana kumburi



Saida tadauki fin awa asaman sannan tafito

Kallo daya zakayi mata kafara tantamar anya musulmace?

Sanye take da yellow din top ta roba mai dogon hannu rigar ta mugun lafe a fatarta har ana hango shatin bra dinta

Ta cusa rigar cikin high waist red skinny trouser dinta taci zanzaro, wandon yayi mugun dameta gashi iyakarshi idon kafa
Sai Ta Dora Farar After Mai Adon Red Stones Akai

tasha baby shoes red sai dan siririn yalolon gyale shima jaa data yafama kai wanda ana hangen tulin gashinta ta gyallen don shara2 ne sosai

Fuskarnan tasha heavy makeup sai shining take, hannunta daya rataye da wata guntuwar jar side bag dayan kuma riqeda faskekiyar wayarta


_yes! Am the princess of the sacred kingdom who rule the life and deathhh_

_am the Queen of the ocean who shines through the rays_

_am the fairly girl in the fairly tale of wonderlandddd_

_so keep calm... Cos the ruling is mineee_

Da wannan waqar ta sauko qasa ta nufi hanyar waje, bata ko damu da rashin ganin daddynba a falon ta fice

Tun kafin ta qaraso drivernta yataso da gudun tsiya yazo ya budemata kofa

Da waqarta ta iso motar, bata amsa gaisuwar da Bala driver kemata ba sai antayen matsiyacin kallon datayi mashi ta shige motar

Maidawa yayi yarufe ahankali sannan yazagaya dagudu ya bude mazauninshi

Ganin hakan yasa security saurin wangale musu tangamemen gate din, suka so suka gittashi suka fice yana daga masu hannu...✍️

Ya kukaga kafcen😎


Yawan comments dinku zaiyi determine cigaban littafin, make me go gaga with your comments yadda zan zubomuku flows of updates💃


Ummin fasihu🧚🏻‍♀?
8/2/21, 9:31 PM - Buhainat😝: *🙍🏻‍♂️🙍🏻‍♂️DEEN🙍🏻‍♂️🙍🏻‍♂?*
(The heartbreak💔)

An amazing love story💘

Story written by Ashaanty love💖



*002*




"Haba Maimuna? Be kamata akan qaramin abu kizo kina dacin rai ba, idan kika duba duka nawa Zainab din take? Kamata yayi ki dinga mata uzuri akan duk abinda take, nan gaba ko ance tayi baxatayi ba, kowa da kalar quruciyarshi, don Allah ki dinga dagama yarinyarnan qafa kinji?" Ya qarashe cikin sigar rarrashi

Ajiyar zuciya mummy ta sauke bayan ta gama hadiyar qululun takaicin daya tokare mata wuya tace
"Yanzu alhaji laifine don uwa ta kwa6i yarta? Karka manta fa Zainab macece, ko babu komai aure zatayi watarana, yanzu a tunaninka wa zai iya tolerating din nonsense dinta? Yarinya ace kwata kwata bataji? Koda yaushe abinda taga dama shi takeyi? Bata san daidai da akasinshi ba amma kai a matsayin wadda xaka tsawatar mata bakada aiki sai tunzurata? Wannan a tunaninka soyayya ce? Wannan ba soyayya bace ba alhaji, wannan salon sangarci ne da 6ata tarbiya, kai kullum gani kke kamar na tsaneta ne har cewa kake da ba gida na haihu ba da kace ba 'yata bace, yanzu tsawatarwa yaro yazama laifi. Idan banso Zainab ba amatsayin ta na 'ya talin qwal da Allah yabani was zanso? Inasonta kwatankwacin yadda kake ganin kana sonta koma fiye da hakan amma hakan baya nufin zan barta ta lallace kamar batada mafadi, karka manta bakin da karya kewa danta wasa dashi watarana dashi take cizonshi idan yayi ba daidai ba"

Zama yayi kusada ita ya rungumo kafadarta yace
"To shikenan zan kiyaye, ki saki fuskar hakanan, ni wlh tur6una fuskar ne baniso, indai baby ce zan mata magana bazata qaraba"

Dan ta6e baki mummy kawai tayi batareda tace komaiba

"Smile mana" yafada yana leqen fuskarta

Dauke kai tayi saikuma ta tashi daga zaunen datake daga gefen gado tace
"Yanzu muje kayi break din" tafada fuska babu walwala

Tashi shima yayi yace
"To da girman kujeranki, Ai yadda kika ce hakan za'ayi gimbiya" yafada yana dariya

Itadai gaba tayi don she's not in the mood


******


Danno kai qossashiyar motarsu Zainab tayi cikin harabar makarantar.

Tun shigowar motar yan tsirarun mutanen dake wajen suka karkatar da hankalinsu gareta...


Read / Download DEEN

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .

START READING

OR

Login Register

Please Login or Register in order to submit comment

Releted Novels

Releted Album