Subscribe for N1000/month for downloading access and an ad-free site. Contact WhatsApp +2348140419490 if you can't pay / subscribe. SUBSCRIBE

24 yin

KAMAR DA WASA Complete Hausa Novel Document by KAMAR DA WASA


KAMAR DA WASA

Cover Design Copyright and attribute to Marus Graphics

Uploaded by @Taskar

Total Words: 110202



KAMAR DA WASA

Reading Time: 9 Hours

Added On: 25, Feb 2025

Author: Ummi Aisha ,

Ebook Compiler : Admin

Author Group : HASKE WRITERS ASSO

Author Phone : Not Inserted

Book License : Free

Category: Love Novels

File Size: 638.76 kb

File Type: txt

Views: 176+

Download: 470+

Last download: 4 hours ago

Description/Story: [11/28, 08:14] Hafsat Rano: © _*HASKE WRITERS ASSO.*_


*KAMAR DA WASA....!*


_*NA*_

_*UMMI A'ISHA*_


_DA SUNAN ALLAH MAI RAHMA MAI JIN K'AI._



*1*


"Masu sauraro kamar kullum anan shirin namu zai dasa aya ayau kun dai ji mun tattauna akan wata babbar matsala wato ta yadda zakaga saurayi da budurwa sun kwashe shekaru suna gudanar da soyayya amma abin haushi arabu batare da anyi aureba shin laifin waye? Mazan ko matan? kafin inyi sallama daku ina mai janyo hankalin masoya da arike amana, gaskiya da kuma kulawa sannan aguji karya da yaudara domin hakan ba abune mai kyau ba sannan daya daga cikinsu yana raunata soyayya kuma ya illatata, anan zanyi sallama daku sai Allah yakaimu sati nagaba inda zaku jini acikin wani sabon shirin naku mai farin jini wato *Sakon na masoya ne...* kamar kullum nice taku mai gabatar da shirin wato *BILKISU LUKMAN ALIYU* Nabarku lafiya...."

Ahankali yake zare earpiece din dake kunnenshi sakamakon jin wakar _Sulken so...._ ta maye gurbin zazzakar muryarta, cikeda takaici ya kifa kansa asaman keken dinkin da yake zaune akai yana dinka wata kyakkyawar doguwar riga ta mata, tunani yake aransa yanzufa shikenan bazai sake jin muryarta ba sai wani satin indai ba shirye shiryenta na baya wadanda yayi recording zaiji ba domin hatta wannan wanda ta gabatar ayau ma yayi recording dinshi yana nan ajiye cikin wayarshi. Babu zato babu tsammani yaji wani abu saman sumarshi mai kamada almakashi, hannu yasa domin yakamo abin amma yaji anjanye ahankali yabude lumsassun idanuwanshi yatashi zaune, kamar yadda yayi zato husna yagani tsaye sai faman yi masa murmushi take, maimakon ya mayar mata da martanin murmushin da take yimasa sai ya daure fuska kamar ta kawo masa sakon mutuwa.

Bata damuba tabawa kanta masauki da wata kujerar roba wadda ke ajiye agaban keken dinkinshi, bata damu da yanda sauran abokan aikinshi wadanda ke zaune akan kekunansu suna gudanar da ayyukansu yanda zasu dauketa ba domin idan da sabo tasaba, zama tayi ta tallafe kumatunta da hannuwanta tana kallonshi kamar yadda yayi sai dai shi sam ba ita yake kallo ba domin yafada duniyar tunani.

"Prince..., Prince....ina dinkin yarinyar nan?"

Sai lokacin yadawo hayyacinsa sakamakon maganar tj abokin aikinsa da ta daki dodon kunnuwansa, gefenshi ya duba ya ciro wasu kaya acikin leda ya mika masa,

"Wai meke damunka fahad?"

Kallonta yayi adage sannan cikin rashin kulawa yace,

"Mekika gani fa?"

"To ai naganka ne kamar wani marar lafiya" tayi maganar cikin kalar tausayi,

"Lafiya ta lau..." Yabata amsa yana kokarin mikewa tsaye, wata leda ta mika masa tana langwabe kai,

"Please my prince ga uniform dina ka dinka min kaji"

Batare da ya kalleta ba ya karba ya jefa cikin wani kwali dake girke gefen kekensa,wani food flask dan madaidaici mai kyau ta sake mika masa,

"Ga abinci na kawo maka"

Karba yayi ya dora saman keken dinkinsa sannan ahankali kamar wanda tayiwa dole ya furta,

"Thank u"

Jingina tayi tana kallonshi shi kuma yana kallon wayarshi, babu abinda kake ji sai karar keken dinki wanda sauran abokan aikinshi keta faman aiki. Scissors din da ke ajiye kan kekenshi ta dauka ahankali ta kai kan tararriyar sumarshi,

"Inyi maka aski?"

Sake daure fuskarshi yayi yakai hannu ya doke almakashin,

"Kibari bana so, nafada miki bana son wasan banza"

Murmushi tayi tana sunkuyar da kanta,

"To kayi hakuri"

Baice mata komai ba yatashi da niyyar fita nan itama ta mike tana kallonshi ganin haka yasa shi yafasa fitar yawuce can wani lungu kusa da wata drawer ya kwanta, duk da tana son su fita tare amma haka tayi hakuri tawuce tatafi ba don taso ba.

Yajima kwance awurin yana jin sauran yan shagon sunata gulmarsa shida husna amma bai tanka ba har saida lokacin sallar la'asar yayi sannan yatashi,alwala yayi ya shiga masallaci duk da yana son ganin salim abokinshi amma sai yashare yashiga salla wanda acan din yahadu da salim din.

Yana fitowa daga salla keke napep yatare yanufi gida, atsakar gida ya iske mahaifiyarshi tana wanki koda yakarasa kusa da ita kamar yadda yazata kananan kayanshi take wanke masa.

"Ayiyah wankinne dai?"

Murmushi tayi tajuyo ta kalleshi,

"To ai ba komai nakeyi ba shiyasa nace gara inwanwanke maka sauran kayan ma na hadasu zuwa gobe zan bayar akai awanko maka"

"Godiya nake Ayiyah tah, Allah dai yabar min ke"

"Amin autana, maza kaje ga abincinka can a falo na tanadar maka"

Yunkurawa yayi ya mike daga tsugunnen da yake hakan yayi daidai da fitowar mamu,

"D'an nema kadawo ashe?"

"Hajiya mamu wallahi nadawo, kina daga ciki kenan?"

"Andai ji kunya, gandamemen saurayi dakai amma baka iya wanki ba"

Kafin yayi magana ayiyah tayi caraf ta cafke zancen ta hanyar bawa mamuh amsa,

"Tunda yana da masu yimasa ai ko ya iya bashida amfani"

Wata shewa mamu ta saka tana karasowa inda suke,

"To nidai naga yanda za ayi duk ranar da akayi masa aure"

"Yakuwa za ayi? Matarsa ce zata rinka yimasa"

"Idan ta iya ko?"

"Sai ta koya" inji ayiyah, jan yar karamar kujerar tsugunno mamu tayi ta zauna kusa da ayiyan, shi dai bazai iya cigaba da kallon wannan dramar tasu ba shiyasa yawuce dakin ayiyah fuskarshi shimfide da murmushi domin idan da sabo yasaba ganinsu ahaka kusan tun tasowarsa ahaka yake ganinsu bai taba jinsu suna fada ba kai idan baka saniba baka taba cewa kishiyoyine dan ko yanzun ma da suka gama wannan rahar hira ya jiyosu suna yi kuma da alama wankin mamuh take taya ayiyah. Zama yayi saman daddumar dake shimfide cikin falon yasoma bude kwanukan dake jere reras awurin wanda yasan shi aka tanadarwa domin kullum haka ayiyah keyi masa kamar wani mai gida, funkaso da miyar taushe yagani sai shinkafa da wake da manja da salad sannan ga zubo nan mai sanyi da kankara aciki cikin wani madaidaicin jug, hannun riga ya nade yasoma zuba shinkafa da waken domin kusan abubuwan nan na soye soye irinsu waina, sinasir, funkaso duk ba damunshi sukayi ba dan haka yazage yaci shinkafa da wakensa yayi dam yasha sanyayyen zobonshi daga haka ya mike ya fito,su ayiyah har sun kammala wankin sun fada wani aikin kuma sunayi suna hira shiyasa ma ko ganin fitowarshi basuyi ba, dakinsu ya nufa wanda yake cikin soron dake hanyar kofar gida yabude yashiga daga shi sai yayanshi Abba adakin amma yanzu abban baya nan yana can jami'ar Maiduguri wato unimaid yana karantar computer science dan haka sai shi kadai adakin yanzu, kayan jikinshi yarage yabar gajeren wando kadai bayan ya Kara kofar dakin, kan dundumemiyar katifar dake malale adakin yahau ya kwanta bai kai ga rufe idanuwansa ba yajiyo alamun karar shigar sako cikin wayarshi, akasalance ya mika hannu yadauko wayarshi kirar Galaxy S10,BILKISU shine password din kan wayar tashi nan yabude yasoma duba text din duk da baiyi saving number dinba yagane husna ce domin har ya haddace number dinta saboda yanda take damunsa arana sai ta kirashi akalla sau biyar ko fiyeda haka banda text massages kai idan takira ma taji shiru abune mai sauki yaganta ashagonsu ta biyo sawunshi yarasa gane kan wannan yarinyar gashi ta tsani ta ganshi da wata mace suna ko maganane alhalin kuma shi aikinsa na matane tunda dinkin mata shine sana'arshi. Sakon yabude yasoma karantawa kamar haka... _"Ya fahad yakake, ina fata lafiya kake, abincin yayi dadi?"_ murmushi yayi ya ajiye wayar bayan yasata a silent domin shi sai yanzu ma yatuna da wani abincin da ta kawo masa dazu saboda can yabaroshi ashago bararrajewa yayi saman katifarshi domin yin bacci duk da yasan ayiyah ta hanashi wannan dabi'ar ta baccin yamma amma babu yanda zaiyi ne sakamakon yagaji dayawa gashi ya jima bai samu isasshen bacci ba kullum yana kan keke yana dinki.
***
Murmushi tasaki ahankali wanda yayi sanadiyyar bayyanar fararen hakoranta sannan ya bayyanar da kyawawan beautiful point dinta wadanda ke kara kawata kyakkyawar fuskar da Allah yayi mata. Wayar dake makale a kunnenta take jujjuyawa cikeda annashuwa,

"Yes half soul, yanzu dai kabari sai nakoma gidan kawai sai naturo maka...."

Dan Jim tayi tana sauraron abinda yake fada bata kai ga bashi amsaba tamike daga kujerar datake zaune wacce ke rukunin kyawawan kujerun dake zagane cikin zungureren office din wanda ke dauke da kayan alatun more rayuwa banda na'urar sanyaya daki wacce ta cika dakin da sanyi wanda bazai cutar da jikin dan adam ba,
Domin cigaba da karantawa sai ku downloading.
Yadda ake downloading na littafin: ku tabbata kunyi register da shafinmu sanna kunyi login, idan bakuyi register a kasa zakuga maballai guda biyu daya an rubuta LOGIN dayan kuma an rubuta REGISTER sai ku taba su kuyi register, daga nan sai ku yi subscription koda na naira 1000 ne, domin sai kunyi subs dinann ne kadai zaku iya dauko littatafanmu.

Ya ya akeyin Subscription namu : Bayan kun yi Login ko register daga kasa zaku ga wani jan maballi (button) an rubuta SUBSCRIBE sai ku taba shi zai kaiku inda zaku zabi package wato tsarin subs na ku da mu. akwai na wata guda, watanni biyar da shekara guda. da zarar kun zaba zai kaiku inda zaku biya kudin, wanda daga nan sai ku cigaba da downloading kawai abunku

ABUN LURA : duk wani littafi da kuka gani a shafinnan kyauta ne, wannan tsari mun zo da shine don mu samu hanyar da zamu iya rike shafin muna managing na shi, izan ku kayi subs na mu tamkar DONATION ne ku ka yi mana, ku ka bamu kwarin guiwa don mu ciagaba da kawo muku sabbin littatafai, amma duk wanda ya ga bazai iya ba toh zai iya karanta littafin kyauta a cikin shafinnan namu batare da ya downloading ba, kawai ya yi kasa zai ga Koren maballi (button an rubuta) START READING sai ya taba zai kaishi inda zai karanta littafin.

Sannan duk wanda yaga kamn wannan process din zai bashi wahala kai tsaye zai iya min magana ta whatssApp +2348140419490, ya tura min kudin ni kuma zan dora mai subs din akan account na shi

NB: iya ta haka ne zaku iya karanta wannan littafi a shafinmu babu wata hanyar. DAN ALLAH KU DAINA MANA MAGANA AKAN MU TURA MUKU LITTAFI TA WHATSAPP, BAMA TURAWA HANYA GUDA MUKE TURA LITTATAFANMU SHINE WEBSITE NA MU https://taskarnovels.com.ng DUK MAI BUKATAR LITTAFINMU YA JE CAN YA KYAUTA NE, AMMA DOWNLOADING KUWA BA KYAUTA BANE SAI YAYI SUBSCRIPTION NA WEBSITE NAM
This is not the real Download Button


Read / Download KAMAR DA WASA

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .

START READING

OR

Login Register

This is not the real Download Button
Please Login or Register in order to submit comment

Releted Novels

Releted Album