Subscribe for N1000/month for downloading access and an ad-free site. Contact WhatsApp +2348140419490 if you can't pay / subscribe. SUBSCRIBE

24 yin

AUREN HAƊI Complete Hausa Novel Document by AUREN HAƊI


AUREN HAƊI

Cover Design Copyright and attribute to Marus Graphics

Uploaded by @Taskar

Total Words: 74552



AUREN HAƊI

Reading Time: 6 Hours

Added On: 13, Nov 2024

Author: Sameera Harouna ,

Ebook Compiler : Admin

Author Group : ZAMAN AMANA WRITER'S

Author Phone : Not Inserted

Book License : Free

Category: Love Novels

File Size: 397.77 kb

File Type: txt

Views: 1074+

Download: 2939+

Last download: less than 1 second ago

Description/Story: 24/10/2018 à 22:00 - Vous avez créé le groupe “👸PRINCESSE👸”
27/02/2019 à 17:29 - Mamar Latif💃: 💑 AUREN HA'DI💑

_Samira Harouna_

*Wannan labari ne da na yishi a farkon fara rubutu na, amma abisa wasu kura kurai da ke cikin waccen rubutu sabida rashin sanin miye rubutu a waccen lokacin, hakan yasa zan sabinta maku shi ta hanyar canza Salan rubutun da ingantashi fiye da na baya tare da canza wasu abubuwa daga ciki dan jin dad'in ku*

💗💗💗💗💗💗
Bismillahi Rahaman Rahim
💗💗💗💗💗💗

🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S*
( _Gidan zaman lafiya da_ _amana insha Allah)_ 🤜🤛

*Page*

1⃣-5⃣

Duk girman gidan bai hana shi cika ba sabida hidimar bikin da ake, kowa cikin farin ciki ya ke babu bakin ciki a nata hayaniya, shagalin biki kenan na auren da za'a d'aura nan da Minti Ashirin, Amare ne guda hud'u da angayen su.

ban an kara ba naji an bige ni har saida alkalamina ya fad'i k'asa, daga kai nayi naga ko wace shedaniyar ce, wata kosansan Budurwa na gani sai gudu take tana waiwayen bayanta kafin na kula naga wani 'Kakk'arfan Saurayi da gudu yana biyar ta da belt a hannu, bin bayan su nayi har cikin katon falon da ta shiga in da taci k'aro da wata kyakyawar tsohuwa ta b'oye bayanta tana fad'in,

"Dan Allah hajia ki taimake ni kice karya dake ni" tsaye yayi yana huci, cikin zafin ray ya kai mata duka da belt kin hannunshi yanda ya sauka a bayanta ne yasa ta saki k'ara tana Ihu, tsohuwar ce da ranta ya b'ace tace" kai SALMAN ashe ba kada hankali wai miyasa kuke hakane kamar wasu Kananan yara?" juyawa tayi ga yarinyar ta jawo ta tace" mi kika mashi nasan dai haka kawai baya biyo ki ba tunda ba mahaukaci bane shi?" cikin kuka ta fara mata bayani" wallahi hajia kawai muguntar sace ta tashi, daga naje karb'ar charger ta wajen yaya MUBARAK shine fa kawai yake kallo na daga nace ya kama bakin shine wai ya biyo ni" tana rufe baki ya kama kunnanta cikin masifa yace" kinji ko hajia dan ta raina ni ni zata ce wai na kama baki na, ina abin kallo a jikin ta yake, wallahi sai na karyaki in kika k'ara shiga harkata shedaniya kawai" fizge kunnen''ta tayi cikin zafin nama ta mike tsaye zatayi magana kuma sai ta ruga a guje sabida d'aga belt kin yayi zai buga mata, juyawa yayi shi ma yabar wajen.

Saïda tabi kowannen su da kallo kafin tace" na samu hanyar da zanyi Maganin ku tak'adaran yara kawai, kuna yan uwa amma kun zama kamar b'era da mage, Insha Allah Komai ya zo k'arshe daga yaou, idan kuka zama d'aya zaku daina duk, wannan shirmen" wuce wa tayi d'akin kakan yaran inda bata gushe'ba har saida burin ta ya cika.

09:00 aka d'aura auren Amare guda hud'u gami da wadanda aka kara suka zama biyar.

*to yan uwa ya zata kasance idan aka d'aura auren wadanda babu su a cikin jadawalin d'aurin auren yaou?*

Yan Uwa kuna san labarin in'ci gaba?


~Sai naji daga gare ku.~
27/02/2019 à 17:29 - Mamar Latif💃: 💑AUREN HA'DI💑

_Samira Harouna_

*page*

0⃣6⃣-1⃣0⃣

🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S*
( _Gidan zaman lafiya da_ _amana insha Allah)_ 🤜🤛

Sank'ira ne ya fara fadin"(masha Allah, Allah ya nuna mana an d'aura wannan aure na amare da angaye, aure na farko shine tsakanin,Mubarak Siraj Manu da Nadiya Yahaya Manu, na biyu tsakanin Khamis Yahaya Manu da Jawahir Suleiman Manu, na uku shine tsakanin Shamsudeen Suleiman Manu da Hafsat Siraj Manu,sai na hud'u tsakanin Nouradeen Salihu Manu da Khairat Yunus Manu, sai na biyar tsakanin Salman Yunus Manu da amaryar shi Zeinab Abdul-Hamid Manu wato (Ummi)."

Shiru ne ya ratsa illahirin mutanen da ke wurin dan jin aure na biyar,Kallan kallo kawai a keyi saida kowa ya tabbatar sannan aka fara farin ciki, wasu da hukuncin bai masu ba kamar zasu fashe dan bakin ciki Hajara uwar gidan baba yahaya taso ace an had'a Salman da Rumana dan taci buri akan auren su, Ummi da ke d'aki ta nata tsokanar su
Jawahir tana masu shegantaka, yayarta SA'ADATOU da RUKAYYA yayar Jawahir suka shigo suna Bud'a suna murna a nanfa suka fad'a masu halin da ake ciki, Ummi da tak'i yarda fitowa tayi tsakar gida tana tambayar Mahaifiyar ta wato HAWATAN(Hawaou) kasancewar ta buzuwa yasa ake kiranta da Hawatan, tin'da tace" eh Ummi da gaske an d'aura aurenki kema" cikin nuna rashin yarda tace" haba la mamma ta yaya za'a d'aura aure na haka kwatsam ai ba haka ake ma kowa ba sai ni za'a fara kai na?" hannunta ta d'ora a kafad'unta tace" kinga kiyi hak'uri kinji wannan hukuncin kakan kune, kuma ai ba yaou zaki tare ba ke" jaye jikin ta tayi tana fad'in" a'a la mamma hakan ba zaiyiwu ba miyasa sai yaya Salman za'a aura min"? da gudu ta koma d'akin da amare suke ta kwanta ta fara ai kin kuka kamar ranta zai fita, k'awayenta kuma yan uwanta sunyi ban hak'urin amma ina sun kasa dan haka suka rabu da ita.

tunda a kace Ummi na kuka hajia Babba tace a k'yaleta zata ji da ita, d'akin ta shigo ta tayar da ita zaune saïda tasa ta daina kukan sannan ta fara magana cikin nutsuwa da dubun hankali" Zeinab ki nutsu ki saurare ni kiji abinda zan fad'a maki kinji shaleleta"Ummi shi aure da kuke gani darajar shi ce tasa Ubangiji ya hallata shi a tsakanin bayin'sa, darajar aure da kuke gani tafi Karfin tinanin ki sabida daraja da matsayin shine yasa hatta bishiya zakiga an mata aure kafin ta fara toho, sannan aure sunna ce mai k'arfi daga sunnonin Manzo ( S A W ) kuma duk wanda ya raya ta to ha'ki'ka zai samu babban rabo, sannan aure ya nada matuk'ar mahimmanci a rayuwar mu wanda idan da babu shi da Ummi bana jin da yanzu akwai Duniya dan bad'alar da za ayi ba kad'an bace a Sakamakon haka kuma Allah Zai iya kifar da duniyar ma Baki d'aya"

" Ummi wani abun farin ciki anan shine duniyar nan munacin Albarkacin Annabi Muhammad (S A W) ne sannan yara ma suna taka rawa a cikin rangwamen da Allah ya keyi mana, to yanzu Ummi in har hakane mi zaisa ki k'i aure har ki tsaya kina bata lokacin ki wajen kuka, ke da zaki samu wannan manyan mayan rabon, Bugu da k'ari kuma Salman dan uwanki ne kinfi kowa sanin tsakaninki da shi, nice nan na haifi iyayen'ku maza da ke da shi to miye matsala a ciki, nasan dai za kice sabida ba bakwa shiri ne da shi, wannan kuma mai sauki ne In har ki kayi abinda zan fad'a maki" share Hawaye tayi tace"hajia a gaskiya ba'amin Adalci ba, ta yaya za'a d'aura min aure da mutumin da Kusan tsakani na da shi kunsan mugu ne shi ko kad'an ba yada tausayi" kai ta girgiza tace" kash, Ummi ina baki kina rok'o, Salman fa ba kamar yanda kika d'auka bane kece kawai kike masa Kallan mugu shi ma kuma ke kike ja ma kan ki sabida kinsan abinda baya so amma se kika maida wannan abu kamar 'dabi'arki duk lokacin da kika gan shi sai kinyi" amma hajia to miyasa za'a aura min shi ni gaskiya bana san shi?" Ummi kiyi Hak'uri kamar yanda nafad'a maki, idan har kika yi hak'uri kika bi Umarnin mu to basai na fad'a maki ba kisan za kifi kowa jin dad'in Alhaji, amma in kika ki kika bijere tofa kinfi kowa sani wallahi zaki shiga matsala" Ummi ke da Salman duka jikoki na ne naji dad'in wannan HAD'IN AUREN dan ba'ataba irin Shi, ki kwantar da kanki ki zauna lafiya da dan uwanki kiyi masa biyayya domin yanzu shine k'ofar shigar ki Aljanna, kiyi duk abinda yace in dai kina so ki rabauta Duniya da Lahira, ki kyautata mashi idan kina so Allah ya yarda da ke ya saki a cikin bayinsa mafifita, ki zama mace ta gari a wajan Mijinta ki zama mace mai biyayyar aure ki zama yar Aljanna" bayanin da Hajia tayi gaba d'aya amaren sun k'aru da shi kuma sun d'auka saidai a wajan Ummi ba haka abin yake ba.


Tunda Salman yaji sunan sa ya fito a cikin wannan résult wanda shi a wajan shi kamar an kafe sunan yan wuta ne kuma sunan shi ya fito, rud'ewa da kid'imewa da tashin hankali ya ma rasa wanne ne a ciki ya shiga, zai iyya zama da kowace irin yarinya a duniya daga ciki har da karuwa amma banda Ummi dan kuwa yarinyar ta mugun raina shi hakan yasa ya tsane ta duk da suna yan uwa kuma makotan
Domin cigaba da karantawa sai ku downloading.
Yadda ake downloading na littafin: ku tabbata kunyi register da shafinmu sanna kunyi login, idan bakuyi register a kasa zakuga maballai guda biyu daya an rubuta LOGIN dayan kuma an rubuta REGISTER sai ku taba su kuyi register, daga nan sai ku yi subscription koda na naira 1000 ne, domin sai kunyi subs dinann ne kadai zaku iya dauko littatafanmu.

Ya ya akeyin Subscription namu : Bayan kun yi Login ko register daga kasa zaku ga wani jan maballi (button) an rubuta SUBSCRIBE sai ku taba shi zai kaiku inda zaku zabi package wato tsarin subs na ku da mu. akwai na wata guda, watanni biyar da shekara guda. da zarar kun zaba zai kaiku inda zaku biya kudin, wanda daga nan sai ku cigaba da downloading kawai abunku

ABUN LURA : duk wani littafi da kuka gani a shafinnan kyauta ne, wannan tsari mun zo da shine don mu samu hanyar da zamu iya rike shafin muna managing na shi, izan ku kayi subs na mu tamkar DONATION ne ku ka yi mana, ku ka bamu kwarin guiwa don mu ciagaba da kawo muku sabbin littatafai, amma duk wanda ya ga bazai iya ba toh zai iya karanta littafin kyauta a cikin shafinnan namu batare da ya downloading ba, kawai ya yi kasa zai ga Koren maballi (button an rubuta) START READING sai ya taba zai kaishi inda zai karanta littafin.

Sannan duk wanda yaga kamn wannan process din zai bashi wahala kai tsaye zai iya min magana ta whatssApp +2348140419490, ya tura min kudin ni kuma zan dora mai subs din akan account na shi

NB: iya ta haka ne zaku iya karanta wannan littafi a shafinmu babu wata hanyar. DAN ALLAH KU DAINA MANA MAGANA AKAN MU TURA MUKU LITTAFI TA WHATSAPP, BAMA TURAWA HANYA GUDA MUKE TURA LITTATAFANMU SHINE WEBSITE NA MU https://taskarnovels.com.ng DUK MAI BUKATAR LITTAFINMU YA JE CAN YA KYAUTA NE, AMMA DOWNLOADING KUWA BA KYAUTA BANE SAI YAYI SUBSCRIPTION NA WEBSITE NAM
This is not the real Download Button


Read / Download AUREN HAƊI

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .

START READING

OR

Login Register

This is not the real Download Button
Please Login or Register in order to submit comment

Releted Novels

Releted Album