Join Our WhatsApp Group

CIN AMANA KO FANSA Complete Hausa Novel Document by CIN AMANA KO FANSA


CIN AMANA KO FANSA

Cover Design Copyright and attribute to Marus Graphics

Uploaded by @Taskar

Total Words: 39410



CIN AMANA KO FANSA

Reading Time: 3 Hours

Added On: 07, Sep 2023

Author: Zahra Muhammad Mahmud Surbajo ,

Ebook Compiler : Admin

Author Group : Unknown group

Author Phone : Not Inserted

Book License : Free

Category: Love Novels

File Size: 241.24 kb

File Type: txt

Views: 705+

Download: 296+

Last download: 5 days ago

Description/Story: CIN AMANA KO FANSA
Zahra muhammad Mahmud
Made by:- Shuraih Usman
Ku shiga nan kuyi like na shafinmu http://fb.com/hausaebooks

[4/26, 10:10] Zahra Surbajo: 📓📓📓📓📓📓📓📓

*CIN AMANA*

*KO*

*FANSA*

📓📓📓📓📓📓📓📓

*(TRUE LIFE STORY )*





Zahra Muhammad Mahmud





® *PURE MOMENT OF LIFE WRITERS*

*PML*



*Godiya ga Allah mad'aukakin Sarki, tsira da Aminci sutabbata ga annabinmu Muhammad sallallahu ala'ihi wasallam.*



*Wannan labari ba k'agagge bane yafaru dagaske,duk abinda ke ciki anyine da gaske, suna kawai na wa'inda abun yashafa Nasauya,da d'an abinda ba'a rasaba.baya ga haka babu abinda Nasauya*



Ya Allah, yadda nafara rubuta littafinnan lfy,Allah kasa nagamashi lfy.





*page 1*





Y'anmatane su biyu, y'an kimanin shekara goma sha shida da haihuwa,suka rugo da gudu zuwa Cikin d'akin kakarsu suna ta kiranta, uniform ne ajikinsu, alamar daga makaranta suke,



"Grany!!! Grany!!! where are you? we miss you so much,mekika tanadarmana yau."

A zaune suka ganta tana Kallonsu, k'arasawa jikinta sukayi, suka rungumeta, kowacce tamata kiss a gefen kumatunta.



"Kai ni banason iskancinnan naku, ace gird'a gird'a daku Amman har yanzu baku girmaba,wato abinnaku gaba yakeyi,yau kuma harda sumbatata ko?".



Dariya sukayi suka K'ara rungumeta,Khairat ce tace,



"Haba Grany, danma kinsamu munzo gidanki yau shine harda yimana wulak'anci,ni dama wlh banso zuwa ba,Fatima ce da shegen naci tace muzo gidanki,gashi daga zuwanmu kinfara halinnaki."sakin Grany tayi takoma gefe tazauna,



Fatima tace, "Wayyo Sis kiyiwa Grany uzuri, bakiga se kallonmu takeyiba, alamun taji dad'in ganinmu, hala taji haushin bamuyi sallama bane, ko Grany?",tawaiga Tana kallon kakar tasu.



Grany dariya tayi sannan taruk'osu dukansu tace ,



"Haba kha'iriyya ta fushi kikeyi danine?, nicefa babbar k'awarki ranar bikinki,"dariyace takwacemusu dukansu,khairat tace,





"Wai,dagwargwajiya kenan Grany ansha gwargwaro ranar aurena,"cigaba sukayi da dariyar.



Ranar wuni sukayi agidan Grany,seda la'asar suka mata sallama suka wuce gida.





Khairat da Fatima sa'annin junane, dan anhaifi Fatima da Sati biyu aka haifi Khairat.



Iyayensu mata ya da k'anwane,haka zalika, Iyayensu maza suma wa da k'anine.





Alhaji Nasir Abubakar shine mahaifin Fatima,suna kiranshi da Abba,mahaifiyarta Mesuna Hajiya Salamatu suna kiranta da Umma.yaran Alhaji Nasir hud'u biyu maza biyu mata,Yaya Jameel shine babba, se Yaya Umar mebimasa,se Fatima, da autarsu Yasmeen.



Alhaji Mukhtar Abubakar shine mahaifin Khairat,suna kiranshi da Daddy, Wanda wa yake agurin Alhaji Nasir,uwa d'aya uba d'aya,

Matarshi d'aya Hajiya Binta,wacce take yaya ga mahaifiyar Fatima, yaransu guda shida,hud'u mata biyu maza,Aunty Fareeda Itace babba ,se Yaya Kamal mebimata,se Aunty Khadija,se Kha'irat, se Fa'eeza,da autansu Yusuf.



Gidan Alhaji Nasir dana Alhaji Mukhtar ahad'e suke sede katanga data rabasu,

Suna zaune da iyalansu agarin Kaduna awata anguwa Mesuna Tudunwada dede layin k'osai kan katagum road,



kansu ahad'e yake haka na iyalansu komai nasu tarene ko kasuwancin suma a tare sukeyi inda suke Saida kayan sawa kama daga na maza zuwa na mata, da yara, komai suna saidarwa a kasuwar checheniya dake Kaduna.



Zumunci ne me k'arfi a tsakaninsu inda ahalin yanzu babban d'an Alhaji Nasir yana auran Y'ar gidan Alhaji Mukhtar Khadija, harda yaransu guda biyu suna zaune a kinkinau dake Kaduna,ita kuma Farida wani ma'aikacin nepa take aure harda yaranta guda uku.



Rayuwar wannan family rayuwace mecike daso da k'aunar juna.



Grany,wacce sunanta na aynihi Hajiya Asiya amman jikokinta nace mata Grany,yayinda y'ay'anta da sirikanta kecemata Hajiya, Itace tahaifi Iyayensu maza,kuma a kakanninsu ita kad'aice tarage musu sauran duk sunmutu



Kha'irat da Fatima kansu ahad'e yake ko bacci tare sukeyinsa babu abinda ke rabasu suna matuk'ar k'aunar junansu ko kad'an ba'ajin kansu,ajinsu d'aya Boko da Islamiyya, suna da k'ok'ari sosai dan sotari twins ake cemusu,dan duk jarabawa sede suyi bracket, kowa cikinsu beson b'acin ran d'an uwansa.





Maman Yusuf

[4/26, 10:10] Zahra Surbajo: 📓📓📓📓📓📓📓📓📓

*CIN AMANA*

*KO*

*FANSA*

📓📓📓📓📓📓📓📓📓





Zahra Muhammad mahmud





*LOSING SOMEONE WHO DOESN'T RESPECT OR APPRECIATE YOU IS ACTUALLY A GAIN, NOT A LOSS.*





*pure moment of life writers*

*p.m.l*





*page 2*





Rayuwar Fatima da Khairat rayuwace mecike da son juna.



Khairat irin matannanne masu azababen kyau don ko daga nesa ka hangota kasan me kyauce,farace me hanci ga yalwar gashi tamkar indiya, komai da akeso ajikin mace Allah yabata,wannan baiwa da Allah yay matane yasa ta d'auki dogon buri akanta tanaji da wannan kyau da Allah yay mata shiyasa ko saurayi take burin me kud'i,in talaka yazo gurinta seyasha wulak'ancin dako a hanya yaganta baze sake marmarin kulataba,

har k'awayensu na makaranta sunsani shiyasa yanzu kirarin dasuke mata shine matar Manya,jin dad'i take insuka kirata da sunan.



Fatima nada kyau dede misali Amman bata Kama k'afar khairat ba,sede dirin halitta na y'a mace itama Allah yabata,batada da wulak'anci ga kowane ne yanuna yana sonta burinta de Allah yabata miji nagari.



Akan wannan halin na Khairat sunsha yin fad'a da Fatima sabida hakan,inkaji fad'ansu to akan wannan halin na Khairat ne Sam Fatima batason halin.





Yau ba makaranta dan haka su Fatima suka tsefe kansu sukaje Kitso,ahanyarsu ta dawowane wani me liffan yatsaresu,saurayine matashi ba laifi akwai natsuwa da kamala atattare dashi sallama yamusu,



"yan mata barkankude," yafad'i yana kallon Khairat da alamun ita yabiyo.



Khairat bata amsaba sema wata uwar harara data watsa mishi.Fatima ce ta amsa,



"barka kadai malam".



murmushi yayi sannan yace,





"Don Allah kuyi hak'uri da tsaidaku da nayi wlh son yar uwarkine yakamani tunda na hangota duk danaga ita ranta kamar beyi na'am daniba Don Allah kubani number d'inku da Address dannazo har gida nasameta,"yafad'i yana kallon Khairat.



"Dank'ari mune zamu baka address d'inmu harda number waya,to wlh bakaji da kyauba gwara tun wuri kanemi dede kai danmu ba sa'anninka bane dahar zaka wani ce kana sona Allah yakyauta wlh farashin gold beyi karyewar da za'ayiwa jaki mangala dashi ba,"tafad'i rai abace taja hannun Fatima da niyar suwuce subarshi, kwace hannunta Fatima tayi ta tsaya,itako Khairat gaba tayi abunta,cikin sigar tausayawa Fatima tace mishi,



"Don Allah malam kayi hak'uri wlh banji dad'in abinda tayi maka ba, kuma in zan baka shawara ka hak'ura da ita wlh tunda tanuna bata sonka banajin akwai abinda zesa tasoka kayi hak'uri kanemi wata don katsira da mutuncinka kaji,don Allah kuma kayafemata pls,"tafad'i cikin sigar rarrashi.





Murmushi yayi Yace, "bakomai baiwar Allah nagode dake kika saurareni, Amman kinsan sharrin so wlh jinake bazan iya hak'ura da ita ba kitaimaka kibani address d'inku da sunanku pls banak'i shawarar ki bane zuciyata ce bazata iya hak'uraba ki taimakamin pls",yafad'i kamar zeyi kuka.



Ba musu Fatima tabashi abinda ya buk'ata dan ta tausaya mishi daga k'arshe tamishi fatan alkha'iri, dazasu rabu yafad'a mata sunanshi Ahmad.



A hanya tasamu Khairat se cika take tana batsewa kotakanta bata biba sabida inda sabo tasaba da halinta, ahaka suka ci gaba da tafiya bamecewa kowa uffan.



Suna shiga gida d'akinsu suka wuce dan ajiye hijabansu ananne Khairat tacewa Fatima,



"Wai don girman Allah sis se yaushene zaki gane darajata tafi k'arfin irin wa'innan samarin? kina zubarmin da ajina wlh ni matar manyan mutanece,yakamata kigane har yanzu ban samu kalar mijin daya dace daniba, amman ke da Kare da doki kowama address d'inmu kike basu suzo su tak'uramin dan Wlh wannan ma nasan kinbashi address d'in watak'ila ma harda rakiyar phone number mitsss,"tayi tsaki ranta ab'ace.



murmushin takaici Fatima tayi ta dubeta tace,



"Sis kenan wani lokacin inkikayi wani abun senaga kamar ba'a family d'aya mukeba,dan de tarbiyya dede gwargwado iyayenmu suna bamu kuma sunsamu a makarantun da ake koyar damu sanin darajar d'an Adam.Haba Sis kituna fa Allah dakanshi yace yakarrama bani adam kewacece dazaki dunga wulak'anta mutane?,kituna Allahn daya baki kyaun dakike wulakanta mutane sabida shi shine yayi kuma wainda kike wulak'antawar bayan yahanemu dayin hakan, tabbas nabashi address sede inyazo shima ki koreshi kamar yadda kika saba,ni narasa mekike nema aduniyar da watarana ko labarinki baza'aji acikintaba, haba Sis yakamata ki farka daga wannan banzan mafarkin dakikeyi."



"Mafarki fa kikace Sis to wlh kece kike mafarki ni reality show nake yi, koma mezakice naji amman wlh babu yadda za'ayi nakai kaina gidan talauci sede kita fad'in abinda kika dama,kuma wlh shima wannan dakanshi ze kama kansa dan bade niba sede wata wlh."kiran da Umman Fatima tai musune yasa suka bar maganar suka tafi gurin kiran.





Maman Yusuf

[4/26, 10:10] Zahra Surbajo: 📓📓📓📓📓📓📓📓📓

*CIN AMANA*

*KO*

*FANSA*

📓📓📓📓📓📓📓📓📓





Zahra Muhammad mahmud





*Pure moment of life writers*

*pml*





*Page 3*





Yau Ahmad yashirya yazo gurin Khairat hira, dakyar tayarda tafito koda tagashine me kirannata wani uban tsaki taja gami dayimasa kallon uku saura kwata,Shiko se Murmushi yake adole ze saci zuciyar ta tun kamin yay magana tarigashi,





"Amman duk yadda akayi agidanku cikin tumaki kake kwana Shiyasa zama dasu yasa kad'auki halinsu,kai jakin inane nace ma bana sonka bana k'aunarka Amman sabida taurin kunne irin na balama yasa kabiyoni gidanmu wlh baka da zuciya sam ni matar manyan mutanece ba irinka ba ubanme kaci ubanme Kabani dan haka kaje kanemi dede kai d'an wahala kawai",ta fad'a tana tsartar da miyau.



Zuciyar Ahmad kamar zata fashe sabida bak'in ciki,tunda yake wani mahaluki betaba cimishi mutunci irin hakaba se yau,hannu yad'aga ze kifa mata Mari sekuma yafasa.



Wata shewa tayi sannan tace,"hattarade d'an samari ni ba irin wa'innan matan bace da ake duka wlh ka kuskura katab'ani sekayi danasani wawa kawai,



Dakyar ya iya cemata,



"Ni acikin tumaki nake Kwana amman wlh bantab'a tsammanin tumaki suna haifar y'ay'an mutum ba se akanki,baki da hankali bakisan darajar mutane ba Kije duniya ce zaki had'u da dede ke komai daran dad'ewa,yana gama fad'amata haka yaja liffan d'inshi yabarta atsaye baki bud'e. Dagudu tashige cikin gida tana kuka kai tsaye d'akinsu tanufa inda ta sami Fatima na kwance tana chatting a wayarta,fad'awa kanta tayi tana kuka, afirgice Fatima ta ruk'ota sabida batasan damuwar Khairat ko kad'an in akwai abinda kesata damuwa toshine ganin hawayen Khairat,arud'e take tambayarta,



"Sis keda waye don Allah Ki sanar dani abinda aka miki zaki sani cikin damuwa pls",cikin kuka Khairat tace,

"Sis nida shegen Ahmad d'innanne yau ancimin mutuncin da tunda nake bawanda yatab'a yimin",tasake rushewa da kuka.



"me yayi miki just tell me",

Cikin kuka takwashe duk abinda yafaru ta fad'amata bata b'oye komai ba,duk da Fatima taji zafin kiran Iyayensu tinkiyoyi dayayi amman Seta daure tace,



"Wow that's good,gaskiya gayennan yaburgeni wlh inason mutumin dayasan darajar iyayensa, ke kin kira iyayensa tinkiyoyi why not baze kira naki da sunanba ?bayan kece kike aykata abinda kowa yagani ze d'auka tinkiyoyinne iyayenmu,ni wlh banji haushinshiba ke nake jin haushi sabida kece kika ja yazagesu,"





"Sis kinada hankali kuwa?, su Abba fa yazaga amman shine bakiji haushinshiba Lalle ma Sis wlh kinbani mamaki,"



Dariya Fatima tayi tace,tana k'ok'arin fita daga d'akin cikin dariya,



"Wayyo ga abin duka amman ba Kara Allah yataroki Sis",tak'arasa ficewa daga d'akin.





Ranar wuni Khairat tayi kuka dan takaicin zagin iyayenta da akayi,wanzami bayason jarfa dama.





Yau ana bikin wata k'awarsu acan cikin unguwar rimi GRA,dan haka Khairat shiri take kamar zata sauya fata dan kwalliya ita ala dole zata samu saurayi me kud'i tunda bikin manyane,Fatima dariya kawai takeyi tana mata fatan shiriya.



Sun isa gidan bikin k'arfe hud'u na yamma nanfa kawayensu aka shiga koda kyan da Khairat tayi habawa tuni tafara shan k'amshi ita ga me kyau Musammam insuka kirata da sunan datake matuk'ar k'aunar wato matar Manya kanta har girma yake k'arawa.



5:30pm suka tafi dinner zokuga Khairat yadda take tafiya kamar Bazata taka k'asaba ita adole zata jawo hankalin mutane kanta Fatima ko gaba tayi ta kyaleta.



Dayake k'awar tasu wani Reps ta aura to gurin dinner y'an majalisu ne sosai suka zo,anyi duk abinda akeyi agurin dinner inda aka bukaci Khairat da Fatima suyi jawabin godiya ga manyan bak'i ,kunsani base nafad'iba,khairat gwalli da iyayi bawanda batayiba me hoto se d'aukarta yakeyi ,har tagama Fatima ta amsa tunda Fatima tafara mgn hankalin wani d'an majalisa me wakiltar Kaduna south,yadawo kanta sosai ta burgeshi shigowarshi kenan yatarar tana mgn,beji Lokacin da Khairat tai nataba.



Koda aka tashi agurin dinner da sauri yasa wani excode d'inshi yakaiwa Fatima wayarshi yace tasa mishi number d'inta amman be fad'i kowaye yaturoshiba kawai yace wani bawan Allah, Fatima ba wulak'anci amsa tayi tasa number tayi flashing anata wayar,Khairat wacce haushin rashin kasuwar datayi yacikata Masifa tadunga yiwa Fatima akan me zata bada number d'inta ga wani banza,Fatima bata kulataba Illa janta da tayi su tafi gida,dagudu me hoton dayayi hotunan bikin yak'araso gurinsu gaishesu yayi sannan yafad'i abinda yakawo shi Wai Khairat yake so😜.ay Khairat rushewa Tay da kuka tashiga tsine mishi tunda yace yana sonta,Fatima ko inbanda dariya ba abinda takeyi dakyar tajata Suka tafi gida.





Maman Yusuf

[4/26, 10:10] Zahra Surbajo: 📓📓📓📓📓📓📓📓📓

*CIN AMANA*

*KO*

*FANSA*

📓📓📓📓📓📓📓📓📓







Zahra Muhammad Mahmud





*pure moment of life writers*

*pml*





*page 4-5*







Koda suka isa gida Khairat gaban mirror taje ta tsaya tana k'arewa kanta kallo,can kuma tasake fashewa da kuka ta fad'a kan gadonsu,Fatima wacce dariya tagama kamata da k'yar ta daure tace.



"Sis lafiyarki k'alau kuwa?, wai kukan me kikeyine haka?".



Cikin kuka Khairat tafara magana.



"Haba ki dubenifa wai ace duk had'uwar nan tawa manyan mutanennan bawanda yakalleni bare yace yana sona,nibama wannan ne yake sani kukaba more than 3hours nad'auka ina Kwalliyar nan Amman wai ace me hotone kawai na burge ay dole nay kuka,"taci gaba da kukanta harda majina.



Fatima ko inbanda dariya ba abinda takeyi sabida gaba d'aya takasa magana abun yabata dariya sosai. Fita Khairat tayi a d'akin sabida dariyar da Fatima take mata.



Tunda wannan D'an majalisa ya amshi number Fatima se yau ya gwada kiranta kimanin sati guda kenan da had'uwarsu,lokacin daya kira suna zaune ita da Y'ar darunta wato Khairat suna labarin wani littafi da ake rubutawa na online writers nawata marubuciya Zahra Muhammad mahmud me suna *Allah gatan bawa*.ajiyar zuciya Khairat tayi tace.



"Ya Ubangiji nima kasa nayi irin wannan dacen da jarumar littafinnan ilham tayi,nima nasamu miji kamar Anwar Tunda nima kyakkyawace",ta fad'i harda d'aga hannu sama,dariya Fatima tayi tace.



"Allah yataro minke Sister".



k'arar wayar Fatima ce takatse musu hirar,number tagani da kamar karta d'aga cande kuma ta d'auka,tace,



"Salamu alaikum".



"Wa'alaiki salam ya ma'abociyar natsuwa da hankali,".



Tsigar jikinta seda ta tashi sabida jin daddad'ar muryar me maganar, katseta yayi da cewa.



"Am sorry princess...


Read / Download CIN AMANA KO FANSA

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .

START READING

OR

Login Register

Please Login or Register in order to submit comment

Releted Novels

Releted Album